Sashe 55
Dabiar Zuciya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Yayi bacci kaltum,babban baccin da babu wanda yasan ranar tashinsa sai Allah,yayi kwanciyar da zai huta,irin hutun da muka gaza samar masa" kasa fahimtar maganar ummansu tayi kwata kwata,kamar ma ba hausa take mata ba,muryarta na rawa tace
"Kamar yaya ummanmu?"
"Allah ya karbi ran bilal,ina fatan kuma ya huta kenan har aljanna" batasan ledar hannunta ta fadi ba,batasan ta zame ta fadi ba ita kanta,qafarta ta bugu da qarfen gadon,abunda ta iya sani shine wani kuka data saki wanda ya amsa kuwwa a dukka ilahirin lungu da saqo na dakin,kukan da yaja hankalin dukka mutanen dakin,har ma da wadanda basusan bilal din ya rasu ba,ya kuma ja hankalin su samir dake bakin gadon dan malam salahu suna dubashi,ya waiwaya yana tuna inda yasan wannan muryar da irin kukan,sai idanunsa suka hange masa ita.
"Ya salam" ya fada yana jin qirjinsa yana bugawa,tabbas wani ne ya mutu,juyawa yayi a hankali zuwa inda take ummansu da wasu mata na qoqarin dagata tare da bata baki,bai tsaya ba sai daya isa gaban gadon,ya saka hannu ya bude rufin,saiga bilal,the hard work boy title din da yake masa.
Sakin abun rufar yayi yayi baya yana fadin
"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" yana jin wani abu yana zaga kwanyarsa,bai taba tunani ko kawowa ransa haka ba,duka duka yaushe sukaje dubashi,ya daga kai ya sake kallon gawar,ko a haka cikinsa ya nuna kumburin da yayi harta saman mayafin da aka rufeshi
32
D/Z
*wannan littafin na kudine,sharinga dinsa zuwa wasu gurare tamkar zalunci ne garemu,kiyiwa girman Allah ki barshi a inda kika ganshi,idan kin da buqatar karantawa ki biya naki ta wadannan numbers din dake qasa*
08184017082
Ko kuma
09134848107
32
Shi ya dinga kai kawo tsakanin biyan bill din kudin bilal dana dan malam salahu,duk da cewa shi bilal nashi kudin ma ba wani masu yawa bane,saboda bai jima ba,duk motsin da zaiyi fuskar yaron yake hanga,wani tausayi yana ratsashi.
Tare da amiru suke komai,duk inda yasa qafa yana biye dashi,saidai bakinsa fal yake da tambayoyi ga sarakin game da su umman.
Bai sake shiga mamaki ba sai daya ji samir din yana bada umarnin sanya gawar bilal cikin motarsu,ya kalleshi,duk da baice komai ba,umman da kaltum daketa rusa kuka cikin wani yanayi mai matuqar ban tausayi suna daga baya,shi da samir din suna gidan gaba,malam salahu na musu addu'ar sauka qalau da samu rahama ga mamacin,samir din ya tada motar suka fice daga asibitin.
Kukanta kawai ke tashi cikin motar,ta kasa tsaida kukan ko dai dai da minti daya
"Don Allah bilal ka tashi,ka tashi kace wasa kake mana" shine abinda take fada lokaci bayan lokaci tana girgizashi,.
Sannu a hankali kukan yaci gaba da ratsa kunnuwansu,harda samir da sitiyarin motar ke hannunsa,lokaci bayan lokaci yakan ce
"Hasbunallahu wa ni'imal wakil" a sarari,daga bisani saiya sanya casset na karatun qur'anu,qira'ar khusari,wanda hakan ya rage kaifin kukan kaltum.
Suna isa qauyen labarin rasuwar bilal ya ratsa ko ina,kafin kace meye wannan jama'a sun fara cika gidan,habiba na daya daga cikin wadanda suka fara zuwa,sun shigo tana riqe a hannun surukarta tana gunjin kuka,tana faduwa tana tashi,tana kiran bilal din tare da fatan abunda ke faruwan ya zama mafarki,xuwanta ya sake sanyawa kaltume dake ta son bawa kanta juriya sa qwarin gwiwa saita sare,suka taru suka dinga kuka baji ba gani,sai inna da bata jima da isowa ba,tana doje daga bakin qofa tahau musu fada,fadan da badan cikin yanayi yake ba duk sai sun tsaya kallonta,saboda mamakin dama innar tasan Allah?.
Cikin abinda bai gaza awa biyu ba aka gama shirya bilal,a sannan kaltum ta sake aro juriya,ta taka tana rangaji kamar zata fadi,saboda yadda takejin iska tana yawo da ita ta fita harabar gidansun,inda abokan bilal suka cika,harda wadanda kaltum ma bata sansu ba,ba 'yan unguwar bane.
Abokinsa na kusa kusa ta kira
"Ka tambaya cikin abokanku,ko akwai wanda yake bin bilal bashi?" Kai ya kada cikin alhini
"A iya sanina babu,saidai ma wadanda bilal yakebi....amma bari na tambaya" juyawa yayi ya koma cikinsu,amsoshin dake fita daga bakunansu duka irin wadda ya bata ne daxun kafin yakai ga tambayarsu
Hawaye taji yana sauko mata,haka rayuwarsa ta qare gaba daya,ya nema da guminsa da qarfinsa,yaci iya cinsa,ya baiwa 'yan uwansa,ya bada bashi ga abokansa,koda zasu cinye bashin ba zasu biyashi ba.
Rudewa gidan yayi da koke koke,yadda gidansu ke cike damqam da mata ashe a waje abun yafi haka,mamaki ya kusan kama kowa na jama'ar da bilal ya tara,idan bakasan waye ya rasu ba,zakayi tunanin cewa wani babban mutum ne ya rasu,saboda yawan al'ummar daya samu,suna ji suna gani bayan an gama sallar ama daukeshi akayi gaba dashi,ya barsu da kuka,ya barsu da kewa,ya barsu cikin gidan da ake yunqurin korarsa,sai gashi tun ba'a koreshi ba,shi ya tattara nasa ya nasa ya tafi inda ba dawo,inda kowanne me rai zaije.
Cikin dare a ranar ta kasa bacci,ganin komai take kamar wani wasan kwaikwayo,kamar wani wasa ne bilal din yake musu,kamar yaje ne zai dawo musu,ta dinga juyi tana kuka,yayin da gefe guda kuma abinda ya faru a wunin duka ya dinga dawo mata,yadda su ya munzali da muzammilu suka dinga rawar qafa wajen hada gawar bilal,sune kawo turare sune kawo sabulu da likkafani,idan ka gani kai ba zakace sune sila ko muzajar mutuwarsa ba,Allah ya sani,ba zata iya gogewa ba,ba zata iya hana kanta kallonsu a matsayin wadanda sukayi sila ko sanadiyyar tafiyar bilalunsu zuwa qiyama ba.
Sai kuma ta hango fuskar mahaifinsu,yadda yaye tsugunne gaban gawar bilal,gawar da sai da aka gama hada bilal din sannan ubangiji ya bashi ikon qarasowa,don bai samu labari da wuri ba,saboda a ranar yayi sammakon zuwa wani waje.
Ganin juyin bana qare bane saita miqe don ta dauro alwala,sai sukaci karo da ummanta,da alama itama baccin ya gagareta ne,batasan sanda wani sabon kukan ya qwace mata ba
"Da kika ce abar habiba ta zauna,da haka zaku zauna kenan ke da ita kuyita yi masa kuka?,kukan da bashi da wani amfani ko rana a wajensa?" Abinda umman tace kenan tana cika buta da ruwa don daura alwala.
To cikin kwanakin zaman makokin abubuwa da yawa sun faru,sunga jama'a masu yawa,wadanda basu tsmmatarwa bilal din ba,jama'a masu kamala da mutunci,wadanda zaka zaci ba zasu zo gun jana'izar yaro ba,yaron ma mata gata irin bilal,amma sai gasu,kowa yazo kuma saiya koka kan rasuwar yaron,saboda yadda kusan kowa ke amfanar sa,bashi da qyuya ko san jiki ko kadan,baisan rashin kunya ko fitsara ba ko kadan,girmama kowa yake,hakanan bashi da abokin fada.
Kudadensa da mutane suka kakkarba bashi masu tsoron Allah suka dinga kawowa ummanmu da kaltum sunyi mamaki,saboda wani ma basuyi tunanin bashi zai shiga tsakaninsu ba,yawan kudin da suka riqe sai yanzu suke biya,inda a zamanin da yake raye suka biyashin,babu shakka da sun isa ya kafa qaramar sana'a,da bai mutu cikin wahalar daya mutu ba,da bai mutu yana neman kudin da za'a masa aiki ba.
Yawan mutanen da suke zuwa gaisuwa ba shakka banda taimakon Allah,da kuma taimakon kawu ado da gwaggo indo da basusan da abinda zasu ci dasu ba,saidai a taimakon wadan nan bayin Allahn aka dinga dafa abinci ana ci.
Inna kuwa rabonta da gidan tun randa aka dauki gawar bilal,bayan an dawo daga binneshi,kawu ado yasa aka sauke buhun shinkafa babba dana wake,saita hau cewa a diba mata,wannan ai ya yiwa zuwaira da ahalinta yawa,ta dauko babbar qatuwar leda baqa ta buda bakinta.
Ran wasu daga cikin 'yan uwa ya baci,amma saboda kowa yana shakkarta,saboda masifarta da bala'i yasa aka rasa mai tanka mata,sai wasu daga cikin jikokinta da suka fara qananun maganganu.
Ganin da gaske take yasa yakumbo indo ta murje idanunta tayi mata magana
"Inna,wannan kayan abincinfa ba dafawa akace a dinga yi ana ciyar da masu xaman makoki,kuma ko a hakanma yayi kadan,saina aika an sake siyo wani buhun" mita ta hau yi,har sai da taga ran yakumbo indon ya baci,kasancewarta 'yar gaban goshinta da batason tayi fushi,tilas ta haqura,daga bisani ma ana sallame sallar la'asar tace zata koma gida,ba wanda ya hanata ko ya tambayeta ba'asi,hasalima ma hakan yafi ma kowa kwanciyar hankali.
********Sanyi gami da lallausan qamshi ne kawai ke fita daga qawatacce kuma madaidaicin falon,wanda zai burge duk wani mutum ko da ina matsayinsa da arziqinsa yakai.
Zaratan samarin ne su biyu kacal cikin falon,wato samir da Aamiru,samir din na sanye da wata riga short sleeve shirts da wando da iyakacinsa qaurinsa,dukkansu ruwan toka da adon baqi,wanda suka zauna jikinsa suka fitar da duk wata qira tasa tan murdewar jiki da murjewa, system ne a gabansa,yana duba wasu dokuna da akayi masa tallansu tun daga wata qasar,irin dokunansu ne na can,kasancewarsa mutum mai son dawakai,wanda a yanzu haka yana da guda uku nashi na qashin kansa,hakan duk sanda za'a gabatar da wasan tseren dokuna na polo to yana daga gaba gaba wajen zuwa,ba'a nigeria kawai ba,wani lokaci qafa da qafa yake fita wata qasar idan za'ayi,musamman idan akwai wanda yakeso a cikin wandanda xasuyi gasar tseren dawakan,wannan dabi'a tasa na daya daga cikin dalilan da yasa sunan saraki ya bishi.
Amiru kuwa na kwance saman doguwar sofa yana amsa waya,yanayin yadda yake wayar ya isa ya gaya maka cewa wayace ta masoya,don kuwa iya murmushin da yake fita saman fuskarsa kadai zai gaya maka hira ce ta musamman.
Kowa abinda yake gabansa yakeyi,kuma kowa najin dadin sabgarsa,har zuwa wani lokaci da aamirun ya gama wayar,sai ya miqe ya zauna kana ya zuro qafafunsa qasa,idanunsa akan samir,wanda ya gama zaben dawakan da yakeso cikin wadanda suka turo masa video dinsu
"Yauwa,ina jinka,kace mene?" Inji amiru yana miqa hannu,ya janyo drink din da jawahir ta shigo musu dashi,musamman saboda yayan nata.
Idanunsa masu kwarjini da kuma girma,wanda hasken system ya qarawa kyau ya daga ya watsawa aamiru yana murza tafun hannayensa waje daya,saboda sanyin ac din daya dan fara damunsa,duba da yanayin sanyi sanyi da aka fara a gari
"Kaga malam,yi ta kanka kawai,zama zanyi nata yi maka bayani?,ko dan aikinka ne ni da zan zauna inta maimaita maka zance bayan ka gama gabatar da naka uzurin?" Dariya Aamir ya qyalqyale da ita yana jjiye cup din hannunsa
"Kamar yaya ummanmu?"
"Allah ya karbi ran bilal,ina fatan kuma ya huta kenan har aljanna" batasan ledar hannunta ta fadi ba,batasan ta zame ta fadi ba ita kanta,qafarta ta bugu da qarfen gadon,abunda ta iya sani shine wani kuka data saki wanda ya amsa kuwwa a dukka ilahirin lungu da saqo na dakin,kukan da yaja hankalin dukka mutanen dakin,har ma da wadanda basusan bilal din ya rasu ba,ya kuma ja hankalin su samir dake bakin gadon dan malam salahu suna dubashi,ya waiwaya yana tuna inda yasan wannan muryar da irin kukan,sai idanunsa suka hange masa ita.
"Ya salam" ya fada yana jin qirjinsa yana bugawa,tabbas wani ne ya mutu,juyawa yayi a hankali zuwa inda take ummansu da wasu mata na qoqarin dagata tare da bata baki,bai tsaya ba sai daya isa gaban gadon,ya saka hannu ya bude rufin,saiga bilal,the hard work boy title din da yake masa.
Sakin abun rufar yayi yayi baya yana fadin
"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" yana jin wani abu yana zaga kwanyarsa,bai taba tunani ko kawowa ransa haka ba,duka duka yaushe sukaje dubashi,ya daga kai ya sake kallon gawar,ko a haka cikinsa ya nuna kumburin da yayi harta saman mayafin da aka rufeshi
32
D/Z
*wannan littafin na kudine,sharinga dinsa zuwa wasu gurare tamkar zalunci ne garemu,kiyiwa girman Allah ki barshi a inda kika ganshi,idan kin da buqatar karantawa ki biya naki ta wadannan numbers din dake qasa*
08184017082
Ko kuma
09134848107
32
Shi ya dinga kai kawo tsakanin biyan bill din kudin bilal dana dan malam salahu,duk da cewa shi bilal nashi kudin ma ba wani masu yawa bane,saboda bai jima ba,duk motsin da zaiyi fuskar yaron yake hanga,wani tausayi yana ratsashi.
Tare da amiru suke komai,duk inda yasa qafa yana biye dashi,saidai bakinsa fal yake da tambayoyi ga sarakin game da su umman.
Bai sake shiga mamaki ba sai daya ji samir din yana bada umarnin sanya gawar bilal cikin motarsu,ya kalleshi,duk da baice komai ba,umman da kaltum daketa rusa kuka cikin wani yanayi mai matuqar ban tausayi suna daga baya,shi da samir din suna gidan gaba,malam salahu na musu addu'ar sauka qalau da samu rahama ga mamacin,samir din ya tada motar suka fice daga asibitin.
Kukanta kawai ke tashi cikin motar,ta kasa tsaida kukan ko dai dai da minti daya
"Don Allah bilal ka tashi,ka tashi kace wasa kake mana" shine abinda take fada lokaci bayan lokaci tana girgizashi,.
Sannu a hankali kukan yaci gaba da ratsa kunnuwansu,harda samir da sitiyarin motar ke hannunsa,lokaci bayan lokaci yakan ce
"Hasbunallahu wa ni'imal wakil" a sarari,daga bisani saiya sanya casset na karatun qur'anu,qira'ar khusari,wanda hakan ya rage kaifin kukan kaltum.
Suna isa qauyen labarin rasuwar bilal ya ratsa ko ina,kafin kace meye wannan jama'a sun fara cika gidan,habiba na daya daga cikin wadanda suka fara zuwa,sun shigo tana riqe a hannun surukarta tana gunjin kuka,tana faduwa tana tashi,tana kiran bilal din tare da fatan abunda ke faruwan ya zama mafarki,xuwanta ya sake sanyawa kaltume dake ta son bawa kanta juriya sa qwarin gwiwa saita sare,suka taru suka dinga kuka baji ba gani,sai inna da bata jima da isowa ba,tana doje daga bakin qofa tahau musu fada,fadan da badan cikin yanayi yake ba duk sai sun tsaya kallonta,saboda mamakin dama innar tasan Allah?.
Cikin abinda bai gaza awa biyu ba aka gama shirya bilal,a sannan kaltum ta sake aro juriya,ta taka tana rangaji kamar zata fadi,saboda yadda takejin iska tana yawo da ita ta fita harabar gidansun,inda abokan bilal suka cika,harda wadanda kaltum ma bata sansu ba,ba 'yan unguwar bane.
Abokinsa na kusa kusa ta kira
"Ka tambaya cikin abokanku,ko akwai wanda yake bin bilal bashi?" Kai ya kada cikin alhini
"A iya sanina babu,saidai ma wadanda bilal yakebi....amma bari na tambaya" juyawa yayi ya koma cikinsu,amsoshin dake fita daga bakunansu duka irin wadda ya bata ne daxun kafin yakai ga tambayarsu
Hawaye taji yana sauko mata,haka rayuwarsa ta qare gaba daya,ya nema da guminsa da qarfinsa,yaci iya cinsa,ya baiwa 'yan uwansa,ya bada bashi ga abokansa,koda zasu cinye bashin ba zasu biyashi ba.
Rudewa gidan yayi da koke koke,yadda gidansu ke cike damqam da mata ashe a waje abun yafi haka,mamaki ya kusan kama kowa na jama'ar da bilal ya tara,idan bakasan waye ya rasu ba,zakayi tunanin cewa wani babban mutum ne ya rasu,saboda yawan al'ummar daya samu,suna ji suna gani bayan an gama sallar ama daukeshi akayi gaba dashi,ya barsu da kuka,ya barsu da kewa,ya barsu cikin gidan da ake yunqurin korarsa,sai gashi tun ba'a koreshi ba,shi ya tattara nasa ya nasa ya tafi inda ba dawo,inda kowanne me rai zaije.
Cikin dare a ranar ta kasa bacci,ganin komai take kamar wani wasan kwaikwayo,kamar wani wasa ne bilal din yake musu,kamar yaje ne zai dawo musu,ta dinga juyi tana kuka,yayin da gefe guda kuma abinda ya faru a wunin duka ya dinga dawo mata,yadda su ya munzali da muzammilu suka dinga rawar qafa wajen hada gawar bilal,sune kawo turare sune kawo sabulu da likkafani,idan ka gani kai ba zakace sune sila ko muzajar mutuwarsa ba,Allah ya sani,ba zata iya gogewa ba,ba zata iya hana kanta kallonsu a matsayin wadanda sukayi sila ko sanadiyyar tafiyar bilalunsu zuwa qiyama ba.
Sai kuma ta hango fuskar mahaifinsu,yadda yaye tsugunne gaban gawar bilal,gawar da sai da aka gama hada bilal din sannan ubangiji ya bashi ikon qarasowa,don bai samu labari da wuri ba,saboda a ranar yayi sammakon zuwa wani waje.
Ganin juyin bana qare bane saita miqe don ta dauro alwala,sai sukaci karo da ummanta,da alama itama baccin ya gagareta ne,batasan sanda wani sabon kukan ya qwace mata ba
"Da kika ce abar habiba ta zauna,da haka zaku zauna kenan ke da ita kuyita yi masa kuka?,kukan da bashi da wani amfani ko rana a wajensa?" Abinda umman tace kenan tana cika buta da ruwa don daura alwala.
To cikin kwanakin zaman makokin abubuwa da yawa sun faru,sunga jama'a masu yawa,wadanda basu tsmmatarwa bilal din ba,jama'a masu kamala da mutunci,wadanda zaka zaci ba zasu zo gun jana'izar yaro ba,yaron ma mata gata irin bilal,amma sai gasu,kowa yazo kuma saiya koka kan rasuwar yaron,saboda yadda kusan kowa ke amfanar sa,bashi da qyuya ko san jiki ko kadan,baisan rashin kunya ko fitsara ba ko kadan,girmama kowa yake,hakanan bashi da abokin fada.
Kudadensa da mutane suka kakkarba bashi masu tsoron Allah suka dinga kawowa ummanmu da kaltum sunyi mamaki,saboda wani ma basuyi tunanin bashi zai shiga tsakaninsu ba,yawan kudin da suka riqe sai yanzu suke biya,inda a zamanin da yake raye suka biyashin,babu shakka da sun isa ya kafa qaramar sana'a,da bai mutu cikin wahalar daya mutu ba,da bai mutu yana neman kudin da za'a masa aiki ba.
Yawan mutanen da suke zuwa gaisuwa ba shakka banda taimakon Allah,da kuma taimakon kawu ado da gwaggo indo da basusan da abinda zasu ci dasu ba,saidai a taimakon wadan nan bayin Allahn aka dinga dafa abinci ana ci.
Inna kuwa rabonta da gidan tun randa aka dauki gawar bilal,bayan an dawo daga binneshi,kawu ado yasa aka sauke buhun shinkafa babba dana wake,saita hau cewa a diba mata,wannan ai ya yiwa zuwaira da ahalinta yawa,ta dauko babbar qatuwar leda baqa ta buda bakinta.
Ran wasu daga cikin 'yan uwa ya baci,amma saboda kowa yana shakkarta,saboda masifarta da bala'i yasa aka rasa mai tanka mata,sai wasu daga cikin jikokinta da suka fara qananun maganganu.
Ganin da gaske take yasa yakumbo indo ta murje idanunta tayi mata magana
"Inna,wannan kayan abincinfa ba dafawa akace a dinga yi ana ciyar da masu xaman makoki,kuma ko a hakanma yayi kadan,saina aika an sake siyo wani buhun" mita ta hau yi,har sai da taga ran yakumbo indon ya baci,kasancewarta 'yar gaban goshinta da batason tayi fushi,tilas ta haqura,daga bisani ma ana sallame sallar la'asar tace zata koma gida,ba wanda ya hanata ko ya tambayeta ba'asi,hasalima ma hakan yafi ma kowa kwanciyar hankali.
********Sanyi gami da lallausan qamshi ne kawai ke fita daga qawatacce kuma madaidaicin falon,wanda zai burge duk wani mutum ko da ina matsayinsa da arziqinsa yakai.
Zaratan samarin ne su biyu kacal cikin falon,wato samir da Aamiru,samir din na sanye da wata riga short sleeve shirts da wando da iyakacinsa qaurinsa,dukkansu ruwan toka da adon baqi,wanda suka zauna jikinsa suka fitar da duk wata qira tasa tan murdewar jiki da murjewa, system ne a gabansa,yana duba wasu dokuna da akayi masa tallansu tun daga wata qasar,irin dokunansu ne na can,kasancewarsa mutum mai son dawakai,wanda a yanzu haka yana da guda uku nashi na qashin kansa,hakan duk sanda za'a gabatar da wasan tseren dokuna na polo to yana daga gaba gaba wajen zuwa,ba'a nigeria kawai ba,wani lokaci qafa da qafa yake fita wata qasar idan za'ayi,musamman idan akwai wanda yakeso a cikin wandanda xasuyi gasar tseren dawakan,wannan dabi'a tasa na daya daga cikin dalilan da yasa sunan saraki ya bishi.
Amiru kuwa na kwance saman doguwar sofa yana amsa waya,yanayin yadda yake wayar ya isa ya gaya maka cewa wayace ta masoya,don kuwa iya murmushin da yake fita saman fuskarsa kadai zai gaya maka hira ce ta musamman.
Kowa abinda yake gabansa yakeyi,kuma kowa najin dadin sabgarsa,har zuwa wani lokaci da aamirun ya gama wayar,sai ya miqe ya zauna kana ya zuro qafafunsa qasa,idanunsa akan samir,wanda ya gama zaben dawakan da yakeso cikin wadanda suka turo masa video dinsu
"Yauwa,ina jinka,kace mene?" Inji amiru yana miqa hannu,ya janyo drink din da jawahir ta shigo musu dashi,musamman saboda yayan nata.
Idanunsa masu kwarjini da kuma girma,wanda hasken system ya qarawa kyau ya daga ya watsawa aamiru yana murza tafun hannayensa waje daya,saboda sanyin ac din daya dan fara damunsa,duba da yanayin sanyi sanyi da aka fara a gari
"Kaga malam,yi ta kanka kawai,zama zanyi nata yi maka bayani?,ko dan aikinka ne ni da zan zauna inta maimaita maka zance bayan ka gama gabatar da naka uzurin?" Dariya Aamir ya qyalqyale da ita yana jjiye cup din hannunsa