Sashe 6
Dabiar Zuciya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Baya taja ta gaidashi fuskarta kadaran kadaham,saboda babu wani cikakken shaquwa tsakaninsu,ba wata mu'amala bace can mai zurfi take hadasu ba,iyakarsu dama gaisuwar,shi ashirun baya gidan,yayi aure shida matarsa,gidansa yana can bayan gari,lokaci lokaci yake zuwa gidan,ya gaida mahifinsu ya bashi ihsanin daya kawo masa,zuwan nasan ma kusan asha ruwan tsuntsaye ne,yakan dan dauki wasu kwanaki bai zo ba,hakama me bi masa zubairu,shima kusan kalar tashi rayuwar kenan,qaninsu ne yakubu bai kai gayin aure ba,saidai yana nema har ma ankai kudin na gani ina so,shima dai duk da baiyi auren ba ba kasafai yake zaman gidan ba,wani lokaci yazo yayi kwanaki sannan yayi tafiyarsa,saboda kusan ya fisu rashin kirki ma duk cikin su ukun,duk da suma bawai kirkin suka cika ba,don sau daya basu taba kallon umma a matsayin mahaifiyarsu ba,abinda yasa kaltum ta shata musu layi gaba dayansu,daga gaisuwa ba abinda ke shiga tsakaninsu,saidai idan sunso su din sun qara daga saman hakan.
Basu fiya jure halaye da dabi'un mahaifinsu kamar yadda su kaltume ke dauka ba,hakan ya sanya suke nesa nesa dashi,sai lokaci zuwa lokaci yake ganinsu.
Kadaran kadaham shima ya amsa,suka wuce bayan wasila itama ta gaisheshi,suka jera zuwa dandalin,jefi jefi suna hira da suwaiban,har suka soma gamuwa da wasu daga cikin 'yammatan qauyen da suma suka makara basu fito da wuri ba,don haka suka rankaya gaba daya da duk wadda suka hadun suka nufi filin.
Sanda suka isa wajen ya cika,samari na hannun hagu a tsaitsaye,yammata na hannun dama,gada ake sosai,kowacce na baje basirarta,yayin da daga bayan fage kuma masu saida rake ne,gyada,balangu da sauran kayan maqulashe,wajen akwai haske sosai,duk da babu wutar nepa,amma sun haskaka wajen da wuta ta kara da kuma fitilun aci bal bal dama fitilun qwayaye na masu siye da siyarwar dake filin,sun riga dasun saba dama,wutar nepa wahala take musu,sukan jima kafin suga wulgawarta,ba kasafai suke damuwa ba,tunda ba wani amfani da ita sosai dama sukeyi ba.
Suna isa kaltume taja ta toge
"Ki shigo don Allah,kin dade bakiyi mana waqarki bafa" magiyar da wasu qwayensu guda biyu nana da basira suka fara yi mata,wanda taja hankalin wasu yammatan suma suka fara roqarta,saboda basira da baiwar murya da Allah ya bata ya sanya kusan kowa keson waqenta,duk da tana tsaiwa ne kawai a filin,bata rawa sam,zata basu wajen su kuma suna juyawa
"Dalla ku qyaleta....don taga tana da murya shine take jawa mutane rai" kubra daya daga cikin qawayen nasu ta fada cikin jin haushi tana komawa cikin filin.
Ko kallonta kaltume bata yi ba tace dasu
"Yau ban shirya yin waqa ba,amma kuyi haquri,duk randa na sake zuwa a shirye,zanzo da wuri nizan fara yi ma" dole suka qyaleta,saboda sunsan halinta,tunda tace ba zata din ba to ba zata ba,saita zauna saman wani kututturen dabino da aka sareshi qasansa yayi saura,tana kallon yadda suke gudanar da al'amuransu.
Kiran sunanta da taji anyi daga gefanta ya sanyata daga kanta da sauri,nasiru ne,saurayi guda daya tilo a garin daya samu damar zuwa jami'a,saurayin da 'yammatan garin ke rububi qwarai da burin ganin sun mallakeshi,saboda ruwan karatun boko daya fara wankeshi,ya kuma fara sauya masa yanayi da kamanni da 'yan garin.
Basarwa tayi kamar bata ganshi ba,tana boye murmushin fuskarta,saboda ita din gwanace dama a wannan gefan,tana tuna yadda ya cimmata sanda take samowa inna ruwa a rafi,ya gabatar mata da soyayyarsa,yace a yanzun zai koma makaranta ne zaiyi jarabawa,amma idan ya dawo zai dakaci amsarta.
Saidai zuciyarta ta rabu biyu gami da kokwanto da kuma shakka,saboda wasila data shaida mata cewa kowa na masa kallon kafiri dan wuta kuma dan iska,idonsa ya bude da yawa wai a yadda takejin labari,saboda sudai babu wata makaranta da akeyi me dadewa haka har shekaru masu yawa irin nasa,anfi kyautata zaton kawai sheqe ayarsa da iskancinsa yake tafiya yi birni,amma haka kawai taji jikinta bai bata abinda wasilan ke fada haka bane,saboda tasan jama'ar qauyensu,gwanaye ne kuma qwararru wajen yada jita jita da kuma qadar da abinda basu sani ba,basu da tabbas ma akan hakan.
Kiran sunanta daya sakeyi ya katse mata tunaninta,saita sake waiwayawa ta kalleshi,murmushi ya sakar mata,wanda ya tilastata sassauta fuskarta itama
"Ko zaki daure ki taso mu koma daga can,saboda muryoyin wadan nan basa bari aji maganar mutun sosai,don Allah ba jimawa zakiyi ba,gaisawa kawai zamuyi" shuru tayi tana nazari,tun daxu dama takeson tafiyar,inda ace ma da habiba suka zo da tuni tayi tafiyarta,to habiban ciwon kai takeyi,dalilin da yasa ta barota kenan,ta yiwa wasila magana tun daxu yfi sau uku sai tace mata bari tayi waqar qarshe saisu tafi amma shuru,tana ganin wannan ce damarta kawai da zata koma gida,saboda dare na sakeyi,don haka ta miqe,cike da farincikin yadda ta amsa masa ya motsa yabi bayanta,wani gefe na zuciyarsa yana hango masa banbanci qarara tsakaninta da yammatan garin.
Tana jingine da wani teburin me rake tana sauraren yadda yaketa qoqarin tsara mata kalamai,ba laifi ya burgeta fiye da sauran samarin qauyen,wadanda a cikinsu har yanzu babu wanda ta taba tsaiwa dashi a matsayin saurayinta,duk wanda ta kalla sai taga nutsuwa da hankalinsa baikai mata yadda takeso ba,wani irin fata ne mai girma ya ginu cikin zuciyarta,tun daga lokacin data budi idanu ta fahimci sarai rayuwar gidansu,ta karanci wanne irin miji mahaifiyarsu ke aure,saita samu kanta da gayawa kanta da kanta,lallai ya zama tamkar wajibi a garesu ita da 'yar uwarta....yin dogon tsinkaye da nazari,sanya hankulansu cikin jikinsu kafin fidda mijin aure.
Abu daya zuciya da qwaqwalwarta ke gaya mata shine....namiji mai ilimi shine haske kuma mafitarsu,duk da ita din ba wata me karatu bace,bata tsira da komai ba banda karatun muhammadiyya da take nema a kullum,amma wata iriyar qwaqwalwa mai zurfi da nauyin tunani....gamida quality na auna dai dai da kuma akasinsa Allah ya bata,a tsahon nazarin data debe lokutta masu tsaho da batasan adadinsu tana yi ba,zuciyarta ta gaya mata jahilci na taja rawa wajen kauda danne haqqin mata,da kuma zaluntarsu.
Idan akace ilimi bawai ana nufin karatun boko ba,a'ah,ana magana ne kan karatun addini,wanda shine tsanu na farko dake saita rayuwar namiji,ya karbi iyalinsa ya kula dasu ta hanyar data dace,tunda shine na farko daya fara koya mana yadda zamu mu'amalanci junanmu tsakanin mutum da mutum hary zuwa gidan aure,ta hanyar haska mana madubin rayuwar gidan ma'aiki S A W(yake 'yar uwata,indai kinason kubuta daga sharrin kurkukun gidan aure,da baqincikin namiji,a farkon zabin abokin rayuwarki,kiyi qoqari ki zabi namiji me ilimin addini me kuma aiki dashi sama da kowanne irin miji daya mallaki koma wanne irin qyalqyali na duniya,haqiqa idan kikayi hakan kin samawa kanki kyakkyawar mafita da makoma ke da yaran da zaki samarwa al'umma).
Ya dade yana tsara mata kalaman da taji ta gamsu dashi,ya kuma kwanta a ranta,yace ta jirashi minti kadan,bata ankara ba sai gashi ya dawo gareta da tarin siyayya fal leda
"Muje na rakaki,kinga hanyoyin sun soma duhu" ya fada yana murmushi,batace komai ba tayi gaba,ya biyota riqe da ledar da baikai ga miqa mata ita ba.
Basuyi nisa ba idanuwanta suka hango mata asiya cikin wata duhuwa,sosai ta zubawa wajen idanu da kyau,abinda ta gani ya sanyata dauke idanunta babu shiri tana kiran sunan Allah,abu daya da zai hanata riskar asiyan shine nasiru,ba zataso ya gani koya fuskanci wani abu ba,tunda baqo yake ga rayuwarsu,zuciyarta tayi mata baqiqqirin,har bata iya fahimtar abinda nasirun kece mata sosai,a haka suka qarasa qofar gidansu,saiya miqa mata ledar yana murmushi,bay taja kawai ba tare data amsa ba tana kada kai
"Ka barshi na gode"
"Don Allah ki karba,haba kattum,duka saboda na siya fa,indai bawai baki amsa tayina bane" ganin ya damu ya sanyata ta saka hannu ta karba,bata fiya son amsar abu daga hannun samari ba,sabida tasan halin ummansu sarai,ta musu iyaka,hakanan ta shata musu layi daga amsar abun hannun wani,sa'annan tana tsoron karbar abun hannun wani ya zamana aurensu baiyuwu ba,kamar yadda ta faffaru a baya.
Tun a sannana akwai ragowar zumunci tsakaninta da asiya,ita ke feqewa tana zaqalqalewa
"Wallahi karbi abunki,ai bake kika roqa ba,baki sukayi" to koda bata karba din ba asiyan zata karbar mata ita,ta kuma fita ci ma.
Godiya ta yi masa sukayi sallama sannan ta nufi cikin gidan,tun kafin ta isa sassansu ta jiyo muryar kawu iliya shida matarsa,tambaya yake ina asiya,tana kuma shaida masa cewa ita ta aiketa gidan kuluwa,bata dade ai da fita ba,kuma yanzu zata dawo.
Wani abu mai kama da tausayin kawu iliyan ya ratsa kaltum,duk da kasancewar shi dinma babu wata qauna da kulawa da yake nuna musu,shida uwar dakin nasa xamuje ta tadda mujemu,wanda su kansu har yanzu basusan meye ainihin wannan tsana kyara da tsangwama da suke nuna musu ba,amma duk da hakan....abun tausayi ne mace ta rufi uba game da yaransa,rufewar kuma da zata iya zame musu cutarwa me girma cikin rayuwarsu....dama rayuwar wadanda ke kusa dasu.
Sallamar da takeyi ne ta maqale a fatar bakinta sanda ta cusa kai sassan nasu,sakamakon ganin mahaifinsu zaune saman tabarma daga gefan dakinsa,ummanta na duqe daga gefan nasa,idanunsa ya zube fes bisa fuskarta yana mata wani kallo mai nauyi da ban tsoro.
"Kin dawo daga yawon karuwancin naki?" Taji kalmar mai azabar nauyi ta sauka a kunnuwanta,da sauri ummanta ta cira kanta tana kallonshi,habiba dake kwance cikin dakinsu ta miqe ta zauna sosai ba tare data shirya ba,yayin da itama kaltume take kallonsa a matuqar tsorace,kafin ta duqa a wajen a hankali jikinta yana rawa.
Kalaman nashi na yau sunyi tsauri fiye da kullum,a baya yakance kin dawo daga yawon naki!,amma a yau abin nasa yaci gaba,har ya iya dangantata diyar cikinsa da yawon karuwanci?,wannan wanne irin alkaba'i ne?,ledar hannunta ta zame daga hannun nata,saita fadi a wajen ta tarwatse,kayan da suke ciki wanda itama batasan meye da meye a ciki ba suka sukayi dai dai a wajen,ita umman tasu da baban nasu sukabi kayan da kallo.
Basu fiya jure halaye da dabi'un mahaifinsu kamar yadda su kaltume ke dauka ba,hakan ya sanya suke nesa nesa dashi,sai lokaci zuwa lokaci yake ganinsu.
Kadaran kadaham shima ya amsa,suka wuce bayan wasila itama ta gaisheshi,suka jera zuwa dandalin,jefi jefi suna hira da suwaiban,har suka soma gamuwa da wasu daga cikin 'yammatan qauyen da suma suka makara basu fito da wuri ba,don haka suka rankaya gaba daya da duk wadda suka hadun suka nufi filin.
Sanda suka isa wajen ya cika,samari na hannun hagu a tsaitsaye,yammata na hannun dama,gada ake sosai,kowacce na baje basirarta,yayin da daga bayan fage kuma masu saida rake ne,gyada,balangu da sauran kayan maqulashe,wajen akwai haske sosai,duk da babu wutar nepa,amma sun haskaka wajen da wuta ta kara da kuma fitilun aci bal bal dama fitilun qwayaye na masu siye da siyarwar dake filin,sun riga dasun saba dama,wutar nepa wahala take musu,sukan jima kafin suga wulgawarta,ba kasafai suke damuwa ba,tunda ba wani amfani da ita sosai dama sukeyi ba.
Suna isa kaltume taja ta toge
"Ki shigo don Allah,kin dade bakiyi mana waqarki bafa" magiyar da wasu qwayensu guda biyu nana da basira suka fara yi mata,wanda taja hankalin wasu yammatan suma suka fara roqarta,saboda basira da baiwar murya da Allah ya bata ya sanya kusan kowa keson waqenta,duk da tana tsaiwa ne kawai a filin,bata rawa sam,zata basu wajen su kuma suna juyawa
"Dalla ku qyaleta....don taga tana da murya shine take jawa mutane rai" kubra daya daga cikin qawayen nasu ta fada cikin jin haushi tana komawa cikin filin.
Ko kallonta kaltume bata yi ba tace dasu
"Yau ban shirya yin waqa ba,amma kuyi haquri,duk randa na sake zuwa a shirye,zanzo da wuri nizan fara yi ma" dole suka qyaleta,saboda sunsan halinta,tunda tace ba zata din ba to ba zata ba,saita zauna saman wani kututturen dabino da aka sareshi qasansa yayi saura,tana kallon yadda suke gudanar da al'amuransu.
Kiran sunanta da taji anyi daga gefanta ya sanyata daga kanta da sauri,nasiru ne,saurayi guda daya tilo a garin daya samu damar zuwa jami'a,saurayin da 'yammatan garin ke rububi qwarai da burin ganin sun mallakeshi,saboda ruwan karatun boko daya fara wankeshi,ya kuma fara sauya masa yanayi da kamanni da 'yan garin.
Basarwa tayi kamar bata ganshi ba,tana boye murmushin fuskarta,saboda ita din gwanace dama a wannan gefan,tana tuna yadda ya cimmata sanda take samowa inna ruwa a rafi,ya gabatar mata da soyayyarsa,yace a yanzun zai koma makaranta ne zaiyi jarabawa,amma idan ya dawo zai dakaci amsarta.
Saidai zuciyarta ta rabu biyu gami da kokwanto da kuma shakka,saboda wasila data shaida mata cewa kowa na masa kallon kafiri dan wuta kuma dan iska,idonsa ya bude da yawa wai a yadda takejin labari,saboda sudai babu wata makaranta da akeyi me dadewa haka har shekaru masu yawa irin nasa,anfi kyautata zaton kawai sheqe ayarsa da iskancinsa yake tafiya yi birni,amma haka kawai taji jikinta bai bata abinda wasilan ke fada haka bane,saboda tasan jama'ar qauyensu,gwanaye ne kuma qwararru wajen yada jita jita da kuma qadar da abinda basu sani ba,basu da tabbas ma akan hakan.
Kiran sunanta daya sakeyi ya katse mata tunaninta,saita sake waiwayawa ta kalleshi,murmushi ya sakar mata,wanda ya tilastata sassauta fuskarta itama
"Ko zaki daure ki taso mu koma daga can,saboda muryoyin wadan nan basa bari aji maganar mutun sosai,don Allah ba jimawa zakiyi ba,gaisawa kawai zamuyi" shuru tayi tana nazari,tun daxu dama takeson tafiyar,inda ace ma da habiba suka zo da tuni tayi tafiyarta,to habiban ciwon kai takeyi,dalilin da yasa ta barota kenan,ta yiwa wasila magana tun daxu yfi sau uku sai tace mata bari tayi waqar qarshe saisu tafi amma shuru,tana ganin wannan ce damarta kawai da zata koma gida,saboda dare na sakeyi,don haka ta miqe,cike da farincikin yadda ta amsa masa ya motsa yabi bayanta,wani gefe na zuciyarsa yana hango masa banbanci qarara tsakaninta da yammatan garin.
Tana jingine da wani teburin me rake tana sauraren yadda yaketa qoqarin tsara mata kalamai,ba laifi ya burgeta fiye da sauran samarin qauyen,wadanda a cikinsu har yanzu babu wanda ta taba tsaiwa dashi a matsayin saurayinta,duk wanda ta kalla sai taga nutsuwa da hankalinsa baikai mata yadda takeso ba,wani irin fata ne mai girma ya ginu cikin zuciyarta,tun daga lokacin data budi idanu ta fahimci sarai rayuwar gidansu,ta karanci wanne irin miji mahaifiyarsu ke aure,saita samu kanta da gayawa kanta da kanta,lallai ya zama tamkar wajibi a garesu ita da 'yar uwarta....yin dogon tsinkaye da nazari,sanya hankulansu cikin jikinsu kafin fidda mijin aure.
Abu daya zuciya da qwaqwalwarta ke gaya mata shine....namiji mai ilimi shine haske kuma mafitarsu,duk da ita din ba wata me karatu bace,bata tsira da komai ba banda karatun muhammadiyya da take nema a kullum,amma wata iriyar qwaqwalwa mai zurfi da nauyin tunani....gamida quality na auna dai dai da kuma akasinsa Allah ya bata,a tsahon nazarin data debe lokutta masu tsaho da batasan adadinsu tana yi ba,zuciyarta ta gaya mata jahilci na taja rawa wajen kauda danne haqqin mata,da kuma zaluntarsu.
Idan akace ilimi bawai ana nufin karatun boko ba,a'ah,ana magana ne kan karatun addini,wanda shine tsanu na farko dake saita rayuwar namiji,ya karbi iyalinsa ya kula dasu ta hanyar data dace,tunda shine na farko daya fara koya mana yadda zamu mu'amalanci junanmu tsakanin mutum da mutum hary zuwa gidan aure,ta hanyar haska mana madubin rayuwar gidan ma'aiki S A W(yake 'yar uwata,indai kinason kubuta daga sharrin kurkukun gidan aure,da baqincikin namiji,a farkon zabin abokin rayuwarki,kiyi qoqari ki zabi namiji me ilimin addini me kuma aiki dashi sama da kowanne irin miji daya mallaki koma wanne irin qyalqyali na duniya,haqiqa idan kikayi hakan kin samawa kanki kyakkyawar mafita da makoma ke da yaran da zaki samarwa al'umma).
Ya dade yana tsara mata kalaman da taji ta gamsu dashi,ya kuma kwanta a ranta,yace ta jirashi minti kadan,bata ankara ba sai gashi ya dawo gareta da tarin siyayya fal leda
"Muje na rakaki,kinga hanyoyin sun soma duhu" ya fada yana murmushi,batace komai ba tayi gaba,ya biyota riqe da ledar da baikai ga miqa mata ita ba.
Basuyi nisa ba idanuwanta suka hango mata asiya cikin wata duhuwa,sosai ta zubawa wajen idanu da kyau,abinda ta gani ya sanyata dauke idanunta babu shiri tana kiran sunan Allah,abu daya da zai hanata riskar asiyan shine nasiru,ba zataso ya gani koya fuskanci wani abu ba,tunda baqo yake ga rayuwarsu,zuciyarta tayi mata baqiqqirin,har bata iya fahimtar abinda nasirun kece mata sosai,a haka suka qarasa qofar gidansu,saiya miqa mata ledar yana murmushi,bay taja kawai ba tare data amsa ba tana kada kai
"Ka barshi na gode"
"Don Allah ki karba,haba kattum,duka saboda na siya fa,indai bawai baki amsa tayina bane" ganin ya damu ya sanyata ta saka hannu ta karba,bata fiya son amsar abu daga hannun samari ba,sabida tasan halin ummansu sarai,ta musu iyaka,hakanan ta shata musu layi daga amsar abun hannun wani,sa'annan tana tsoron karbar abun hannun wani ya zamana aurensu baiyuwu ba,kamar yadda ta faffaru a baya.
Tun a sannana akwai ragowar zumunci tsakaninta da asiya,ita ke feqewa tana zaqalqalewa
"Wallahi karbi abunki,ai bake kika roqa ba,baki sukayi" to koda bata karba din ba asiyan zata karbar mata ita,ta kuma fita ci ma.
Godiya ta yi masa sukayi sallama sannan ta nufi cikin gidan,tun kafin ta isa sassansu ta jiyo muryar kawu iliya shida matarsa,tambaya yake ina asiya,tana kuma shaida masa cewa ita ta aiketa gidan kuluwa,bata dade ai da fita ba,kuma yanzu zata dawo.
Wani abu mai kama da tausayin kawu iliyan ya ratsa kaltum,duk da kasancewar shi dinma babu wata qauna da kulawa da yake nuna musu,shida uwar dakin nasa xamuje ta tadda mujemu,wanda su kansu har yanzu basusan meye ainihin wannan tsana kyara da tsangwama da suke nuna musu ba,amma duk da hakan....abun tausayi ne mace ta rufi uba game da yaransa,rufewar kuma da zata iya zame musu cutarwa me girma cikin rayuwarsu....dama rayuwar wadanda ke kusa dasu.
Sallamar da takeyi ne ta maqale a fatar bakinta sanda ta cusa kai sassan nasu,sakamakon ganin mahaifinsu zaune saman tabarma daga gefan dakinsa,ummanta na duqe daga gefan nasa,idanunsa ya zube fes bisa fuskarta yana mata wani kallo mai nauyi da ban tsoro.
"Kin dawo daga yawon karuwancin naki?" Taji kalmar mai azabar nauyi ta sauka a kunnuwanta,da sauri ummanta ta cira kanta tana kallonshi,habiba dake kwance cikin dakinsu ta miqe ta zauna sosai ba tare data shirya ba,yayin da itama kaltume take kallonsa a matuqar tsorace,kafin ta duqa a wajen a hankali jikinta yana rawa.
Kalaman nashi na yau sunyi tsauri fiye da kullum,a baya yakance kin dawo daga yawon naki!,amma a yau abin nasa yaci gaba,har ya iya dangantata diyar cikinsa da yawon karuwanci?,wannan wanne irin alkaba'i ne?,ledar hannunta ta zame daga hannun nata,saita fadi a wajen ta tarwatse,kayan da suke ciki wanda itama batasan meye da meye a ciki ba suka sukayi dai dai a wajen,ita umman tasu da baban nasu sukabi kayan da kallo.