Sashe 21
Dabiar Zuciya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"meye a ciki?"umman ta tambayeta
"nima ban buda ba,nasuru ne ya bani"rai umman tata ta bata
"amma ban hanaki karbar komai daga hannunsa ba?"barin abinda takeyi tayi ta langabe kanta
"amma ummanmu....saida nace bazan karba bafa,ya dage,yace idan baki amince ba zai dawo ya karbi abinsa"
"wai wanne nusurun?,ba wanda ya aiko aka tambayar masa neman aurenta ba?"
"eh shifa"umman ta fada ranta a hade,sai yakumbo indo ta janyo ledar ta buda,ta ciro kayan da suke ciki.
Atamfa leda ce guda biyu da aka yiwa dinkin riga da xani, yakumbo ta janyo ledar tana maidasu ciki tana cewa
"haba yaaya,ke kuwa ki barta mana ta amsa,ai ba'a hana amsar kyauta irin wannan,samarin yanzun ma da ba kowane mai kyautar ba,ki barta ta sanya abunta,tunda ba aikin banza ake ba,ansan da zamansa,akwai maganar manya a ciki.....ke kaltume,dauki abunki ki adana"sosa taji dadi cikin ranta,saita karba din sannan ta wuce dakinta,tana juyo uammansun tana cewa
"ni tsorona daya....gaba kada aje abun nan bai yuwu bafa azo ana zancan maida duk abinda ya bata"
"in sha Alla hakan ba zata faru ba,kuma don dai yau daya ta karba ma aiba wani abun bane"yakumbo indo ta bata amsa,saidai gefe daya na zuciyarta yana tuna mata maganganun lanti na dazu.
habiba ta samu wadda ta fito daga wanka bayan wanda aka yi mata,tana goge jikinta da turaren da umma altine ta bata,kayan ta zazzage tana nuna mata,ga tunaninta sai taga habiban ta kyabe baki
"wato yaya kin gwammace ki amshi kayan wani kina farinciki,amma ni na kada dake na raya ki dauki wasu daga cikin na lefe na kema ki dinka....amma daga ke har umma kowa yaqi,bansan ko wani abun nayi muku ba"murmushi kaltum tayi,tsakaninta da 'yan uwanta qauna ce sosai,suna son junansu, kowa kuma buri yake ya faranta ran dan uwansa,wannan shine kadai abun farinciki guda daya da suka tsira da shi
"habiba,kinfi kowa sanin yanayin qauyen nan,bawai minqi dauka bane,amma kinason mutuncinmu ya zube ne?,kaf kayan lefenki a qirge suke a idanun jama'a kin sani,ya sa ido sun riga da sun gama gane meye da meye a ciki,kiyi haquri karki bata ranki,wataranma fa ke zaki dinga dinkawa umma kayan sawar nan,idan ta nice kuma,ni dinma ai kinga ba wai jimawa nasuru zaiyi ba zai aiko da saka rana,daga nan nima zan samu nawa lefen ko?"da kalamai.na hikima masu kyau ta cirewa habiba haushin da taji nasu,sai suka shiga wata hirar ta daban.
*************
washegari ne za'ayi kamun amarya da yamma,don haka tunda safe da kaltum ta gama duk aikin da tasan ya kamata tayi,ta cimma umman tasu ita da yakumbo indo da kuma inna altine,tace zata gidansu suwaiba,don jiya bata ganta ba waje wankan amarya,tace mata saita dawo,sannan ta bata saqo gidan wata mata dake saida kabewa can wajen hayin makaranta,tace takai mata kudin,ta gobe ce da za'ayi amfani da ita,ta karba tayi mata sallama ta nufi qofa.
Har ta kusa fita umman ta kirata
"ki biya ta wajen umman asiya,naji dazu tana neman wanda zata aika wajajen,ki karba aiken ki hada gaba daya".
dan jim kaltum tayi,saboda har ga Allah ita batason hada sabga da inna laure,amma hakanan ta amsawa umman sannan ta fice.
Sau uku tana sallama amma shuru ba'a amsa ba,ga magana qasa qasa tana jiyowa daga dakin inna lauren,da alama akwai mutane a rumfar tata,don haka saita qara matsawa ko zasu jiyo sallamarta.
"ke wallahi zamanin nan kowa a waye yake,duk yarinyar da kika gani tana dan taba tabe taben nan fa,duk ƙarya cr suce basayi"
"kai asiya....nidai gaskiya kamar bazan iya ba,haka kawai duk abi a sassaka maka hannu lungu da saqonka"
"to ai saikije kita zama,yo Allah na tuba taɓawa dai da shiga ba,wallahi indai xaka cemin ungo sakar maka zanyi,to sai me tunda ba nunawa zaiyi a jikina ba?".
Kadan ya rage numfashin kaltum yayi qaura daga jikinta sabida hirar da taji tana tashi da muryar asiya da muryar kuma wata da batasan wacece ba,kamar ta juya sai kuma ta kasa,ta qarasa da hanzari tana bankade labulen dakin,sai sukayi ido hudu,ita da wata yarinya ce 'yar gidan malam qaura,sak sukayi da ganinta,ranta a matuqar bace,zuciyarta na tafarfasa ta dubi asiyan
"kiji tsoron Allah,wallahi kiji tsoron ranar da zaki mutu,kin gwammaci saida mutuncinki saboda wani abun duniya?me zasu baki?,zasu baki yanke talauci ne?kome zasu baki dama rabonki ne,da kinyi haquri kinbi ta hanya mai kyau zaki sami koma meye har inda kike din,kome xasu baki idan kudine zasu qare,idam sutura ce wataran tsumma ce,idan kuma abun ciye ciye na kwadayine masai xaki tsugunna ki kasayarwa dasu,zunubinki kuma yana rubuce nan cikin littafinki,yana jiran randa zaki tsaya gaban zatin Allah ki kare kanki.......
Cikin salon na me kama da nade tabarmar kunya asiyan ta miqe
"kinga malamar munafunci,wadda ta damun da sanya ido a rayuwar wasu,ashe haka kika koma yiwa mutane labe?"hannu kaltum ta daga mata cikin fushi
"kada ki sake bakinki ya sake furta wata mummunar kalma a kaina,idan ba haka ba zan miki hauka wallahi"ta fahimci ran kaltum din a bace yake sosai,ta kuma san halinta sarai,kuma bata manta bugun da tasha kwanaki a hannunta ba,don haka ta koma magana ciki ciki
"hauka ai kowa ma ya iyashi"
"banza shashasha wadda batasan ciwon kanta dana rayuwarta ba,ki guji randa duniya zata miki hukunci ta kuma baki darasi"daga haka ta juya tabar bangaren ba tare data karbi aiken ba,hasalima ta manta abinda ya kawota sashen.
Tana tafe ita daya tana tariyar komai,sunanta taji an kira,ta gane muryar waye,saita waiwaya tana qoqarin sakin fuskarta,nasuru ne,ta gaidashi kamar ko yaushe,ya tambayeta inda zata,tace gidansu suwaiba,sai yace suje ya taka mata,ba don taso ba tayi gaba ya bi bayanta,don ba dabi'arta bace jerawa da wani namiji,idan ka cire dan uwanta bilal.
Suna tafe cikin ransa yana yabawa da tsaftarta,uwa uba iya magana da kamewa,komai nata a nutse yake,ya dade da sanin cewa ta banbamta da sauran matan karkarar,abinda yaja hankalinsa sosai kenan a kanta,har yaji sha'awar mallakarta.
A qofar gidan ya tsaya yace zai jirata,ita kuma ta shige ciki.
A tsakar gidansu ta samesu ita da babarta,babar tana gyara waken awara,suwaiban na zaune daga gefe,sanye da rigar atamfa waddabta banbanta da zanin jikinta,hira suke a sake da babartata,saidai kaltum nayin sallama fara'ar fuskar tata ta janye sosai,ta koma kadaran kadaham,kamar ma dai bataji dadin ganinta ba.
Duk da hakan kaltum bata kawowa ranta komai ba,ta tsugunna ta gaida babar suwaiba din,sannan ta dubi suwaiban tana jifanta da harara,duk da fuskarta akwai wadatar murmushi
"aini wallahi nayi fushi,ace bikin habiba guda?,na zaci ko babu ni a bikin habiba sai inda qarfinki ya qare?"
"Bana jin dadi ne?"ta fada cikin halin ko in kula,tana kawar da fuskarta gefa guda
"Ayyah,Allah ya sawwaqe,ai da nazo ne da niyyar inyi miki tas,amma rashin lafiya aita kori komai,Allah ya sawwaqe,amma dai yau zaki zo ko?"
"wataqila"ta sake amsa mata cikin shakulaton bangaro,wanda a wannan karon mamakinua fara kama zuciyar kaltum,batasan me yasa suwaiban ta sauya ba,gaba daya ta canza kamar ba ita ba,amma ita kam iya tsahon canzawarta batasan wanne irin laifi tayi mata ba,bare ta nemi sulhu ko ta bata haquri ba,jikinta a sanyaye ta miqe
"shikena zan wuce...idan kinji dadin jikin naki ki daure ki leqo.....nabar nasuru a waje yana jirana"juyowa tayi daga inda ta maida fuskarta tana duban kaltum,wannan karon fuskarta tada washe ba kamar dazu ba
"au tare kuke?"
"eh,mun hadu hanya ne yace bari ya rakoni"miqewa tayi tana gyara daurin xaninta
"muje na rakaki.....babarmu aramin mayafinki"tace da babar tasu sanda take futowa daga sashen nasu, saita zare mayafin daga wuyanta ta miqa mata,ta daura saman kanta tabi bayan kaltum.
Bakinta a washe da fara'a ta qarasa gaban nasiru
"ranka ya dade,dama ana ganinku?,tunda ita qawar tawa bata da kirki taqi ta hadamu,ai aikai yaci ace kayi zumunci da babbar qawa"murmushi yayi sannan yace
"Alla ne dai bai nufa nazo ba,amma yanzu daya nufa gashi munzo tare da itama gaba daya",gaidashi ta soma yi ya amsa yana tambayarta wasu abubuwan da ba'a rasa tambayar mutum haduwar farko.
Koda suka gama kaltum tayi tunanin shikenan zasu wuce ne,saiga suwaiba ta zauna sosai tana ta sokowa nasiru hirararki,labarai kala kala,tun kaltum na tsaye har ta gaji ta nemi wajen zama.
Ganin har rana tana qara zafi,suwaiba kuma taqi barin hirar haka,saita dubi nasiru
"inajin zan wuce.....saboda ummanmu na jirana,daga nan akwai inda zanje,suwaiba saina ganki"ta fada tana miqewa, sai nasirun yayi zumbur
"a'ah bari muje,nima zan leqa gona zamuyi magana da baba" tuni kaltum din ta soma yin gaba abunta,sakato suwaiba tayi tana dubansu sanda yake mata sallama,tana tsaye a wajen har suka wuceta.
11
A mararrabar hanya suka rabu da nasirun,shi yabi hanyar da zata sadashi da gonakinsu,ita kuma tabi hanyar da zata kaita gidan matar da zata kaiwa kudin kabewa.
Tun daga nesa ta hangi sashen da tsohuwar makarantarsu take da al'umma a tsaitsaye,wasu manyan lafiyayyun kyawawan motoci guda uku fake a gefe,saita dauke kanta ta wuce zuwa gidan mari mai Saida kayan miya,ta shiga suka gama magana ta bata kudin ta fito.
Idanunta sake sauka yayi ta gefan makarantar,har yanzun mutane ne a tsaye a wajen suna zagaya makarantar,zuwa yanzu jama'ar dake cika wajen sun dadu,don an samu dadin 'yan kallo,wadanda kallon motocin dake wajen da kuma aikin da taga kamar ana danyi ya kawo,cikin masu kallon kuwa harda manya.
Baki ta tabe tana dannjan tsaki,mutane suna bata mamaki,komai qanqantar abu abun kallo ne a wajensu
"yaya"taji kamar muryar bilal tana qwalla mata kira,saita dakata da tafiyar sannan ya waiwaya.
Bilal dinne kuwa,ta zuba masa idanu tana jiran qarasowarshi,kamar ko yaushe fututu dashi,da wahala kaga bila din tsatsaf dashi,idan ba ranaku irin na juma'a ba ko kuma ranakun idi, saboda koda yaushe cikin aikin wahala da neman kudi yake.
"nima ban buda ba,nasuru ne ya bani"rai umman tata ta bata
"amma ban hanaki karbar komai daga hannunsa ba?"barin abinda takeyi tayi ta langabe kanta
"amma ummanmu....saida nace bazan karba bafa,ya dage,yace idan baki amince ba zai dawo ya karbi abinsa"
"wai wanne nusurun?,ba wanda ya aiko aka tambayar masa neman aurenta ba?"
"eh shifa"umman ta fada ranta a hade,sai yakumbo indo ta janyo ledar ta buda,ta ciro kayan da suke ciki.
Atamfa leda ce guda biyu da aka yiwa dinkin riga da xani, yakumbo ta janyo ledar tana maidasu ciki tana cewa
"haba yaaya,ke kuwa ki barta mana ta amsa,ai ba'a hana amsar kyauta irin wannan,samarin yanzun ma da ba kowane mai kyautar ba,ki barta ta sanya abunta,tunda ba aikin banza ake ba,ansan da zamansa,akwai maganar manya a ciki.....ke kaltume,dauki abunki ki adana"sosa taji dadi cikin ranta,saita karba din sannan ta wuce dakinta,tana juyo uammansun tana cewa
"ni tsorona daya....gaba kada aje abun nan bai yuwu bafa azo ana zancan maida duk abinda ya bata"
"in sha Alla hakan ba zata faru ba,kuma don dai yau daya ta karba ma aiba wani abun bane"yakumbo indo ta bata amsa,saidai gefe daya na zuciyarta yana tuna mata maganganun lanti na dazu.
habiba ta samu wadda ta fito daga wanka bayan wanda aka yi mata,tana goge jikinta da turaren da umma altine ta bata,kayan ta zazzage tana nuna mata,ga tunaninta sai taga habiban ta kyabe baki
"wato yaya kin gwammace ki amshi kayan wani kina farinciki,amma ni na kada dake na raya ki dauki wasu daga cikin na lefe na kema ki dinka....amma daga ke har umma kowa yaqi,bansan ko wani abun nayi muku ba"murmushi kaltum tayi,tsakaninta da 'yan uwanta qauna ce sosai,suna son junansu, kowa kuma buri yake ya faranta ran dan uwansa,wannan shine kadai abun farinciki guda daya da suka tsira da shi
"habiba,kinfi kowa sanin yanayin qauyen nan,bawai minqi dauka bane,amma kinason mutuncinmu ya zube ne?,kaf kayan lefenki a qirge suke a idanun jama'a kin sani,ya sa ido sun riga da sun gama gane meye da meye a ciki,kiyi haquri karki bata ranki,wataranma fa ke zaki dinga dinkawa umma kayan sawar nan,idan ta nice kuma,ni dinma ai kinga ba wai jimawa nasuru zaiyi ba zai aiko da saka rana,daga nan nima zan samu nawa lefen ko?"da kalamai.na hikima masu kyau ta cirewa habiba haushin da taji nasu,sai suka shiga wata hirar ta daban.
*************
washegari ne za'ayi kamun amarya da yamma,don haka tunda safe da kaltum ta gama duk aikin da tasan ya kamata tayi,ta cimma umman tasu ita da yakumbo indo da kuma inna altine,tace zata gidansu suwaiba,don jiya bata ganta ba waje wankan amarya,tace mata saita dawo,sannan ta bata saqo gidan wata mata dake saida kabewa can wajen hayin makaranta,tace takai mata kudin,ta gobe ce da za'ayi amfani da ita,ta karba tayi mata sallama ta nufi qofa.
Har ta kusa fita umman ta kirata
"ki biya ta wajen umman asiya,naji dazu tana neman wanda zata aika wajajen,ki karba aiken ki hada gaba daya".
dan jim kaltum tayi,saboda har ga Allah ita batason hada sabga da inna laure,amma hakanan ta amsawa umman sannan ta fice.
Sau uku tana sallama amma shuru ba'a amsa ba,ga magana qasa qasa tana jiyowa daga dakin inna lauren,da alama akwai mutane a rumfar tata,don haka saita qara matsawa ko zasu jiyo sallamarta.
"ke wallahi zamanin nan kowa a waye yake,duk yarinyar da kika gani tana dan taba tabe taben nan fa,duk ƙarya cr suce basayi"
"kai asiya....nidai gaskiya kamar bazan iya ba,haka kawai duk abi a sassaka maka hannu lungu da saqonka"
"to ai saikije kita zama,yo Allah na tuba taɓawa dai da shiga ba,wallahi indai xaka cemin ungo sakar maka zanyi,to sai me tunda ba nunawa zaiyi a jikina ba?".
Kadan ya rage numfashin kaltum yayi qaura daga jikinta sabida hirar da taji tana tashi da muryar asiya da muryar kuma wata da batasan wacece ba,kamar ta juya sai kuma ta kasa,ta qarasa da hanzari tana bankade labulen dakin,sai sukayi ido hudu,ita da wata yarinya ce 'yar gidan malam qaura,sak sukayi da ganinta,ranta a matuqar bace,zuciyarta na tafarfasa ta dubi asiyan
"kiji tsoron Allah,wallahi kiji tsoron ranar da zaki mutu,kin gwammaci saida mutuncinki saboda wani abun duniya?me zasu baki?,zasu baki yanke talauci ne?kome zasu baki dama rabonki ne,da kinyi haquri kinbi ta hanya mai kyau zaki sami koma meye har inda kike din,kome xasu baki idan kudine zasu qare,idam sutura ce wataran tsumma ce,idan kuma abun ciye ciye na kwadayine masai xaki tsugunna ki kasayarwa dasu,zunubinki kuma yana rubuce nan cikin littafinki,yana jiran randa zaki tsaya gaban zatin Allah ki kare kanki.......
Cikin salon na me kama da nade tabarmar kunya asiyan ta miqe
"kinga malamar munafunci,wadda ta damun da sanya ido a rayuwar wasu,ashe haka kika koma yiwa mutane labe?"hannu kaltum ta daga mata cikin fushi
"kada ki sake bakinki ya sake furta wata mummunar kalma a kaina,idan ba haka ba zan miki hauka wallahi"ta fahimci ran kaltum din a bace yake sosai,ta kuma san halinta sarai,kuma bata manta bugun da tasha kwanaki a hannunta ba,don haka ta koma magana ciki ciki
"hauka ai kowa ma ya iyashi"
"banza shashasha wadda batasan ciwon kanta dana rayuwarta ba,ki guji randa duniya zata miki hukunci ta kuma baki darasi"daga haka ta juya tabar bangaren ba tare data karbi aiken ba,hasalima ta manta abinda ya kawota sashen.
Tana tafe ita daya tana tariyar komai,sunanta taji an kira,ta gane muryar waye,saita waiwaya tana qoqarin sakin fuskarta,nasuru ne,ta gaidashi kamar ko yaushe,ya tambayeta inda zata,tace gidansu suwaiba,sai yace suje ya taka mata,ba don taso ba tayi gaba ya bi bayanta,don ba dabi'arta bace jerawa da wani namiji,idan ka cire dan uwanta bilal.
Suna tafe cikin ransa yana yabawa da tsaftarta,uwa uba iya magana da kamewa,komai nata a nutse yake,ya dade da sanin cewa ta banbamta da sauran matan karkarar,abinda yaja hankalinsa sosai kenan a kanta,har yaji sha'awar mallakarta.
A qofar gidan ya tsaya yace zai jirata,ita kuma ta shige ciki.
A tsakar gidansu ta samesu ita da babarta,babar tana gyara waken awara,suwaiban na zaune daga gefe,sanye da rigar atamfa waddabta banbanta da zanin jikinta,hira suke a sake da babartata,saidai kaltum nayin sallama fara'ar fuskar tata ta janye sosai,ta koma kadaran kadaham,kamar ma dai bataji dadin ganinta ba.
Duk da hakan kaltum bata kawowa ranta komai ba,ta tsugunna ta gaida babar suwaiba din,sannan ta dubi suwaiban tana jifanta da harara,duk da fuskarta akwai wadatar murmushi
"aini wallahi nayi fushi,ace bikin habiba guda?,na zaci ko babu ni a bikin habiba sai inda qarfinki ya qare?"
"Bana jin dadi ne?"ta fada cikin halin ko in kula,tana kawar da fuskarta gefa guda
"Ayyah,Allah ya sawwaqe,ai da nazo ne da niyyar inyi miki tas,amma rashin lafiya aita kori komai,Allah ya sawwaqe,amma dai yau zaki zo ko?"
"wataqila"ta sake amsa mata cikin shakulaton bangaro,wanda a wannan karon mamakinua fara kama zuciyar kaltum,batasan me yasa suwaiban ta sauya ba,gaba daya ta canza kamar ba ita ba,amma ita kam iya tsahon canzawarta batasan wanne irin laifi tayi mata ba,bare ta nemi sulhu ko ta bata haquri ba,jikinta a sanyaye ta miqe
"shikena zan wuce...idan kinji dadin jikin naki ki daure ki leqo.....nabar nasuru a waje yana jirana"juyowa tayi daga inda ta maida fuskarta tana duban kaltum,wannan karon fuskarta tada washe ba kamar dazu ba
"au tare kuke?"
"eh,mun hadu hanya ne yace bari ya rakoni"miqewa tayi tana gyara daurin xaninta
"muje na rakaki.....babarmu aramin mayafinki"tace da babar tasu sanda take futowa daga sashen nasu, saita zare mayafin daga wuyanta ta miqa mata,ta daura saman kanta tabi bayan kaltum.
Bakinta a washe da fara'a ta qarasa gaban nasiru
"ranka ya dade,dama ana ganinku?,tunda ita qawar tawa bata da kirki taqi ta hadamu,ai aikai yaci ace kayi zumunci da babbar qawa"murmushi yayi sannan yace
"Alla ne dai bai nufa nazo ba,amma yanzu daya nufa gashi munzo tare da itama gaba daya",gaidashi ta soma yi ya amsa yana tambayarta wasu abubuwan da ba'a rasa tambayar mutum haduwar farko.
Koda suka gama kaltum tayi tunanin shikenan zasu wuce ne,saiga suwaiba ta zauna sosai tana ta sokowa nasiru hirararki,labarai kala kala,tun kaltum na tsaye har ta gaji ta nemi wajen zama.
Ganin har rana tana qara zafi,suwaiba kuma taqi barin hirar haka,saita dubi nasiru
"inajin zan wuce.....saboda ummanmu na jirana,daga nan akwai inda zanje,suwaiba saina ganki"ta fada tana miqewa, sai nasirun yayi zumbur
"a'ah bari muje,nima zan leqa gona zamuyi magana da baba" tuni kaltum din ta soma yin gaba abunta,sakato suwaiba tayi tana dubansu sanda yake mata sallama,tana tsaye a wajen har suka wuceta.
11
A mararrabar hanya suka rabu da nasirun,shi yabi hanyar da zata sadashi da gonakinsu,ita kuma tabi hanyar da zata kaita gidan matar da zata kaiwa kudin kabewa.
Tun daga nesa ta hangi sashen da tsohuwar makarantarsu take da al'umma a tsaitsaye,wasu manyan lafiyayyun kyawawan motoci guda uku fake a gefe,saita dauke kanta ta wuce zuwa gidan mari mai Saida kayan miya,ta shiga suka gama magana ta bata kudin ta fito.
Idanunta sake sauka yayi ta gefan makarantar,har yanzun mutane ne a tsaye a wajen suna zagaya makarantar,zuwa yanzu jama'ar dake cika wajen sun dadu,don an samu dadin 'yan kallo,wadanda kallon motocin dake wajen da kuma aikin da taga kamar ana danyi ya kawo,cikin masu kallon kuwa harda manya.
Baki ta tabe tana dannjan tsaki,mutane suna bata mamaki,komai qanqantar abu abun kallo ne a wajensu
"yaya"taji kamar muryar bilal tana qwalla mata kira,saita dakata da tafiyar sannan ya waiwaya.
Bilal dinne kuwa,ta zuba masa idanu tana jiran qarasowarshi,kamar ko yaushe fututu dashi,da wahala kaga bila din tsatsaf dashi,idan ba ranaku irin na juma'a ba ko kuma ranakun idi, saboda koda yaushe cikin aikin wahala da neman kudi yake.