Sashe 52
Dabiar Zuciya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Shuru ya ratsa tafiyar tasu,hakan yasa samir yin amfani da wannan damar
"Ba abu bane me kyau ba mutum na aiki qarqashinka,ka jishi shuru ka kasa bincikar lafiyarsa,idan lafiya lau yake to alhmdlh,idan kuma bashi da lafiya....sai kayi tattaki kaje ka duba lafiyarsa,wannan shine halin ma'aiki S A W,yayi cigiyar matar dake share masallaci kullum bayan ya jita shuru,aka shaida masa ta rasu,yaje kan kabarinta yayi mata addu'ar samun rahama,yayi cigiyar mutumin da yake ba musulmi ba,wanda kullum sai yazo yayi wani abun cutarwa ga ma'aiki,aka shaida masa bashi da lafiya ne,yayi tattaki yaje dubashi,qarshe ya laqqana masa kalmar shahada,ya karba ya musulunta,ya mutu a musulmi" saiya tsagaita yana tuna daga inda ya samu wannan karatun,yana tuna sanda take karantar dasu,yana hango lokaci da yanayin tarrrr a idanunsa,amma me yasa komai ya goge?,me yasa komai ya shafe?,me yasa dukkan wani abu da zai tuna masa da ita babu shi?,tambayar da yakewa kansa kenan a wasu lukutan.
"Allahu akhbar.....Allah ya bamu ikon yin koyi" hannafi ya fada
"Ameen ameen" umar ya amsa masa,girma da qimar samir na qaruwa a idanuwansa,ba dan kasuwa bane kadai,badan babban dan siyasa bane kawai,ba jagora bane zalla,ba mai kudi bane tsantsa,a'ah....yana da wata nagarta,nagartar da sai a tara mutane dubu masu irin abinda Allah ya bashi a rayuwa basu da ita.
Tafiyar minti biyar takawosu qofar gidansu bilal,shuru a yashe babu kowa
"Tab,kada Allah ya kawo wannan mafadacin uban nata......" Hannafi ya fada yana leqe da kansa ko zai hangi wani
"Kamar yaya?,daga ganinmu sai yahau fada?"
"Bakasan amadu ba,tosu kansa matar da yaran ba dadinsa suke ji ba,bashi da kirki bashi da mutunci...."
"Hannafi....."muyar saraki ta ratsa tattaunawarsu
"Yallabai" ya waiwayo yana amsawa cikin girmamawa
"Muyi abinda ya kawomu"
"To...to yallabai,bismillah mu shiga mana" wani kallo samir yayi masa
"A musulunce haramunne ka shiga gidan mutane ba tare da neman izini ba,Allah cewa yayi kada ku shiga gidajen daba naku ba,har sai kunyi sallama kun nemi izini daga masu gidan......koda kunyi sallamar ma idan suka ce ku koma to ku koma"
"Afuwa ranka ya dade,bari ayi sallama" ya fada yana yaye muryarsa ya doka sallama,yayin da samir ya koma gefe ya goye hannayensa a qirji yana nazarin gidan,gajeriyar katanga wadda idan anso haurawa ba wani abu bane mai wahala,tako ina zagwanyewa take,da alama tafi samun wannan matsalar da damuna,ita kanta qofar gidan kyakkyawan bugu guda daya rak ya isa ya kaita qasa.
Leqowar inna laure yasa hannafi ya dakata da doka sallamar,sunsan juna,sai suka fara gaisawa da ita su samir na tsaye a gefe,da fari cikin fara'a fuskarta take,amma sanda taji wajen wa sukazo sai fara'ar ta dauke dif daga fuskarta,ta koma qarewa su samir kallo.
Ajiyar zuciya ta saki a boye sanda ta gama kallonsu,a haka dai fea suke,amma bataga alamun nera a tattare dasu ba,duk da hakan tanajin ba zata iya yi musu iso wajen zuwaira ba,sai tace
"Ka jira" kawai ta juya zuwa ciki.
Minti daya biyu shuru,dai dai sanda asiya ta keto cikin shigar wani lace,lace ne mai kyau amma an masa dinkin ganin dama,tana tafe tana tauna chewing gum,tana taku ɗai ɗai,tana jin kaf qauyen babu yarinyar data kama qafarta,sani da iya gayu,da kuma morewa rayuwarta,kallo itama ta bisu dashi,daga bisani ta sauke idanunta kan fuskar samir,ido ta zuba masa,can qasa kadan kadan tana hangar wani kyau da tsarin halittar da bata taba ganin irinta ba,wanda ba kowacce mace zata tantance hakan ba,sa irinsu da suka fara gogewa da duniya da sanin maza.
Kwarjinin daya zuba mata da idanunsa su suka sanyata janye nata idon ba shiri,ajiyar zuciya na qwace mata ba tare data sani ba,sai tayi cikin gida,wanda shigarta yayi dai dai da budar bakin hannafi
"Yar kusun uwa mara kunya,kin addabi 'yar uwarki da rashin mutunci,ke ko koyi da ita bakya yi......" Kallon da samir din ya sake watsa masa yasa yaja bakinsa ya tsuke,saiya waske ta hanyar qarawa gaba ya cusa wuyansa cikin soron yana sake kwarara sallama.
Kaltum dake wankin kayan umma a magangarar ruwa,ta waiwaya ta dubi umma dake zaune saman kan bilal dake kwance,wanda ta gama bawa maganin data jiqa
"Ummanmu kamar sallama ake a waje ko?"
"Eh nima naji,sa hijabinki kije ku duba" dan jim tayi,sam ita yanzu bata son fita ko nan da can,saboda kada ta hadu da auwalu da take ganinsa kamar wani baqin kumurci
"Ummanmu,idan kuma baqin asiya ne fa?"
"Babu lallai,tunda kikaji basu amsa ba" saita tsame hannunta daga ruwan dattin,ta goge jikin tsohon zaninta,ta janyo hijabinta da bata rabo dashi ta zura sannan ta durfafi soron.
Ganin baquwar fuska haf biyu saita ci gaba da takawa a hankali,haka kawai gabanta na faduwa,tana addu'ar ya rabbi ya kauda matsala,ubangiji yasa ba wata sabuwar wutar bace ta kunno kai.
Shi ya fara hangota,tana tahowa a hankali,iska na kadata kamar zata fadi tsabar sirantaka,ba ita kadai iskar ke kadawa ba,harda tsumman zanin jikinta,da hijabinta da yake mannewa a jikinta saboda yadda ya fara tsufa,ga kuma yanayin sanyi da aka fara shiga.
"Ina yininku?" Ta fada a tausashe tana dan rusunawa,muryarta cike da fargaba,karon farko da yaji muryarta dab dashi,karo na uku da mamakin yadda Allah ya bata murya ya mamayeshi,koda yake.....ya tabajin wata hira tasu auta cewar..... majority masu kyan fuska ba kasafai suke da murya mai dadi ba......wadanda kuma suke basu da wani kyau,Allah yakan basu baiwar murya
"Lafiya lau" hannafi da umar suka amsa,sannan hannafin ya dora
"Ya jikin bilalun?,munzo dubashi ne daga wajen aiki" kanta tada sosa sannan tace
"Bari to na fara gayawa ummanmu,saiku shigo"
"To babu laifi"cewar hannafin,saita juya da dan hanzari fiye dana dazu,da alama ta samu qwarin gwiwa ne.
Hijabi ummansu ta saka,ta sanyata kuma ta sake shinfida musu wata tabarmar daban,tare da aje musu ruwa a kwanon sha,sannan ta koma tayi musu iso.
Sosai bilal yayi mamaki,ya kuma ji dadin zuwansun,duk da yadda yake jin jiki.
A nutse kuma cike da hikima samir yake karantar yanayin yaron,yanayin yadda yaga jikinsa a nasa ilimin ya kamaci a kaishi asibiti,saboda yadda yanayin launin idanunsa suka dan jirkita.
Da gani koda ba'a gaya maka ba yasan suna cikin rayuwa ta buqata,saidai babban abinda ya burgeshi,yanayin yadda komai nasu yake a killace a kuma tsaftace,daga inda yake yana hangen yadda take zaune tana wanki da sili silin hannunta,wadanda suke juya kayan da qyar,da alama ba nata bane,tunda ta musu iso ta koma saman kujerar 'yar tsuguno taci gaba da wankinta.
Yanajin ya kamata ya tallafi rayuwarsu da abinda zai iya,duk mutumin da kunnensa ko idanuwansa suka nuna masa shi a muhallin mabuqaci,kawai yana gayawa kansa Allah ne yayi nufin nuna masan domin ya taimakeshi da abinda ya hore masa na arziqinsa,bare bilal.....haka kawai yakejin yaron ya kwanta masa tun daga wancan lokacin da tazo amsar haqqin dan uwanta har wajen aikin,bai fahimci abinda tayin ba sai daga bisani,daya dinga shiga cikin ma'aikatan yana rayuwa dasu a matsayin ma'aiakaci,ya gane cewa wani zalunci akayi tazo ta dakusar dashi.
Tunaninsa ya katse sanda malam amadu ya danno gidan da wata iriyar sallama,dukkansu su ukun sai yaga reaction dinsu ya canza,har kaltum dake wanki a zaune ta kasa ci gaba da zama,ta saki wankin tana masa sannu da zuwar daya amsa da qyar ta wuce quryar daki.
Bai ankara dasu ba sai daya gama shigowa,saiya kuma saki fuska,kamar ba shine wanda ya shigowa iyalansa a wani yanayi ba.
Suna gama gaisawa samir ya miqe daga tsugonnan da yayi a gaban bilal,don dama bai zauna ba,duk da cewa fes tabarmar take,umar ya kalla kana ya fice bayan ya sake yiwa bilal da umma fatan samun sauqin bilal anan kusa,ya fahimci abinda yake nufi,don haka yana fita ya soma qoqarin ciro kudi,sai hannafi ya qyara masa ya cusawa bilal din qasan filo,don yasan halin malam amadu,haka kuwa akayi,don har suka fice bai lura da kudin ba.
"Bashi da tausayin iyalansa,shegiyar masifa da shegen son kudi kamar tsohon bazawari" maganar data bawa unar dariya kenan suka fito suna darawa,saidai suna iske saraki tsaye a qofa gidan kowa ya kama kanshi suka sake takawa zuwa inda suka fito.
"Gida zamu wuce,inason nakai gida nan da minti talatin" saraki yafada bayan ya gama kallon agogon hannunsa,a mamakance umar ya kalleshi,har ya kasa boye abinda ke bakinsa
"Yallabai kai da bakason gudun wuce qa'ida?"
"Yau nace maka kayi?" Qaramin murmushi yana subuce masa,yau din babbar rana ce mai mihimmanci a wajensa,yau Aamirunsa zai dawo gida,bayan tsahon lokacin daya dauka basa tare,yana buqatar bawa amirun mamaki bayan ya kashe wayoyinsa gaba daya ya kasa samunshi,saidai kawai ya ganshi.
Kamar yadda ya buqata haka kuwa umaf ya tsula gudu iya son ransa a yau din,duk da haka sanda suka iso mintunan ba zasu iseshi ya koma gida yayi wanka ya shirya ba sannan ya tafi tarar amirun ba,don haka yacewa umar su wuce kawai airport din da kayan jikinsa,duk da cewa sun diba qura ba laifi.
Su uku ne a tafe dukkansu sanye da doguwa riga abaya,yammata uku sai qaramar yarinya daya,daya daga cikin 'yammatan tana riqe da hannun yarinyar daketa faman tsalle tsalle tana son qwacewa
"Laaaa uncle?" Yarinyar ta fada tana qoqarin xame hannunta daga cikin hannun budurwar,abinda yaja hankalin mubina kenan daketa faman hira,ta waiwaya tana dakawa yarinyar tsawa
"Meye hakane afra?" Kafin ta gama maganar ma tuni ta kubuce ta durfafi inda samir yake tsaye,wanda sam hankalinsa ma baya wajen bare yaga tahowar yarinyar,saiji yayi kawai an kama qafafunshi ana cewa
"Uncle....ina ka tafi?" A hankali ya sauke kansa yana kallon fuskar yarinyar,ya tunata,murmushi ya wadaci fuskarsa,saiya tsugunna a gabanta ya kama hannayenta
"Umm....ummm" ya fadi yana qoqarin tuna sunanta
"Afra" ta amsa mishi tana dariya,sai dariya ta qwace masa,shegen wayo ne da yarinyar da alama,gashi harta fahimci abinda yakeson cewa,ta kuma tuna masa
"Keda wa kukazo?" Waiwaya tayi inda mubina tayi mutuwar tsaye tun sanda ta ganshi,tana nuna mishi ita da hannunsa,suka hada idanu na sakanni,saiya janye qwayar idonshi daga kanta,kallonsa kawai ya sanya tayi suman tsaye,taja numfashinta da qyar,ta tattaro dauriyarta tana takawa zuwa inda suke tsugunne,mamaki yana cikata na irin yadda ya gwanance a iya shariya.
Sau daya tak ya daga kai ya kalleta ya maida ga afra sukaci gaba da hirarsu kamar wadanda sukayi mugun sabo da juna,ganin da gaske kamar bai ganta ba saita dan gyara muryarta kadan sannan tace
"Ba abu bane me kyau ba mutum na aiki qarqashinka,ka jishi shuru ka kasa bincikar lafiyarsa,idan lafiya lau yake to alhmdlh,idan kuma bashi da lafiya....sai kayi tattaki kaje ka duba lafiyarsa,wannan shine halin ma'aiki S A W,yayi cigiyar matar dake share masallaci kullum bayan ya jita shuru,aka shaida masa ta rasu,yaje kan kabarinta yayi mata addu'ar samun rahama,yayi cigiyar mutumin da yake ba musulmi ba,wanda kullum sai yazo yayi wani abun cutarwa ga ma'aiki,aka shaida masa bashi da lafiya ne,yayi tattaki yaje dubashi,qarshe ya laqqana masa kalmar shahada,ya karba ya musulunta,ya mutu a musulmi" saiya tsagaita yana tuna daga inda ya samu wannan karatun,yana tuna sanda take karantar dasu,yana hango lokaci da yanayin tarrrr a idanunsa,amma me yasa komai ya goge?,me yasa komai ya shafe?,me yasa dukkan wani abu da zai tuna masa da ita babu shi?,tambayar da yakewa kansa kenan a wasu lukutan.
"Allahu akhbar.....Allah ya bamu ikon yin koyi" hannafi ya fada
"Ameen ameen" umar ya amsa masa,girma da qimar samir na qaruwa a idanuwansa,ba dan kasuwa bane kadai,badan babban dan siyasa bane kawai,ba jagora bane zalla,ba mai kudi bane tsantsa,a'ah....yana da wata nagarta,nagartar da sai a tara mutane dubu masu irin abinda Allah ya bashi a rayuwa basu da ita.
Tafiyar minti biyar takawosu qofar gidansu bilal,shuru a yashe babu kowa
"Tab,kada Allah ya kawo wannan mafadacin uban nata......" Hannafi ya fada yana leqe da kansa ko zai hangi wani
"Kamar yaya?,daga ganinmu sai yahau fada?"
"Bakasan amadu ba,tosu kansa matar da yaran ba dadinsa suke ji ba,bashi da kirki bashi da mutunci...."
"Hannafi....."muyar saraki ta ratsa tattaunawarsu
"Yallabai" ya waiwayo yana amsawa cikin girmamawa
"Muyi abinda ya kawomu"
"To...to yallabai,bismillah mu shiga mana" wani kallo samir yayi masa
"A musulunce haramunne ka shiga gidan mutane ba tare da neman izini ba,Allah cewa yayi kada ku shiga gidajen daba naku ba,har sai kunyi sallama kun nemi izini daga masu gidan......koda kunyi sallamar ma idan suka ce ku koma to ku koma"
"Afuwa ranka ya dade,bari ayi sallama" ya fada yana yaye muryarsa ya doka sallama,yayin da samir ya koma gefe ya goye hannayensa a qirji yana nazarin gidan,gajeriyar katanga wadda idan anso haurawa ba wani abu bane mai wahala,tako ina zagwanyewa take,da alama tafi samun wannan matsalar da damuna,ita kanta qofar gidan kyakkyawan bugu guda daya rak ya isa ya kaita qasa.
Leqowar inna laure yasa hannafi ya dakata da doka sallamar,sunsan juna,sai suka fara gaisawa da ita su samir na tsaye a gefe,da fari cikin fara'a fuskarta take,amma sanda taji wajen wa sukazo sai fara'ar ta dauke dif daga fuskarta,ta koma qarewa su samir kallo.
Ajiyar zuciya ta saki a boye sanda ta gama kallonsu,a haka dai fea suke,amma bataga alamun nera a tattare dasu ba,duk da hakan tanajin ba zata iya yi musu iso wajen zuwaira ba,sai tace
"Ka jira" kawai ta juya zuwa ciki.
Minti daya biyu shuru,dai dai sanda asiya ta keto cikin shigar wani lace,lace ne mai kyau amma an masa dinkin ganin dama,tana tafe tana tauna chewing gum,tana taku ɗai ɗai,tana jin kaf qauyen babu yarinyar data kama qafarta,sani da iya gayu,da kuma morewa rayuwarta,kallo itama ta bisu dashi,daga bisani ta sauke idanunta kan fuskar samir,ido ta zuba masa,can qasa kadan kadan tana hangar wani kyau da tsarin halittar da bata taba ganin irinta ba,wanda ba kowacce mace zata tantance hakan ba,sa irinsu da suka fara gogewa da duniya da sanin maza.
Kwarjinin daya zuba mata da idanunsa su suka sanyata janye nata idon ba shiri,ajiyar zuciya na qwace mata ba tare data sani ba,sai tayi cikin gida,wanda shigarta yayi dai dai da budar bakin hannafi
"Yar kusun uwa mara kunya,kin addabi 'yar uwarki da rashin mutunci,ke ko koyi da ita bakya yi......" Kallon da samir din ya sake watsa masa yasa yaja bakinsa ya tsuke,saiya waske ta hanyar qarawa gaba ya cusa wuyansa cikin soron yana sake kwarara sallama.
Kaltum dake wankin kayan umma a magangarar ruwa,ta waiwaya ta dubi umma dake zaune saman kan bilal dake kwance,wanda ta gama bawa maganin data jiqa
"Ummanmu kamar sallama ake a waje ko?"
"Eh nima naji,sa hijabinki kije ku duba" dan jim tayi,sam ita yanzu bata son fita ko nan da can,saboda kada ta hadu da auwalu da take ganinsa kamar wani baqin kumurci
"Ummanmu,idan kuma baqin asiya ne fa?"
"Babu lallai,tunda kikaji basu amsa ba" saita tsame hannunta daga ruwan dattin,ta goge jikin tsohon zaninta,ta janyo hijabinta da bata rabo dashi ta zura sannan ta durfafi soron.
Ganin baquwar fuska haf biyu saita ci gaba da takawa a hankali,haka kawai gabanta na faduwa,tana addu'ar ya rabbi ya kauda matsala,ubangiji yasa ba wata sabuwar wutar bace ta kunno kai.
Shi ya fara hangota,tana tahowa a hankali,iska na kadata kamar zata fadi tsabar sirantaka,ba ita kadai iskar ke kadawa ba,harda tsumman zanin jikinta,da hijabinta da yake mannewa a jikinta saboda yadda ya fara tsufa,ga kuma yanayin sanyi da aka fara shiga.
"Ina yininku?" Ta fada a tausashe tana dan rusunawa,muryarta cike da fargaba,karon farko da yaji muryarta dab dashi,karo na uku da mamakin yadda Allah ya bata murya ya mamayeshi,koda yake.....ya tabajin wata hira tasu auta cewar..... majority masu kyan fuska ba kasafai suke da murya mai dadi ba......wadanda kuma suke basu da wani kyau,Allah yakan basu baiwar murya
"Lafiya lau" hannafi da umar suka amsa,sannan hannafin ya dora
"Ya jikin bilalun?,munzo dubashi ne daga wajen aiki" kanta tada sosa sannan tace
"Bari to na fara gayawa ummanmu,saiku shigo"
"To babu laifi"cewar hannafin,saita juya da dan hanzari fiye dana dazu,da alama ta samu qwarin gwiwa ne.
Hijabi ummansu ta saka,ta sanyata kuma ta sake shinfida musu wata tabarmar daban,tare da aje musu ruwa a kwanon sha,sannan ta koma tayi musu iso.
Sosai bilal yayi mamaki,ya kuma ji dadin zuwansun,duk da yadda yake jin jiki.
A nutse kuma cike da hikima samir yake karantar yanayin yaron,yanayin yadda yaga jikinsa a nasa ilimin ya kamaci a kaishi asibiti,saboda yadda yanayin launin idanunsa suka dan jirkita.
Da gani koda ba'a gaya maka ba yasan suna cikin rayuwa ta buqata,saidai babban abinda ya burgeshi,yanayin yadda komai nasu yake a killace a kuma tsaftace,daga inda yake yana hangen yadda take zaune tana wanki da sili silin hannunta,wadanda suke juya kayan da qyar,da alama ba nata bane,tunda ta musu iso ta koma saman kujerar 'yar tsuguno taci gaba da wankinta.
Yanajin ya kamata ya tallafi rayuwarsu da abinda zai iya,duk mutumin da kunnensa ko idanuwansa suka nuna masa shi a muhallin mabuqaci,kawai yana gayawa kansa Allah ne yayi nufin nuna masan domin ya taimakeshi da abinda ya hore masa na arziqinsa,bare bilal.....haka kawai yakejin yaron ya kwanta masa tun daga wancan lokacin da tazo amsar haqqin dan uwanta har wajen aikin,bai fahimci abinda tayin ba sai daga bisani,daya dinga shiga cikin ma'aikatan yana rayuwa dasu a matsayin ma'aiakaci,ya gane cewa wani zalunci akayi tazo ta dakusar dashi.
Tunaninsa ya katse sanda malam amadu ya danno gidan da wata iriyar sallama,dukkansu su ukun sai yaga reaction dinsu ya canza,har kaltum dake wanki a zaune ta kasa ci gaba da zama,ta saki wankin tana masa sannu da zuwar daya amsa da qyar ta wuce quryar daki.
Bai ankara dasu ba sai daya gama shigowa,saiya kuma saki fuska,kamar ba shine wanda ya shigowa iyalansa a wani yanayi ba.
Suna gama gaisawa samir ya miqe daga tsugonnan da yayi a gaban bilal,don dama bai zauna ba,duk da cewa fes tabarmar take,umar ya kalla kana ya fice bayan ya sake yiwa bilal da umma fatan samun sauqin bilal anan kusa,ya fahimci abinda yake nufi,don haka yana fita ya soma qoqarin ciro kudi,sai hannafi ya qyara masa ya cusawa bilal din qasan filo,don yasan halin malam amadu,haka kuwa akayi,don har suka fice bai lura da kudin ba.
"Bashi da tausayin iyalansa,shegiyar masifa da shegen son kudi kamar tsohon bazawari" maganar data bawa unar dariya kenan suka fito suna darawa,saidai suna iske saraki tsaye a qofa gidan kowa ya kama kanshi suka sake takawa zuwa inda suka fito.
"Gida zamu wuce,inason nakai gida nan da minti talatin" saraki yafada bayan ya gama kallon agogon hannunsa,a mamakance umar ya kalleshi,har ya kasa boye abinda ke bakinsa
"Yallabai kai da bakason gudun wuce qa'ida?"
"Yau nace maka kayi?" Qaramin murmushi yana subuce masa,yau din babbar rana ce mai mihimmanci a wajensa,yau Aamirunsa zai dawo gida,bayan tsahon lokacin daya dauka basa tare,yana buqatar bawa amirun mamaki bayan ya kashe wayoyinsa gaba daya ya kasa samunshi,saidai kawai ya ganshi.
Kamar yadda ya buqata haka kuwa umaf ya tsula gudu iya son ransa a yau din,duk da haka sanda suka iso mintunan ba zasu iseshi ya koma gida yayi wanka ya shirya ba sannan ya tafi tarar amirun ba,don haka yacewa umar su wuce kawai airport din da kayan jikinsa,duk da cewa sun diba qura ba laifi.
Su uku ne a tafe dukkansu sanye da doguwa riga abaya,yammata uku sai qaramar yarinya daya,daya daga cikin 'yammatan tana riqe da hannun yarinyar daketa faman tsalle tsalle tana son qwacewa
"Laaaa uncle?" Yarinyar ta fada tana qoqarin xame hannunta daga cikin hannun budurwar,abinda yaja hankalin mubina kenan daketa faman hira,ta waiwaya tana dakawa yarinyar tsawa
"Meye hakane afra?" Kafin ta gama maganar ma tuni ta kubuce ta durfafi inda samir yake tsaye,wanda sam hankalinsa ma baya wajen bare yaga tahowar yarinyar,saiji yayi kawai an kama qafafunshi ana cewa
"Uncle....ina ka tafi?" A hankali ya sauke kansa yana kallon fuskar yarinyar,ya tunata,murmushi ya wadaci fuskarsa,saiya tsugunna a gabanta ya kama hannayenta
"Umm....ummm" ya fadi yana qoqarin tuna sunanta
"Afra" ta amsa mishi tana dariya,sai dariya ta qwace masa,shegen wayo ne da yarinyar da alama,gashi harta fahimci abinda yakeson cewa,ta kuma tuna masa
"Keda wa kukazo?" Waiwaya tayi inda mubina tayi mutuwar tsaye tun sanda ta ganshi,tana nuna mishi ita da hannunsa,suka hada idanu na sakanni,saiya janye qwayar idonshi daga kanta,kallonsa kawai ya sanya tayi suman tsaye,taja numfashinta da qyar,ta tattaro dauriyarta tana takawa zuwa inda suke tsugunne,mamaki yana cikata na irin yadda ya gwanance a iya shariya.
Sau daya tak ya daga kai ya kalleta ya maida ga afra sukaci gaba da hirarsu kamar wadanda sukayi mugun sabo da juna,ganin da gaske kamar bai ganta ba saita dan gyara muryarta kadan sannan tace