Sashe 48
Dabiar Zuciya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Uhumm,ya kuma kenan,ai dama idan ka daurewa yaro gindi wahala ya sameka,nan ya daukarmin langa langa ya saida ya cinye kudin,uwar bata iya tabuka komai ba,to saiki taso kije kiga gingimemen aikin da danki ya janyo miki" yana kaiwa nan yayi gaba,munzali da muzammilu suka take masa baya.
A rude kaltum dake tsaye ta dubi ummansu,har yanzu bata fasa aikin tsinke zogale da takeyi ba,kai bakace da ita ake ba,kamar kaltum zata saki kuka tace
"Ummanmu....ki taso kije" bata daga kanta ba ta amsa mata
"Na taso nayi me?" Jin hakan sai kaltum din ta kasa jumurin jira,cikin hanzari ta nufi qofa.
Gidan nasu ya cika kamar wanda ake wani dan biki,bilal na tsakiya kamar an samu nama,tsakanin babansu da munzali,harma da muzammilu,suna sauraren jawaban qarya daga bakin musbahu,wanda yana kaiwa qarshe,ba tare da baban ya tsaya anji ta bakin bilalun ba yace
"Ai nasan za'a rina,tunda ka faro daga gida dama na waje sune al'umma ta gaba.....kai musbahu,kuje,gobe da safe da kaina zan tasoshi har zuwa wajen aikin naku" saiya juya ya baiwa munzali umarni sukai bilal ciki,suka tankadashi sai sashen nasu
"Don ubanka ina kayan mutane?" Baban dake tsaye bisa kansa kamar zai hadiyeshi ya fada,cikin qwalla bilal yace
"Wallahi baba ban taba daukan kayan kowa ba...."
"Qarya kake munafukin yaro.....ba daga kaina ka fara ba?,tunda ba zaka fada ba,munzali ku lallasamin dan banza" ya fada yana ja baya.
Ai kuwa tamkar suna jiransa ne suka hau dukan bilal babu ji babu gani,irin duka na rashin hankali,dukan da babu tsari a cikinsa,duka tako ina,duk inda suka samu ko hannunsu yakai nausa suke,tun yana iya jurewa har ya fara zabga ihu yana neman taimako,kaltum ta kasa daurewa,ta durfafesu cikin qaraji tana neman su bari,amma ina,babu wanda ya saurareta a cikinsu,saima duka da munzali yakai mata,wanda dama tun wancan lokacin bai huce da ita ba
"Tofa....qauna,saboda soyayya shine zaki hana a hukunta yaro,tunda ya fara dauke dauke kuma wa yasan me zai faru naj gaba?" Inna laure dake tsaye abinta daga bakin qofa tana shan kallo tavfada hankalinta kwance,kamar ba dukan daya wuce qa'ida sukema bilal ba.
Kuka ta fashe dashi ganin yadda bilal din ya zube gaba daya ya daina yunqurin qwatar kansa sanda suka kaima cikinsa suka kusan a tare munzalin da muzammilun,a gigice tayi wajen ummansu
"Ummanmu,don Allah ki hanasu.....zasu kasheshi wallahi,kinga ya fadi fa ummanmu,kice wani abu.......
28
D/z
*wannan littafin na kudine,sharinga dinsa zuwa wasu gurare tamkar zalunci ne garemu,kiyiwa girman Allah ki barshi a inda kika ganshi,idan kin da buqatar karantawa ki biya naki ta wadannan numbers din dake qasa*
08184017082
Ko kuma
09134848107
Wani irin miqewa tayi da hanzari,har tana hankade kaltum dake duqe a gabanta tana son tace wani abu
"Kada wanda ya sake tabamin yaro a cikinku" muryar ummanmu ta ratsa tsakanin ihun bilal da dukan da suke masa.
Tsabar mamakin da sukaji ya sanyasu tsaiwa cak daga abinda sukeyi din,kowannensu ya waiwayo cike da mamaki,mamakin jin kalma daga bakinta dangane da danta a rana ta farko a lokaci na farko,tsahon zamansu da ita,tarin kawaici dauke kai gami da haquri dake cikin dabi'unta yau dukka ta kauda,basu taba jin kalma makamanciyar wannan daga bakinta ba,sai a yau din.
Idanu dukkansu suka zuba mata sanda take takowa inda bilal ke kwance hajaran majaran,idanuwanta na tara ruwan qwallar da taketa bakin qoqarin hanata zubowa.
Hannu ta sanya zata dago bilal din,muryar babansu tayi mata waigi
"Sakeshi,kada ki kuskura ki tabashi" ya fada cikin fushi,bata fasa sanya hannu ta daga shin ba kamar yadda ya haneta,ta miqar dashi tsaye,tsaiwar daya kasa yinta da kyau,saida kaltum ta rugo ta tayata riqeshi.
"Zuwaira!,ni nake bada umarnin a hukunta min dana,gaban 'ya'yana kike nuna musu ban isa ba?,bayan rainin da kika saka suka riga suka gama yimin shi?,ni zaki hana hukunta dana,nace kada kiyi ki aikata?" Yana fada cike da kunya da kuma mamakin yadda a yau ta saba umarninsa,abinda bazaice ga ranar data taba yinsa ba tsahon zamansu da ita
"Tabdijan,to wallahi wallahi billahillazi ba'ayi matar da zan bada umarni a gidana ta bijire ba,ba'ayi matar da zan gyatta kara ta tsallake ba.....duk zuba miki idanun da nayi kika lalata min yaro bai isheki ba?,to ki tattara ya naki ya naki ki tafi gidanku.....kai munzali.....muje"ya fada yana saba babbar rigarsa yanayin gaba kamar zai tashi sama,sai suka mara masa baya suma ba tare da sun tsaya jiran komai ba.
Kalmar ta tafi gidan nasu ta shigeta da wani irin qarfi da ba zata,kalmar da bata taba shiga tsakaninsu ba kenan tunda sukayi aure,sanoda haqurin datake hadiya a kulli yaumin,bata taba kawowa ranta amadun zai iya gaya mata haka ba,a tsayin shekarun da suka kwashe a tare,rauni ne sosai ya mamayeta,yayin da tausayin mahaifiyarta ya rufe kaltum,ta san tsoronta,tasan fargabarta,tasan dalilin daya sanya taji rauni akan kalmar taje gidansu.
"Mu tafi ummanmu,mu tafi mubar masa gidan kamar yadda ya buqata" kaltum ta fada da wani irin emotion me taba zuciya,a lokacin da suka sanya bilal a gaba,wanda har yanzu dafe yake da cikinsa.
Kai umman ta girgiza
"Babu abinda zamu kaltume,bamu da inda ya wuce nan din,koda zan tafi ku baku da gidan daya wuce nan,nan ne gidanku,a nan zaku ci gaba da zama" sai muryarta ta fara rawa,da alama kuka keson cij qarfinta,kukan da tuni kaltum ta fashe da nata,ganin irin murqususun da bilal yakeyi.
Basu gushe ba suna zaune a haka tsahon kusan awa guda suka sake jin tafiyar mahaifin nasu,kowanne yayi sak yana duban hanya.
Turus yayi daga nesa yana qare musu kallo,cikin wata hargoqa da hargagi ya fara nunata da yatsa
"Ba cewa nayi ki tattara kayanki ki tafi gida ba?,to ki hada ya naki ya naki,na baki minti goma,ki tabbatar kafin na fito daga daki babu ke a wajen nan,yau zaki gane idan ina da amfani" daga haka yayi fuuu ya wuce dakinsa ya bankada ya shige.
Tsam ta miqe daga tsakiyarsu ta nufi dakinta,kaltume ta rufa mata baya cikin kuka kai taba zuciya,tana tsaye umman tasu ta zari kayanta guda uku ta zura hijabinta sannan ta juyo ta sake fitowa,kaltum ta biyota tana cewa
"Ummanmu.....ki tsaya na dauko mana kayanmu kinji don Allah" waiwayowa tayi ta dubesu,cikin muryar dake nuna nauyin abinda take dannewa
"Ba inda zaku kaltume,nan ne gidanku,baku da inda ya wuce nan...."
"Ki tattara tsiyarki su biki,babu wanda zai zaunar min daga ita har shi,yara kamar yaran Allah bani,maza kubi uwarku" ya fada yana watsa hannu,kamar wanda ke kaɗa kaji dake son yi masa ɓarna.
A sukwane ta shiga dakinta ta figi hijabinta,ta tazo ta taimakawa bilal suka rufa mata baya duk a cikin hanzari,ganin cewa tuni har ita din tayi gaba.
Tsaiwa tayi da tafiyar da take sanda tajiyo takun sawunsu a bayanta,ta waiwayo tana kallonta tana riqe da bilal
"Me yasa zaku biyoni kaltum,ko kuma gidan mahaifinku,can ne marufar asirinku"
"Kiyi haquri ummanmu,ba zamu iya komawa ba,ba zamu iya barinki ba,koda zamu koma ma ummanmu ta yaya zamu barki a irin wannan daren ke daya ki tafi har gidan inna?,barema tunda ya koreki tare ya koremu".
Tsaiwa tayi tana hadiye wani abu mai tauri daya riqe mata maqoshi,tana kallon yadda take riqe da bilal cikin ciwo,ko ina na jikinsa rawar sanyi yake saboda duka,da alama zazzabine ke shirin kada shi.
Itama tanajin wani wawakeken rauni na shirin kama zuciyarta tun daga wannan lokacin na rabuwa dasu,bata ce su koma saboda fushi ko qyamata ba,ta fada ne saboda nuna musu muhimmancin mahaifinsu cikin rayuwarsu,an kai gabar da bazata iya sake cewa su koma ba,don haka ga juya taci gaba da tafiya suka mara mata baya.
Kafin sukai gidan innar sun shafe lokaci mai da tsaho saboda yanayin jikin bilal,ga kuma tafiyar qasa,hakan ya qarawa dare tsaho kafin su isa,don har sunyi tsammanin ma zasu taras da gidan a garqame,saidai sun taki sa'a,gidan yana a bude ne,amma kuma an sayashi,da alama gab ake da rufeshi.
Sallama kusan hudu umman tayi amma ba'a amsa ba,saita qarasa zuwa qofar dakin mahaifiyarta ta daga labulen tana sake maimaita sallamar.
Saman gadonta na rufa ta hangeta a kashingide daga baki baki,da alama bacci ne ya kwaeheta ba tare data shirya hakan ba,saita saki labulen tana komawa da baya,ta dubi su kaltum
"Muje,inna tayi bacci" ta fada tana yin gaba,tare da duba dakunan dake cikin dakin,ta bude musu daya daga ciki,wanda babu komai ciki sai sumunti da tabarmar kaba.
Cikin kayantabta cire zani ya shimfidawa bilal saman tabarmar,kaltum ta taimaka masa ya kwanta,dukkansu idanuwansa a kansa yadda yake murqususu,zuciyar kaltum ta sake karyewa,cikin hawaye tace da ummansu
"ummanmu.....ruwan zafi ya kamata a saka masa a jikinsa fa,idan ba haka ba bazai iya barci ba" ita kanta tasan da hakan,amma batason daga shigowarsu gidan su taba wani abun na innar ba tare da saninta ba.
Saidai kafin ta qare tunaninta tuni har kaltum ta isa kitchen din innar,ta kuma fara hada wuta,babu jimawa ta dora ruwan,bai dauki lokaci ba ya tafasa,ta juyoshi ta nufo inda dakin da suke ta ajjiye a tsakaninsu,sannan ta taimaka masa ya tashi ya zauna da qyar yana nishi yana numfarfashi.
Dankwalin ummansu ta karba ta fara gasa masa jiki,tuni ya fara nishi yana kiran wayyo Allah,duk inda tasa ruwan mai zafi zafi ta danna masa sai ya saki ihu cike da radadi yana murgina kai yana cije labba.
Ihu ihun bilal din ya farkar da inna a firgice,saura kadan tayi adungure daga saman gadon nata zuwa qasa,sai data kaza kunne,ta tabbatar bil'adama me sannan ta zame ta sauko daga gadon dankwalinta a hannu tana sauri kamar zata ci da baka,tanason ganin wadanda suka shigo gidan.
Ta tur qyauren dakin dai dai sanda kaltum ta gana gasa masa jikin,ta kuma maidashi ya kwanta
"Me zan gani haka ni zainabu?,zuwaira?,meye haka?" Ta fada cikin hargagi da masifarta wadda ta riga data zame mata jinin jikinta
"Wallahi mune innah" sosai ta shigo dakin tana qare musu kallo
"Aina gani,naga kune din,yo meye haka za'amin irin wannan gangankon da tsakar dare a diro min gida ba tare da masaniyata ko izini na ba?,kamar masu fashi da makami?" Dan shuru umman tayi,tana fasalta da harshen da zata yiwa inna bayani
"Ki bude baki kiyimin magana,keda 'ya'yanki kun yimin duru duru" tayi maganar tana rungume hannayenta a qirji,tana kuma sake zubawa inna ido
A rude kaltum dake tsaye ta dubi ummansu,har yanzu bata fasa aikin tsinke zogale da takeyi ba,kai bakace da ita ake ba,kamar kaltum zata saki kuka tace
"Ummanmu....ki taso kije" bata daga kanta ba ta amsa mata
"Na taso nayi me?" Jin hakan sai kaltum din ta kasa jumurin jira,cikin hanzari ta nufi qofa.
Gidan nasu ya cika kamar wanda ake wani dan biki,bilal na tsakiya kamar an samu nama,tsakanin babansu da munzali,harma da muzammilu,suna sauraren jawaban qarya daga bakin musbahu,wanda yana kaiwa qarshe,ba tare da baban ya tsaya anji ta bakin bilalun ba yace
"Ai nasan za'a rina,tunda ka faro daga gida dama na waje sune al'umma ta gaba.....kai musbahu,kuje,gobe da safe da kaina zan tasoshi har zuwa wajen aikin naku" saiya juya ya baiwa munzali umarni sukai bilal ciki,suka tankadashi sai sashen nasu
"Don ubanka ina kayan mutane?" Baban dake tsaye bisa kansa kamar zai hadiyeshi ya fada,cikin qwalla bilal yace
"Wallahi baba ban taba daukan kayan kowa ba...."
"Qarya kake munafukin yaro.....ba daga kaina ka fara ba?,tunda ba zaka fada ba,munzali ku lallasamin dan banza" ya fada yana ja baya.
Ai kuwa tamkar suna jiransa ne suka hau dukan bilal babu ji babu gani,irin duka na rashin hankali,dukan da babu tsari a cikinsa,duka tako ina,duk inda suka samu ko hannunsu yakai nausa suke,tun yana iya jurewa har ya fara zabga ihu yana neman taimako,kaltum ta kasa daurewa,ta durfafesu cikin qaraji tana neman su bari,amma ina,babu wanda ya saurareta a cikinsu,saima duka da munzali yakai mata,wanda dama tun wancan lokacin bai huce da ita ba
"Tofa....qauna,saboda soyayya shine zaki hana a hukunta yaro,tunda ya fara dauke dauke kuma wa yasan me zai faru naj gaba?" Inna laure dake tsaye abinta daga bakin qofa tana shan kallo tavfada hankalinta kwance,kamar ba dukan daya wuce qa'ida sukema bilal ba.
Kuka ta fashe dashi ganin yadda bilal din ya zube gaba daya ya daina yunqurin qwatar kansa sanda suka kaima cikinsa suka kusan a tare munzalin da muzammilun,a gigice tayi wajen ummansu
"Ummanmu,don Allah ki hanasu.....zasu kasheshi wallahi,kinga ya fadi fa ummanmu,kice wani abu.......
28
D/z
*wannan littafin na kudine,sharinga dinsa zuwa wasu gurare tamkar zalunci ne garemu,kiyiwa girman Allah ki barshi a inda kika ganshi,idan kin da buqatar karantawa ki biya naki ta wadannan numbers din dake qasa*
08184017082
Ko kuma
09134848107
Wani irin miqewa tayi da hanzari,har tana hankade kaltum dake duqe a gabanta tana son tace wani abu
"Kada wanda ya sake tabamin yaro a cikinku" muryar ummanmu ta ratsa tsakanin ihun bilal da dukan da suke masa.
Tsabar mamakin da sukaji ya sanyasu tsaiwa cak daga abinda sukeyi din,kowannensu ya waiwayo cike da mamaki,mamakin jin kalma daga bakinta dangane da danta a rana ta farko a lokaci na farko,tsahon zamansu da ita,tarin kawaici dauke kai gami da haquri dake cikin dabi'unta yau dukka ta kauda,basu taba jin kalma makamanciyar wannan daga bakinta ba,sai a yau din.
Idanu dukkansu suka zuba mata sanda take takowa inda bilal ke kwance hajaran majaran,idanuwanta na tara ruwan qwallar da taketa bakin qoqarin hanata zubowa.
Hannu ta sanya zata dago bilal din,muryar babansu tayi mata waigi
"Sakeshi,kada ki kuskura ki tabashi" ya fada cikin fushi,bata fasa sanya hannu ta daga shin ba kamar yadda ya haneta,ta miqar dashi tsaye,tsaiwar daya kasa yinta da kyau,saida kaltum ta rugo ta tayata riqeshi.
"Zuwaira!,ni nake bada umarnin a hukunta min dana,gaban 'ya'yana kike nuna musu ban isa ba?,bayan rainin da kika saka suka riga suka gama yimin shi?,ni zaki hana hukunta dana,nace kada kiyi ki aikata?" Yana fada cike da kunya da kuma mamakin yadda a yau ta saba umarninsa,abinda bazaice ga ranar data taba yinsa ba tsahon zamansu da ita
"Tabdijan,to wallahi wallahi billahillazi ba'ayi matar da zan bada umarni a gidana ta bijire ba,ba'ayi matar da zan gyatta kara ta tsallake ba.....duk zuba miki idanun da nayi kika lalata min yaro bai isheki ba?,to ki tattara ya naki ya naki ki tafi gidanku.....kai munzali.....muje"ya fada yana saba babbar rigarsa yanayin gaba kamar zai tashi sama,sai suka mara masa baya suma ba tare da sun tsaya jiran komai ba.
Kalmar ta tafi gidan nasu ta shigeta da wani irin qarfi da ba zata,kalmar da bata taba shiga tsakaninsu ba kenan tunda sukayi aure,sanoda haqurin datake hadiya a kulli yaumin,bata taba kawowa ranta amadun zai iya gaya mata haka ba,a tsayin shekarun da suka kwashe a tare,rauni ne sosai ya mamayeta,yayin da tausayin mahaifiyarta ya rufe kaltum,ta san tsoronta,tasan fargabarta,tasan dalilin daya sanya taji rauni akan kalmar taje gidansu.
"Mu tafi ummanmu,mu tafi mubar masa gidan kamar yadda ya buqata" kaltum ta fada da wani irin emotion me taba zuciya,a lokacin da suka sanya bilal a gaba,wanda har yanzu dafe yake da cikinsa.
Kai umman ta girgiza
"Babu abinda zamu kaltume,bamu da inda ya wuce nan din,koda zan tafi ku baku da gidan daya wuce nan,nan ne gidanku,a nan zaku ci gaba da zama" sai muryarta ta fara rawa,da alama kuka keson cij qarfinta,kukan da tuni kaltum ta fashe da nata,ganin irin murqususun da bilal yakeyi.
Basu gushe ba suna zaune a haka tsahon kusan awa guda suka sake jin tafiyar mahaifin nasu,kowanne yayi sak yana duban hanya.
Turus yayi daga nesa yana qare musu kallo,cikin wata hargoqa da hargagi ya fara nunata da yatsa
"Ba cewa nayi ki tattara kayanki ki tafi gida ba?,to ki hada ya naki ya naki,na baki minti goma,ki tabbatar kafin na fito daga daki babu ke a wajen nan,yau zaki gane idan ina da amfani" daga haka yayi fuuu ya wuce dakinsa ya bankada ya shige.
Tsam ta miqe daga tsakiyarsu ta nufi dakinta,kaltume ta rufa mata baya cikin kuka kai taba zuciya,tana tsaye umman tasu ta zari kayanta guda uku ta zura hijabinta sannan ta juyo ta sake fitowa,kaltum ta biyota tana cewa
"Ummanmu.....ki tsaya na dauko mana kayanmu kinji don Allah" waiwayowa tayi ta dubesu,cikin muryar dake nuna nauyin abinda take dannewa
"Ba inda zaku kaltume,nan ne gidanku,baku da inda ya wuce nan...."
"Ki tattara tsiyarki su biki,babu wanda zai zaunar min daga ita har shi,yara kamar yaran Allah bani,maza kubi uwarku" ya fada yana watsa hannu,kamar wanda ke kaɗa kaji dake son yi masa ɓarna.
A sukwane ta shiga dakinta ta figi hijabinta,ta tazo ta taimakawa bilal suka rufa mata baya duk a cikin hanzari,ganin cewa tuni har ita din tayi gaba.
Tsaiwa tayi da tafiyar da take sanda tajiyo takun sawunsu a bayanta,ta waiwayo tana kallonta tana riqe da bilal
"Me yasa zaku biyoni kaltum,ko kuma gidan mahaifinku,can ne marufar asirinku"
"Kiyi haquri ummanmu,ba zamu iya komawa ba,ba zamu iya barinki ba,koda zamu koma ma ummanmu ta yaya zamu barki a irin wannan daren ke daya ki tafi har gidan inna?,barema tunda ya koreki tare ya koremu".
Tsaiwa tayi tana hadiye wani abu mai tauri daya riqe mata maqoshi,tana kallon yadda take riqe da bilal cikin ciwo,ko ina na jikinsa rawar sanyi yake saboda duka,da alama zazzabine ke shirin kada shi.
Itama tanajin wani wawakeken rauni na shirin kama zuciyarta tun daga wannan lokacin na rabuwa dasu,bata ce su koma saboda fushi ko qyamata ba,ta fada ne saboda nuna musu muhimmancin mahaifinsu cikin rayuwarsu,an kai gabar da bazata iya sake cewa su koma ba,don haka ga juya taci gaba da tafiya suka mara mata baya.
Kafin sukai gidan innar sun shafe lokaci mai da tsaho saboda yanayin jikin bilal,ga kuma tafiyar qasa,hakan ya qarawa dare tsaho kafin su isa,don har sunyi tsammanin ma zasu taras da gidan a garqame,saidai sun taki sa'a,gidan yana a bude ne,amma kuma an sayashi,da alama gab ake da rufeshi.
Sallama kusan hudu umman tayi amma ba'a amsa ba,saita qarasa zuwa qofar dakin mahaifiyarta ta daga labulen tana sake maimaita sallamar.
Saman gadonta na rufa ta hangeta a kashingide daga baki baki,da alama bacci ne ya kwaeheta ba tare data shirya hakan ba,saita saki labulen tana komawa da baya,ta dubi su kaltum
"Muje,inna tayi bacci" ta fada tana yin gaba,tare da duba dakunan dake cikin dakin,ta bude musu daya daga ciki,wanda babu komai ciki sai sumunti da tabarmar kaba.
Cikin kayantabta cire zani ya shimfidawa bilal saman tabarmar,kaltum ta taimaka masa ya kwanta,dukkansu idanuwansa a kansa yadda yake murqususu,zuciyar kaltum ta sake karyewa,cikin hawaye tace da ummansu
"ummanmu.....ruwan zafi ya kamata a saka masa a jikinsa fa,idan ba haka ba bazai iya barci ba" ita kanta tasan da hakan,amma batason daga shigowarsu gidan su taba wani abun na innar ba tare da saninta ba.
Saidai kafin ta qare tunaninta tuni har kaltum ta isa kitchen din innar,ta kuma fara hada wuta,babu jimawa ta dora ruwan,bai dauki lokaci ba ya tafasa,ta juyoshi ta nufo inda dakin da suke ta ajjiye a tsakaninsu,sannan ta taimaka masa ya tashi ya zauna da qyar yana nishi yana numfarfashi.
Dankwalin ummansu ta karba ta fara gasa masa jiki,tuni ya fara nishi yana kiran wayyo Allah,duk inda tasa ruwan mai zafi zafi ta danna masa sai ya saki ihu cike da radadi yana murgina kai yana cije labba.
Ihu ihun bilal din ya farkar da inna a firgice,saura kadan tayi adungure daga saman gadon nata zuwa qasa,sai data kaza kunne,ta tabbatar bil'adama me sannan ta zame ta sauko daga gadon dankwalinta a hannu tana sauri kamar zata ci da baka,tanason ganin wadanda suka shigo gidan.
Ta tur qyauren dakin dai dai sanda kaltum ta gana gasa masa jikin,ta kuma maidashi ya kwanta
"Me zan gani haka ni zainabu?,zuwaira?,meye haka?" Ta fada cikin hargagi da masifarta wadda ta riga data zame mata jinin jikinta
"Wallahi mune innah" sosai ta shigo dakin tana qare musu kallo
"Aina gani,naga kune din,yo meye haka za'amin irin wannan gangankon da tsakar dare a diro min gida ba tare da masaniyata ko izini na ba?,kamar masu fashi da makami?" Dan shuru umman tayi,tana fasalta da harshen da zata yiwa inna bayani
"Ki bude baki kiyimin magana,keda 'ya'yanki kun yimin duru duru" tayi maganar tana rungume hannayenta a qirji,tana kuma sake zubawa inna ido