Sashe 49
Dabiar Zuciya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Inna,mun samu sabani ne da baban habi,shine yace na taho gida" wani dan zakudawa innar tayi kamae wadda ta taka wani abu,kana ta daidaita tsaiwarta
"Shine sai kika tattaro qwanki da qwarqwatarki keda ahalinki kaffff kika taho gidan inna mai masaukin baqi ko?,wadan nan marasa kunyar 'ya'yan naki,gaskiya ba'a taba rainamin hankali ba irin yau....to banda ma zuwaira ta yaya kike tunanin zan amsheki a gidana?,koda ke daya ce bare keda bataliyar wannan yaran haka saket,wato nice me wuyan dauka ko?...." Sai innar ya ranqwafo dai dai saitin umman
"To na rantse da aradu badai a gidana ba,babu masaukinki a gidana,saboda haka sahunki a likkafa kisan inda kika kama,badai nam ba,bare azo a dauramin nauyin babu gaira babu dalili"..
"Ke kuma keda wa kike ta maganganu?" Muryar jafaru dake riqe da leda ta ratso dakin
"Wacece idan ba zuwaira ba,haka kawai ta debomin bataliyar tara tayo yaji dasu,na riqeta na riqe mata 'ya'ya,uban daya haifesu ba yaqi su bare ni karan kada miya?"
Qaraso shigowa dakin jafaru yayi,ya ajjiye ledar hannunsa a gefansa yana cewa
"Wallahi na zaci ma wasune,ashe umma ce,yanzu inna banda abunki,umma zuwaira ai dolenki ce,ko 'ya'ya dari tazo dasu kuwa"
"A'ah,bada ni ba sa lallen karya,'ya'yana ne suke dawainiya dani,banga dalilin da za'a doramin nauyi ba,saboda haka dole ta tattara yanzu yanzu ba anjima ba tasan inda dare yayi mata".
Tun jafaru na daukar abun da wasa har ya haqiqance da gaske inna take,duk irin mamakin da yake kanta saida mamakinsa ya ninku,qarshe ma ya fahimci cewa qoqarin sata ta barsu su zauna da yakeyi qara damal mala al'amarin kawai yake,don haka saiya sauka daga wannan bigiren,ya soma yunqurin qyalesu zuwa safiya,idan Allah ya kaimu wayewar gari,da qyar yasha kanta,ta fice tana maganganu tare da kumfar baki
"Saboda kinga akwa wadatar dakuna,to dakuna na bana zamanku bane,ba kuma gadon ubanki a ciki bare kice ban kyauta ba,ubanku bai barmin komai ba a gidansa sai wancan rugurgujajjen dakin,nan duka arziqin ubansu indo nake ci".
Tunda ta fita dakin ya dauki shuru,tsakaninsu babu mai iya cewa komai,baka jin komai sai nishin bilal,wanda ko sau daya inna bata ma damu ta tambayi me ya sameshi ba,burinta kawai su fice mata daga gida shine abinda ya dameta.
Cikin hijabi kaltum ta shige ta dinga ruzgar kuka,gani take kwata kwata basuzo duniya a sa'a ba,kota wanne bangare qyamata ce da baqinjini yake bibiyarsu,tana iya jin yadda ummans keta sauke ajiyar zuciya akai akai,kamar qaramin yaron da aka yiwa shegen duka.
Tun bilal na nishi lokaci lokaci yana cewa
"Wayyo Allaj cikina" har wani wahalallen bacci mata dadi yayi awon gaba dashi.
Duk yadda kaltume kejin wannan daren bacci yayi kadan ya dauketa amma sai daya gwada mata qarfa qarfarsa,can tsakiyar dare sanda suke zaune ita da ummanta,kowa tunaninsa yayi nisa kan meye makomars a gobe da safe idan inna ta tsaya kan ra'ayinta na su bar mata gida?,da wannan tambaya mai nauyi da firgici baccin ya sureta.
Ƙaqqarfar bugun qofar da aka yiwa dakin ta samu nasarar ratsawa har cikin tsakiyar baccinsu,ya haifar musu da farkawa gaba dayansu a firgice daga dan gajeran barcin da ya wafci idanuwansu,duka kowanne ya miqe ya zauna daram saman mazaunansa suna duban qofar,yayin carar zakaru ke tashi daga wancan gida zuwa wannan gida,da alama a yanzu ne assalatu tayi.
Inna ce tsaye a kansu tana dubansu,kai kace daren jiya batayi barci ba,kamar ta zauna gadin daren ne tana jiran asuba tayi
"Saiku tashi ko?,kusan inda dare yayi muku" ta fada kanta tsaye,tana sake matse fuska.
Mamaki maganarta ta basu,kaltum takai dubanta ga tsakar gidan,dudum yake,duhunsa bashi da maraba da tsakiyar dare,hakan kuwa ba abun mamaki bane,saboda ko salla ba'a shiga ba a qananun masallatan dake qauyukan
"Wai da gaske kike inna?,to ina zamuje?"
"Ki tambayi uwarki!" Innan ta fada tana zazzaro idanuwa,tare da nuna ummanmu da yatsa,waiwayawa tayi kuwa ta kalli ummansu,wadda ta sad da kai
"Duk yanayin data samu kanta ita ta jama kanta,babu yadda banyi da ita kada ta haifeku a gidan nan ba,ta fito ta samu wani mai damshin arziqin ta aura amma taqi,sai data tara ku kuma sannan yanzu haka kawai saita debomin wallahi,to ba dani ba sam,duniya da girma da fadi,ai maye baya ci kansa ba" ta fada tama riqe da qugunta kamar qaramar yarinya
"Kiyi haquri inna zuwa gobe,ko anjima gari ya sake wayewa....zamu tafi" cewar umma cikin sanyin murya,a karon farko kenan tsakanin jiya da yau a aka fara dambarwar
"Me? Inji akuya?,idan kin isa shegiya nake,billahillazi kinyi kadan,ko sakan bazan qara muku ba,ku tashi ku fita?,idan kunqi kuwa saina tijara ku" ta fada cikin bambami da daga murya
"Qofar gida zan tsaya ma naga fitarku,wallahi bame qara yimin minti guda a guda" ta sanya kai tana shirin ficewa daga dakin sukayi karo da jafaru
"Wai inna maganar ce ne da farar safiya ko ince tsakar dare?,haba inna,ko gari ai kya bari ya gama wayewa ko?" Ya fada cikin jin takaicin halin innar
"Kai jafaru,kai jafaru,kai jafaru,sau nawa na kira sunanka?,ba sau uku ba?,to wallahi wallahi ka fita daga idanuna,idan ka qara magana a nan saina tsintstsinka maka mari" tafada tana huci gami da zare masa ido,ala dole yaja bakinsa yayi shuru yana kallo tana ci gaba da tijararta har zuwa qofar gida,fadi take
"Ki fito ku barmin gidana,wallahi sai kun tafi,ku fita ko nasa a fitarmin daku" cikin daga murya,wanda sautinta ya karade dukka maqotan take gefe da gefe gaba da bayan gidansu,ya kuma fara jan hankalin jama'a wadanda suka tattashi domin bada farali na sallar asuba,masu fita zuwa masallaci maza,dama mata masuyin sallar a cikin gidajensu.
Kafin kace meye mutane sun dan fara tattaruwa,dai dai sanda ummanmu dasu kaltum ke fitowa a gidan,kaltum na riqe da bilal da har yanzu jikinsa baiyi qwari ba,ummansu na riqe da 'yan kayanta data debo.
Fitowarsu tasa jama'a suka koma kallon kallo,kowa ka kalla fuskarsa cike da alhini da kuma mamaki,anya kuwa innar kanta qalau?,wasu daga cikin jama'ar suka soma yiwa kansu tambaya,wasu kuwa sun riga da sunsan lafiya ras take,saboda sanin hali yafi sanin kama,kowa Yasan innar yasan abinda zata aikata da wanda ba zata aikata ba,a tsahon shekarun da take zaunen a nan,duk mutumin daya zauna da ita ya santa da halaye gusa biyu datayi shura dasu,zallar masifa da kuma son abun duniya,ba shakka iya wadan nan dabi'u kawai sun isa suyi mata jagora ga abinda ta aikata din a yanzu.
Suna sake nisa da ita kunnuwansu na sake kasa kama maganganu da hargowar data ke musu,idanuwan ummanmu a wannan karon sun gaza riqe ruwan hawaye da suka danno cikin idanuwanta,irin abinda innar tayi mata a yanzu yana cikin lissafin irin abubuwan da take zato tunani ko mafarkin innar zata iyayi mata a rayuwa,ta shiga matuqar rudani da mamakinta,ta zaci koda bare ne wanda innar bata sanshi ba bawai gudan jininta ba bazata aikata masa haka ba,wai dama haka qin jininta yayi nisa cikin ran inna?,laifinta kawai don babansu bashi da komai,bai mallaki abun duniya ba har ya mutu?,laifinta don taqi kashe aurenta sanda arziqi da dukiyar amadu ta durqushe?,ta gaza tantance wanne ne laifi cikin abinda ke faruwa,dabi'ar da inna ke nuna mata lailan wa naharan?,ko kuma ita abinda ta aikata da kuma yanayin rayuwa a mahaifinsu ya sami kanshi kafin rasuwarsa?.
"Ummanmu......ina zamuje yanzu?" Muryar bilal dake cike da gajiya da kuma ciwo ta fargar da ita cewa a hanya suke,sai a sanna ta daga kanta,sunyi nisa da gidan inna,zuwa sannan an shishshiga masallatai sallar asubahi
"Muje gidan umma altine" kaltum ta amsa masa maimakon umman tasu
"Ko umma?'" ta maida tambayar gareta don ta samu tabbacin abinda ta yanke din ya yiwa umman tasu.
Har cikin ranta taji bai dace sujewa altine ba,saboda ita kanta neman dauki da taimako takeyi,nauyin dake kanta itama tallafi take buqata,zuwanta wajenta a irin wannan lokacin tamkar rashin sanin abinda ya kamata ne,uwa uba ma ita din qanwarta ce bawai yaya ba,don haka saita girgizawa kaltum kai
"A'ah,ba gidanta zamu je ba,itama tana da wasu wahalhalu da dawainiya a kanta....."
"To gidan yakumbo indo?" Bilal yayi saurin sake fada,da alama a jigace yake,so yake kawai su samu muhalli ko wanne iri ne da zai bashi damar hutu.
Nan ma kai umman ta girgiza
"Itama macace,a qarqashin wani take,ba zamuje mu dora mata jigilar mu ba har mu uku"
"To gidan kawu ado" wannan karon kaltum ce ta fadi haka,shuru umma tayi,yayin da suma dukka sukayi shurun suna dubanta,daga kai tayi,sai taga dukkaninsu ita suka zubawa ido suna jiran suji amsa
"Shikenan,muje can din" ta gada tana riqe hannun bilal da kyau,don kaltum ta samu ta huta itama,don tafiyace miqaqqiya a qafa daga nan zuwa gian kawu ado,tunda babu wani abun hawa sa zasu hau da zai rage musu wahalar tafiyar,a qalla zasu iya shafe awanni biyu kafin sukai.
29
D/Z
*wannan littafin na kudine,sharinga dinsa zuwa wasu gurare tamkar zalunci ne garemu,kiyiwa girman Allah ki barshi a inda kika ganshi,idan kin da buqatar karantawa ki biya naki ta wadannan numbers din dake qasa*
08184017082
Ko kuma
09134848107
Kafin su iso gidan kawu ado gari yayi haske tarwai,don har wasu daga cikin mutane sun fara fita zuwa sabgogin gabansu na rayuwa.
Area din da gidan kawu ado yake,area ce mai dan kyau,saboda akwai gidajen dake da ginin bulo ma,kamar yadda gidan kawu adon yake ginin bulo,da malalen siminti a tsakar gidansu,wanda hakan yasa gidan ya bambanta da sauran gidaje wansa jar qasa tayi musu qawanya har cikin tsakae gidajensu.
Da sallama suka shiga gidan,matarsa dake cikin dakin girki ta amsa tana leqo da kanta daya dan rage girma saboda hayaqin icce da take amfani dashi.
Suna hada ido da umma saita miqe tana fitowa daga dakin girkin
"Lale maraba,kune a tafe?" Ta fada fuskarta a washe tana qoqarin goge fuskarta,gefe daya qasan zuciyarta tana mamaki
"Wallahi mune tsaiba,kin ganmu da sassafe ko?" Murmushi tayi tana qoqarin karbar kayan hannun umman,don tsaiban badai kirki da daraja dangin mijinta ba
"Ah haba dai yaya?,wacce safiya?,bayan yara ma duka sun wuce makaranta?,ku shigo daga ciki mana" ta fada tana yin gaba,umma bilal da kaltum bita a baya,tana sake musu barka da zuwa.
Faffadar rumfarta dake malale da leda da kujeru 'yan duƙui duƙui suka shiga,ta ajjiye kayan itama tana zama idanuwanta kan bilal
"Shine sai kika tattaro qwanki da qwarqwatarki keda ahalinki kaffff kika taho gidan inna mai masaukin baqi ko?,wadan nan marasa kunyar 'ya'yan naki,gaskiya ba'a taba rainamin hankali ba irin yau....to banda ma zuwaira ta yaya kike tunanin zan amsheki a gidana?,koda ke daya ce bare keda bataliyar wannan yaran haka saket,wato nice me wuyan dauka ko?...." Sai innar ya ranqwafo dai dai saitin umman
"To na rantse da aradu badai a gidana ba,babu masaukinki a gidana,saboda haka sahunki a likkafa kisan inda kika kama,badai nam ba,bare azo a dauramin nauyin babu gaira babu dalili"..
"Ke kuma keda wa kike ta maganganu?" Muryar jafaru dake riqe da leda ta ratso dakin
"Wacece idan ba zuwaira ba,haka kawai ta debomin bataliyar tara tayo yaji dasu,na riqeta na riqe mata 'ya'ya,uban daya haifesu ba yaqi su bare ni karan kada miya?"
Qaraso shigowa dakin jafaru yayi,ya ajjiye ledar hannunsa a gefansa yana cewa
"Wallahi na zaci ma wasune,ashe umma ce,yanzu inna banda abunki,umma zuwaira ai dolenki ce,ko 'ya'ya dari tazo dasu kuwa"
"A'ah,bada ni ba sa lallen karya,'ya'yana ne suke dawainiya dani,banga dalilin da za'a doramin nauyi ba,saboda haka dole ta tattara yanzu yanzu ba anjima ba tasan inda dare yayi mata".
Tun jafaru na daukar abun da wasa har ya haqiqance da gaske inna take,duk irin mamakin da yake kanta saida mamakinsa ya ninku,qarshe ma ya fahimci cewa qoqarin sata ta barsu su zauna da yakeyi qara damal mala al'amarin kawai yake,don haka saiya sauka daga wannan bigiren,ya soma yunqurin qyalesu zuwa safiya,idan Allah ya kaimu wayewar gari,da qyar yasha kanta,ta fice tana maganganu tare da kumfar baki
"Saboda kinga akwa wadatar dakuna,to dakuna na bana zamanku bane,ba kuma gadon ubanki a ciki bare kice ban kyauta ba,ubanku bai barmin komai ba a gidansa sai wancan rugurgujajjen dakin,nan duka arziqin ubansu indo nake ci".
Tunda ta fita dakin ya dauki shuru,tsakaninsu babu mai iya cewa komai,baka jin komai sai nishin bilal,wanda ko sau daya inna bata ma damu ta tambayi me ya sameshi ba,burinta kawai su fice mata daga gida shine abinda ya dameta.
Cikin hijabi kaltum ta shige ta dinga ruzgar kuka,gani take kwata kwata basuzo duniya a sa'a ba,kota wanne bangare qyamata ce da baqinjini yake bibiyarsu,tana iya jin yadda ummans keta sauke ajiyar zuciya akai akai,kamar qaramin yaron da aka yiwa shegen duka.
Tun bilal na nishi lokaci lokaci yana cewa
"Wayyo Allaj cikina" har wani wahalallen bacci mata dadi yayi awon gaba dashi.
Duk yadda kaltume kejin wannan daren bacci yayi kadan ya dauketa amma sai daya gwada mata qarfa qarfarsa,can tsakiyar dare sanda suke zaune ita da ummanta,kowa tunaninsa yayi nisa kan meye makomars a gobe da safe idan inna ta tsaya kan ra'ayinta na su bar mata gida?,da wannan tambaya mai nauyi da firgici baccin ya sureta.
Ƙaqqarfar bugun qofar da aka yiwa dakin ta samu nasarar ratsawa har cikin tsakiyar baccinsu,ya haifar musu da farkawa gaba dayansu a firgice daga dan gajeran barcin da ya wafci idanuwansu,duka kowanne ya miqe ya zauna daram saman mazaunansa suna duban qofar,yayin carar zakaru ke tashi daga wancan gida zuwa wannan gida,da alama a yanzu ne assalatu tayi.
Inna ce tsaye a kansu tana dubansu,kai kace daren jiya batayi barci ba,kamar ta zauna gadin daren ne tana jiran asuba tayi
"Saiku tashi ko?,kusan inda dare yayi muku" ta fada kanta tsaye,tana sake matse fuska.
Mamaki maganarta ta basu,kaltum takai dubanta ga tsakar gidan,dudum yake,duhunsa bashi da maraba da tsakiyar dare,hakan kuwa ba abun mamaki bane,saboda ko salla ba'a shiga ba a qananun masallatan dake qauyukan
"Wai da gaske kike inna?,to ina zamuje?"
"Ki tambayi uwarki!" Innan ta fada tana zazzaro idanuwa,tare da nuna ummanmu da yatsa,waiwayawa tayi kuwa ta kalli ummansu,wadda ta sad da kai
"Duk yanayin data samu kanta ita ta jama kanta,babu yadda banyi da ita kada ta haifeku a gidan nan ba,ta fito ta samu wani mai damshin arziqin ta aura amma taqi,sai data tara ku kuma sannan yanzu haka kawai saita debomin wallahi,to ba dani ba sam,duniya da girma da fadi,ai maye baya ci kansa ba" ta fada tama riqe da qugunta kamar qaramar yarinya
"Kiyi haquri inna zuwa gobe,ko anjima gari ya sake wayewa....zamu tafi" cewar umma cikin sanyin murya,a karon farko kenan tsakanin jiya da yau a aka fara dambarwar
"Me? Inji akuya?,idan kin isa shegiya nake,billahillazi kinyi kadan,ko sakan bazan qara muku ba,ku tashi ku fita?,idan kunqi kuwa saina tijara ku" ta fada cikin bambami da daga murya
"Qofar gida zan tsaya ma naga fitarku,wallahi bame qara yimin minti guda a guda" ta sanya kai tana shirin ficewa daga dakin sukayi karo da jafaru
"Wai inna maganar ce ne da farar safiya ko ince tsakar dare?,haba inna,ko gari ai kya bari ya gama wayewa ko?" Ya fada cikin jin takaicin halin innar
"Kai jafaru,kai jafaru,kai jafaru,sau nawa na kira sunanka?,ba sau uku ba?,to wallahi wallahi ka fita daga idanuna,idan ka qara magana a nan saina tsintstsinka maka mari" tafada tana huci gami da zare masa ido,ala dole yaja bakinsa yayi shuru yana kallo tana ci gaba da tijararta har zuwa qofar gida,fadi take
"Ki fito ku barmin gidana,wallahi sai kun tafi,ku fita ko nasa a fitarmin daku" cikin daga murya,wanda sautinta ya karade dukka maqotan take gefe da gefe gaba da bayan gidansu,ya kuma fara jan hankalin jama'a wadanda suka tattashi domin bada farali na sallar asuba,masu fita zuwa masallaci maza,dama mata masuyin sallar a cikin gidajensu.
Kafin kace meye mutane sun dan fara tattaruwa,dai dai sanda ummanmu dasu kaltum ke fitowa a gidan,kaltum na riqe da bilal da har yanzu jikinsa baiyi qwari ba,ummansu na riqe da 'yan kayanta data debo.
Fitowarsu tasa jama'a suka koma kallon kallo,kowa ka kalla fuskarsa cike da alhini da kuma mamaki,anya kuwa innar kanta qalau?,wasu daga cikin jama'ar suka soma yiwa kansu tambaya,wasu kuwa sun riga da sunsan lafiya ras take,saboda sanin hali yafi sanin kama,kowa Yasan innar yasan abinda zata aikata da wanda ba zata aikata ba,a tsahon shekarun da take zaunen a nan,duk mutumin daya zauna da ita ya santa da halaye gusa biyu datayi shura dasu,zallar masifa da kuma son abun duniya,ba shakka iya wadan nan dabi'u kawai sun isa suyi mata jagora ga abinda ta aikata din a yanzu.
Suna sake nisa da ita kunnuwansu na sake kasa kama maganganu da hargowar data ke musu,idanuwan ummanmu a wannan karon sun gaza riqe ruwan hawaye da suka danno cikin idanuwanta,irin abinda innar tayi mata a yanzu yana cikin lissafin irin abubuwan da take zato tunani ko mafarkin innar zata iyayi mata a rayuwa,ta shiga matuqar rudani da mamakinta,ta zaci koda bare ne wanda innar bata sanshi ba bawai gudan jininta ba bazata aikata masa haka ba,wai dama haka qin jininta yayi nisa cikin ran inna?,laifinta kawai don babansu bashi da komai,bai mallaki abun duniya ba har ya mutu?,laifinta don taqi kashe aurenta sanda arziqi da dukiyar amadu ta durqushe?,ta gaza tantance wanne ne laifi cikin abinda ke faruwa,dabi'ar da inna ke nuna mata lailan wa naharan?,ko kuma ita abinda ta aikata da kuma yanayin rayuwa a mahaifinsu ya sami kanshi kafin rasuwarsa?.
"Ummanmu......ina zamuje yanzu?" Muryar bilal dake cike da gajiya da kuma ciwo ta fargar da ita cewa a hanya suke,sai a sanna ta daga kanta,sunyi nisa da gidan inna,zuwa sannan an shishshiga masallatai sallar asubahi
"Muje gidan umma altine" kaltum ta amsa masa maimakon umman tasu
"Ko umma?'" ta maida tambayar gareta don ta samu tabbacin abinda ta yanke din ya yiwa umman tasu.
Har cikin ranta taji bai dace sujewa altine ba,saboda ita kanta neman dauki da taimako takeyi,nauyin dake kanta itama tallafi take buqata,zuwanta wajenta a irin wannan lokacin tamkar rashin sanin abinda ya kamata ne,uwa uba ma ita din qanwarta ce bawai yaya ba,don haka saita girgizawa kaltum kai
"A'ah,ba gidanta zamu je ba,itama tana da wasu wahalhalu da dawainiya a kanta....."
"To gidan yakumbo indo?" Bilal yayi saurin sake fada,da alama a jigace yake,so yake kawai su samu muhalli ko wanne iri ne da zai bashi damar hutu.
Nan ma kai umman ta girgiza
"Itama macace,a qarqashin wani take,ba zamuje mu dora mata jigilar mu ba har mu uku"
"To gidan kawu ado" wannan karon kaltum ce ta fadi haka,shuru umma tayi,yayin da suma dukka sukayi shurun suna dubanta,daga kai tayi,sai taga dukkaninsu ita suka zubawa ido suna jiran suji amsa
"Shikenan,muje can din" ta gada tana riqe hannun bilal da kyau,don kaltum ta samu ta huta itama,don tafiyace miqaqqiya a qafa daga nan zuwa gian kawu ado,tunda babu wani abun hawa sa zasu hau da zai rage musu wahalar tafiyar,a qalla zasu iya shafe awanni biyu kafin sukai.
29
D/Z
*wannan littafin na kudine,sharinga dinsa zuwa wasu gurare tamkar zalunci ne garemu,kiyiwa girman Allah ki barshi a inda kika ganshi,idan kin da buqatar karantawa ki biya naki ta wadannan numbers din dake qasa*
08184017082
Ko kuma
09134848107
Kafin su iso gidan kawu ado gari yayi haske tarwai,don har wasu daga cikin mutane sun fara fita zuwa sabgogin gabansu na rayuwa.
Area din da gidan kawu ado yake,area ce mai dan kyau,saboda akwai gidajen dake da ginin bulo ma,kamar yadda gidan kawu adon yake ginin bulo,da malalen siminti a tsakar gidansu,wanda hakan yasa gidan ya bambanta da sauran gidaje wansa jar qasa tayi musu qawanya har cikin tsakae gidajensu.
Da sallama suka shiga gidan,matarsa dake cikin dakin girki ta amsa tana leqo da kanta daya dan rage girma saboda hayaqin icce da take amfani dashi.
Suna hada ido da umma saita miqe tana fitowa daga dakin girkin
"Lale maraba,kune a tafe?" Ta fada fuskarta a washe tana qoqarin goge fuskarta,gefe daya qasan zuciyarta tana mamaki
"Wallahi mune tsaiba,kin ganmu da sassafe ko?" Murmushi tayi tana qoqarin karbar kayan hannun umman,don tsaiban badai kirki da daraja dangin mijinta ba
"Ah haba dai yaya?,wacce safiya?,bayan yara ma duka sun wuce makaranta?,ku shigo daga ciki mana" ta fada tana yin gaba,umma bilal da kaltum bita a baya,tana sake musu barka da zuwa.
Faffadar rumfarta dake malale da leda da kujeru 'yan duƙui duƙui suka shiga,ta ajjiye kayan itama tana zama idanuwanta kan bilal