Sashe 26
Dabiar Zuciya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Duk da mamakin ganinsa a tsaye bai taba kwanukan ba,amma murmushi bai bar fuskarta ba
"Ya haka samir?,kai da zaka fita,ka zauna kaci mana"
"Babu komai mommy,zanci wajen hajiya,duk a yakema ba wata yunwa nake ji ba",saita dan tsuke fuska kadan
"Samir,kanason ka jawomin hajiy qarama tayi tunanin baka samun kulawa kenan?" Murmushin daya bayyanar da haqoransa yayi
"Haba mommy,nidin kamar qaramin yaro,karki damu" bata amsa masa ba,ta miqa masa ledar hannunta
"Gashi ka kai mata,kace ina gaidata da kyau kafin na shigo" sai daya kalli ledar kafin ya amsa,idan ba mantawa yayi ba jiya aka kawo mata abinda ke ciki,kuma juyin duniya auta jawahir tayi ta diban mata amma tace sam,idan tanaso su niqi gari ta basu address sukai namansu suma yi musu,amma gashi kacokam ta kyautar ga hajiya qarama,duk da rugurgujajjiyar alaqa sa dangantakar dake tsakaninsu
"Xataji" ya amsa yana juyawa
"Saika dawo"ta furta tana juyawa itama don barin falon.
Gefansa ya ajiye ledar a seat mai zaman banza,ya saka muqulli yana yunqurin tada motar wayarsa ta katseshi.
Wani qawataccen murmushi wanda yake jimawa kafin ya fita daga fuskarsa ya bayyana bayan an karanto masa sunan wanda yake kiran nasa,amsa kiran yayi, bai kuma bari anyi magana daga wancan sashen ba shi ya fara cewa
"Kai....kada kacemin kun dawo" dariya aka saki
"Mun dawo,minti hamsin kenan" fuska yadan bata
"Amma baka kyauta ba, at least ai ka gayamin ko nazo na tarbi abba a airport"
"Idan kana free a sannan ba,nafa sanka?"saiya lumshe idanunsa sannan ya bude
"Jokes apart don Allah,abba ne fa?"
"I know,wasa nake maka nima"
"Ok ka tsammaci zuwa na,am on my way" bai jira amsarsa ba ya katse kiran,ya tada motar da hanzari,da alamu uzurinsa da saurinsa ya qaru akan nada.
Har ya gota supermarket din saiya rage gudu kuma,yayi reverse ya dawo a hankali,ya samu waje ya tsaida motar sannan ya kasheta ya fito.
Baya taba iya shiga wajen hajiya qaraman hannunsa haka,yana ganin girma da qimarta,yana girmama qaunar da take nuna masa,duk da yawan fadanta,saiya taka cikin nutsuwa zuwa cikin supermarket din.
A hankali yake duba abubuwan da yasan tafiso yana zabarsu daya bayan daya,har sai daya kammala gaba daya,sannan ya nufi inda suke ajjiye Madara don ya siya mata,yasan qaunarta da madara tun ba yau ba,musamman ta gari.
Yana shan wata kwana yarinyar na bullowa itama cikin gudu irin na yaran da basu rufa shekara uku a duniya ba,taqin dake tsakaninsu kadan ne,da alama akwai wanda ya biyota,saiya tsaya ya mata lamfo,tana qarasowa ya dauketa cak zuwa sama,suka hada idanu,saita qara sakin dariya sosai tana cewa
"Anty mubina ce...."ko kafin ta rufe bakinta daga maganar anty mubinan kuwa ta bayyana,siririya farar budurwa,wadda shekarunta basufi ashirin ba,sanye da abaya ruwan jinin kare,ta yafa mayafinta saman kanta ba tare da tayi rolling ba,wanda hakan ya bayyana wani daga sashen gashinta da yake a tsefe.
Tsaiwa tayi tana duban yarinyar tana kuma duban samir dake dauke da ita,tana kuma sake maqaleshi tunda ta hangi mubina din,rada yayi ma yarinyar a kunne,sai taga ta sakeshi,maimakon ya miqa mata ita,saiya dauki kwandonsa ya juya yabar wajen,ya nufi wajen biya,tilas badon taso ba ta soma binsu a baya,qirjinta na dukan uku uki,ganin yayi gaba da yarinyar mutane.
A saman canter ya dora yarinyar yana tambayarta sunanta
"Afra" ta bashi amsa,saiya ciro atm dinsa ya miqa musu ya sanya musu pin bayan sun buqaci hakan sannan ya maida hankalinsa kan afra yana tambayarta meya sakata gudu
"Wai don na cewa anty mubina.....mu bari sai dan anjima saimu tafi,ta barni na gama kallo shine tace a'ah" dariya sosai yarinyar ta bashi,yasaki faffadan murmushi yana dubanta
"Waye yace miki ana zama cikin shago?,ba anan ake kallo ba kinji?,idan kinason yin kallo akaiki wajen wasa" yanayin fuskar yarinyar yaga ya canza,saita narke fuska
"Aida abbana ke kaini"
"Yanzu fa?"ya tambayeta shima yana rage fara'ar fuskarsa
"Anty mubina tacemin ya rasu,kuma idan aka mutu ai ba'a dawowa ko?" Juyawa yayi ya dubi sashen da mubinan ke tsaye tana kallonsu,sosai ranshi ya baci,tausayin yarinyar ya kamashi,ta yaya yarinya qarama kamar wannan zata dinga gaya mata babanta ya mutu kuma bazai dawo ba,ba mamaki she's mad.
Kafin ya sake cewa komai ya miqo masa katin yana shaida masa an gama cirewa
"Hold it.....ina zuwa"ya fada yana sake saba yarinyar a kafadarsa ya koma cikin shagon.
Siyayya ya dinga mata sosai,duk abinda ta nuna tana so saiya daukar mata,har sai data ce babu saura sannan suka dawo wajen biya,ya sauketa yana sake miqa musu,suka lissafa suka zari kudinsu suka zuba masa a leda,saiya riqe hannunta,suka qarasa inda mubina ke tsaye,wanda zuwa yanzu ta sake tsurewa sosai,ga tsoro ka fargaba,kamar ta dora hannu saman ka tayita ihu,tana qiyasta dukan da zata yiwa afra ne kawai da irin wannan giggiwar tata yau da takeson janyo musu tashin hankali.
Tura afra yayi gabanta,ya hangi hararar da take zabga mata,cikin husky voice dinsa yace
"Wawanci ne gayawa yaro wani nasa mai muhimmanci ya rasu,it hurts alot koda agun babba ne bare yaro da kanshi bazai iya dauka ko jurewa ba"saiya zame hannunsa daga cikin na afra,ya ajjiye ledar
"Don't do it again....." Ya fada sounding seriously Yana kaiwa haka ya juya ya soma takawa,sai kuma ya tsaya,ba tare daya waiwayo ba yace
"Karki sake ki taba lafiyarta koda wasa" saiya qara gaba,ya dauki ledarsa yabar shagon.
Bata dauke idanunta daga kanshi ba sai daya fice,taja iska sosai har cikin hunhunta tana jin sauran qamshin daya tafi ya bari a wajen,hakanan taji ta kasa dukan afran,tana shirin jan hannunta taji an dafa kafadarta,ta waiwaya a hankali,basma ce
"Waye wancan,wani mai zafin kika samo hala?"ta fada tana murmushi murmushi dariya dariya,sai datasa hannunta ta zame hannun basman daga kafadarta sannan tace
"Wannan me sanyi ne tako ina"
"Wannan uban kayan da kika debo fa mubina?kinsan dai maama tace kada mu diba kaya da yawa ko?" Basman ta tambayeta tana duban ledar gabanta
"Daga mai sanyi ne,shi ya siyawa afra"sai tayi hanyar barin shagon itama,yayin da basma ta biyota cikin mamaki tana jera mata tambayar ta sanshi ne
"Ko sau daya"ta amsa mata a taqaice sanda suke isa bakin motarsu,don a yanayin da take ciki bata buqatar dogon surutu da doguwar magana irin ta basman.
A farfajiyar harabar gidan yayi parking,kallo daya zaka fahimci gidan akwai wadatar rayuwa da kuma sukuni,yana kashe motar ma'aikatan dake farfajiyar gidan suka qaraso inda yake,dukkaninsu cikin sakin fuska,saiya fito ya maida murfin motar ya rufe,yana basu hannu daya bayan daya suna gaisawa,suna ganin girma da mutuncinsa,saboda yadda yake baiwa duk wanda ya cancanta irin girman daya dace dashi,kusan yasan darajar kowa,yana kuma mutunta kowa,kamar ba ma'aikatan gidan ba,ihsani yayi musu kamar yadda ya saba duk sanda Allah ya kawoshi gidan kana ya wuce zuwa cikin ainihin gidan.
,daya daga cikin ma'aikatan yana riqe da ledar daya mata siyayyar a ciki.
Da sallama ya shiga falon bayan ya karba ledarsa,ta amsa masa sanda take zaune gaban zainaba me mata kitso,tana lallabe mata kan nata da manyan kitso dan hannu biyu,duk da girma amma sumaeta tana nan,saboda sunyi gadon gashi sosai,duba da irin asalin jinsin yaren da suka fito.
Ana qarshe dama suke,don haka bai jima da zama ba zainaba ta gama tayi mata sallama ta tafi bayan ta sallameta,saiya zamo daga saman kujeran ya zauna qasam carfet sosai shima yana duban hajiya qarama tare da sake gaidata,gami da yi mata barka da dawowa,cikin kulawa da kuma jin dadi ta amsa,saita daga murya tana kiran 'yar aikinta.
Ba jimawa ta qaraso,ta rage tsaho sosai tana gaida samir,duk kuwa da cewa ta girmeshi,ya kuma dade yana hanasu duqa masa wajen gaidashi amma sun kasa,saboda girma da qimarsa sosai da suke gani
"Ki kawowa samir abinci"ta umarceta,saita amaa tana juyawa da sauri zuwa ciki.
Ledojin gabansa ya ajye gaban hajiya qarama wadda ke qoqarin daure kanta da dankwalin atamfar jikinta
"Ga wannan hajiya,babu yawa,wannan ledar kuma.... mummy ce tace a kawo miki" yana kallon yadda ta tabe baki,sannan ta saka hannu taja iya ledar daya kawo mata tana cewa
"Ni nace ta kawomin wani abu ne?,saboda irin haka fa yas ako yayan bai gayawa na dawo ba,don karta cikani da kayayyakin da ba domin Allah aka shiryasu ba,sai don shegiyar riya da son iyawa" shuru samir kawai yayi baice komai ba,don dama bashi daya cewar,yana ganin tunda aka kai wadan nan tsayin shekarun babu jituwa tsakanin hajiar da mummy,baya tunanin nan gaba za'a samu,yana daya daha cikin abubuwan dake sanyashi a tunani,wadanda har yau ya gaza samun amsoshinsu,meye tsakanin hajiyar da mummy da har yanzu ta kasa qaunarta,duk da tarin kyautatawar mummyn a gareta,hakanan shidai da idanunsa bai taba ganin mummy ta damu game da abinda hajiya qarama take mata ba,bata taba nuna fushi gazawa ko qpsawa ba,amma hakan baisa hajiya qarama yin haquri ya zubda makamanta ba.
Abinda ba kasafai yake yinsa ba,tunda yana ganin sha'ani ne daya shafesu,hakanan na sama dashi ma sunyi sun gaji sun bari,amma a yau din saiya murmusa sannan yace
"Kiyi haquri hajiyata..... nummy kan da murna da kirkin nan nata ta bada saqon a baki,duk da kuwa har autarta ta hana,amma keta zabeki ta baki" baki ta sake tabewa tana dan jifansa da harara
"Yoni ina ruwana?,nina sanyata?,ai bani nace tayi kyautar ba,data sani ma auta din ta baiwa taci ta more,tunda na tabbata kudin uba nata ne,kirki kuma da kake maganarsa,ai ba zata gayawa aminatu kirki ba" ambatar sunan saiya hado da faduwar gabansa,wadda ta tilasta masa lumshe idanu yana furta
"La'ilaha illallah" zuciyarsa,tsahon wasu sakanni sanna ya bude idanun nasa,sai suka fada cikin na hajiya qarama,da yaga kamar tsareshi tayi da idanu tun dazun tanw kallonshi
"Ai wallahi Allah ya kyauta.....kuma duk nisan jifa qasa zai fado,kuma qauna nidai jidda ta samu soyayyata har abada,saidai ta wadanda ta rufewa idanu da wani hali wanda ni nasa shiga akayi kasuwa aka samoshi" daga haka ta miqe qafarta wadda da alama itace meyi mata ciwon,har tana shure ledar da mummyn ta batan,saika dauka da gayya tayi hakan.
Dai dai nan mai aikin ta dawo da abinci a shirye ta ajjiye gabansa,hajiya qarama tace
"Dauki wannan ledar ki shiga da ita ciki,idan abun kaiwa baka ne ki rabe muku keda jummai"godiya ta shiga jerawa hajiyan,sannan ta duqa ta dauka zata wuce da ita,a lokacin affan yayi sallama,dan hajiya qarama na qarshe wato autanta.
"Ya haka samir?,kai da zaka fita,ka zauna kaci mana"
"Babu komai mommy,zanci wajen hajiya,duk a yakema ba wata yunwa nake ji ba",saita dan tsuke fuska kadan
"Samir,kanason ka jawomin hajiy qarama tayi tunanin baka samun kulawa kenan?" Murmushin daya bayyanar da haqoransa yayi
"Haba mommy,nidin kamar qaramin yaro,karki damu" bata amsa masa ba,ta miqa masa ledar hannunta
"Gashi ka kai mata,kace ina gaidata da kyau kafin na shigo" sai daya kalli ledar kafin ya amsa,idan ba mantawa yayi ba jiya aka kawo mata abinda ke ciki,kuma juyin duniya auta jawahir tayi ta diban mata amma tace sam,idan tanaso su niqi gari ta basu address sukai namansu suma yi musu,amma gashi kacokam ta kyautar ga hajiya qarama,duk da rugurgujajjiyar alaqa sa dangantakar dake tsakaninsu
"Xataji" ya amsa yana juyawa
"Saika dawo"ta furta tana juyawa itama don barin falon.
Gefansa ya ajiye ledar a seat mai zaman banza,ya saka muqulli yana yunqurin tada motar wayarsa ta katseshi.
Wani qawataccen murmushi wanda yake jimawa kafin ya fita daga fuskarsa ya bayyana bayan an karanto masa sunan wanda yake kiran nasa,amsa kiran yayi, bai kuma bari anyi magana daga wancan sashen ba shi ya fara cewa
"Kai....kada kacemin kun dawo" dariya aka saki
"Mun dawo,minti hamsin kenan" fuska yadan bata
"Amma baka kyauta ba, at least ai ka gayamin ko nazo na tarbi abba a airport"
"Idan kana free a sannan ba,nafa sanka?"saiya lumshe idanunsa sannan ya bude
"Jokes apart don Allah,abba ne fa?"
"I know,wasa nake maka nima"
"Ok ka tsammaci zuwa na,am on my way" bai jira amsarsa ba ya katse kiran,ya tada motar da hanzari,da alamu uzurinsa da saurinsa ya qaru akan nada.
Har ya gota supermarket din saiya rage gudu kuma,yayi reverse ya dawo a hankali,ya samu waje ya tsaida motar sannan ya kasheta ya fito.
Baya taba iya shiga wajen hajiya qaraman hannunsa haka,yana ganin girma da qimarta,yana girmama qaunar da take nuna masa,duk da yawan fadanta,saiya taka cikin nutsuwa zuwa cikin supermarket din.
A hankali yake duba abubuwan da yasan tafiso yana zabarsu daya bayan daya,har sai daya kammala gaba daya,sannan ya nufi inda suke ajjiye Madara don ya siya mata,yasan qaunarta da madara tun ba yau ba,musamman ta gari.
Yana shan wata kwana yarinyar na bullowa itama cikin gudu irin na yaran da basu rufa shekara uku a duniya ba,taqin dake tsakaninsu kadan ne,da alama akwai wanda ya biyota,saiya tsaya ya mata lamfo,tana qarasowa ya dauketa cak zuwa sama,suka hada idanu,saita qara sakin dariya sosai tana cewa
"Anty mubina ce...."ko kafin ta rufe bakinta daga maganar anty mubinan kuwa ta bayyana,siririya farar budurwa,wadda shekarunta basufi ashirin ba,sanye da abaya ruwan jinin kare,ta yafa mayafinta saman kanta ba tare da tayi rolling ba,wanda hakan ya bayyana wani daga sashen gashinta da yake a tsefe.
Tsaiwa tayi tana duban yarinyar tana kuma duban samir dake dauke da ita,tana kuma sake maqaleshi tunda ta hangi mubina din,rada yayi ma yarinyar a kunne,sai taga ta sakeshi,maimakon ya miqa mata ita,saiya dauki kwandonsa ya juya yabar wajen,ya nufi wajen biya,tilas badon taso ba ta soma binsu a baya,qirjinta na dukan uku uki,ganin yayi gaba da yarinyar mutane.
A saman canter ya dora yarinyar yana tambayarta sunanta
"Afra" ta bashi amsa,saiya ciro atm dinsa ya miqa musu ya sanya musu pin bayan sun buqaci hakan sannan ya maida hankalinsa kan afra yana tambayarta meya sakata gudu
"Wai don na cewa anty mubina.....mu bari sai dan anjima saimu tafi,ta barni na gama kallo shine tace a'ah" dariya sosai yarinyar ta bashi,yasaki faffadan murmushi yana dubanta
"Waye yace miki ana zama cikin shago?,ba anan ake kallo ba kinji?,idan kinason yin kallo akaiki wajen wasa" yanayin fuskar yarinyar yaga ya canza,saita narke fuska
"Aida abbana ke kaini"
"Yanzu fa?"ya tambayeta shima yana rage fara'ar fuskarsa
"Anty mubina tacemin ya rasu,kuma idan aka mutu ai ba'a dawowa ko?" Juyawa yayi ya dubi sashen da mubinan ke tsaye tana kallonsu,sosai ranshi ya baci,tausayin yarinyar ya kamashi,ta yaya yarinya qarama kamar wannan zata dinga gaya mata babanta ya mutu kuma bazai dawo ba,ba mamaki she's mad.
Kafin ya sake cewa komai ya miqo masa katin yana shaida masa an gama cirewa
"Hold it.....ina zuwa"ya fada yana sake saba yarinyar a kafadarsa ya koma cikin shagon.
Siyayya ya dinga mata sosai,duk abinda ta nuna tana so saiya daukar mata,har sai data ce babu saura sannan suka dawo wajen biya,ya sauketa yana sake miqa musu,suka lissafa suka zari kudinsu suka zuba masa a leda,saiya riqe hannunta,suka qarasa inda mubina ke tsaye,wanda zuwa yanzu ta sake tsurewa sosai,ga tsoro ka fargaba,kamar ta dora hannu saman ka tayita ihu,tana qiyasta dukan da zata yiwa afra ne kawai da irin wannan giggiwar tata yau da takeson janyo musu tashin hankali.
Tura afra yayi gabanta,ya hangi hararar da take zabga mata,cikin husky voice dinsa yace
"Wawanci ne gayawa yaro wani nasa mai muhimmanci ya rasu,it hurts alot koda agun babba ne bare yaro da kanshi bazai iya dauka ko jurewa ba"saiya zame hannunsa daga cikin na afra,ya ajjiye ledar
"Don't do it again....." Ya fada sounding seriously Yana kaiwa haka ya juya ya soma takawa,sai kuma ya tsaya,ba tare daya waiwayo ba yace
"Karki sake ki taba lafiyarta koda wasa" saiya qara gaba,ya dauki ledarsa yabar shagon.
Bata dauke idanunta daga kanshi ba sai daya fice,taja iska sosai har cikin hunhunta tana jin sauran qamshin daya tafi ya bari a wajen,hakanan taji ta kasa dukan afran,tana shirin jan hannunta taji an dafa kafadarta,ta waiwaya a hankali,basma ce
"Waye wancan,wani mai zafin kika samo hala?"ta fada tana murmushi murmushi dariya dariya,sai datasa hannunta ta zame hannun basman daga kafadarta sannan tace
"Wannan me sanyi ne tako ina"
"Wannan uban kayan da kika debo fa mubina?kinsan dai maama tace kada mu diba kaya da yawa ko?" Basman ta tambayeta tana duban ledar gabanta
"Daga mai sanyi ne,shi ya siyawa afra"sai tayi hanyar barin shagon itama,yayin da basma ta biyota cikin mamaki tana jera mata tambayar ta sanshi ne
"Ko sau daya"ta amsa mata a taqaice sanda suke isa bakin motarsu,don a yanayin da take ciki bata buqatar dogon surutu da doguwar magana irin ta basman.
A farfajiyar harabar gidan yayi parking,kallo daya zaka fahimci gidan akwai wadatar rayuwa da kuma sukuni,yana kashe motar ma'aikatan dake farfajiyar gidan suka qaraso inda yake,dukkaninsu cikin sakin fuska,saiya fito ya maida murfin motar ya rufe,yana basu hannu daya bayan daya suna gaisawa,suna ganin girma da mutuncinsa,saboda yadda yake baiwa duk wanda ya cancanta irin girman daya dace dashi,kusan yasan darajar kowa,yana kuma mutunta kowa,kamar ba ma'aikatan gidan ba,ihsani yayi musu kamar yadda ya saba duk sanda Allah ya kawoshi gidan kana ya wuce zuwa cikin ainihin gidan.
,daya daga cikin ma'aikatan yana riqe da ledar daya mata siyayyar a ciki.
Da sallama ya shiga falon bayan ya karba ledarsa,ta amsa masa sanda take zaune gaban zainaba me mata kitso,tana lallabe mata kan nata da manyan kitso dan hannu biyu,duk da girma amma sumaeta tana nan,saboda sunyi gadon gashi sosai,duba da irin asalin jinsin yaren da suka fito.
Ana qarshe dama suke,don haka bai jima da zama ba zainaba ta gama tayi mata sallama ta tafi bayan ta sallameta,saiya zamo daga saman kujeran ya zauna qasam carfet sosai shima yana duban hajiya qarama tare da sake gaidata,gami da yi mata barka da dawowa,cikin kulawa da kuma jin dadi ta amsa,saita daga murya tana kiran 'yar aikinta.
Ba jimawa ta qaraso,ta rage tsaho sosai tana gaida samir,duk kuwa da cewa ta girmeshi,ya kuma dade yana hanasu duqa masa wajen gaidashi amma sun kasa,saboda girma da qimarsa sosai da suke gani
"Ki kawowa samir abinci"ta umarceta,saita amaa tana juyawa da sauri zuwa ciki.
Ledojin gabansa ya ajye gaban hajiya qarama wadda ke qoqarin daure kanta da dankwalin atamfar jikinta
"Ga wannan hajiya,babu yawa,wannan ledar kuma.... mummy ce tace a kawo miki" yana kallon yadda ta tabe baki,sannan ta saka hannu taja iya ledar daya kawo mata tana cewa
"Ni nace ta kawomin wani abu ne?,saboda irin haka fa yas ako yayan bai gayawa na dawo ba,don karta cikani da kayayyakin da ba domin Allah aka shiryasu ba,sai don shegiyar riya da son iyawa" shuru samir kawai yayi baice komai ba,don dama bashi daya cewar,yana ganin tunda aka kai wadan nan tsayin shekarun babu jituwa tsakanin hajiar da mummy,baya tunanin nan gaba za'a samu,yana daya daha cikin abubuwan dake sanyashi a tunani,wadanda har yau ya gaza samun amsoshinsu,meye tsakanin hajiyar da mummy da har yanzu ta kasa qaunarta,duk da tarin kyautatawar mummyn a gareta,hakanan shidai da idanunsa bai taba ganin mummy ta damu game da abinda hajiya qarama take mata ba,bata taba nuna fushi gazawa ko qpsawa ba,amma hakan baisa hajiya qarama yin haquri ya zubda makamanta ba.
Abinda ba kasafai yake yinsa ba,tunda yana ganin sha'ani ne daya shafesu,hakanan na sama dashi ma sunyi sun gaji sun bari,amma a yau din saiya murmusa sannan yace
"Kiyi haquri hajiyata..... nummy kan da murna da kirkin nan nata ta bada saqon a baki,duk da kuwa har autarta ta hana,amma keta zabeki ta baki" baki ta sake tabewa tana dan jifansa da harara
"Yoni ina ruwana?,nina sanyata?,ai bani nace tayi kyautar ba,data sani ma auta din ta baiwa taci ta more,tunda na tabbata kudin uba nata ne,kirki kuma da kake maganarsa,ai ba zata gayawa aminatu kirki ba" ambatar sunan saiya hado da faduwar gabansa,wadda ta tilasta masa lumshe idanu yana furta
"La'ilaha illallah" zuciyarsa,tsahon wasu sakanni sanna ya bude idanun nasa,sai suka fada cikin na hajiya qarama,da yaga kamar tsareshi tayi da idanu tun dazun tanw kallonshi
"Ai wallahi Allah ya kyauta.....kuma duk nisan jifa qasa zai fado,kuma qauna nidai jidda ta samu soyayyata har abada,saidai ta wadanda ta rufewa idanu da wani hali wanda ni nasa shiga akayi kasuwa aka samoshi" daga haka ta miqe qafarta wadda da alama itace meyi mata ciwon,har tana shure ledar da mummyn ta batan,saika dauka da gayya tayi hakan.
Dai dai nan mai aikin ta dawo da abinci a shirye ta ajjiye gabansa,hajiya qarama tace
"Dauki wannan ledar ki shiga da ita ciki,idan abun kaiwa baka ne ki rabe muku keda jummai"godiya ta shiga jerawa hajiyan,sannan ta duqa ta dauka zata wuce da ita,a lokacin affan yayi sallama,dan hajiya qarama na qarshe wato autanta.