Sashe 91
Dabiar Zuciya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Na gamsu da dukka bayanai da hujjojinki,kuma a wannan karon ina ji a jikina zan aiwatar da tunaninki,muga kalar naki takun" kalaman da suka sanya fitar murmushi daga fuskarta hajiya shuwa,ta daga hannu tana jinjinawa mummy.
.
"Ya na ganki ke kadai?,Ina kaltum din?" Hajiya qarama ta tambayi jawahir wadda take fidda kayan jikinta da suka jiqe da ruwan sama.
Tsaiwa tayi da cire kayan,ta ta waiwayo ta dubi hajiya qarama
"Sun rigamu fitowa fa,basu iso ba kenan?"
"Nidai babu wanda na gani a cikinsu"
"Ok,bari na gama na kira ya sarakin" ta fadi tana dauko kayan da zata sauya din masu dan kauri saboda sanyin ruwan da ya ratsata,sai data gama shiryawa sannan ta zauna ta soma kiransa.
Tana shiga amma ba'a dagawa,already ya sanyata a silent ne,kaltum dake duqunqune cikin bargo tana sheqar lallausan qamshin turarensa daya kama kayansa tana iya hango hasken wayar saboda a saman kanta take a ajjiiye,saidai batason yin magana kwata kwata,tafison ya dauka tayi baccin ne kamar yadda ga zata,tun sanda ya bata rigarsa ta sanya kunya da nauyi suka cikata,saboda barin nata kayan da yayi cikin mota.
Shafa addu'arsa yayi a hankali,sannan yaja bargon daya dora saman dogayen qafafunsa ya dawo zuwa qugunsa,sannan ya zame a hankali ya kwanta a hannunsa na dama.
A hankali ya lumshe idanunsa kana ya budesu,idanunsa suka sauka a bayanta,duk da cewa baya iya hango komai na jikinta sai bargon data duqunquna har kanta da shi.
Wani numfashi mai nauyi ya sauke,yanayi irin wannan yana saukar masa da feelings sosai tun ba yanzu ba,qamshin qasa hade da sassanyar iskar damina ta dare,saiya sanya hannayensa tsakiyar gwiwoyinsa kamar maijin sanyi,haka kawai kasancewarta kusa dashi ke neman dagula lissafinsa,tsahon rayuwarsa wannan shine karo na farko daya taba hada makwanci da diya mace,yaso ya barta ta kwana a qasa kamar yadda ta zaba,saidai kuma yaga hakan bai dace ba,duba da sanyin ruwan dake sauka,ga kuma tiles da ya yiwa dakin qawanya.
Hasken wayar ya hango,wanda ya bayyana bayan walqawar walqiya a sararin samaniya,walqiyar data sanya kaltum runtse ido sosai da kuma curewa waje guda tana addu'a qasan ranta,kan Allah yasa ba tsawa za'a saki ba.
Hannu ya miqa ta saman kanta zai janyo wayar,dai dai sanda qarar tartsatsin walqiya mai qarfi ya baje a fadin duniya ya sauka zuwa kunnen kowanne abu me rai dake sararin subhana.
"Alhamdulillahil lazi yusabbihur ra'adu bi hamdih,wal mala'ikatu min khifatihi" saraki ya fada a hankali yana dan runtse ido saboda qarar tsawar,sannan ya bude idanun nasa a hankali ya sauke a kanta.
Baiyi tsammanin cewa batayi bacci ba saida aka saki tsawar yaji yanda ta firgita,har kuma bayan shudewr tsawar yana iya jin yadda ta sake tattarewa waje daya,bai fasa dauko wayar ba,ya budeta ya shiga app din karatun qur'ani,qira'ar shaik abdur rahmani assudais,ya kunna suratul baqra,ya sanya volume dinta saisa saisa (indai har zaki iya kwana da waya saman kanki bayan kin gama danne dannenki,to yana da kyau ki koyi sanya karatun qur'ani cikin dakinki sanda zaki kwanta bacci,cikin qaramin volume ba mai yawa ba,hakan yana taimakawa wajen yin bacci me dadi mai kuma cike da nutsuwa,uwa uba ga tsaro da zaya baki daga dukkan sharri,koda bunu chargy indai akwai wuta,jonata a socket,ki kunna qur'anin,yana playing tana chargy,zaki mamakin yadda wayarki zata cika da wuri,ga kuma qur'anin yana yi har safiya,koda chargynki ya kusa qarewa kika kunna,wani hukuncin Allah wayar bata mutuwa,tana kaiwa har safiya yanayi,Allah ya bamu albarkacin qur'ani mai girma,alfarmar shugaba S A W👏🏽👏🏽).
Saman kansu ya sanya wayar,ya raba a hankali zuwa bayanta ya kwantar da jikinsa,idanunta ta lumshe gaba daya zuciyarta ta soma gudu yadda ta saba a duk sanda ya rabota....lokacin data jishi cikin bargon da take,hannunsa saman ruwan cikinta,muryarsa can qasa kamar meyin rada yana cewa
"You are safe..... good night" cikin son yin aiki da maganarsa ta rufe idonta a hankali tana sauke numfashi,dumin kowanne na ratsa dan uwansa yana haifar masa da wani yanayi na daban.........
_to sai ince asuba ta gari kalsam_
53
DZ
"Ina hanya,yanzu zamu iso,koma meye idan nazo ka tambaya" abunda ya fada kenan sanda yake jingine da motarsa a farfajiyar gidan saukar baqin,saiya latse wayar kawai sanda yaji amirun nason masa cari,ya soma sanya wayar a aljihun wandon shaddarsa,lokaci guda kuma yana daga kansa.
A kanta idanunsa suka sauka,tana sanya da atamfa riga da zani,sai mayafi wanda yayi matuqar dacewa da kayan jikinta.
Kyakkyawar kalar fatarta ta haska tarwai cikin kalolin kayan jkinta,kwantaccen gashinta me santsi ya fiti ta gefe da gefan kunnenta,da kuma qeyarta inda ta nadeshi kamar alkaki.
Baisan sanda ajiyar zuciya ta kubce masa ba,yana tuna yadda hannunsa ya dinga yawo a jikinta daren jiya cikin mafarkinsa,wani abu ya tsarga masa sanda ta daga fararen idanunta suka sauka akansa,saiya sanya hannayensa duka cikin aljihun wandonsa yana qyara tsaiwarshi da kyau.
Faduwar gaba taji sosai,karon farko data ganshi da shigar da bata taba ganinsa da ita ba,shigar shadda fara sol sai maiqo da walqiya takeyi,wadda akayi mata aikin zare baqi,takalmi sau ciki wanda shima yake nashi kalar qyallin,hannunsa sanye da Rolex me asalin tsadan,sumar kanshi wadda bata da wani yawa sai sheqi takeyi saboda hularshi dake aje saman motar bai sanya ba.
Hardewa taji ta fara yi saboda takalman qafarta masu dan tsinin dunduniya da sukayi mata kyau suka kuma sake qawata kwalliyarta.
Tana dab da isowa inda yake ya sanya hannunsa saman motar ya.janyo hularsa ya aza a kansa,har a sannan bai fasa kallonta ba.
"Kinyi kyau" kalmar data subuce masa a bakinsa kamar fitar kibiya,hakan ya qara aza mata nauyinsa.
A hankali ya kutsa da motar cikin layin gidan ya dikko,duk kuwa da saurin da ya dinga yi amma hakan baisa ya iso a sanda yaso ba,saboda wani laziness da yakeji a jikinsa gaba daya,a hankali ya dannan wani madanni dake gefansa ya dage dukka gilasan motar sama sanda yake yiwa motar gun tsaiwa,hannu tasa zata bude motar
"Wait" taji ya fada,hakan yasa ta tsaya din kamar yadda ya buqata,ta qagauta ne su raba jaha,don ita kadai tasan wanne yanayi take riskar kanta a ciki duk sanda suka kadaice irin haka,wani mugun nauyi da kunyarsa takeji fiye da kowanne lokaci.
Wayarsa ya ciro ya dannan numbers din jawahir, ringing biyu ta daga,zata barke masa da surutun nan nata ya dakatar da ita,yace ta fito ya sameshi a waje,sannan ya aje wayar .
Daga nesa ya hangi fitowarta,tayi duru duru tana nemansu,saiya dan danna mata horn sannan ya bude motar ya fita,dai dai nan ta iso,saiya dan saka kansa kadan yace da kaltum din ta fito.
"Wai a ina kuka kwana kaltum?" Ta tambayi kaltum din cikin mamaki da kokwanto,saidai kafin tace komai samir din ya tsaidata
"Ba'a sani ba tambaya,ku wuce muje" bata qara tambayar ba,saidai tana mata susa a rai,tare da tambayar kanta inda sukaje suka kwana,kuma su biyu,ba muharraman juna ba,duk da cewa ta yarda da hali da dabi'ar yayan nata,dama ta kaltum din.
Suna gaba yana biye dasu a baya,duk da jama'a na tsaidashi suna gaisawa,duk inda ya wulga sai ya dauki hankalin jama'a,farinji da kwarjini gareshi,uwa uba yadda yake kyautatawa al'umma ya siya masa soyayyar jama'a me yawan gaske,a haka suka isa babban falon yadikko,wanda yalwar gidan da wadatar guraren zama ya sanya babu yawaitar mutane,kusan suna dakuna......
"A ina kika samo wannan beb din......ban santa ba a cikin danginmu" daya daga cikin samarin dake xaune a falon ya fada,abinda kuma kunnuwan samir suka jiye masa sanda yake shigowa,idonsa ya sauka kan yaron wanda ake kira da muntasir.
Sallamarsa yasa maganar da yake shirin yi ta yanke,duka suka waiwaya,sannan suka miqe cikin nuna girmamawa suna masa sannu da zuwa kafin su fara gaidashi.
Fuskarsa a hade tsam ya kalli jawahir
"Ina mummy?"
"A gidan haj shuwa ta kwana,amma munyi waya tace min ta taho,duk yadda akayi ta kusan qarasowa" ido ya lumshe kana ya bude cikin sakannin da basu wuce biyu ba,haka kawai cikin zuciyarsa jininsa baya son matar,kuma bazai iya tuna wani laifi data taba yi masa ba,koda na kallon banza kuwa
"Ki rakata wajen hajiya qarama"
"To" ta amsa masa tana yin gaba,kaltum tabi bayanta,saiya tsinci kansa da rakasu da ido.
Muntasir ya tabo dan uwansa
"Kaga guy din nan,ashe shima ya iya kallon mata?" Boyayyar dariyar ciki ya sake
"Waye baison mace dama?,aisu sunfi qarfin zuciya da qwaqwalwar kowa,saidai idan bai samu ba,bare wannan....ta wanku fa,kalar fatarta ta musammance wlh,ga wani kyau mai sanyi alaji,wanda saita matsoka kake ganinsa",dif sukayi sanda ya waiwayo ya dubesu,don kalamansu na qarshe sun shiga kunnensa,baisan me yake taba zuciyarsa ba duk sanda sukayi magana irin wanann,dukansu ba sa'ansa a cikinsu,don haka ya miqe ya nufi bangaren dakin ya dikko don su gaisa,tun kafin daddy ya qaraso yaji basu gaisa din ba.
Fara'a fal fuskar hajiya qarama,farincikin ganin kaltum ya bayyana sosai
"Lale maraba da diyata,ina nan inata kewarki,dama yanzu nake shirin kiran saraki naji can gidan abokin nasa zaku yita zama ne?,sai amirun yacemin matar abokince bata jin dadi sosai,kin dan tsaya kin taimaka mata ta kintsa gidan" itadai murmushi kawai take,kanta a qasa tana jinjina yadda amiru ya iya tsara irin wannan qaryar,duk da tayi mata dai dai,don bata da kowacce amsa da xata bata.
"bari naje mu qarasa packaging abincin 'yan daurin aure.....ina zuwa kaltum" ta fada tana juyawa gami da ficewa daga dakin,zuciyarta dai na tantamar labarin da amiru ya bawa haj qaraman kan rashin kwanansu gida,tunda a gabanta ne yake neman shima inda suka shiga,ture batun tayi,sabida batason baiwa shaidan qofa akansu,ta yarda da kowa a cikinsu.
Sai data zauna sosai sannan ta daga kai da niyyar gaida hajiya qarama,saidai gaisuwar taso.maqale mata a maqogaro,saboda sauka da idanunta sukayi kan wani hoto dake maqale a bangon dakin da yake tamkar na hajiya qaraman,saboda duk sanda tafiya ta kawosu azare a nan take sauka,idan zata tafi kuma ta rufe ta bawa ya dikko maqullin.
Hoto ne dauke da taswirar fuskar matar dake a jikin hoton data taho dashi zuwa azare,wanda tayi masa duban duniya amma ta rasa inda ta yada shi,gabansa kadan wani hoton ne irinsa,tana sanye da atamfa da akayi mata riga da xani,ta yane jikinta da mayafin atamfar,wadda ta haskata ta kuma fidda kyanta sosai.
.
"Ya na ganki ke kadai?,Ina kaltum din?" Hajiya qarama ta tambayi jawahir wadda take fidda kayan jikinta da suka jiqe da ruwan sama.
Tsaiwa tayi da cire kayan,ta ta waiwayo ta dubi hajiya qarama
"Sun rigamu fitowa fa,basu iso ba kenan?"
"Nidai babu wanda na gani a cikinsu"
"Ok,bari na gama na kira ya sarakin" ta fadi tana dauko kayan da zata sauya din masu dan kauri saboda sanyin ruwan da ya ratsata,sai data gama shiryawa sannan ta zauna ta soma kiransa.
Tana shiga amma ba'a dagawa,already ya sanyata a silent ne,kaltum dake duqunqune cikin bargo tana sheqar lallausan qamshin turarensa daya kama kayansa tana iya hango hasken wayar saboda a saman kanta take a ajjiiye,saidai batason yin magana kwata kwata,tafison ya dauka tayi baccin ne kamar yadda ga zata,tun sanda ya bata rigarsa ta sanya kunya da nauyi suka cikata,saboda barin nata kayan da yayi cikin mota.
Shafa addu'arsa yayi a hankali,sannan yaja bargon daya dora saman dogayen qafafunsa ya dawo zuwa qugunsa,sannan ya zame a hankali ya kwanta a hannunsa na dama.
A hankali ya lumshe idanunsa kana ya budesu,idanunsa suka sauka a bayanta,duk da cewa baya iya hango komai na jikinta sai bargon data duqunquna har kanta da shi.
Wani numfashi mai nauyi ya sauke,yanayi irin wannan yana saukar masa da feelings sosai tun ba yanzu ba,qamshin qasa hade da sassanyar iskar damina ta dare,saiya sanya hannayensa tsakiyar gwiwoyinsa kamar maijin sanyi,haka kawai kasancewarta kusa dashi ke neman dagula lissafinsa,tsahon rayuwarsa wannan shine karo na farko daya taba hada makwanci da diya mace,yaso ya barta ta kwana a qasa kamar yadda ta zaba,saidai kuma yaga hakan bai dace ba,duba da sanyin ruwan dake sauka,ga kuma tiles da ya yiwa dakin qawanya.
Hasken wayar ya hango,wanda ya bayyana bayan walqawar walqiya a sararin samaniya,walqiyar data sanya kaltum runtse ido sosai da kuma curewa waje guda tana addu'a qasan ranta,kan Allah yasa ba tsawa za'a saki ba.
Hannu ya miqa ta saman kanta zai janyo wayar,dai dai sanda qarar tartsatsin walqiya mai qarfi ya baje a fadin duniya ya sauka zuwa kunnen kowanne abu me rai dake sararin subhana.
"Alhamdulillahil lazi yusabbihur ra'adu bi hamdih,wal mala'ikatu min khifatihi" saraki ya fada a hankali yana dan runtse ido saboda qarar tsawar,sannan ya bude idanun nasa a hankali ya sauke a kanta.
Baiyi tsammanin cewa batayi bacci ba saida aka saki tsawar yaji yanda ta firgita,har kuma bayan shudewr tsawar yana iya jin yadda ta sake tattarewa waje daya,bai fasa dauko wayar ba,ya budeta ya shiga app din karatun qur'ani,qira'ar shaik abdur rahmani assudais,ya kunna suratul baqra,ya sanya volume dinta saisa saisa (indai har zaki iya kwana da waya saman kanki bayan kin gama danne dannenki,to yana da kyau ki koyi sanya karatun qur'ani cikin dakinki sanda zaki kwanta bacci,cikin qaramin volume ba mai yawa ba,hakan yana taimakawa wajen yin bacci me dadi mai kuma cike da nutsuwa,uwa uba ga tsaro da zaya baki daga dukkan sharri,koda bunu chargy indai akwai wuta,jonata a socket,ki kunna qur'anin,yana playing tana chargy,zaki mamakin yadda wayarki zata cika da wuri,ga kuma qur'anin yana yi har safiya,koda chargynki ya kusa qarewa kika kunna,wani hukuncin Allah wayar bata mutuwa,tana kaiwa har safiya yanayi,Allah ya bamu albarkacin qur'ani mai girma,alfarmar shugaba S A W👏🏽👏🏽).
Saman kansu ya sanya wayar,ya raba a hankali zuwa bayanta ya kwantar da jikinsa,idanunta ta lumshe gaba daya zuciyarta ta soma gudu yadda ta saba a duk sanda ya rabota....lokacin data jishi cikin bargon da take,hannunsa saman ruwan cikinta,muryarsa can qasa kamar meyin rada yana cewa
"You are safe..... good night" cikin son yin aiki da maganarsa ta rufe idonta a hankali tana sauke numfashi,dumin kowanne na ratsa dan uwansa yana haifar masa da wani yanayi na daban.........
_to sai ince asuba ta gari kalsam_
53
DZ
"Ina hanya,yanzu zamu iso,koma meye idan nazo ka tambaya" abunda ya fada kenan sanda yake jingine da motarsa a farfajiyar gidan saukar baqin,saiya latse wayar kawai sanda yaji amirun nason masa cari,ya soma sanya wayar a aljihun wandon shaddarsa,lokaci guda kuma yana daga kansa.
A kanta idanunsa suka sauka,tana sanya da atamfa riga da zani,sai mayafi wanda yayi matuqar dacewa da kayan jikinta.
Kyakkyawar kalar fatarta ta haska tarwai cikin kalolin kayan jkinta,kwantaccen gashinta me santsi ya fiti ta gefe da gefan kunnenta,da kuma qeyarta inda ta nadeshi kamar alkaki.
Baisan sanda ajiyar zuciya ta kubce masa ba,yana tuna yadda hannunsa ya dinga yawo a jikinta daren jiya cikin mafarkinsa,wani abu ya tsarga masa sanda ta daga fararen idanunta suka sauka akansa,saiya sanya hannayensa duka cikin aljihun wandonsa yana qyara tsaiwarshi da kyau.
Faduwar gaba taji sosai,karon farko data ganshi da shigar da bata taba ganinsa da ita ba,shigar shadda fara sol sai maiqo da walqiya takeyi,wadda akayi mata aikin zare baqi,takalmi sau ciki wanda shima yake nashi kalar qyallin,hannunsa sanye da Rolex me asalin tsadan,sumar kanshi wadda bata da wani yawa sai sheqi takeyi saboda hularshi dake aje saman motar bai sanya ba.
Hardewa taji ta fara yi saboda takalman qafarta masu dan tsinin dunduniya da sukayi mata kyau suka kuma sake qawata kwalliyarta.
Tana dab da isowa inda yake ya sanya hannunsa saman motar ya.janyo hularsa ya aza a kansa,har a sannan bai fasa kallonta ba.
"Kinyi kyau" kalmar data subuce masa a bakinsa kamar fitar kibiya,hakan ya qara aza mata nauyinsa.
A hankali ya kutsa da motar cikin layin gidan ya dikko,duk kuwa da saurin da ya dinga yi amma hakan baisa ya iso a sanda yaso ba,saboda wani laziness da yakeji a jikinsa gaba daya,a hankali ya dannan wani madanni dake gefansa ya dage dukka gilasan motar sama sanda yake yiwa motar gun tsaiwa,hannu tasa zata bude motar
"Wait" taji ya fada,hakan yasa ta tsaya din kamar yadda ya buqata,ta qagauta ne su raba jaha,don ita kadai tasan wanne yanayi take riskar kanta a ciki duk sanda suka kadaice irin haka,wani mugun nauyi da kunyarsa takeji fiye da kowanne lokaci.
Wayarsa ya ciro ya dannan numbers din jawahir, ringing biyu ta daga,zata barke masa da surutun nan nata ya dakatar da ita,yace ta fito ya sameshi a waje,sannan ya aje wayar .
Daga nesa ya hangi fitowarta,tayi duru duru tana nemansu,saiya dan danna mata horn sannan ya bude motar ya fita,dai dai nan ta iso,saiya dan saka kansa kadan yace da kaltum din ta fito.
"Wai a ina kuka kwana kaltum?" Ta tambayi kaltum din cikin mamaki da kokwanto,saidai kafin tace komai samir din ya tsaidata
"Ba'a sani ba tambaya,ku wuce muje" bata qara tambayar ba,saidai tana mata susa a rai,tare da tambayar kanta inda sukaje suka kwana,kuma su biyu,ba muharraman juna ba,duk da cewa ta yarda da hali da dabi'ar yayan nata,dama ta kaltum din.
Suna gaba yana biye dasu a baya,duk da jama'a na tsaidashi suna gaisawa,duk inda ya wulga sai ya dauki hankalin jama'a,farinji da kwarjini gareshi,uwa uba yadda yake kyautatawa al'umma ya siya masa soyayyar jama'a me yawan gaske,a haka suka isa babban falon yadikko,wanda yalwar gidan da wadatar guraren zama ya sanya babu yawaitar mutane,kusan suna dakuna......
"A ina kika samo wannan beb din......ban santa ba a cikin danginmu" daya daga cikin samarin dake xaune a falon ya fada,abinda kuma kunnuwan samir suka jiye masa sanda yake shigowa,idonsa ya sauka kan yaron wanda ake kira da muntasir.
Sallamarsa yasa maganar da yake shirin yi ta yanke,duka suka waiwaya,sannan suka miqe cikin nuna girmamawa suna masa sannu da zuwa kafin su fara gaidashi.
Fuskarsa a hade tsam ya kalli jawahir
"Ina mummy?"
"A gidan haj shuwa ta kwana,amma munyi waya tace min ta taho,duk yadda akayi ta kusan qarasowa" ido ya lumshe kana ya bude cikin sakannin da basu wuce biyu ba,haka kawai cikin zuciyarsa jininsa baya son matar,kuma bazai iya tuna wani laifi data taba yi masa ba,koda na kallon banza kuwa
"Ki rakata wajen hajiya qarama"
"To" ta amsa masa tana yin gaba,kaltum tabi bayanta,saiya tsinci kansa da rakasu da ido.
Muntasir ya tabo dan uwansa
"Kaga guy din nan,ashe shima ya iya kallon mata?" Boyayyar dariyar ciki ya sake
"Waye baison mace dama?,aisu sunfi qarfin zuciya da qwaqwalwar kowa,saidai idan bai samu ba,bare wannan....ta wanku fa,kalar fatarta ta musammance wlh,ga wani kyau mai sanyi alaji,wanda saita matsoka kake ganinsa",dif sukayi sanda ya waiwayo ya dubesu,don kalamansu na qarshe sun shiga kunnensa,baisan me yake taba zuciyarsa ba duk sanda sukayi magana irin wanann,dukansu ba sa'ansa a cikinsu,don haka ya miqe ya nufi bangaren dakin ya dikko don su gaisa,tun kafin daddy ya qaraso yaji basu gaisa din ba.
Fara'a fal fuskar hajiya qarama,farincikin ganin kaltum ya bayyana sosai
"Lale maraba da diyata,ina nan inata kewarki,dama yanzu nake shirin kiran saraki naji can gidan abokin nasa zaku yita zama ne?,sai amirun yacemin matar abokince bata jin dadi sosai,kin dan tsaya kin taimaka mata ta kintsa gidan" itadai murmushi kawai take,kanta a qasa tana jinjina yadda amiru ya iya tsara irin wannan qaryar,duk da tayi mata dai dai,don bata da kowacce amsa da xata bata.
"bari naje mu qarasa packaging abincin 'yan daurin aure.....ina zuwa kaltum" ta fada tana juyawa gami da ficewa daga dakin,zuciyarta dai na tantamar labarin da amiru ya bawa haj qaraman kan rashin kwanansu gida,tunda a gabanta ne yake neman shima inda suka shiga,ture batun tayi,sabida batason baiwa shaidan qofa akansu,ta yarda da kowa a cikinsu.
Sai data zauna sosai sannan ta daga kai da niyyar gaida hajiya qarama,saidai gaisuwar taso.maqale mata a maqogaro,saboda sauka da idanunta sukayi kan wani hoto dake maqale a bangon dakin da yake tamkar na hajiya qaraman,saboda duk sanda tafiya ta kawosu azare a nan take sauka,idan zata tafi kuma ta rufe ta bawa ya dikko maqullin.
Hoto ne dauke da taswirar fuskar matar dake a jikin hoton data taho dashi zuwa azare,wanda tayi masa duban duniya amma ta rasa inda ta yada shi,gabansa kadan wani hoton ne irinsa,tana sanye da atamfa da akayi mata riga da xani,ta yane jikinta da mayafin atamfar,wadda ta haskata ta kuma fidda kyanta sosai.