Sashe 11
Dabiar Zuciya Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Saidai abu daya da baba laure ta kasa fahimta,ta kuma kasa yiwa tufkar hanci,asiya tun tana qaramarta yarinyace maras kunya,bata da kunya ko qanqani,fadace fadace kullum yinsa akeyi da ita,dambe da maza ba sabon abu bane a wajenta,babu wanda take kunya ko tsoro,manyance a wajenta abun ba'a magana,maganganu kuwa idan tayisu saika dauka.macen aurenta ne,a sannan ana ganin a bakin mahaifiyarta da bata da kintsi take jinsu,musamman idan tayi baqi suna hirarsu,tun ana kallon abun a matsayin quruciya da tunanin zata daina,harya zame mata jiki,ta girma ta tashi a haka,sannu sannu kuma sai dabi'ar kwadayi ta shigi asiyan,wanda buri da son rayuwar jin dadi....da kuma son ganin ta kerewa duk wata sa'arta cikin qauyen suka haifar mata da hakan,dalilin kenan da ya sanya ta duqufa karatunta,duk da cewa bata da wata basira ko qwaqwalwa,idan kaga yadda take sakewa da malamanta,har wani lokaci suna wasan jakai kamar qananun yara xakayi.mamaki,wannan sake musun da takeyi ya sanya ko yaushe ita ce ke zuwa ta daya a ajinsu,don haka ma,saiya zamana bata wani damu da karatun ba,tunda zata zo ta daya,zata nunawa babarta,ita kuwa tayita tiqar rawa tana murna tare da yada habaici,shikenan tana ganin babu wani sauran damuwa,takanje makarantar sanda ta gama yawonta da xuwa duk inda zata,wanda kusan rabi amsar kudi ne daga hannun samari,wadanda saisun gama wasan banxa kamar wani miji da mata sannan su bata.
Ko sau daya baba laure bata taba damuwa da ganin gilmawar kudi a hannun asiya ba,bayan ta sani cewa....ba ita ta bata ba,ba mahaifinta ne ya bata ba,tunda dukkaninsu basu dashi,ba wata sanaa suke ko takeyi ba,amma sam hakan ba damuwarta bane,musamman idan ta tashi buqatar kudi,asiyan zata ranta mata,kota bata kyauta.
A hankali baba lauren ta fahimta samari ne ke yiwa 'yarta hidima,a maimakon shiga tashin hankali a matsayinta na uwa,tsaurara bincike da yanke duk wata alaqa,saita hau murna,ranar kamar zata taka kan shege,ta yiwa yarta kirari a filin tsakar gidan nasu
"Kaga diyar da ba'a haifi kamarta ba kaf fadin qauyen ƊINYA,yarinya mai farinjini tamkar daren sallah,ah....ashe nidai na haifi mai sharen min hawayena ban sani ba,daa na qwallafa raina akan wadancan sakarkarun su muxammilu,wadanda saisunga dama zasu waiwayo gida su bani abinda sukaga dama,Allah ya karemin ke,ya tsole idanun maqiya" dukka wadan nan maganganun ta yisu ne sanda asiyan ta miqa mata danƙwaleliyar gasashshiyar kaza sukutum da guda,da sassanyar fanta,dukkan maganganunta kuma da umma take,wadda ta fito tana kwashe shanyar kayansu da habiba ta manta bata kwashe ba.
Bata ce komai ba sai data gama ta kaisu sassansu sannan ta dawo inda baba laure take,ta yanke gaya mata gaskiya ne saboda girman zumunci da zaman tare,sannan ko banza JININ YARANSU DAYA,ko banza basu isa su cire jinin su asiya daga nasu bilal ba,har abada duniya ba zata daina kiransu da sunan 'YAN UWA BA!,ba tun yau ba,tasha jin gulmammaki akan asiyan da irin abubuwan da takeyi,sai Allah ya nuna mata sau biyu itama,amma bata taba tunkarar baba lauren ba,a tunaninta na kada ta daga mata hankali,tana shawarar kiran asiyan tayi.mata fada sai kuma akayi haka.
Fara nade ledarta tayi ganin tahowar umman,duk da ta sani cewa ita din sam ba makwadaiciya bace,hasalima tana cika da mamakin yadda take da haquri da kuma wadatar zuci,duk da bata da komai,hakanan mijinta baya kula da ita,amma hakan bai sauya dabi'a ko halayyarta ba
"Laure,ni a nawa tunanin,wannan abun da kikayi bashi ya kamata kiyi ba,ke uwace mace,wanda tasan ciwon yaranta,ya kamata ki fara sanin dawa dawa asiya ke tare dasu?,meye alaqar dake tsakaninsu?,idan aurenta suke da niyyar yi....."
"Dakata zuwaira" baba lauren ta tsaidata
"Babu alaqar dake tsakaninsu saita alkhairi,yarinyata kintsatsiya ce,kuma na yarda da tarbiyyarta,don haka kada.kizo min da wani qabli da ba'adi,farinjinin samari ne dai kawai da Allah ya bata,kuma koni ban isa na dakushe ba" saita kwashe kayanta tayi sassanta tana mita,zucuyarta baqiqqirin,kawai gani take babu wani babu wata,baqinciki zuwaira take tsagoransa,tunda ita kaltum kusan duk wanda yazo tafiya yake,habiba kuma a sannan bata tsaiwa da kowa,don tana ganin tayi quruciya,duk da cewa a qauye suke,amma ita tarbiyya idan za'a bada ita,babu alfanun duba yanayin muhalli,a bada ita kawai yadda ya dace,wannan shine abinda ke wakana a tsakaninsu da kalar halayyar asiya da.mahaifiyarta,wanda sannu a hankali abunda asiyan takeyi yake bunqasa ba tare da sanin lauren ba,tunda tun a karon farko taga goyon baya qarara daga mahaifiyartata,babu bincike ko.matsantawa cikin lamuranta,kudi takeso.....kuma tana kawo mata su,shikenan an wuce wajen 👌🏽👌🏽👌🏽👌🏽👌🏽.
"Ke 'yar baqa dake nake" baba lauren ta sake fada cikin daga murya,sai kaltum ta dakata,ta waiwayo tana duban baban,ko kafin lauren ta sake samun sukunun yin magana saita jiyo sautin bilal tun daga zaurensu,hakan yaja hankalinta zuwa zauren da hanzari ba tare data sake sauraren lauren ba.
Tabbas bilal ne,ya shigo futu futu dashi kamar wanda aka turbuda a qasa,yana dingisawa yayin da hawaye ke wanke masa fuska.
A rude ta nufeshi ta kama kafadunsa tana kallonsa
"Kai bilal?,meye haka?,lafiya me ya sameka?" Muryarsa a dakushe ya soma magana da qyar
"Su musbahu ne,mun gama aiki an biyamu kudinmu,shine suka ce wai ba zasu raba dani ba,ni kuma nace saboda me,wallahi saisun bani kudina tunda haqqina ne,shine suka taru suka yimin duka,kuma don nace zan tona musu asiri ne,muna kwabin qasa suka kwashe kayan aikin suka boye,wai idan muka gama aikin zasu je su siyar su qara samun yawan kudin aikin" sosai ran kaltum ya baci,ba wanannan ne karon farko da suka fara dukan bilal ba,bama su ba,wasu mutanen da yawa cikin qauyen,saboda suna ganin kamar bashi da wani gata ko galihu,bata iya tanka masa da komai ba ta kamashi suka koma cikin gidan,tana jin baba laure tana dariya
"Oh...aikin qwadago badai wuya ba,toh...mudai namu rabon yana jikin biro da takarda in sha Allahu,daga me yawon qwadago sai me gawon kitse sumar jama'a,suma dake cike da datti da annakiya,kai....itadai zuwaira bata iya haihuwa ba....hhhhhh" ta qarashe da dariyar dake nuna cikar nishadi da farinciki.
Har tasa qafa sashensu saita tsaya cak saboda kalaman da kunnenta suka dauko mata,uwa uba dariya ta biyo baya daga bakin lauren da baquwarta abu,wadda kusan kome ke wanzuwa na samun goyon baya da asiya tayi da shawarar zainabun ce,wadda a kullum ita ke nunwa baba laure 'yarta me sa'a ce,ta barta,kada ta toshe musu kafar samu,duk maganar da mutane zasuyi zallar baqinciki ne,abun ke dorasu akan komai.
Kaltum din zata iya jurewa komai amma banda taba qima da mutuncin mahaifiyarta,taba qimar mahaifiyarta shine abu na qarshe da mutum zai mata,koda kuwa shi waye,don haka saita saki bilal,ta dawo da baya,yayin da laure ta zuba mata idanu zuciyarta cike fal da taraddadin kada kaltum din ta yarfata,tunda tafi kowa sanin halinta kan mahaifiyarta.
Bata tsaya ba kuwa sai data isa gabansu,idanunta cikin na baba lauren ta maida mata amsar data tashi hankalin baba laure
"Ummata itace kuwa ta iya haihuwa,tunda ta haifi tsaftatattun 'ya'ya,babu me yawon bin maza.....babu kuma wanda ta bazama duniyar qabilu da arna neman abun duniya,yaranta na killace gabanta tana qoqarin basu tarbiyya da kulawa,duk da tsananun babunta,don haka babu haihuwar datafi wannan sa'a" saita juya abinta,tana sake dannar zuciyarta,saboda tana jin amsar data bayar dinma kamar bata isa ba,kamar bata isa ta wanke mata hucin da zuciyarta ke fitarwa ba.
06
*Kiji tsoron Allah☝🏽,karka/karki taba haqqin wasu,saboda akwai ranar biya,randa baka da abun biyan🤌🏾*
*KI TUNTUBA WADAN NAN NUMBERS DIN DON SAMUN DAMAR KARANTA NAKI HANKALI KWANCE*
08184017082
KO KUMA
09134848107
____________________________
_ASSALAMU ALAIKUM BEAUTIFUL PEOPLE!! ZAFAFA BIYAR FAMILY💯💯🙌🏽❤️_
_MUNGODE DA ZABIN LITTAFAN ZAFAFA BIYAR. ALLAH YA KARA BUDI YA KUMA BAR ZUMUNCI_
_KAMAR KO DA YAUSHE, WANNAN KARON MA MUNZO DA KOKON BARAR YOUTUBE CHANNEL DIN YARON MU, SUDEIS MASOYI KUMA MAKARANCI, MAHADDACIN ALKUR’ANI MA GIRMA_
_WANNAN KARON MA DAN ALLAH A TEMAKA ADANNA WA CHANNEL DINSA KARARRWA DOMIN KASANCEWA DA MU A DUK SANDA MUKA DORA FEFAN BIDIYON SA, A TALLAFA A KALLA A KUMA DANNA MASA SUBSCRIPTION. HAKAN NA KARAWA SUDEIS KWARIN GWIWAR SAKE DAGEWA YA KUMA KARA KAIMI WAJEN YIN KARATUN SOSAI. MUNGODE KWARAI💯🙌🏽❤️_
_GA CHANNEL DIN DAKE YOUTUBE NAN👇🏾_
https://youtube.com/c/sudaiskura
_Sudais is a young boy who has passion in recitation of the Holy Qur'an at a very young age._
_Please help him grow his YouTube channel by subscribing and liking his videos to encourage the little boy. Jazakumullahu khairan🙏🏻_
______________________________
"Kambu" ta furta da qarfi,wani irin zabura baba laure tayi ta durfafi kaltum dake niyyar shigewa sashensu,kafin ta ankara harta shaqo wuyanta ta fisgota baya
"Ni kike zagi don u****rki kaltume?" Ta fada cikin hargowa da daga murya
"Kibar zagarmin uwa baba"
"An zagetan....ko zaki rama mata ne 'ya'yan kuka?" Ta sake fadi hannunta riqe da bayan hijabin kaltum,wanda tuni ya feke sanadiyyar fisgotan da tayi,dubanta take ranta na sake baci,yana kuma raya mata abubuwa da yawa akan baba lauren,batason tayi rashin kunya,kota aikata abinda zai sanya ran ummanta ya baci....kafin tayi tunani na gaba ruwan ashar ya fara fitowa daga bakin lauren,wanda ya sanya umma fitowa daga daki kusan a tare ita da habiba bayan sun saki aikin da sukeyi.
Abinda ta gani din ya bata mamaki,laure riqe da hijabin kaltum tana dura mata ashariya,abu na tsaye abinta tana kallonsu hankalinta kwance.
Ko sau daya baba laure bata taba damuwa da ganin gilmawar kudi a hannun asiya ba,bayan ta sani cewa....ba ita ta bata ba,ba mahaifinta ne ya bata ba,tunda dukkaninsu basu dashi,ba wata sanaa suke ko takeyi ba,amma sam hakan ba damuwarta bane,musamman idan ta tashi buqatar kudi,asiyan zata ranta mata,kota bata kyauta.
A hankali baba lauren ta fahimta samari ne ke yiwa 'yarta hidima,a maimakon shiga tashin hankali a matsayinta na uwa,tsaurara bincike da yanke duk wata alaqa,saita hau murna,ranar kamar zata taka kan shege,ta yiwa yarta kirari a filin tsakar gidan nasu
"Kaga diyar da ba'a haifi kamarta ba kaf fadin qauyen ƊINYA,yarinya mai farinjini tamkar daren sallah,ah....ashe nidai na haifi mai sharen min hawayena ban sani ba,daa na qwallafa raina akan wadancan sakarkarun su muxammilu,wadanda saisunga dama zasu waiwayo gida su bani abinda sukaga dama,Allah ya karemin ke,ya tsole idanun maqiya" dukka wadan nan maganganun ta yisu ne sanda asiyan ta miqa mata danƙwaleliyar gasashshiyar kaza sukutum da guda,da sassanyar fanta,dukkan maganganunta kuma da umma take,wadda ta fito tana kwashe shanyar kayansu da habiba ta manta bata kwashe ba.
Bata ce komai ba sai data gama ta kaisu sassansu sannan ta dawo inda baba laure take,ta yanke gaya mata gaskiya ne saboda girman zumunci da zaman tare,sannan ko banza JININ YARANSU DAYA,ko banza basu isa su cire jinin su asiya daga nasu bilal ba,har abada duniya ba zata daina kiransu da sunan 'YAN UWA BA!,ba tun yau ba,tasha jin gulmammaki akan asiyan da irin abubuwan da takeyi,sai Allah ya nuna mata sau biyu itama,amma bata taba tunkarar baba lauren ba,a tunaninta na kada ta daga mata hankali,tana shawarar kiran asiyan tayi.mata fada sai kuma akayi haka.
Fara nade ledarta tayi ganin tahowar umman,duk da ta sani cewa ita din sam ba makwadaiciya bace,hasalima tana cika da mamakin yadda take da haquri da kuma wadatar zuci,duk da bata da komai,hakanan mijinta baya kula da ita,amma hakan bai sauya dabi'a ko halayyarta ba
"Laure,ni a nawa tunanin,wannan abun da kikayi bashi ya kamata kiyi ba,ke uwace mace,wanda tasan ciwon yaranta,ya kamata ki fara sanin dawa dawa asiya ke tare dasu?,meye alaqar dake tsakaninsu?,idan aurenta suke da niyyar yi....."
"Dakata zuwaira" baba lauren ta tsaidata
"Babu alaqar dake tsakaninsu saita alkhairi,yarinyata kintsatsiya ce,kuma na yarda da tarbiyyarta,don haka kada.kizo min da wani qabli da ba'adi,farinjinin samari ne dai kawai da Allah ya bata,kuma koni ban isa na dakushe ba" saita kwashe kayanta tayi sassanta tana mita,zucuyarta baqiqqirin,kawai gani take babu wani babu wata,baqinciki zuwaira take tsagoransa,tunda ita kaltum kusan duk wanda yazo tafiya yake,habiba kuma a sannan bata tsaiwa da kowa,don tana ganin tayi quruciya,duk da cewa a qauye suke,amma ita tarbiyya idan za'a bada ita,babu alfanun duba yanayin muhalli,a bada ita kawai yadda ya dace,wannan shine abinda ke wakana a tsakaninsu da kalar halayyar asiya da.mahaifiyarta,wanda sannu a hankali abunda asiyan takeyi yake bunqasa ba tare da sanin lauren ba,tunda tun a karon farko taga goyon baya qarara daga mahaifiyartata,babu bincike ko.matsantawa cikin lamuranta,kudi takeso.....kuma tana kawo mata su,shikenan an wuce wajen 👌🏽👌🏽👌🏽👌🏽👌🏽.
"Ke 'yar baqa dake nake" baba lauren ta sake fada cikin daga murya,sai kaltum ta dakata,ta waiwayo tana duban baban,ko kafin lauren ta sake samun sukunun yin magana saita jiyo sautin bilal tun daga zaurensu,hakan yaja hankalinta zuwa zauren da hanzari ba tare data sake sauraren lauren ba.
Tabbas bilal ne,ya shigo futu futu dashi kamar wanda aka turbuda a qasa,yana dingisawa yayin da hawaye ke wanke masa fuska.
A rude ta nufeshi ta kama kafadunsa tana kallonsa
"Kai bilal?,meye haka?,lafiya me ya sameka?" Muryarsa a dakushe ya soma magana da qyar
"Su musbahu ne,mun gama aiki an biyamu kudinmu,shine suka ce wai ba zasu raba dani ba,ni kuma nace saboda me,wallahi saisun bani kudina tunda haqqina ne,shine suka taru suka yimin duka,kuma don nace zan tona musu asiri ne,muna kwabin qasa suka kwashe kayan aikin suka boye,wai idan muka gama aikin zasu je su siyar su qara samun yawan kudin aikin" sosai ran kaltum ya baci,ba wanannan ne karon farko da suka fara dukan bilal ba,bama su ba,wasu mutanen da yawa cikin qauyen,saboda suna ganin kamar bashi da wani gata ko galihu,bata iya tanka masa da komai ba ta kamashi suka koma cikin gidan,tana jin baba laure tana dariya
"Oh...aikin qwadago badai wuya ba,toh...mudai namu rabon yana jikin biro da takarda in sha Allahu,daga me yawon qwadago sai me gawon kitse sumar jama'a,suma dake cike da datti da annakiya,kai....itadai zuwaira bata iya haihuwa ba....hhhhhh" ta qarashe da dariyar dake nuna cikar nishadi da farinciki.
Har tasa qafa sashensu saita tsaya cak saboda kalaman da kunnenta suka dauko mata,uwa uba dariya ta biyo baya daga bakin lauren da baquwarta abu,wadda kusan kome ke wanzuwa na samun goyon baya da asiya tayi da shawarar zainabun ce,wadda a kullum ita ke nunwa baba laure 'yarta me sa'a ce,ta barta,kada ta toshe musu kafar samu,duk maganar da mutane zasuyi zallar baqinciki ne,abun ke dorasu akan komai.
Kaltum din zata iya jurewa komai amma banda taba qima da mutuncin mahaifiyarta,taba qimar mahaifiyarta shine abu na qarshe da mutum zai mata,koda kuwa shi waye,don haka saita saki bilal,ta dawo da baya,yayin da laure ta zuba mata idanu zuciyarta cike fal da taraddadin kada kaltum din ta yarfata,tunda tafi kowa sanin halinta kan mahaifiyarta.
Bata tsaya ba kuwa sai data isa gabansu,idanunta cikin na baba lauren ta maida mata amsar data tashi hankalin baba laure
"Ummata itace kuwa ta iya haihuwa,tunda ta haifi tsaftatattun 'ya'ya,babu me yawon bin maza.....babu kuma wanda ta bazama duniyar qabilu da arna neman abun duniya,yaranta na killace gabanta tana qoqarin basu tarbiyya da kulawa,duk da tsananun babunta,don haka babu haihuwar datafi wannan sa'a" saita juya abinta,tana sake dannar zuciyarta,saboda tana jin amsar data bayar dinma kamar bata isa ba,kamar bata isa ta wanke mata hucin da zuciyarta ke fitarwa ba.
06
*Kiji tsoron Allah☝🏽,karka/karki taba haqqin wasu,saboda akwai ranar biya,randa baka da abun biyan🤌🏾*
*KI TUNTUBA WADAN NAN NUMBERS DIN DON SAMUN DAMAR KARANTA NAKI HANKALI KWANCE*
08184017082
KO KUMA
09134848107
____________________________
_ASSALAMU ALAIKUM BEAUTIFUL PEOPLE!! ZAFAFA BIYAR FAMILY💯💯🙌🏽❤️_
_MUNGODE DA ZABIN LITTAFAN ZAFAFA BIYAR. ALLAH YA KARA BUDI YA KUMA BAR ZUMUNCI_
_KAMAR KO DA YAUSHE, WANNAN KARON MA MUNZO DA KOKON BARAR YOUTUBE CHANNEL DIN YARON MU, SUDEIS MASOYI KUMA MAKARANCI, MAHADDACIN ALKUR’ANI MA GIRMA_
_WANNAN KARON MA DAN ALLAH A TEMAKA ADANNA WA CHANNEL DINSA KARARRWA DOMIN KASANCEWA DA MU A DUK SANDA MUKA DORA FEFAN BIDIYON SA, A TALLAFA A KALLA A KUMA DANNA MASA SUBSCRIPTION. HAKAN NA KARAWA SUDEIS KWARIN GWIWAR SAKE DAGEWA YA KUMA KARA KAIMI WAJEN YIN KARATUN SOSAI. MUNGODE KWARAI💯🙌🏽❤️_
_GA CHANNEL DIN DAKE YOUTUBE NAN👇🏾_
https://youtube.com/c/sudaiskura
_Sudais is a young boy who has passion in recitation of the Holy Qur'an at a very young age._
_Please help him grow his YouTube channel by subscribing and liking his videos to encourage the little boy. Jazakumullahu khairan🙏🏻_
______________________________
"Kambu" ta furta da qarfi,wani irin zabura baba laure tayi ta durfafi kaltum dake niyyar shigewa sashensu,kafin ta ankara harta shaqo wuyanta ta fisgota baya
"Ni kike zagi don u****rki kaltume?" Ta fada cikin hargowa da daga murya
"Kibar zagarmin uwa baba"
"An zagetan....ko zaki rama mata ne 'ya'yan kuka?" Ta sake fadi hannunta riqe da bayan hijabin kaltum,wanda tuni ya feke sanadiyyar fisgotan da tayi,dubanta take ranta na sake baci,yana kuma raya mata abubuwa da yawa akan baba lauren,batason tayi rashin kunya,kota aikata abinda zai sanya ran ummanta ya baci....kafin tayi tunani na gaba ruwan ashar ya fara fitowa daga bakin lauren,wanda ya sanya umma fitowa daga daki kusan a tare ita da habiba bayan sun saki aikin da sukeyi.
Abinda ta gani din ya bata mamaki,laure riqe da hijabin kaltum tana dura mata ashariya,abu na tsaye abinta tana kallonsu hankalinta kwance.