← Book details Dabiar Zuciya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 42 OF 117

Sashe 42

Dabiar Zuciya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Eh shine saqona,ni dama can bason abun nake ba,wannan baqar yarinyar me kama......" Hannu umma ta daga mata,don ba zata lamunci cin fuska ba kuma,ga mari ga tsinka jaka?

"Ya isa,tunda dai kin isar da saqonki kuje,Allah ya bamu alkhairinsa" borin kunya lanti ta soma ita da 'yan rakiyarta,suka hau qananun maganganu,saboda basu zaci zuwan abun haka ba,suna qananun haibaice habaice da yarda maganganu suka fita a sashen,umma ta bisu da idanu.

Bisa mamakinta sai tajiyo muryar inna laure tana musu su gaida gida

"Mukusantanta mutum biyu" maganar ta dawo kan umma,su waye suka bada shaidar zurr kan abinda basuji ba basu gani ba?,basu da tabbaci?,mutum biyu makusantanta su waye kenan?,tambayar data yi mata nauyi aka,saita juya kamar kazar da qwai ya fashe mata a ciki ta nufi dakinsu kaltum inda take jiyo sautin kukanta.

Labule ta daga,tana tsaye daga vakin qofar dakin ta kalleta
"Kul.....kada na sake jin kukanki a kan namiji,Allahn daya baki nasuru shi zai sake baki wanda ya fishi da izinin ubangiji" da wannan ummanmu ta saki labulen ta wuce zuwa nata dakin,tana ta qoqarin tausar kanta da kanta,wannan babban abune da muninsa baici ta gayawa kowa shi ba,irin damuwar daya kamata isu isu su hadiyeta ne,ko kuma su tona rami su binneta.

Nan inda take ta sulale ta qoqarin tilastawa kanta ta hana kanta kuka kamar yadda ummanmu ta buqata,wani abu ya riqe mata wuya kamar zai tafi da numfashinta,da sauri da sauri tayi saurin kama

"Ya hayyu ya qayyumu,ya zuljalalu wal ikram" ta dinga maimaitawa a fili,saidai can qasa ta yadda idan ba'a kusa kake ba babu kallai ka iya jiyota.

Tsahon lokaci gidan ya dauki shuru,saika dauka babu umma bare kaltume a ciki,kowa yana kwance yana jinyar zuciyarsa,yayin da suka dinga jiyo karakainar inna laure da 'yan waqoqinta,tanata shige da fice daga qofar sashen zuwa nata sashen,wanda hakan duka baya wuce taji ya suke ciki ne,bayin Allahn kowanne na kwance yana tufka da warwara,salla ce kawai ta azahar ta tadasu,a haka la'asar ta riskesu.

La'asar din data zo musu da wani babban tashin hankalin na daban,bayan kaltum ta idar da sallar la'asar,tana zaune saman abun sallarta tana karanta sunayen Allah.

Kamar daga sama sukaji muryar mahaifinsu,babu sallama a bakinsa,sai faman qwalawa ummansu kira da yakeyi kamar tshon makahin da ya warke daga makanta,kira ne da kana jinsa zai kada hanjin cikinka,musamman idan kasan halayyarsa.

Kaltum dake zaue batasan sanda ta miqe tsaye ta dafe qirjinta ba,tun kafin taji abinda mahaifin nata zai furta ta tabbatar tashin hankali ne ya samesu,idan ka ganta a sannan sai kayi tsammani ana cewa kyat zata zura aguje.

Ko addu'ar da takeyi din bata samu damar kaiwa qarshe ba ta yanke tana ambatar

"Hasbunallahu wa ni'imal wakil" sannan ta fito daga dakin.

Yana tsaye tsakiyar tsakar gidan,tamkar xaici babu,fushi da masifa sun bayyana muraran akan fuskarsa da kuma duk wani motsi nasa,zirga zirga yake yakai gauro yakai mari amma masifa ta hanashi shiga daki ya cimmata har sai data fito ta kawo kanta

"Ina kattume?" Ya jefawa umman tambayar

"Tana dakinsu" ta amsa tana kafeshi da idanu,gabantana faduwa,saboda batasan da wacce yazo ba

"Ba shakka zuwaira....yadda auren kattume yayi rawa,har iyayen yaron nan sukazo suka amshi kudinsu haka naki auren yake rawa......ke zan baiwa wannan saqon,duk da na tabbatar tana jina.....iyayen nasuru sun zo har wajen sana'ata sun karbi kudin aurensu....to inason ki gayawa 'yarki.....ki gaya mata da babbar murya,ki jaddada mata cewa.....sanda tayi abun kunyarta ni ban sani ba,hakanan batayi shawara dani ba,to ki gaya mata,na bata wata daya kacal.....wata daya kacal ta fitar da mijin aure,ta kuma kawomin shi,idan kuma ba haka ba,billahillazi la'ilaha illa huwa saina bada ita sadaka ga duk meso,ga duk wanda Allah yayi rabonsa ya tsaga" daga haka ya juya fuuuu cike da fushi,iska tana cika babbar rigarsa tana qara kumbura surarsa ya fice waje abinsa.

A hankali umma ta dafa katangar dake kusa da ita,sannan ta koma ta zauna a hankali tana furta

"La haula wala quwwata illa billahil aliyyul azim" ta furta a hankali,tana son hana kanta kukan da taji yana son qwace mata,zuciyarta na kwabarta,idan ita tayi kuka ita kuma kaltum tace meye?,sai tayi fakare ko zataji sautin kukan kaltum din kamar yadda taso yi a daxun ta hanata,saidai shuruuuu....abinda ya dauki hankalinta kenan,ta miqe a hankali ta nufi dakin.

Koda ta yaye labulen wayam dakin babu kowa,sakin labulen tayi zulumi yana cikata,ina tayi?,tasan dai kafin shigowar mahaifin nasu tana dakin,kuma baya ya fita ita din tana zaune a nan,amma bataga fitarta ba.

Qwararawa kanta gwiwa tayi ta soma lalubenta daga bandaki zuwa qarama da babbar tsakar gidan gidan,saidai babu ita babu dalilinta,don haka ta koma ta zauna a hankali tana kiran sunan Allah,tare da addu'an ba wani abun na daban ke shirin faruwa ba bayaga wannan wanda suke ciki a yanzu.......

ZAFAFA KARO NA FARKO

SUNAYEN SU:

1_GUDU DA WAIWAYE NA BILLYN ABDULL

2_KAI MIN HALACCI
NA MISS XOXO

3_BURI DAYA
NA MAMUH GEE

4_DAURIN BOYE
NA SAFIYYAH HUGUMA

5_SAUYIN KADDARA
NA HAFSAT RANO

DUKA BIYAR DIN AKAN NERA 500

SAI ZAFAFA TAKU NA BIYU

1-DAURIN GORO
NA HAFSAT RANO

2-ALKAWARIN ALLAH NA
SAFIYYAH HUGUMA

3_QAUNAR MU
NA MAMH GEE

4_IGIYAR ZATO
NA MSS XOXO

5_WUTSIYAR RAKUMI
NA BILLYN ABDULL.

DUKA BIYAR DIN AKAN NERA 500.

SAI ZAFAFA TAKU NA 3,

1_MIN QALB
NA MAMUH GEE

2_SARAN BOYE
NA BILLYN ABDULL

3_KIBIYAR AJALI.
NA MISS XOXO

4_ABINDA KE CIKIN ZUCIYA
NA HAFSAT RANO

5_SIRADIN RAYUWAR BILKISU
NA SAFIYYAH HUGUMA

DUKA DOCUMENTS DIN BIYAR AKAN NERA DUBU DAYA DA DARI BIYAR (1,500)

SAI ZAFAFA TAKU NA HUDU.

1-ALKIBLA
NA SAFIYYAH HUGUMA

2_DALAAL
NA MISS XOXO

3_UBAYD MALEEK
NA MAMUH GEE

4_MABUDIN ZUCIYA
NA HAFSAT RANO

5_MAKAUNIYAR KADDARA
NA BILLYN ABDULL

DUKA LITTAFAN BIYAR AKAN NERA DUBU DAYA DA DARI BIYAR (1,500)

SAI ZAFAFA KARO NA BIYAR DA AKE A HALIN YANZU, (ON GOING PAID NOVS)

1-SO DA ZUCIYA
NA MSS XOXO

2-TAKUN SAAKA
NA BILLYN ABDULL

3_HALIN GIRMA NA HAFSAT RANO

4_DAB'IZAR ZUCIYA
NA SAFIYYAH HUGUMA

5-DEEN MALEEK
NA MAMUH GEE

DUKA BIYAR DIN NERA DUBU DAYA NE( 1K)IDAN AN KAMMALA SU KUMA 1500.

YADDA ZAKU BIYA NAKU KUDIN BOOKS DIN:

ACCOUNT NAME: MUSAA ABDULLAHI SAFIYYAH..

BANK NAME: KEYSTONE BANK

SAI A TURA SHEDAR BIYA ZUWA GA:

08184017082

IDAN KUMA KATIN MTN ZAKU TURA KO VTU SAI A TURA TA:

09134848107

D/Z
24
*_MANZAN ALLAH S A W YACE: Duk wanda yaci abinci,bayan ya gama cin abincin yace:ALHAMDULILLAHIL LAZI AD'AMANI HAAZA,WA RA ZAQANEHI MIN GHAIRI HAULIN MINNI WALA QUWWA Allah zai gafarta masa abinda ya gabata na zunubinsa"_*
_______________________________

*ZUWA GA MAKARANTA DABI'AR ZUCIYA❤‍🩹❤‍🩹*

*_kuyi haquri,muci gaba da bin komai a hankali,kuci gaba da haquri da duk abinda zaku ga ya afku,kar muyi gaggawa,kowanne labari da irin salonsa,hakanan sau tari idan kace zakabi salon da masu karatu keso tabbas zaka shiga sahun marubutan dake tafka shirme da rubuta labarin da bashi da ma'ana sam,babu kuma manufa,labarin daya gaza isar da saqonshi,wanda su kansu masu karatun basa gane hakan sai an gama littafi😁😁,saboda a sanda suka qagu aje wani bigire suna tsaka da shauqi ne,basa gane idan an musu hakan ba dai dai bane sai bayan kammaluwar littafi,muna godiya a gareku da bakwa gajiya da kasancewa da ZAFAFABIYAR,Allah yayi mana jagoranci cikin dukka lamuranmu🤲🏽🤲🏽🤲🏽,muje zuwa_*

Jefa qafarta kawai take ba tare da tana kallon gabanta ba,wani zafi qirjinta yake mata,kamar yadda taji idanuwanta na suya,saboda radadin hawayen dake taruwa cikinsu,wanda sukeson zubda kansu amma ta hanasu sauka.

Tunda ta samu nasarar fitowa daga cikin gidansu saboda sanda mahaifinta ke zazzagar masifa,cikin tashin hankali,saboda batason kunnuwanta su sake ji.mata wasu kalaman na daban bayan wadanda taji,A hankali ta yiwa kanta hanya zuwa bakin rafi,cikin ikon Allah kuma bata hadu da kowa a hanya ba,bare ya tsareta da tambaya ko ya kawo mata cikas.

Dab da ruwan ta zauna,yayin data rungume gwiwoyinta dukka a qirjinta,ta kuma zubawa ruwan idanu,babu abinda ke yawo a kanta sai kalaman mahaifinta,tana jin yadda suke yawo a saman kanta,kamar ana mata tsawa cikin kunnuwa.

Wani rauni ne ya mamaye zuciyarta,wanda ya sanyata ballewa da kuka,kukan da ya taho da nauyi da kuma qarfinsa,saboda yawa da girman damuwar da take ciki,kuka take sosai,irin kuka daka rasa matallafi ko wanda zaka dora kanka a kafadarsa da zummar samun lallashi ko kuma qwarim gwiwa.

A hankali yake tattaki a kewayen gurin,yana sake nazarin filin,tako ina filin yayi,kuma zai dace da gidan gona qwarai da gaske,yana buqatar wasu shawarwari daha wajen wani mutum babba mai hankali,kamar dai mahaifinsa,saidai shi yasan bashi da wannan gurbin ko kuma damar,saboda ya riga daya sani,abune mawuyaci mahaifin nasa ya fahimceshi,baisan meyasa ba kasafai yake fahimtar dumuwarsa ba?,baisan me yasa bai auna damuwarsa da ra'ayinsa da kuma abinda yakeso akan mizanin ababen da yake buqatar a kula shi domin su?,wani aikin sai uwa.......wani sashe na zuciyarsa ya gaya masa,maganar data sanyashi lumshe idanu yanajin wata faduwar gaba da wani suka a qirjinsa

"La'ilaha illallah" ya furta a hankali,baikai kuma ga hade labbansa ba sautin kukan ya shiga kunnuwansa.

Da sauri ya bude idanuwan nasa,sannan ya fara waige waige a nutse yana neman daga inda kukan ke fitowa.

Taku ya soma yi zuwa gaba kadan ganin bai samu nasarar ganin mai kukan ba,sai sautin kukan dake ci gaba da tashi,takun nasa da bai haura goma ba ya hangeta.

A durqushe take kamar me neman gafara,saidai kuma kuka take haiqan mai cike da nuna rauni da kuma gazawa.

Idanu sosai ya zuba mata,yana iya hangenta tar daga inda yake tsayen,hannayensa soke a aljihun wandonsa
"Kuka?" Ya fada cikin zuciyarsa kama me tambayar kansa da kansa,a ganin da ya mata tun karon farko,zarrar da yake ganin tana da ita,baiyi tsammanin ganinta cikin hali na kuka irin haka ba,saiya soma takawa a hankali yana nufarta.

Saidai tun baiyi nisa ba yaja ya tsaya,gami da takawa kansa da kansa burki,sam ba halinshi bane,ba kuma dabi'arsa bace shiga shirgin daba nashi bane,yana ganin kuma bai kamata ace a yanzu ya fara ba,kan mutanen da yake hangen baqin dabi'u wanda jahilci rashin ilimi da rashin wayewa ya haifar musu da su.

"Kattume.....kattume" kiran sunanta ya mamaye wajen,shi da ita dukka suka maida idanuwansu ga inda kiran ke fitowa.

Lantana ce afujajan,tana tafe kamar zata tashi sama,sai kaltum din ta zuba mata idanu tana kallonta da dan sauran hawaye da suka fuskarta kwalliya.
Chapter 42 · 0% Book details