Sashe 27
Dabiar Zuciya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Wannan ledar fa?"ya fada cikin salo na raha kamar yadda yanayinsa yake,yana amsar ledar daga hannun mai aikin saboda son ganin qwaqwaf,yana bude ledar ya bude idanu
"Hajjaju.....wannan lafiyayyen kilishin fa?" Fuska ta tsuke sosai,bata ko waiwaya ta dubeshi ba tace
"Daga inda ka aikeni,su sukace na kawo maka babana" ya fahimci kamar adan hasale take,saiya saki murmushi
"Allah ya huci zuciyar hajjwju" ya sanya hannu yana gutsirar kilishin ya jefa a bakinsa sannan ya bata ledar ta wuce shima ya qaraso inda suke zaune.
"The giant ya saraki" affan ya fada cikin salo na barkwanci,wanda ya sanya samir murmusawa,saiya miqa masa hannu,shima affan ya bashi hannun suka gaisa,sa'annan ya soma laluben wajen zama yana fadin
"Barka da warhaka yaya"
"Yauwa affan.....ya karatu?"
"Hmmmm....gashinan alhmdlh,yanata gasamu"ya amsa masa yana shafa qeyarsa zuwa wuyansa
"Ni yau ka ganni yaya ko cikakken abinci wallahi ban samu na zauna naci ba,yanzunma takaddun kawai na ajjiye na shigo nan" gyara zamanshi samir yayi sosai yana fadin
"Saika matso muci tare"ya bude murfin kwanim abincin yana ajiyeshi a gabansa,hakan ya baiwa affan damae matsowa yana cewa
"Kai amma fa na gode yaya daka bani damar cin abinci dakai" maganar affan ta sanya murmushi ya subucewa samir,idan ya biyewa affan abincinma bazai bari suci sosai ba,ya cika surutu kamar jawahir,shi yasa tasu tazo daya,wani lokaci har yakan tsokanesu da cewa zai musu baiko shida ita,zasu dace sosai,saboda yanayin surutunsu daya,saidai suyita dariya shi da ita,saboda su sam basa ganin surutun nasu da yake fada din,kawai dai qilan sabodashi bai bawa hira muhimmanci mai yawa cikin rayuwa da lokuttansa ba,yana selecting lokutan hira da abubuwan da sukafi muhimmanci ya ambata ne.
D/Z
14
*Zafafa biyar na kudi ne,ki siya ki karanta naki cikin aminci ba tare da kin shiga haqqin kowa ba*
Ku tuntubi wadan nan numbers din
08184017082
Ko kuma
09134848107
Suna cin abincin suna hira,affan din yana bawa samir labarin makaranta,yanayin karatun nasu irin wahalarshi da sauransu,lokaci lokaci hajiya qarama na sanya musu baki,har suka gama,affan ya kira jummai ta debe kwanukan,saiya miqe tsaye yana miqa ya dubi hajiya qarama
"Hajjaju zanje nadan kwanta,baccin jiya da banyi ba duk ya cikamin idanu"
"Ala kiyaye"ta amsa shi,saiya waiwaya ya dubi samir daketa faman goge hannu duk da cewa ya wanke,da yake shi mutum ne da ba kasafai yake cin abinci da cokali ba
"Yaa saraki.....zanje nadan watsa ruwa,idan na sameka to,idan ban sameka ba a gaidamin twin sister na" dan qaramin murmushi ya saki,kana yace
"zata ji" saboda yasan wa yake,da haka yabar musu falon su biyu kadai.
Shuru ne ya ratsa na wadansu sakanni sannan hajiya qarama ta gyara qafarta dake miqe daya kan daya
"Muhammadu" ta kirashi da sunan da ba kasafai ake kiransa dashi ba,samir ko saraki yaso ya shafe na ainihin,saiya daga kai ya dubeta yana amsawa
"Ina waccar maganar da uwarka data taso da ita?,ina fatan dai ta mutu kamar yadda ka gayamin?" Kai ya jinjina a nutse yana duban hajiyan,saita gyada kan nata itama
"Kun kyautawa kanku......abinda yasa nayi kiranka shine,kaga daga ni har mahaifinka kowanne so yake ka fitar da macen aure,bama mu kadai ba,duk wani masoyinka,hatta da yadikko dake azare,kayi qoqari ka zabi yarinya cikin dangi ko wajen dangi,bana so luma bana qaunar na sake jin labarin wai jidda ce zata zaba maka ko ta zabar maka wadda zaka aura,saboda halan bazai haifar mana da daa mai ido ba a tsakanina da ita,idan kuma baka maida kai ka zabi mace ba,to tabbas ni zan zabar maka,don suna nan sun kua guda goma wadanda nasa abincika minsu,kuma kowacce ta isa macen aure" murmushi ne zai subuce masa,amma sai ya sanya tafi hannunsa saman bakinsa,kamar mai shafa kwantaccen gashin daya zagaye habar tasa zuwa qasan hancinsa,a hankali yana duban hajiya har takai qarshe,cikin girmamawa yace
"In sha Allah ba za'a kai haka ba,nan kusa zan kawo miki ita ta gaidaki" wanda shi kansa yasan ya fada ne kawai,saboda a yanzun koda bindiga aka ritsashi ba zaice ga wadda yaji ta kwanta masa ko yake soyayya da ita ba,duk da tarin masoyan da yake dasu,wasu sun bayyana,wasu suna dakon kayansu,hakanan kullum wayewar garin Allah baya rasa samun saqonni daga wajen mata kala daban daban,wasunsu ma baisan su waye ba.
******************
Karfe tara da ashirin na safiya yana tsaye cikin falon,wanda babu kowa,daga shi sai mai aiki dake hada masa breakfast da xaici ya fita,kasancewar yau jawahir bata nan,ta fita tun takwas tana da lactures,haka ma daddy tun bakwai ya fita,suna da wata tafiya shida mai girma gwamna,najwa na ciki tana bacci,mommy ma tana nata dakin,saidai ta leqo tace a hada masa abun karyawar,zata shiga wanka ta fito.
Sai data gama hadawa sannan tadan russuna sanda yake danne danne a wayarsa,yayi kyau cikin wani yadin maza da aka yiwa dinkin zamani,wanda ya dace sosai da jikinsa,fuskarsa kawai zaka kalla kasan yan tafiya da zamani,komai nasa dai dai a muhallinsa
"An gama yallabai" dauke idanunsa yayi daga saman wayar,ya dubeta
"Yauwa......sannu" kai ya gyada taja baya ta soma barin wajen,sai taji yace
"Zo mana" ba tare data jinkirta ba ta dawo inda ta tsaya daxun,yana hada tea din yana motsashi da cokali saboda ya rage zafi ya dubeta
"Me ya faru su baba mai gadi basa samun abinci kullum sau uku a rana?" Shuru tayi kanta a qas,tana nazarin abinda zata fada,bai katse ta ba amma yaci gaba da sauraren amsarta ba tare da ya sake cewa komai ba,sai daya kurba tea din sannan ya sake maimaita tambayar,dai dai sannan mommy ke fitowa,taji tambayar da yake yi din,don haka tace da ita
"Jeki zuwaira" ta fada tana jan kujera daya ta zauna tana dubanshi.
Second kusan uku sannan tace dashi
"Bansan ya zan musu fada su gane ba,nasha gaya musu babban abuj kunya ne ace mun kasa ciyar da ma'aikatanmu.....amma in sha Allah daga yau hakan ba zata sake faruwa va,zanwa tufkar hanci" kansa ya jinjina sannan ya aje cup din hannunsa
"Bai kamata mu dinga qoshi suna kwana da yunwa ba,alhalin mu sujewa aiki,sun sadaukar da lafiyarsu da qarfinsu duk saboda mu.....ki musu magana mommy a gyara please,idan mangyaran bai yuwu ba ni da kaina zanyi maganin abun,i sure daddy bai san da haka ba" kai ta daga tana dubansa
"Tunda nace an gama daga yau, trust me an gama din son" ta fadi da murmushi kan fuskarta,shima saiya saki murmushin.
Sama sama ya qara abincin kana ya miqe,saboda kiran da umar da murtala sukayi masa kan sun iso,ya dubi mummyn
"Zamu wuce mummy......ni suke jira"idanunta saman fuskarsa ta jinjina kai
"Allah ya tsare,sai kun dawo"
"Koda daddy zaiyi qorafin nan......"
"Baka da damuwa da wannan,jeka abinka" ta tareshi tun kafin yakai qarshen maganar,hakan ya masa dadi,tako wanne bangare ya tsaya tana tare dashi,tana kuma bashi goyon baya dari bisa dari akan duk abinda ya yanke,don haka cikin karsashi da jin dadi ya juya ya nufi qofar fita,yayin data rakashi da idanuwanta harya gama ficewar.
Nannauyar ajiyar zuciya ta saki,sannan ta maida idanunta gurbin daya tashi yanzu a kai na wasu sakanni,sannan ta janye idanun nata,taja sauran kayan breakfast din daya gama ta fara hadawa,don itama tana son ta fita taje ta dawo kafin azahar.
**********Daga gefe daya na tsakar gidan nasu dake a share fes take zaune,saman kujera 'yar tsuguno,tana yiwa wata matashiya da bata wuce sa'arta ba kitso,da qyar take kama kan,don babu yadda zata yine,da lashakka ma bazata mata kitson ba,duba da yadda kanta yayi datti,har wani toka toka yakeyi,saidai a wannan karon ta tayar da neman kudi sosai,kitso take babu ji babu gani,dalilim ciwon qafar mahaifiyarta da a yanzu ya fara daga mata hankali,saboda kullum qara gaba yakeyi,burinta kawai a hada kudin magani da zata kai asibiti,ko yaya ta samu relief na ciwon dake jin jikinta.
Bilal ne daga gefe zaune yake daura qwabja qwabjan takalmansa da yake fita aiki kullum dasu,surutu yaketa mata saidai hankalinta bai wajen gaba daya,nata can tana lissafa adadin abinda ta tara ne,duk da kitson data kama babu dare babu rana tanayi.
"Inama zan samu wanda zai dinga sayen zanena" ta fada cikin zuciyarta,saboda yawan zanan data tara da kayan da bilal ya kawo mata,saidai duk wanda tayi ma maganar dariya yakeyi cikin karkarar,yana ganin zallar haukarta,waye zai wani sayi zane?,yayi me dashi?,mutum daya ne take ganin kamar zai mata hanya ko yasan inda za'a siya din,wani abokin nasuru ne da yace mata ya taba zuwa kano,ya wuce ya wani waje yaga an maqala zanw cikin glass ana siyarwa,tunda ya bata labarin bata manta ba,saita yanke ta tanbayeshi ko za'a dace,saidai kash nasurun yace mata baya nan,amma tana sanya ran dawowarshi cikin satin.
Sai daya gama daura takalman sannan ya miqe yana kakkabe jikinsa
"Na tafi yaya,inajin ma yau zan dan dawo da wuri,zan samowa umma wani abun da zata ci,don yau za'a fara biyanmu kudin aikinmu inji oganmu,mun kusa gama rushe ko ina da ina,aikin ginin kawai za'a fara"
"Toh Allah yasa"
"Amin" ya amsa yana yin gaba da dan hanzari,yana tafe yana dan buga duwatsun da yaci karo dasu,yana ji da takalmin sosai,ji yake babu kamarshi.
Tana gamawa wadda takewa kitson kitso ta kakkabe jikinta,ta wanke hannunta sosai sannan ta sake tattara wajen,gidan habiba takeson zuwa,don tun shekaran jiya take aike kan tazo din amma.bata je ba,don Allah ya sani tun asali ita dama ba maison yawo bace,koda cikin qawayensu duk wadda akayi biki da wahala ka ganta ta koma gidan a kusa.
Sai data leqa dakin umman ta tabbatar bacci takeyi,sannan ta shiga nata dakin,ta dauki hijabinta ta maqala sannan ta fito tana dan jan qofar kara da aka sakayawa sashen nasu sannan tayi gaba.
Tana shirin fita asiya na shigowa da uniform jikinta,duk me hankalin daya kalleta yasa ba daga makaranta ta dawo ba,don fes take a nutse,babu wasu alamu dake nuna gajiya da tarin yunwa irin tadan makaranta tattare da ita,kallon banza data saba yiwa kaltum shi ta watsa mata,ita kam bata ma isheta duba ba,don haka kota gefan da take bata kalla ba tayi gaba abinta,abu dayane data sani shine,ba zata dauki ranini ba,sannan a dake asiyan ba zata dauki komai a jikinta ba.
"Hajjaju.....wannan lafiyayyen kilishin fa?" Fuska ta tsuke sosai,bata ko waiwaya ta dubeshi ba tace
"Daga inda ka aikeni,su sukace na kawo maka babana" ya fahimci kamar adan hasale take,saiya saki murmushi
"Allah ya huci zuciyar hajjwju" ya sanya hannu yana gutsirar kilishin ya jefa a bakinsa sannan ya bata ledar ta wuce shima ya qaraso inda suke zaune.
"The giant ya saraki" affan ya fada cikin salo na barkwanci,wanda ya sanya samir murmusawa,saiya miqa masa hannu,shima affan ya bashi hannun suka gaisa,sa'annan ya soma laluben wajen zama yana fadin
"Barka da warhaka yaya"
"Yauwa affan.....ya karatu?"
"Hmmmm....gashinan alhmdlh,yanata gasamu"ya amsa masa yana shafa qeyarsa zuwa wuyansa
"Ni yau ka ganni yaya ko cikakken abinci wallahi ban samu na zauna naci ba,yanzunma takaddun kawai na ajjiye na shigo nan" gyara zamanshi samir yayi sosai yana fadin
"Saika matso muci tare"ya bude murfin kwanim abincin yana ajiyeshi a gabansa,hakan ya baiwa affan damae matsowa yana cewa
"Kai amma fa na gode yaya daka bani damar cin abinci dakai" maganar affan ta sanya murmushi ya subucewa samir,idan ya biyewa affan abincinma bazai bari suci sosai ba,ya cika surutu kamar jawahir,shi yasa tasu tazo daya,wani lokaci har yakan tsokanesu da cewa zai musu baiko shida ita,zasu dace sosai,saboda yanayin surutunsu daya,saidai suyita dariya shi da ita,saboda su sam basa ganin surutun nasu da yake fada din,kawai dai qilan sabodashi bai bawa hira muhimmanci mai yawa cikin rayuwa da lokuttansa ba,yana selecting lokutan hira da abubuwan da sukafi muhimmanci ya ambata ne.
D/Z
14
*Zafafa biyar na kudi ne,ki siya ki karanta naki cikin aminci ba tare da kin shiga haqqin kowa ba*
Ku tuntubi wadan nan numbers din
08184017082
Ko kuma
09134848107
Suna cin abincin suna hira,affan din yana bawa samir labarin makaranta,yanayin karatun nasu irin wahalarshi da sauransu,lokaci lokaci hajiya qarama na sanya musu baki,har suka gama,affan ya kira jummai ta debe kwanukan,saiya miqe tsaye yana miqa ya dubi hajiya qarama
"Hajjaju zanje nadan kwanta,baccin jiya da banyi ba duk ya cikamin idanu"
"Ala kiyaye"ta amsa shi,saiya waiwaya ya dubi samir daketa faman goge hannu duk da cewa ya wanke,da yake shi mutum ne da ba kasafai yake cin abinci da cokali ba
"Yaa saraki.....zanje nadan watsa ruwa,idan na sameka to,idan ban sameka ba a gaidamin twin sister na" dan qaramin murmushi ya saki,kana yace
"zata ji" saboda yasan wa yake,da haka yabar musu falon su biyu kadai.
Shuru ne ya ratsa na wadansu sakanni sannan hajiya qarama ta gyara qafarta dake miqe daya kan daya
"Muhammadu" ta kirashi da sunan da ba kasafai ake kiransa dashi ba,samir ko saraki yaso ya shafe na ainihin,saiya daga kai ya dubeta yana amsawa
"Ina waccar maganar da uwarka data taso da ita?,ina fatan dai ta mutu kamar yadda ka gayamin?" Kai ya jinjina a nutse yana duban hajiyan,saita gyada kan nata itama
"Kun kyautawa kanku......abinda yasa nayi kiranka shine,kaga daga ni har mahaifinka kowanne so yake ka fitar da macen aure,bama mu kadai ba,duk wani masoyinka,hatta da yadikko dake azare,kayi qoqari ka zabi yarinya cikin dangi ko wajen dangi,bana so luma bana qaunar na sake jin labarin wai jidda ce zata zaba maka ko ta zabar maka wadda zaka aura,saboda halan bazai haifar mana da daa mai ido ba a tsakanina da ita,idan kuma baka maida kai ka zabi mace ba,to tabbas ni zan zabar maka,don suna nan sun kua guda goma wadanda nasa abincika minsu,kuma kowacce ta isa macen aure" murmushi ne zai subuce masa,amma sai ya sanya tafi hannunsa saman bakinsa,kamar mai shafa kwantaccen gashin daya zagaye habar tasa zuwa qasan hancinsa,a hankali yana duban hajiya har takai qarshe,cikin girmamawa yace
"In sha Allah ba za'a kai haka ba,nan kusa zan kawo miki ita ta gaidaki" wanda shi kansa yasan ya fada ne kawai,saboda a yanzun koda bindiga aka ritsashi ba zaice ga wadda yaji ta kwanta masa ko yake soyayya da ita ba,duk da tarin masoyan da yake dasu,wasu sun bayyana,wasu suna dakon kayansu,hakanan kullum wayewar garin Allah baya rasa samun saqonni daga wajen mata kala daban daban,wasunsu ma baisan su waye ba.
******************
Karfe tara da ashirin na safiya yana tsaye cikin falon,wanda babu kowa,daga shi sai mai aiki dake hada masa breakfast da xaici ya fita,kasancewar yau jawahir bata nan,ta fita tun takwas tana da lactures,haka ma daddy tun bakwai ya fita,suna da wata tafiya shida mai girma gwamna,najwa na ciki tana bacci,mommy ma tana nata dakin,saidai ta leqo tace a hada masa abun karyawar,zata shiga wanka ta fito.
Sai data gama hadawa sannan tadan russuna sanda yake danne danne a wayarsa,yayi kyau cikin wani yadin maza da aka yiwa dinkin zamani,wanda ya dace sosai da jikinsa,fuskarsa kawai zaka kalla kasan yan tafiya da zamani,komai nasa dai dai a muhallinsa
"An gama yallabai" dauke idanunsa yayi daga saman wayar,ya dubeta
"Yauwa......sannu" kai ya gyada taja baya ta soma barin wajen,sai taji yace
"Zo mana" ba tare data jinkirta ba ta dawo inda ta tsaya daxun,yana hada tea din yana motsashi da cokali saboda ya rage zafi ya dubeta
"Me ya faru su baba mai gadi basa samun abinci kullum sau uku a rana?" Shuru tayi kanta a qas,tana nazarin abinda zata fada,bai katse ta ba amma yaci gaba da sauraren amsarta ba tare da ya sake cewa komai ba,sai daya kurba tea din sannan ya sake maimaita tambayar,dai dai sannan mommy ke fitowa,taji tambayar da yake yi din,don haka tace da ita
"Jeki zuwaira" ta fada tana jan kujera daya ta zauna tana dubanshi.
Second kusan uku sannan tace dashi
"Bansan ya zan musu fada su gane ba,nasha gaya musu babban abuj kunya ne ace mun kasa ciyar da ma'aikatanmu.....amma in sha Allah daga yau hakan ba zata sake faruwa va,zanwa tufkar hanci" kansa ya jinjina sannan ya aje cup din hannunsa
"Bai kamata mu dinga qoshi suna kwana da yunwa ba,alhalin mu sujewa aiki,sun sadaukar da lafiyarsu da qarfinsu duk saboda mu.....ki musu magana mommy a gyara please,idan mangyaran bai yuwu ba ni da kaina zanyi maganin abun,i sure daddy bai san da haka ba" kai ta daga tana dubansa
"Tunda nace an gama daga yau, trust me an gama din son" ta fadi da murmushi kan fuskarta,shima saiya saki murmushin.
Sama sama ya qara abincin kana ya miqe,saboda kiran da umar da murtala sukayi masa kan sun iso,ya dubi mummyn
"Zamu wuce mummy......ni suke jira"idanunta saman fuskarsa ta jinjina kai
"Allah ya tsare,sai kun dawo"
"Koda daddy zaiyi qorafin nan......"
"Baka da damuwa da wannan,jeka abinka" ta tareshi tun kafin yakai qarshen maganar,hakan ya masa dadi,tako wanne bangare ya tsaya tana tare dashi,tana kuma bashi goyon baya dari bisa dari akan duk abinda ya yanke,don haka cikin karsashi da jin dadi ya juya ya nufi qofar fita,yayin data rakashi da idanuwanta harya gama ficewar.
Nannauyar ajiyar zuciya ta saki,sannan ta maida idanunta gurbin daya tashi yanzu a kai na wasu sakanni,sannan ta janye idanun nata,taja sauran kayan breakfast din daya gama ta fara hadawa,don itama tana son ta fita taje ta dawo kafin azahar.
**********Daga gefe daya na tsakar gidan nasu dake a share fes take zaune,saman kujera 'yar tsuguno,tana yiwa wata matashiya da bata wuce sa'arta ba kitso,da qyar take kama kan,don babu yadda zata yine,da lashakka ma bazata mata kitson ba,duba da yadda kanta yayi datti,har wani toka toka yakeyi,saidai a wannan karon ta tayar da neman kudi sosai,kitso take babu ji babu gani,dalilim ciwon qafar mahaifiyarta da a yanzu ya fara daga mata hankali,saboda kullum qara gaba yakeyi,burinta kawai a hada kudin magani da zata kai asibiti,ko yaya ta samu relief na ciwon dake jin jikinta.
Bilal ne daga gefe zaune yake daura qwabja qwabjan takalmansa da yake fita aiki kullum dasu,surutu yaketa mata saidai hankalinta bai wajen gaba daya,nata can tana lissafa adadin abinda ta tara ne,duk da kitson data kama babu dare babu rana tanayi.
"Inama zan samu wanda zai dinga sayen zanena" ta fada cikin zuciyarta,saboda yawan zanan data tara da kayan da bilal ya kawo mata,saidai duk wanda tayi ma maganar dariya yakeyi cikin karkarar,yana ganin zallar haukarta,waye zai wani sayi zane?,yayi me dashi?,mutum daya ne take ganin kamar zai mata hanya ko yasan inda za'a siya din,wani abokin nasuru ne da yace mata ya taba zuwa kano,ya wuce ya wani waje yaga an maqala zanw cikin glass ana siyarwa,tunda ya bata labarin bata manta ba,saita yanke ta tanbayeshi ko za'a dace,saidai kash nasurun yace mata baya nan,amma tana sanya ran dawowarshi cikin satin.
Sai daya gama daura takalman sannan ya miqe yana kakkabe jikinsa
"Na tafi yaya,inajin ma yau zan dan dawo da wuri,zan samowa umma wani abun da zata ci,don yau za'a fara biyanmu kudin aikinmu inji oganmu,mun kusa gama rushe ko ina da ina,aikin ginin kawai za'a fara"
"Toh Allah yasa"
"Amin" ya amsa yana yin gaba da dan hanzari,yana tafe yana dan buga duwatsun da yaci karo dasu,yana ji da takalmin sosai,ji yake babu kamarshi.
Tana gamawa wadda takewa kitson kitso ta kakkabe jikinta,ta wanke hannunta sosai sannan ta sake tattara wajen,gidan habiba takeson zuwa,don tun shekaran jiya take aike kan tazo din amma.bata je ba,don Allah ya sani tun asali ita dama ba maison yawo bace,koda cikin qawayensu duk wadda akayi biki da wahala ka ganta ta koma gidan a kusa.
Sai data leqa dakin umman ta tabbatar bacci takeyi,sannan ta shiga nata dakin,ta dauki hijabinta ta maqala sannan ta fito tana dan jan qofar kara da aka sakayawa sashen nasu sannan tayi gaba.
Tana shirin fita asiya na shigowa da uniform jikinta,duk me hankalin daya kalleta yasa ba daga makaranta ta dawo ba,don fes take a nutse,babu wasu alamu dake nuna gajiya da tarin yunwa irin tadan makaranta tattare da ita,kallon banza data saba yiwa kaltum shi ta watsa mata,ita kam bata ma isheta duba ba,don haka kota gefan da take bata kalla ba tayi gaba abinta,abu dayane data sani shine,ba zata dauki ranini ba,sannan a dake asiyan ba zata dauki komai a jikinta ba.