← Book details Dabiar Zuciya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 107 OF 117

Sashe 107

Dabiar Zuciya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Idanunta ta mayar ta lumshe itama,saboda yadda gaba daya kowacce gaba ta jikinta lakarta ke mutuwa,ta dora hannuwanta saman nashi hannun tana son zamesu daga mararta,saboda yadda ya tsayar qara gudun zuciyarta

"Karki cire......baki qara wani period din ba?" Ya tambayeta muryarsa qasan maqoshi,kamar wanda ke mata rada,fitar furucin ya qara rudata,saita girgixa masa kai da sauri alamun a'ah

"But....me yasa baki gaya min ba sanda ya dawo?,ko baki shirya karbata a matsayin mijinki ba?" Gaba daya ya sake rudata dajin abinda ya fada din,miji?,ita a yanzu har isarta takai yayi matar aure da ita?,kamar yasan me take tunani,saiya saketa,yaja baya kadan,sannan ya juyo da ita tana fuskantarshi,ya zuba mata idanu da birkitattun idanuwansa da suka sauya launu,tun tun tuntuni......baisan wane baiwa ne da ita haka ba,da yakan samu kansa cikin burkicewa duk sanda jikkunansu xasu hadu waje guda,ko don bai saba hakan ba sai a kanta?.

Dukka tafukan hannayensa biyu ya saka a kuncinta na dama dana hagu,ya dago fuskarta sosai ta yadda zai iya kallon qwayar idanunta

"Bansan ke alheri bace a rayuwata sai a yanzu,ban kuma sani ba.....ko zai iya karbar wannan samir din a matsayin mijinki?" Idanunta ta runtse,tambayar tayi mata tsauri sosai,yana kasheta ne da wannan tsaiwar tasa cikin jikinta ba tare daya sani ba,muryarsa kadai matuqar dab da ita take hautsina mata tunani take,tasa ta manta abinda takeyi

"Bansan wanne irin tukuici kike da buqata daga wajena ba"

"Ka kaini gida,inason naga ummata" ta samu kanta da fada,hawaye kuma ya biyo bayan maganar tata.

Kai ya fara girgizawa
"No....no, stop it please" ya fada yana sanya yatsansa yana dauke mata hawayen saman fuskar tata,ido ya tsura mata sosai yana kallon zanen fuskarta,komai yana zaune bisa muhallinsa bisa tsari da halitta me kyau,wannan shine kallo mafi kurkusa daya taba yiwa kaltum din,dan madaidaicin bakinta idanunsa yakai kai,ya zarto da hannunsa wajen zuwa daidai hancinta,ya dora yatsansa guda biyu ya soma zagaye tattausan lips dinta.

Da hanzari ta qwace fuskarta ta hanyar ja da baya saboda jin wani shock da tayi kamar an jata,tun daga yatsun qafarta har zuwa qwaqwalwarta,sai ya harde hannayensa yana fidda murmushi yadda ta juya baya ta kasa hada ido dashi,idanunta na nuna zallar kunyarsa data kamata.

Qarasawa yayi inda flask din yake ya dauko ya biyota dashi,ya ajiye kusa da ita yana cewa

"Zan dauki lokaci me tsaho ina koya miki yadda zaki rayu dani,babu abinda kika sani dangane dani illa kamannin fuskata......a yau na shiryawa shaidawa dukkan wanda ya kamata cewa KE MATATA CE" Haka kawai taji gabanta yayi mugun bugawa,tsoro ya kamata,saita daga fararen idaunta ta kalleshi kafin ta janyesu,ta koma qoqarin sauke tukunyar kunu.

Duk sanda ta kalleshi da fararen idanun nan nata yakanji wani abu ya tsarga masa,ba tun yau ba,ba tun wannan lokacin ba....yakejin hakan,kusan tun ganin farko da yayi mata,ya manta rabon da yaga mace mai fararen idanu kar haka irin nata,sai ya dauka wannan banbancin ne.

"Bakya sona ne?,ko ban miki ba?" Ya fada yana ware hannayensa gaba daya bayan ya zagayo gabanta ya tsaya,a sace ta kalleshi ta dauke kai,cikin ranta tana fadin,komai kyau isa mulki dukiya ko nasabar mace,bata isa ta kalli samir yace baiyi mata ba.....indai ba irin mazan aljanna takeso a kawo mata duniya ba

"Kalleni sosai....." Ya fada yana sake matsota,sai tayi saurin ja da baya,sannan ta take ta fice daga kitchen din da gaggawa,don tabbas ta bari yaci gaba da hada jikinsa da nata.....batasan iya yadda adadin sonsa zaikai cikin zuciyarta ba.

******Qarfe bakwai na dare ne,cikin shigar laffaya mai azabar kyau butter colour ta nannade jikinta,kamar yadda take kusan rabin shigarta kenan a shekarun baya tun duniya tana kwance.

Samir ne ya sake knocking qofar,wanda cikim jagulewar rai da zuciya dama yayo rakiyar,don kawai bazai iya saba umarnin momman tasa ba.

Karo na kusan biyar ya sake bugawa kafin ya iya jiyo maganar daddyn can qasa

"Waye?"

"Samir ne....momma keson magana da kai" daga nan inda yake tsaye,yana iya jiyo qarar saukowarsa da qarfi,da alama amsar da samir din ya bashi tayi masa ba zata,ba'a kuma cika minti daya ba qofar ta bude,karo na farko tun bayan satittikan da suka shude daya rufe da kansa.

Kallo daya samir yayi masa tausayinsa ya sauko masa,gaba daya ya hada wata qasumba a fuskarsa da kansa,wadda ta cika da furfura,ramar da yayi ta bayyana har saman fuskarsa,wasu qashi dukka sun bayyanar masa.

Idanunsa nakan momma din a sanda ya bude qofar,sannan ya matsa yana basu damar shigowa.

Samir yana iya ganin yadda ya saka wani qyalle yana kadewa momma kujerar tare da gaya mata ta zauna,saidai a maimakon hakan saita koma can wani waje nesa kadan ta jingina,fuskarta kuma babu alamun annuri ko fara'a ta fara magana

"Na riga dana hada kayana,inason komawa qasata cikin dangina,nazo ne domin karbar shaidar sakina.....saboda al'adarmu saikin nuna ta koda wani auren naki na gaba zai taso,ina fatan ba zamu tsawaita magana ko bata lokaci ba" sosai tashin hankali ya bayyana kan daddyn,sai samir ya kauda kansa,saboda tausayin daddyn nasa,ya dade da yi.masa uzuri,saboda yasan dukkan abinda ya faru MAKIRCI DA KISSA ne sukayi aikinsu,mummunar kissa abar qyamata.

Muryar daddyn a dakushe ya fara magana
"Raihana....kiyimin rai don Allah......karki ce zaki tafi ki barni,kunyar ki da kunyar yadda zan tunkareki ya sanya na kulle kaina tsahon wadan nan kwanakin,saboda bani da wani abu da zan gaya miki wanda zan wanke kaina,nasan cewa na rusa dukkan wata yarda da aminci dake tsakaninmu"

"Kayi haquri na roqeka nima,komai da ka yimin na yafe maka albarkacin danka,amma a yanzu ina buqatar shaida ta,saboda inason na koma qasata cikin ahalina na qarasa rayuwata"

"Har yanzu da aurena a kanki raihana......saboda bayan na rubuta saki guda daya......munyi rigima sosai da hafsa a sannan duk da ba'a ganki ba bakya nan,ganin yadda ran hafsa ya baci sai nace na maidaki,kuma daga ranar har kawo yau a yanzun ban janye ba......saidai in sake jadda miki cewa ke matata ce,hafsa itace shaidata"

Wani nannauyan numfashi samir ya sauke,yanajin wani sanyi yana ratsa zuciyarsa,saidai cikin lokaci kadan momma ta kafe kan batasan wannan ba,don haka samir ya zare jikinsa daga dakin,bai kuma tsaya ako ina ba sai dakin hajiya qarama.

Baiyi qasa a gwiwa ba ya gaya mata abinda ke faruwa a sashen daddyn,daquwa ta watsa masa
"Don qaniyarka me yasa zaka rakatan?,me yasa baka zo ka sameni ba tukunna" kanshi ya shafa,yadda yaga hajiya qaraman ta miqe cikin gaggawa yasan komai zai dai daita,mayafinta taja kuwa ta fice,shi kuma ya koma ya zauna cikin kujerun dake dakin yana sauraron dawowarta.

Kusa awa guda hajiya qaraman ta sake dawowa,da alama ansha fama ansha gwagwarmaya,saidai yanayin fuskarta kawai ya tabbatar masa komai ya dai daita

"Kaje yaya yanason ganinka" tsam ya miqe yabi bayanta har zuwa sashen daddyn.

Kallo daya yayi musu dariya taso kubce masa,fuskar daddyn wasai ,saidai momma da har yanzu a cunkushe take,fuskarta na nuna fushi,amma kuma idan kayi mata kallon tsanaki zakasan cewa fushi ne akeyi irin na masoya.

Gaban daddyn ya qarasa ya duqa
"Gani daddy" gyara zamansa yayi sosai yana kallonsa

"Samir....inason in sake neman afuwarku ne gaba daya kan dukkan wani abu da ya faru"

"Daddy.....kasa a ranka nidai a wajena.....kamar komai bai faru ba......saidai.....inason dukkaninku kuyimin afuwa,saboda na aikata wani babban kuskure watanni masu yawa da suka shude,kuma na kasa gayawa kowa a cikinku" dif sukayi,kowa yana dubansa,kowa kuma da abinda zucuyarsa take ayyana masa,aka rasa me magana,sai daddy

"Na yadda dakai samir,kome zaka aikata ina da kyakkyawan fatan da zaton bazai zama mai munin da zai cutar da al'umma addini ko mutuncinka ba,kada kaji komai,sanar dani" zama yayi sosai,cikin nutsuwa ya shiga shaida musu dukkan abinda ya faru,tun daga lokacin da ya fara sanin bilal,rayuwar kaltum har zuwa yadda auren ya dauru.

"Alhamdulillah" hajiya qarama ta furta tare da wata ajiyar zuciya mai qarfi

"Mun godewa Allah da ya sanya iya haka ce ta faru.....hankalina har ya kwanta" to ga momma da daddy ma kusan abinda ya faru kenan,saboda ya sanya kowa a cikin taraddadi,saidai amsar daddy ta sake kwantar masa da hankali

"koda kaltum bata zauna damu ba....koda ita ke da buqatar ta aureka tabbas zamu aura mata kai.....barema tun zuwanta.....babu wanda bai yaba da dabi'u da halayenta ba"

"Banajin a duniya akwai yarinyar da zanso banda kai bayan ita" amsar da ta fito daga bakin momma kenan,sai ya runtse idanu yana tasbihi ga ubangijinsa,lallai duk wanda ya nufaci ubangiji wajen aikata wani aiki.....to babu makawa zai shige masa gaba,zai share masa hawayensa,hakanan duk wanda yaji tsoron Allah xai samar masa mafita......zai kuma azurtashi ta inda baya zato.

🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥

*_DA ZAFINSU_*

*_A TSARE SUKE_*

*_SUN TANADESU_*

*_CIKIN SALO NA HIKIMA DA BAN SHA'AWA_*

*_ƘAWATATTU kuma ZAFAFAN DOCUMENTS HAR GUDA 25 na ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR da aka tanadar muku dasu_*

*_tun daga batch 01 har batch 05,duka bisa farashin rangwame_*

*_MAZA TUNTUBESU TA WADANNAN LAMBOBIN WAYAR KAMAR HAKA_*

_WADANDA SUKESON TURAWA TA ACCOUNT SU YIWA WANNAN NUMBER WAYAR MAGANA_

08184017082

_MASU TURA KATIN WAYA KO VTU KUMA_
09134848107

*_TARON GAMAYYAR ZAFAFAN MARUBUTA.....MASU ZAFAFAN ALQALUMMA_*

62

*10:48*

Yana tsaye gaba mudubi yana sharce ruwan kansa,yana kuma kallon kansa a madubin,sosai fuskarsa ta wadatu da murmushi,musamman idan ya tuna abubuwan da suka faru a wunin yau din,gaba daya dukkan wata matsala tasa ta warware cikin ikon Allah,abinda ya rage masa a yanzu kawai shine yadda zaiyi da jawahir ya badda mummunan labari a kanta,don ko shari'ar gidan masu tabin hankali a dazu da safe aka qareta,kyauro da sauran mutum uku da suka taimaka masa wajen ajiyar momma na wadan nan shekarun,an yanke musu hukuncin daurin rai da rai.

Sake murmusawa yayi da ya tuna yadda hajiya qarama ta tubure haiqan da gaskiya aka baro momma sashen daddy,duk da kuwa itama tuburewar da taso yi,saidai rigimar hafsatun tata tafi tata girma.

A yau komai ya kawo qarshe,ya tabbata kaltum ta zama tasa,wadanda ya kamata su sani sun riga da sun sani,sun karba su lamunce masa,iya wannan kadai idan ya tuna yana sanyashi nishadi.

Da fari tausayin kaltum ya fara,bai sani ba so ashe yana farawa daga tausayi,ya fara sonta ne ba tare da yasan sonta yake ba,ya aza cewa tausayinta da tausayin rayuwar da suke ciki yake yi,da kuma sabo da sukayi da da uwanta bilal.
Chapter 107 · 0% Book details