Sashe 89
Dabiar Zuciya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Igiyar da akayi daga tsakiyar ciki don daure rigar ta zauna daidai jikin me ita,ta taimaka wajen fitar da surar albarkar qirjin da Allah ya bata,wanda sam batasan hakan ya faru ba,saboda ko madubi bata tsaya kalla ba,idanunta sun sake shanyewa saboda rashin wadataccen baccin da bata samu ba a daren jiya,babu koma a fuskarta banda wata powder da jawahir ta siya mata ta masu kalae fatarta, powder din kuwa ba qaramin kyau takewa fatarta ba,sai labbanta daketa qyallin man lebe daya qarawa leban nata taushi da kyau.
Baisan ajiyar zuciya ya saki ba,saida ya tsinci zuciyarsa tana tuhumarsa da yadda ya qure kaltum din da kallo har ta kamashi yana kallon nata,abinda ya sanyata jin kunya,ta saka hannu a hankali ta bude gidan gaba ta zura jikinta kafin qafafunta da suka sha hill shoes su biyo baya,abinda ya qarawa adon nata kyau,budurcinta daya fara bayyana ya sake fitowa fili muraran.
"Ina yini" ta gaidashi a ladabce tana dora purse dinta saman cinyarta
"Lafiya lau" ya amsa mata yana kallon yadda garin ya fara hada hadari,ba kasafai yakeson tuqi da damina ba saboda ruwa,yaso tafiya ne a jirgi,so amma duka yau babu jirgin da zai tashi daga kano zuwa bauchi,don haka ya maida tafiyar kawai a mota,saboda lokaci ya riga ya qure,gobe ne daurin aure,a haka ma yayi missing events masu yawa,ya kuma sha mita da qorafi wajen amiru,amma duka ya shareshi,don dama shi ba kasafai ya fiya shiga irin wadan nan shagulgulan ba sai wadanda suka zama dole.
Yana qoqarin tayar da motar qamshinta nason dagula masa lissafi,sai zai murza key din sai yaji kamar bazai iya ba,kamar wanda aka zarewa dukka lakar jikinsa,har taji shurun yayi yawa,ta daga kanta daga murza yatsun hannunta da take tare da wassafa yadda xasuyi tafiya tare dashi ta awanni masu tsaho daga ita saishi.
Kallon datayi masa akayi katari shima ita yake kalla,a hankali ya motsa labbansa,idanunsa kan dan qaramin bakinta
"Wannan rigar....." Sai kuma yayi shuru ba tare daya qarasa ba,ya cire hannunsa daga kan motar a hankali ya nufo inda take zaune,numfashinta ta dauke gaba daya ganin ya nufo da hannunsa qasan qirjinta.
Yatsa daya ya saka ya kunce igiyar data daure tsakiyar rigar da ita,take rigar ta ware,ta batar da duk wani shape nata daya fito.
Sake qamewa tayi tare da runtse idonta ganin ya matso da jikinsa gaba daya inda take,qwayar idanunsa cikin nata,cikin second biyu qamshin turarensa,da hucin numfashinsa da dumin jikinsa gaba daya suka mamayeta.
Seat belt ya zaro a hankali ya zagayo da ita ta saman cikinta,wanda garin hakan yadan shafi qirjinta da bayan hannunsa,al'amarin daya sanyashi jin wani shock tun daga yatsun qafarsa zuwa kwanyarsa,ya sauke numfashi me nauyi sanda ya gama saka mata ya maida bayansa ya jigina da kujera yana qoqarin maintaining nutsuwarsa.
Har zuwa sanda ya bude nashi idanun,ya murxa key din ya tashi motar yana karanta addu'ar matafiya a fili amma qasa qasa.
Tata addu'ar itama ta fara karantawa sanda suka ficewa daga gidan,wanda basuyi wata doguwar tafiya ba ya sanya karatun daya daga cikin shahararrun malamai kuma bayin Allahn da ubangiji yayi mana kyautarsu wato mlm dr umar sani fage.
Karatun kusan shine ya janye hankalin kowannensu,karatu ne cike da tarin hikima da kuma maganganu na fasaha,tare da tunkuda bawa zuwa kusanta kai da Allah matuqar kusantuwa,tun tana iya jin abinda malamin ke fada tana kokawa da bashin baccin data ci jiya,har yayi nasarar yin awon gaba da ita ta daina jin komai.
Tafiyar awa uku da rabi suka shiga garin azare,kai tsaye suka nufa cikin garin,zuwa lokacin garin azare ya fara duhu saboa hadarin da ya yiwa sama rumfa,saidai mutane da yawa basu kawo zubarshi ba,saboda wannan kusan shine hadarin farko tun bayan sanya ran shigowar damina.
Idanunta biyu a sannan,sabida sun tsaya sunyi salla,ya siya musu take away duk da itadin bata iya ci a gabansa ba.
Ringing wayarsa tayi,yana tuqi a hankali da hannu daya,yasa daya hannun ya daga wayar ya sanyata a kunne idanunsa na bisa titi.
Magana suke da amiru,ya shaida masa akwai dinner din mr and mrs da za'a gabatar takwas na dare,amma saboda ganin hadari yasa an maidota nan da awa biyu
"This is none of my business.....meye amfanin gayamin?,kai kanka ba zaka samu shiga ba tunda tuzurun banza ne,har gwara gwara ni" dariya sosai amiru ya qyalqyale da ita,bazai biye masa suyi abinda suka saba ba,don so yake yallaboshi yazo kodon saboda kada angon ya fassara wani abu daban,saboda yarinyar da zai aura din tadan so samir
"Wai tula ne zaiwa audi gori......gwara kai ame?,tuxurantaka?,meye marabar dambe da fada,ni dakai ai duk d same,amma dai afuwa master,na yadda da kai,yanzu abinda za'ayi,kada ka wuce gida,ka tsaya dai dai Round about din nan da zaka shiga titin gidan ya dikko,kafin ka shiga titin ka tsaya,am on my way" katse wayar kawai yayi ba tare daya amsawa amirun ba,sai ya koma tuqi a hankali yana duban hanya.
Tun kafin su qarasa ya hangi samir din jingine da wata sabuwar baqar mota,dai dai sanda motar take fakawa,daidai lokacin yaga ya cusa kanshi ta window din motar,da alama magana yake da wasu,sai samir din ya kashe motar kawai yaci gaba da xama cikin motar ba tare daya fita ba,ganin haka amirun ya tunakarosu,kanshi tsaya ya tsaya side din kaltum,ya bude murfin motar yana cewa
"Sannu da hanya madam,ga mota can shiga ta ciki" duban samir tayi suka hada idanu kana ta dauki jakarta ta fice daga motar,wanta tashinta ya sanya wani abu fadowa daga jikinta,hannu ya miqa yana qoqarin dauko takardar,saiya kula hotone,ya juya hoton a hankali,take idanunsa sukayi arba da fuskar dake jikin hoton,abinda ya sanyashi bin baya kaltum da amiru dake tafiya zuwa wancan motar da kallo,mamaki na mamayarsa na inda ta samo hoton,saiya bude locker din motar ya saka hoton ya rufe yana juya tambayar inda ta samo din cikin ransa.
Ruqunqumeta jawahir tayi sanda suka shiga cikin motar,kamar xata koka cikin kaltum din,jtakam dariya kawai kaltume din ke mata,har zuwa sanda amiru da yaga basu da niyyar rufe motar ya rufe musu ya koma wajen samir.
*********kayan da amirun ya miqe masa ya kalla
"Am telling you fa,babu inda zanje,ina buqatar na huta malam" kicin kicin amiru ya masa,yasan idan baiyi da gasken ba ba zaya je ba
"Wallahi koda wannan shine last thing da xakayi a azare sai kaje" gira ya dage ma amirun dukka biyun yana dubanshi
"Really?" Harara ya watsa mana,saiya fincika kayan daga hannunsa ya watsa gado ya bisu ya kwanta kawai a kai,qyaleshi amiru yayi,tunda yayi hakan yasan zayaje din koda baiso ba.
Kanta ta karkatar ta dubi jawahir
"Don Allah ki shiga na jiraki anan mana" kaltum ta fada tana kwabe fuska,tun daga sanda akayi.mata kwalliyar dake fuskarta har zuwa yanzu duk a takure take,sanda taga fuskarta a madubi sai data tsorata,irin kyan da tayi bata taba zata ko tsammatar ganinsa a fuskarta ba,dukka jama'ar dake wajen sai da suka tsaya suna kallonta,saboda yadda kwalliyar tayi masifar bin lafiyayyar chocolate colour din fatarta ta kwanta sosai.
Idanu jawahir ta fitar
"Wa?,ai wallahi saikin shiga,nima setup mukayi da ya amiru a matsayin miji da mata zamu shiga,kema haka zaki haquri kizo mu shiga.....kinga ma yana kirana,hala ya iso" jawahir ta fada tana daga wayarta tana duban me kiran,sai kawai taga ta balle murfin motar ta fita tana duba ta inda suke.
Ta bangaren da take ta leqo ta mata alamar ta fito,a hankali ta janyo jikinta ta zuro qafafunta daga motar.
Yana tsaye ya basu baya kadan,hannayensa zube a aljihun wandonsa yana duban wajen,ranshi baiso zuwa wajen ba,kawai dai yayine saboda ya faranta ran amirun daya dage.
"Oya....muje already ma an fara event din" amiru ya fada,abinda ya sanya samir juyowa kenan.
A hankali idanunsa suka sauka kanta,tana tsaye dab dashi,sai yaji wuta ta dauke masa na wucin gadi,baisan sanda ya bita da kallo tun daga sama zuwa qasa ba,wani kyau na musamman da bai taba tsammatarsa ba tayi masa,komai ya fito perfect,duk wata baiwa tata ta fito,ta zama cikakkiyar budurwar me tashen shekaru da zata iya jan hankalin kowanne namiji da zai dora idanunsa a kanta.
Wani abu da yaji ya tsaya masa a wuya ya hadiye,ya dauke idonsa daga kanta ya maida kan amiru,saiya miqa hannu ya fincikeshi gefe
"How dare you zaka sata tayi irin wannan kwalliyar amiru?" Idanu amiru ya fitar
"Mene aibu to?"
"Ka manta matar aur......." Maganar ta maqale masa ba tare data gama fita gaba daya ba,saboda rashin sanin ma'anar yin maganar.
Dariyar da amirun ke boyewa tadan fito kadan
"Bari na qarasa maka tunda kunyar qarasawa kake,na manta matar samir ce?,ko?,karka damu,ni kadai na sani fa,amma yau kowa a hakan zai kalleta......muje please muna sake makara" amirun ya fada yana yin gaba da sauri,ya jera shida jawahir itama daketa boye dariyarta,duk da batasan alaqar dake tsakani ba amma cewa take
"Wallahi ya Aamir sunyi kyau sosai,sun dace da juna Allah yadda kasan miji da mata,dama zaiso kaltum, she's cute wlh,duk da bayason baqar mace amma kaltum ta dace dashi,yau ka yima ya samir shigar sauri" murmushi shima yayi ya waiwaya yana satar dubansu sanda suke gab da shigewa hall din.
Shuru ya biyo baya a wajen,tana tsaye a inda take kanta aqasa tana wasa da yatsun hannunta,saboda gaba daya jinta take a takure,yayin da yake tsaye,har yanzu hannayensa zube a aljihunsa yana ci gaba da qare mata kallo,a hankali ya tako zuwa inda take,ya zare hannunsa daya dake aljihunsa ya kama nata hannun,gaba dayansu wani abune yabi ta jijiyarsu ya aikama qwaqwalensu saqo,saiya fara takawa a nutse tana biye dashi,wanda kafin sukai ga shigewa ciki yayyafi mai qarfi ya fara sauka.
Suna shigowa wajen idanun jawahir na kansu,baki ta bude tana mamaki,yau yayansu ne da kama hannun wata?,kasa daurewa tayi sai data tabo amiru.
Daga can baya ya zabar musu sit,tunda suka shiga wajen bai motsa ba kamar yadda itama bai barta ta motsa ko nan da can ba,bayaga ango da yaje ya yiwa Allah ya sanya alkhairi,abinda ke bashi haushi da mamaki shine duk wanda zai wuce ta wajen saiya kallesu yakuma juyowa,wayarsa na hannunsa yana amsa saqonnin da baiyi niyyar dubawa bama,lokaci lokaci yakan saki tsaki ya kuma jewa amiru harara.
Sanda aka fara rabon abubuwan motsa baki jawahir ta matso gurin ganin bata taso ba
Baisan ajiyar zuciya ya saki ba,saida ya tsinci zuciyarsa tana tuhumarsa da yadda ya qure kaltum din da kallo har ta kamashi yana kallon nata,abinda ya sanyata jin kunya,ta saka hannu a hankali ta bude gidan gaba ta zura jikinta kafin qafafunta da suka sha hill shoes su biyo baya,abinda ya qarawa adon nata kyau,budurcinta daya fara bayyana ya sake fitowa fili muraran.
"Ina yini" ta gaidashi a ladabce tana dora purse dinta saman cinyarta
"Lafiya lau" ya amsa mata yana kallon yadda garin ya fara hada hadari,ba kasafai yakeson tuqi da damina ba saboda ruwa,yaso tafiya ne a jirgi,so amma duka yau babu jirgin da zai tashi daga kano zuwa bauchi,don haka ya maida tafiyar kawai a mota,saboda lokaci ya riga ya qure,gobe ne daurin aure,a haka ma yayi missing events masu yawa,ya kuma sha mita da qorafi wajen amiru,amma duka ya shareshi,don dama shi ba kasafai ya fiya shiga irin wadan nan shagulgulan ba sai wadanda suka zama dole.
Yana qoqarin tayar da motar qamshinta nason dagula masa lissafi,sai zai murza key din sai yaji kamar bazai iya ba,kamar wanda aka zarewa dukka lakar jikinsa,har taji shurun yayi yawa,ta daga kanta daga murza yatsun hannunta da take tare da wassafa yadda xasuyi tafiya tare dashi ta awanni masu tsaho daga ita saishi.
Kallon datayi masa akayi katari shima ita yake kalla,a hankali ya motsa labbansa,idanunsa kan dan qaramin bakinta
"Wannan rigar....." Sai kuma yayi shuru ba tare daya qarasa ba,ya cire hannunsa daga kan motar a hankali ya nufo inda take zaune,numfashinta ta dauke gaba daya ganin ya nufo da hannunsa qasan qirjinta.
Yatsa daya ya saka ya kunce igiyar data daure tsakiyar rigar da ita,take rigar ta ware,ta batar da duk wani shape nata daya fito.
Sake qamewa tayi tare da runtse idonta ganin ya matso da jikinsa gaba daya inda take,qwayar idanunsa cikin nata,cikin second biyu qamshin turarensa,da hucin numfashinsa da dumin jikinsa gaba daya suka mamayeta.
Seat belt ya zaro a hankali ya zagayo da ita ta saman cikinta,wanda garin hakan yadan shafi qirjinta da bayan hannunsa,al'amarin daya sanyashi jin wani shock tun daga yatsun qafarsa zuwa kwanyarsa,ya sauke numfashi me nauyi sanda ya gama saka mata ya maida bayansa ya jigina da kujera yana qoqarin maintaining nutsuwarsa.
Har zuwa sanda ya bude nashi idanun,ya murxa key din ya tashi motar yana karanta addu'ar matafiya a fili amma qasa qasa.
Tata addu'ar itama ta fara karantawa sanda suka ficewa daga gidan,wanda basuyi wata doguwar tafiya ba ya sanya karatun daya daga cikin shahararrun malamai kuma bayin Allahn da ubangiji yayi mana kyautarsu wato mlm dr umar sani fage.
Karatun kusan shine ya janye hankalin kowannensu,karatu ne cike da tarin hikima da kuma maganganu na fasaha,tare da tunkuda bawa zuwa kusanta kai da Allah matuqar kusantuwa,tun tana iya jin abinda malamin ke fada tana kokawa da bashin baccin data ci jiya,har yayi nasarar yin awon gaba da ita ta daina jin komai.
Tafiyar awa uku da rabi suka shiga garin azare,kai tsaye suka nufa cikin garin,zuwa lokacin garin azare ya fara duhu saboa hadarin da ya yiwa sama rumfa,saidai mutane da yawa basu kawo zubarshi ba,saboda wannan kusan shine hadarin farko tun bayan sanya ran shigowar damina.
Idanunta biyu a sannan,sabida sun tsaya sunyi salla,ya siya musu take away duk da itadin bata iya ci a gabansa ba.
Ringing wayarsa tayi,yana tuqi a hankali da hannu daya,yasa daya hannun ya daga wayar ya sanyata a kunne idanunsa na bisa titi.
Magana suke da amiru,ya shaida masa akwai dinner din mr and mrs da za'a gabatar takwas na dare,amma saboda ganin hadari yasa an maidota nan da awa biyu
"This is none of my business.....meye amfanin gayamin?,kai kanka ba zaka samu shiga ba tunda tuzurun banza ne,har gwara gwara ni" dariya sosai amiru ya qyalqyale da ita,bazai biye masa suyi abinda suka saba ba,don so yake yallaboshi yazo kodon saboda kada angon ya fassara wani abu daban,saboda yarinyar da zai aura din tadan so samir
"Wai tula ne zaiwa audi gori......gwara kai ame?,tuxurantaka?,meye marabar dambe da fada,ni dakai ai duk d same,amma dai afuwa master,na yadda da kai,yanzu abinda za'ayi,kada ka wuce gida,ka tsaya dai dai Round about din nan da zaka shiga titin gidan ya dikko,kafin ka shiga titin ka tsaya,am on my way" katse wayar kawai yayi ba tare daya amsawa amirun ba,sai ya koma tuqi a hankali yana duban hanya.
Tun kafin su qarasa ya hangi samir din jingine da wata sabuwar baqar mota,dai dai sanda motar take fakawa,daidai lokacin yaga ya cusa kanshi ta window din motar,da alama magana yake da wasu,sai samir din ya kashe motar kawai yaci gaba da xama cikin motar ba tare daya fita ba,ganin haka amirun ya tunakarosu,kanshi tsaya ya tsaya side din kaltum,ya bude murfin motar yana cewa
"Sannu da hanya madam,ga mota can shiga ta ciki" duban samir tayi suka hada idanu kana ta dauki jakarta ta fice daga motar,wanta tashinta ya sanya wani abu fadowa daga jikinta,hannu ya miqa yana qoqarin dauko takardar,saiya kula hotone,ya juya hoton a hankali,take idanunsa sukayi arba da fuskar dake jikin hoton,abinda ya sanyashi bin baya kaltum da amiru dake tafiya zuwa wancan motar da kallo,mamaki na mamayarsa na inda ta samo hoton,saiya bude locker din motar ya saka hoton ya rufe yana juya tambayar inda ta samo din cikin ransa.
Ruqunqumeta jawahir tayi sanda suka shiga cikin motar,kamar xata koka cikin kaltum din,jtakam dariya kawai kaltume din ke mata,har zuwa sanda amiru da yaga basu da niyyar rufe motar ya rufe musu ya koma wajen samir.
*********kayan da amirun ya miqe masa ya kalla
"Am telling you fa,babu inda zanje,ina buqatar na huta malam" kicin kicin amiru ya masa,yasan idan baiyi da gasken ba ba zaya je ba
"Wallahi koda wannan shine last thing da xakayi a azare sai kaje" gira ya dage ma amirun dukka biyun yana dubanshi
"Really?" Harara ya watsa mana,saiya fincika kayan daga hannunsa ya watsa gado ya bisu ya kwanta kawai a kai,qyaleshi amiru yayi,tunda yayi hakan yasan zayaje din koda baiso ba.
Kanta ta karkatar ta dubi jawahir
"Don Allah ki shiga na jiraki anan mana" kaltum ta fada tana kwabe fuska,tun daga sanda akayi.mata kwalliyar dake fuskarta har zuwa yanzu duk a takure take,sanda taga fuskarta a madubi sai data tsorata,irin kyan da tayi bata taba zata ko tsammatar ganinsa a fuskarta ba,dukka jama'ar dake wajen sai da suka tsaya suna kallonta,saboda yadda kwalliyar tayi masifar bin lafiyayyar chocolate colour din fatarta ta kwanta sosai.
Idanu jawahir ta fitar
"Wa?,ai wallahi saikin shiga,nima setup mukayi da ya amiru a matsayin miji da mata zamu shiga,kema haka zaki haquri kizo mu shiga.....kinga ma yana kirana,hala ya iso" jawahir ta fada tana daga wayarta tana duban me kiran,sai kawai taga ta balle murfin motar ta fita tana duba ta inda suke.
Ta bangaren da take ta leqo ta mata alamar ta fito,a hankali ta janyo jikinta ta zuro qafafunta daga motar.
Yana tsaye ya basu baya kadan,hannayensa zube a aljihun wandonsa yana duban wajen,ranshi baiso zuwa wajen ba,kawai dai yayine saboda ya faranta ran amirun daya dage.
"Oya....muje already ma an fara event din" amiru ya fada,abinda ya sanya samir juyowa kenan.
A hankali idanunsa suka sauka kanta,tana tsaye dab dashi,sai yaji wuta ta dauke masa na wucin gadi,baisan sanda ya bita da kallo tun daga sama zuwa qasa ba,wani kyau na musamman da bai taba tsammatarsa ba tayi masa,komai ya fito perfect,duk wata baiwa tata ta fito,ta zama cikakkiyar budurwar me tashen shekaru da zata iya jan hankalin kowanne namiji da zai dora idanunsa a kanta.
Wani abu da yaji ya tsaya masa a wuya ya hadiye,ya dauke idonsa daga kanta ya maida kan amiru,saiya miqa hannu ya fincikeshi gefe
"How dare you zaka sata tayi irin wannan kwalliyar amiru?" Idanu amiru ya fitar
"Mene aibu to?"
"Ka manta matar aur......." Maganar ta maqale masa ba tare data gama fita gaba daya ba,saboda rashin sanin ma'anar yin maganar.
Dariyar da amirun ke boyewa tadan fito kadan
"Bari na qarasa maka tunda kunyar qarasawa kake,na manta matar samir ce?,ko?,karka damu,ni kadai na sani fa,amma yau kowa a hakan zai kalleta......muje please muna sake makara" amirun ya fada yana yin gaba da sauri,ya jera shida jawahir itama daketa boye dariyarta,duk da batasan alaqar dake tsakani ba amma cewa take
"Wallahi ya Aamir sunyi kyau sosai,sun dace da juna Allah yadda kasan miji da mata,dama zaiso kaltum, she's cute wlh,duk da bayason baqar mace amma kaltum ta dace dashi,yau ka yima ya samir shigar sauri" murmushi shima yayi ya waiwaya yana satar dubansu sanda suke gab da shigewa hall din.
Shuru ya biyo baya a wajen,tana tsaye a inda take kanta aqasa tana wasa da yatsun hannunta,saboda gaba daya jinta take a takure,yayin da yake tsaye,har yanzu hannayensa zube a aljihunsa yana ci gaba da qare mata kallo,a hankali ya tako zuwa inda take,ya zare hannunsa daya dake aljihunsa ya kama nata hannun,gaba dayansu wani abune yabi ta jijiyarsu ya aikama qwaqwalensu saqo,saiya fara takawa a nutse tana biye dashi,wanda kafin sukai ga shigewa ciki yayyafi mai qarfi ya fara sauka.
Suna shigowa wajen idanun jawahir na kansu,baki ta bude tana mamaki,yau yayansu ne da kama hannun wata?,kasa daurewa tayi sai data tabo amiru.
Daga can baya ya zabar musu sit,tunda suka shiga wajen bai motsa ba kamar yadda itama bai barta ta motsa ko nan da can ba,bayaga ango da yaje ya yiwa Allah ya sanya alkhairi,abinda ke bashi haushi da mamaki shine duk wanda zai wuce ta wajen saiya kallesu yakuma juyowa,wayarsa na hannunsa yana amsa saqonnin da baiyi niyyar dubawa bama,lokaci lokaci yakan saki tsaki ya kuma jewa amiru harara.
Sanda aka fara rabon abubuwan motsa baki jawahir ta matso gurin ganin bata taso ba