Sashe 96
Dabiar Zuciya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Salamu alaikum" bakinta ya subuce ta furta da sautin da dukka wanda ke cikin dakin xai iya jin abinda tace
"Subhanallah" taji ta furta tana daga kanta da sauri ta saukesu ga kaltum dake riqe da qarfe window din tana kallonta.
Idanu ta zubawa kaltum din tana kallonta,karo na farko data ga wata baquwar fuska haka tsaye a gabanta,yayin da kaltum ke kallonta tana karantar tsantsar kamanni da suke sake bayyana kansu a yanzun da suke kallon juna kallo irin na qurilla,yayin da wani gefe na zuciyarta ke cike fal da mamakin ambaton subhanallah din da taji tayi.
Zuciyarta ta sake raya mata ta aikata wani abu,cikin buguwar qirji ta buda bakinta a hankali
"Samir yana gaisheki" zumbur taga ta miqe kamar wadda wani abu ya tsikara,lamarin da yayi matuqar razana kaltum,har ta dan ja da baya,saboda tana ganin kamar zata rugo da gudu ta cafketa,saidai bata qara wani motsi ba illa zuba mata idanun data sakeyi
"Muhammad samir rashid azare?" Kunnuwanta suka tsinto kalaman da suke fitowa daga bakinta a sanda take ci gaba da tsaiwar.
Ta riga da tasan cikakken sunan daddy,ta kuma tabbatar cikakken sunan samir kenan,saboda haka saita gyada kanta suna ci gaba da kallon juna.
Jikinta yayi matuqar sanyi lokacin da taga hawaye yana saukowa daga fuskar matar daya bayan daya,wani busashen murmushi yana son mamaye fuskarta
"Ke wace?" Ta sake jifanta da tambayar da batasan amsar da zata bata ba,saidai kafin ta amsa din taji takun tafiya,abinda ya sanyata waiwaya da hanxari cike da tsoro da fargaba tana duban hanya.
56
Sake maida kallonta tayi ga qofar dakin bayan ta dauke idanunta daga doguwar hanyar da har yau wanda ke tafiyar baikai ga bayyana zuwa inda take ba,ga mamakinta sai taga qofar na bude,sabanin daxu da ta ganta kamar a rufe,kafin ta kammala tunanin da zatayi taga anja qofar an bude mata,saita sauka da sauri ta sanya kai cikin dakin.
Hannunta taji an fincika,data duba sai taga matar ce,kafin ta gama tantance komai ta isa da ita bakin dan duqurqushin gadonta ta dage mata,ta gane me take nufi,don haka ta shige,ta sauke xanin gadon da ya sauka ya lullube har qasan gadon,tana iya hangenta ta tsakanin labulen ta koma ta zauna kamar yadda take daxun,wanda da zamanta da qarasowar wanda taji takun nasa duka bai wuce second biyar ba.
Yana mita ya shigo,kamar wanda yake magana da mutum me hankali
"Lalle sabi'u yana wasa da aikin nan,baisan girman aikin dana bashi ba,baisan kuma wace hajiya jidda ba,banda guntun iskanci ya za'ayi ya barwa mutane daki a bude?,salon ki fita ya jawo mana jidali?,dole nayi masa jan kunne me qarfi,idan bazai iya ba ya ajiye a bawa wani".
Abinci taga ya ajjiye mata,ya dan tsaya kadan a kanta na wasu daqiqu,ba jimawa wayarsa tayi qara,yayi hanzarin dagawa ya soma amsawa,saiya juya yana ficewa daga dakina da alama wayar da yakeyi ta shagaltar dashi bai rufe dakin ba yadda suka saba ya fice da sauri.
Kaltum dake qasan gadon gaba daya jikinta ya jiqa da gumi,gaba kura baya sayaki,gata a cikin dakin me lalurar tabin hankali,wanda har sarqa aka tanada cikin dakin,da alama ana sanyata lokaci bayan lokaci idan buqatar hakan ta taso,na biyu ta ratso ta shigo wani shinge da aka jima ana mata gargadi kan furta koda kalma daya a kanshi,yau sai gashi,bama zancan muhallin ba,ta keta duk wani gurbi ta dangana da tsakiyar shingen tsundum
"Fito,ba zasu dawo ba sai tsakiyar dare ko kuma gobe....." Taji ta furta da muryarta a sarqe kamar daxun bayan ta yaye xanin gadon.
Mamaki ya sanya kaltum ta xuba mata idanu,ta yaya take magana sak irin ta masu hankali,muryarta ras a kuma nutse?,banda yanayinta babu abinda zai sanyaka kayi tunanin ba lafiyayya bace,kamar tasan tunani da mamakin da takeyi sai ta sake jin muryarta
"Cikin hayyacina nake,kar kiji tsoron komai,fito....ina jin kece addu'ata dana jima inayi" wadannan kalaman nata su suka bata qwarin gwiwar fitowar kamar yadda ta buqata.
Zama tayi dandaryar qasa kamar yadda take daxun,saita yiwa kaltum nuni da wajen xama da hannunta,ta qaraso a hankali har yanzu da ragowar fargaba cikin ranta,saidai kuma ta samu qwarin gwiwa,ta zauna tana fuskantar kaltum din,a hankali ta buda baki
"Duk da bandan wacece ke ba,aiken jidda ce ke ko kuma ubangiji ne ya jeho min ke ki xame min haske kamar yadda na dauki tsayin shekaru ina roqa.......inason insan wacece ke" qas kaltum tayi da kanta,taga abubuwa masu tarin yawa suna kai kawo
"Ni ba kowa bace,face wata mara gata da galihu da samir ya dauko daga qauyensu,ya dawo da ita cikin gidansu,ya bata gata da galihu da kuma dukkanin kulawa"
"Samir dina?,ya zama mai tausayi da taimako kenan kamar yadda nake roqon ubangijina?" Ta fada muryarta na rawa,da alama zuciyarta fa tsinke,kuka na dab da zuwa mata kowanne lokaci.
Kai kaltum ta gyada mata tana dubanta
"Amma ya akayi kika sake dawo kanki cikin wannan hatsarin?,bayan na tabbatar zuwanki na farko qaddara tasa jidda zuwa dake?,kuma ina da yaqinin kin samu kyakkyawan jan kunne daga gareta?kinsan wacece ni ne?" Shuru tayi zuciyarta na raunana,batasan amsar da zata bata ba.
"Zuciyata ce ta kasa nutsuwa,tana ta gayamin na dawo gareki,bayaga tarin mafarkan da suka cika barcina" kai ta gyada tana kallonta,cike da yabawa da jarumtar yarinyar,tunda har tasan jidda,amma ta yadda ta fuskanci kowanne qalubale ta dawo gareta,ba tare da tasan ainihin wacece ita ba.
"Nice mahaifiyar samir.....samir dana ne" maganar data sanya kaltum ta kusa shidewa bayan ta dago da kanta,tabbas ta jima tana qiyasta haka,ta dade tana jin kamar hakane,ashe hakanne da gaske?.
Dauke idanunsa yayi daga kanta sanda take bacew ganinsa,ya sauke wata boyayyar ajiyar zuciya,idanunsa suka sauka kan amiru,sam baisan ya xuba masa ido yana kallonsa bane sai yanzu,wani qaramin murmushi amirun yayi ya dauke kansa,shima sai ya janye idanunsa,ya maida ga jauhar daketa fama da chart,amma rabin hankalinta na ga samir da takeja da hira,saiya miqe a hankali,a sannan ta daga idanunta daga kan waya tana dubansa
"Bakaci ko spoon daya bafa" kai ya girgiza yana zuba hannayensa cikin aljihun wandonsa,a daqiqun da suka dan shude lokaci kadan yana jin kamar akwai wani dan waje da zai iya koda loma biyar ne,to amma bayan barin kaltum wajen.....sai yaji kamar ta tafi da dukkan wani sauran waje daya rage da zai iya zuba abincin
"Am coming"ya fada yana takawa a nutse yana barin wajen,gaba daya hankalinsa yaji ya dauku xuwa wajen daddy,mintunan da likitocin suka bashi zasu duba daddyn yana da tabbacin kafin qarasawarsa dakin sun cika.
A nutse yake takawa zuwa cikin dakin,bayan likitoci sun kammala aikinsu,sun kuma gama masa dukkanin bayanai kan cewa akwai ci gaba a ciwon nasa,su qara haqurin fitar dashi a basu kwana uku,idan hakan yaci tura saisu daukeshin.
Duk duniya baya jin akwai wanda yakejin abinda yakeji a qirjinsa,yana jin wata muguwar kewa tare da fargaba tana shigarsa,idan ya rasa daddyn ya tabbata bashi da kowa kenan,tunda har yau baisan duniyar da MAHAIFIYAR DATA GUDU TA BARSHI TAKE BA,abinda ya kasa goguwa cikin idanunsa,yana iya tuna sanda ta fice daga gidan ta gaban idanunsa,yana kuka yana daga mata hannu,amma ko sau daya bata waiwayo ta kalleshi ba.
Runtse idanunsa yayi,a hankali ya taka zuwa gaban gadon,ya sake janyo kujerarsa da kusan kowanne lokaci take ajjiye a wajen ya zauna gaban daddyn yana ci gaba da kallonsa.
Ya jima yana karanta addu'o'i yana tofa masa saman kansa,kafin ya sanya hannunsa cikin tafin hannun daddyn ya runtse a nasa,sannan a hankali ya saukar da kansa yana kallon hannuwan nasu dake sarqafe da juna.
Motsawa kadan yaga sunyi,abinda yasashi sake qura musu idanu ba qaqqautawa,still ya sake ji da ganin sun motsa din,sai kuma ya damqe hannun nasa gaba daya,abinda ya saka samir daga kansa da hanzari kenan zuwa fuskar daddyn.
Kamar numfashinsa zai dauke saboda farinciki sanda sukayi ido hudu da daddy yana kallonsa,bakinsa ya sarqafe,ya kasa furta kowacce kalma
"Allah yayi maka albarka" yaji kalmar ta fita daga bakin daddyn,saiya sake qura masa ido yana mamakin furucin daga bakinsa,sake maimaitawa daddyn yayi,bakin samir yana rawa yace
"Am....een.....ameen daddy,sannu"saiya gyada masa kai
"Dagani na zauna" ya fada a hankali muryarsa na sarqewa
"Bari a yiwa likita magana" ya fada da sauri yana miqewa
"Fara daga nin tukunna,ba abinda zai faru da izinin Allah,akwai maganar da nakeson gaya maka kafin shigowar kowa" cikin hikima ya dagashin ya jinginar dashi,yana fatan basuyi kuskuren aikata hakan ba,saidai yana zama yadan fara haki
"Daddy....ka bari a kirasun" qaramin murmushi ya saki yana dafa kafadar samir din,cikin hakin ya sake cewa
"Nayita roqon Allah......ya bani aron......rai da lokacin da zanta ce maka......Allah.....yayi maka albarka.....na....godewa Allah da.... .ya aramin din.....,abu na biyu......banason kace komai akan ciwona.....koda kuwa akwai wani abu da kake zato......ina bala?"
Cikin mamakin kalaman daddyn yace
"Yana dakin da aka kwantar dashi,amma da gobe zasu sallameshi" sai daddyn ya gyada kai,yana son cewa wani abun amma hakin ya qara yawa,abinda ya tilastawa samir din fita da hanzari kenan,saidai wani sashe na zuciyarsa ya cika da farincikin da zai iya cewa tunda yake rayuwa a duniya bai taba jin irinsa ba.
"Ni din mahaifiya ce ga samir,yaro daya tilo nawa dake raye a duniya....haifaffiyar qasar sudan ce,birnin Khartoum,munyi auren saurayi da budurwa da rashid a lokacin da yake University of Khartoum wato U of K,bayan ya kammala karatunsa muka tattaro muka dawo qasar nan da zama bisa amincewar dangina da kuma yarda da nagartar halaye da dabi'unsa.
Muna zaune cikin lumana da rufin asiri,da amintattun masu aikina guda biyar,saidai biyu daga cikinsu sunfi shiga raina,kuma minfi shaquwa dasu,zuwaira da kuma harira.
Muna zaune da kowa lafiya a dangin rashid,saidai bani da 'yar uwa qawa kuma aminiyar da nake jinta a raina kamar hafsat,ta daukeni kamar ciki daya muka fito da ita,kamar yadda nima na dauketa hakan.
Mun samu zama na fahimtar juna da qauna,har zuwa lokacin da rashid ya shiga siyasa bayan na haifi samir da wasu 'yan watanni,siyasar data dauke hankalinsa matuqa fiye da yadda yake a da,duk da cewa dukkan wani haqqinmu babu abinda ya sauke ko ya fasa bamu,saidai mun rage samun lokacinsa kamar da,saboda harkokinsa na siyasar da kuma kasuwancinsa da Allah ya sawa albarka yaketa habaka.
"Subhanallah" taji ta furta tana daga kanta da sauri ta saukesu ga kaltum dake riqe da qarfe window din tana kallonta.
Idanu ta zubawa kaltum din tana kallonta,karo na farko data ga wata baquwar fuska haka tsaye a gabanta,yayin da kaltum ke kallonta tana karantar tsantsar kamanni da suke sake bayyana kansu a yanzun da suke kallon juna kallo irin na qurilla,yayin da wani gefe na zuciyarta ke cike fal da mamakin ambaton subhanallah din da taji tayi.
Zuciyarta ta sake raya mata ta aikata wani abu,cikin buguwar qirji ta buda bakinta a hankali
"Samir yana gaisheki" zumbur taga ta miqe kamar wadda wani abu ya tsikara,lamarin da yayi matuqar razana kaltum,har ta dan ja da baya,saboda tana ganin kamar zata rugo da gudu ta cafketa,saidai bata qara wani motsi ba illa zuba mata idanun data sakeyi
"Muhammad samir rashid azare?" Kunnuwanta suka tsinto kalaman da suke fitowa daga bakinta a sanda take ci gaba da tsaiwar.
Ta riga da tasan cikakken sunan daddy,ta kuma tabbatar cikakken sunan samir kenan,saboda haka saita gyada kanta suna ci gaba da kallon juna.
Jikinta yayi matuqar sanyi lokacin da taga hawaye yana saukowa daga fuskar matar daya bayan daya,wani busashen murmushi yana son mamaye fuskarta
"Ke wace?" Ta sake jifanta da tambayar da batasan amsar da zata bata ba,saidai kafin ta amsa din taji takun tafiya,abinda ya sanyata waiwaya da hanxari cike da tsoro da fargaba tana duban hanya.
56
Sake maida kallonta tayi ga qofar dakin bayan ta dauke idanunta daga doguwar hanyar da har yau wanda ke tafiyar baikai ga bayyana zuwa inda take ba,ga mamakinta sai taga qofar na bude,sabanin daxu da ta ganta kamar a rufe,kafin ta kammala tunanin da zatayi taga anja qofar an bude mata,saita sauka da sauri ta sanya kai cikin dakin.
Hannunta taji an fincika,data duba sai taga matar ce,kafin ta gama tantance komai ta isa da ita bakin dan duqurqushin gadonta ta dage mata,ta gane me take nufi,don haka ta shige,ta sauke xanin gadon da ya sauka ya lullube har qasan gadon,tana iya hangenta ta tsakanin labulen ta koma ta zauna kamar yadda take daxun,wanda da zamanta da qarasowar wanda taji takun nasa duka bai wuce second biyar ba.
Yana mita ya shigo,kamar wanda yake magana da mutum me hankali
"Lalle sabi'u yana wasa da aikin nan,baisan girman aikin dana bashi ba,baisan kuma wace hajiya jidda ba,banda guntun iskanci ya za'ayi ya barwa mutane daki a bude?,salon ki fita ya jawo mana jidali?,dole nayi masa jan kunne me qarfi,idan bazai iya ba ya ajiye a bawa wani".
Abinci taga ya ajjiye mata,ya dan tsaya kadan a kanta na wasu daqiqu,ba jimawa wayarsa tayi qara,yayi hanzarin dagawa ya soma amsawa,saiya juya yana ficewa daga dakina da alama wayar da yakeyi ta shagaltar dashi bai rufe dakin ba yadda suka saba ya fice da sauri.
Kaltum dake qasan gadon gaba daya jikinta ya jiqa da gumi,gaba kura baya sayaki,gata a cikin dakin me lalurar tabin hankali,wanda har sarqa aka tanada cikin dakin,da alama ana sanyata lokaci bayan lokaci idan buqatar hakan ta taso,na biyu ta ratso ta shigo wani shinge da aka jima ana mata gargadi kan furta koda kalma daya a kanshi,yau sai gashi,bama zancan muhallin ba,ta keta duk wani gurbi ta dangana da tsakiyar shingen tsundum
"Fito,ba zasu dawo ba sai tsakiyar dare ko kuma gobe....." Taji ta furta da muryarta a sarqe kamar daxun bayan ta yaye xanin gadon.
Mamaki ya sanya kaltum ta xuba mata idanu,ta yaya take magana sak irin ta masu hankali,muryarta ras a kuma nutse?,banda yanayinta babu abinda zai sanyaka kayi tunanin ba lafiyayya bace,kamar tasan tunani da mamakin da takeyi sai ta sake jin muryarta
"Cikin hayyacina nake,kar kiji tsoron komai,fito....ina jin kece addu'ata dana jima inayi" wadannan kalaman nata su suka bata qwarin gwiwar fitowar kamar yadda ta buqata.
Zama tayi dandaryar qasa kamar yadda take daxun,saita yiwa kaltum nuni da wajen xama da hannunta,ta qaraso a hankali har yanzu da ragowar fargaba cikin ranta,saidai kuma ta samu qwarin gwiwa,ta zauna tana fuskantar kaltum din,a hankali ta buda baki
"Duk da bandan wacece ke ba,aiken jidda ce ke ko kuma ubangiji ne ya jeho min ke ki xame min haske kamar yadda na dauki tsayin shekaru ina roqa.......inason insan wacece ke" qas kaltum tayi da kanta,taga abubuwa masu tarin yawa suna kai kawo
"Ni ba kowa bace,face wata mara gata da galihu da samir ya dauko daga qauyensu,ya dawo da ita cikin gidansu,ya bata gata da galihu da kuma dukkanin kulawa"
"Samir dina?,ya zama mai tausayi da taimako kenan kamar yadda nake roqon ubangijina?" Ta fada muryarta na rawa,da alama zuciyarta fa tsinke,kuka na dab da zuwa mata kowanne lokaci.
Kai kaltum ta gyada mata tana dubanta
"Amma ya akayi kika sake dawo kanki cikin wannan hatsarin?,bayan na tabbatar zuwanki na farko qaddara tasa jidda zuwa dake?,kuma ina da yaqinin kin samu kyakkyawan jan kunne daga gareta?kinsan wacece ni ne?" Shuru tayi zuciyarta na raunana,batasan amsar da zata bata ba.
"Zuciyata ce ta kasa nutsuwa,tana ta gayamin na dawo gareki,bayaga tarin mafarkan da suka cika barcina" kai ta gyada tana kallonta,cike da yabawa da jarumtar yarinyar,tunda har tasan jidda,amma ta yadda ta fuskanci kowanne qalubale ta dawo gareta,ba tare da tasan ainihin wacece ita ba.
"Nice mahaifiyar samir.....samir dana ne" maganar data sanya kaltum ta kusa shidewa bayan ta dago da kanta,tabbas ta jima tana qiyasta haka,ta dade tana jin kamar hakane,ashe hakanne da gaske?.
Dauke idanunsa yayi daga kanta sanda take bacew ganinsa,ya sauke wata boyayyar ajiyar zuciya,idanunsa suka sauka kan amiru,sam baisan ya xuba masa ido yana kallonsa bane sai yanzu,wani qaramin murmushi amirun yayi ya dauke kansa,shima sai ya janye idanunsa,ya maida ga jauhar daketa fama da chart,amma rabin hankalinta na ga samir da takeja da hira,saiya miqe a hankali,a sannan ta daga idanunta daga kan waya tana dubansa
"Bakaci ko spoon daya bafa" kai ya girgiza yana zuba hannayensa cikin aljihun wandonsa,a daqiqun da suka dan shude lokaci kadan yana jin kamar akwai wani dan waje da zai iya koda loma biyar ne,to amma bayan barin kaltum wajen.....sai yaji kamar ta tafi da dukkan wani sauran waje daya rage da zai iya zuba abincin
"Am coming"ya fada yana takawa a nutse yana barin wajen,gaba daya hankalinsa yaji ya dauku xuwa wajen daddy,mintunan da likitocin suka bashi zasu duba daddyn yana da tabbacin kafin qarasawarsa dakin sun cika.
A nutse yake takawa zuwa cikin dakin,bayan likitoci sun kammala aikinsu,sun kuma gama masa dukkanin bayanai kan cewa akwai ci gaba a ciwon nasa,su qara haqurin fitar dashi a basu kwana uku,idan hakan yaci tura saisu daukeshin.
Duk duniya baya jin akwai wanda yakejin abinda yakeji a qirjinsa,yana jin wata muguwar kewa tare da fargaba tana shigarsa,idan ya rasa daddyn ya tabbata bashi da kowa kenan,tunda har yau baisan duniyar da MAHAIFIYAR DATA GUDU TA BARSHI TAKE BA,abinda ya kasa goguwa cikin idanunsa,yana iya tuna sanda ta fice daga gidan ta gaban idanunsa,yana kuka yana daga mata hannu,amma ko sau daya bata waiwayo ta kalleshi ba.
Runtse idanunsa yayi,a hankali ya taka zuwa gaban gadon,ya sake janyo kujerarsa da kusan kowanne lokaci take ajjiye a wajen ya zauna gaban daddyn yana ci gaba da kallonsa.
Ya jima yana karanta addu'o'i yana tofa masa saman kansa,kafin ya sanya hannunsa cikin tafin hannun daddyn ya runtse a nasa,sannan a hankali ya saukar da kansa yana kallon hannuwan nasu dake sarqafe da juna.
Motsawa kadan yaga sunyi,abinda yasashi sake qura musu idanu ba qaqqautawa,still ya sake ji da ganin sun motsa din,sai kuma ya damqe hannun nasa gaba daya,abinda ya saka samir daga kansa da hanzari kenan zuwa fuskar daddyn.
Kamar numfashinsa zai dauke saboda farinciki sanda sukayi ido hudu da daddy yana kallonsa,bakinsa ya sarqafe,ya kasa furta kowacce kalma
"Allah yayi maka albarka" yaji kalmar ta fita daga bakin daddyn,saiya sake qura masa ido yana mamakin furucin daga bakinsa,sake maimaitawa daddyn yayi,bakin samir yana rawa yace
"Am....een.....ameen daddy,sannu"saiya gyada masa kai
"Dagani na zauna" ya fada a hankali muryarsa na sarqewa
"Bari a yiwa likita magana" ya fada da sauri yana miqewa
"Fara daga nin tukunna,ba abinda zai faru da izinin Allah,akwai maganar da nakeson gaya maka kafin shigowar kowa" cikin hikima ya dagashin ya jinginar dashi,yana fatan basuyi kuskuren aikata hakan ba,saidai yana zama yadan fara haki
"Daddy....ka bari a kirasun" qaramin murmushi ya saki yana dafa kafadar samir din,cikin hakin ya sake cewa
"Nayita roqon Allah......ya bani aron......rai da lokacin da zanta ce maka......Allah.....yayi maka albarka.....na....godewa Allah da.... .ya aramin din.....,abu na biyu......banason kace komai akan ciwona.....koda kuwa akwai wani abu da kake zato......ina bala?"
Cikin mamakin kalaman daddyn yace
"Yana dakin da aka kwantar dashi,amma da gobe zasu sallameshi" sai daddyn ya gyada kai,yana son cewa wani abun amma hakin ya qara yawa,abinda ya tilastawa samir din fita da hanzari kenan,saidai wani sashe na zuciyarsa ya cika da farincikin da zai iya cewa tunda yake rayuwa a duniya bai taba jin irinsa ba.
"Ni din mahaifiya ce ga samir,yaro daya tilo nawa dake raye a duniya....haifaffiyar qasar sudan ce,birnin Khartoum,munyi auren saurayi da budurwa da rashid a lokacin da yake University of Khartoum wato U of K,bayan ya kammala karatunsa muka tattaro muka dawo qasar nan da zama bisa amincewar dangina da kuma yarda da nagartar halaye da dabi'unsa.
Muna zaune cikin lumana da rufin asiri,da amintattun masu aikina guda biyar,saidai biyu daga cikinsu sunfi shiga raina,kuma minfi shaquwa dasu,zuwaira da kuma harira.
Muna zaune da kowa lafiya a dangin rashid,saidai bani da 'yar uwa qawa kuma aminiyar da nake jinta a raina kamar hafsat,ta daukeni kamar ciki daya muka fito da ita,kamar yadda nima na dauketa hakan.
Mun samu zama na fahimtar juna da qauna,har zuwa lokacin da rashid ya shiga siyasa bayan na haifi samir da wasu 'yan watanni,siyasar data dauke hankalinsa matuqa fiye da yadda yake a da,duk da cewa dukkan wani haqqinmu babu abinda ya sauke ko ya fasa bamu,saidai mun rage samun lokacinsa kamar da,saboda harkokinsa na siyasar da kuma kasuwancinsa da Allah ya sawa albarka yaketa habaka.