Sashe 88
Dabiar Zuciya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Ana gama sallar magarib a kawomin abinci" ya fada yana lalubar qwayar idanunta da taqi bari ya gani
"Tohm" ta amsa mishi a tausashe,saiya juya yana niyyar barin kitchen din,da sauri mubina takai hannu xata karbi brief case dinsa
"Ya saraki....kawo na tayaka mana"
Batasan ta daga kai ta dubi sashen da suke ba saida suka kusa hada ido da samir,saita sauke kanta,tana jin wani abu na matsar zuciyarta,kunnuwanta naga amsar da xaya bata
"Nop,na gode" ya amsa mata yana yin gaba,binsa da kallo mubina tayi,saita koma da baya ta zauna jikinta na mata sanyi,kada fa ace sauqin kan da take hanga tattare dashi ba haka bane?.
Tun sanda suka baro kitchen din kowanne a cikinsu kuzarinsa ragagge ne,ga kaltum bata da tabbacin abinda ya sanya yanayin jikinta sauyawa,saidai tana jin zuciyarta da gangar jikinta duka babu dadi,hakanan ta kasa sakewa da mubina.
Mubina kuwa hasashenta daya ne,a yau din ta shirya ta kuma tattara dukkan wani qwarin gwiwarta na fuskantar samir din,a yau ta shirya shaida masa abinda yake cikin zuciyarta,durqusawa wada ba gajiyawa bace,matuqar zata samu samir a matsayin mijin aure zata iya aikata dukkan wani abu da bai taka kara ya karya ba irin wannan,bai kuma kasance kauce hanya mabayyaniya ba.
Tana saman abun salla bayan ta idar amma tayi nisa a tunani,maganganun saliha ke dawo mata tar a kwanya tun daxu,idan itace da miji irin samir kenan sai taga abinda ya turewa buzu nadi?,ita din zata iya itama kamar yadda saliha tace?,wannan tamkar tunkarar wani babban yaqi ne wanda batasan ya tsakiyarsa zata kaya ba,qarshensa dama nasara ce ko akasinta,batasan wanne matsayi take dashi ko ta taka a zuciyarsa ba bare ta dora daga nan,tafi kowa sanin yawan 'yamnatan dake qaunarsa suke kuma farautar soyayyarsa,tun kafin ta soma jin cewa itama ya kamata ta tabbatarwa da kanta matsayinta a wajensa,tana ji da ganin komai daga wajen jawahir,wani lokaci ita kanta jawahir din takan qi daga wayar wasu da dama daga cikinsu,wadanda ke kamun qafa da ita,to amma idan ta saddaqar.....hakan na nufin zai auri wata a gabanta kenan kamar yadda ta soma jin qishin qishin?,haka na nufin warwarewar igiyar aurensu kenan?, Ta koma ta auri wani?,idan kuma qudurinta ya tabbata fa?,ta yayq zai kalli idanun family dinsa ya shaida musu cewa ita din matarsa ce daya aurota a wani qauye waishi dinya ba tare da sanin magabatansa ba?,idan maganar ta fito waye da waye zai amsheta?,waye kuma zai mata mummunan kallo da mummunan fassara?.
Samun kanta tayi da runtse idanunta sanda sunan mommy da najwa ya darsu a ranta
"Hasbunallahu wa ni'imal wakil" labbanta suka motsa a hankali,kalmar ta kwarara cikin zuciyarta,sannu a hankali kuma hancinta ya cika da qamshin turaren data tabbatar a zahiri take iya jiyoshi,kafin kuma fa bude idanun nata muryar mubina ta cika kunnuwanta.
"Kaltum da magariba fa yace akai masa,nidai a ready,ki debo kayan na tayaki kaiwa,dama inason muyi magana dashi" a nutse ta daga kanta ta sauke ga mubina dake gaban mudubi tana sake fesa turare baya wancan data fesa,wani abu ya matse zuciyar kaltume,amma saita aro jarumta ta miqe tana nannade abun sallarta ba tare data cewa mubina komai ba ta fice izuwa kitchen.
Tana tsaka da harhada kayan abincin mubinan ta shigo,tayi shar cikin wani riga da skert da yadin material na mata me sulbi,sai baza qamshi take kamar tayi barin turare.
Ita tayi uwa tayi makarbiya ta amshe kwandon kayan abincin,kaltum din najin wani abu me kama da haushi yana son sauka a zuciyarta ta sakar mata kwandon,ko banza ita din macace,ya kamata kuma ta mutunta tare da martaba darajarta da mutuncinta na diya mace,bata tanka mata surutanta ba ta dauki flask na tea data hada masa ruwan zafin da bata da tabbacin zaisha tunda batasan zabinsa ba ta bita dashi.
Sanya yake da fara qal din long sleeves shirt,wandon jikinsa ash ne me turuwa,wanda iyakacinsa qauri,sun sameshi zaune da jibgin files a gabansa da alama aikin office ne ya deboshi zuwa gida,waya yake amsawa,amma idanunsa na kan qofar sanda suke shigowa.
Amsa sallamar mubinan yayi yana mamakin shigowarta sashen,saidai kafin ya dauke idanunsa ya hangi kaltum daga bayanta,sanye da madaidaicin hijabi light blue,wanda ya haska zagaggayar fuskarta,ya kuma qara fito da hasken qwayar idanunta.
Duk da amsa waya yake amma yana karantar sanyi cikin yanayinta,daga sanda yaji karatu akan girman amana gaba daya hankalinsa ya sake karkata a kanta,yana jin ashe wani babban nauyi ne akansa daya kamata ya bashi dukkan wata kulawa iyaka qarfinsa.
Ya gama wayar ya katseta yana ajjiyeta gefe,yana daga kai suna hada ido da mubina,saita saki murmushi tana sunkui da kai ita dole taji kunya.
Bai kula da wannan ba,ya fara janye hannun rigarshi zuwa baya tare da lanqwashe qafafunsa sanda take aje masa abincin a gabansa
"Sannu" ya furta can qasa,yanayin da sautin maganar ya fito ya tilasta mata daga kai ta dubeshi,saboda yayi maganar ne tamkar me rada.
Fridge ta nufa da niyyar dauko masa ruwa,sai yace
"Dawo nan ki zauna....jeki cikin gidaki daukomin ruwa mara sanyi" yace da mubina.
Dadi ne sosai ya rufeta,ta miqe da saurinta ta nufi qofar fita,saiya maida dubansa ga kaltum dake laluben wajen zama
"Dawo nan" ya fada yana nuna mata gabanshi,a sanyaye ta dawo ta zauna din inda yace mata,duk da cewa zaman kusa dashi irin haka ya mata nauyi amma ba zata iya kaucewa umarninsa ba
"Mene yake damunki?" Ya jefe mata tambayar yana bin fuskarta data dan cika ta murje da kallo kusan irin na qurilla,dan mitsitsin bakinta yana motsawa kadan kadan, Tambayar ta isketa a bazata,don bata zaci jin haka daga bakinsa ba,saita girgiza kanta
"Babu komai" ta amsa mishi,baice mata komai ba sai yaja abincinsa ya fara ci,ba jimawa mubina ta shigo da ruwan,hakan yasa kaltum miqewa tana neman izinin tafiya,don bata jin zata iya zama mubinan tayi maganar da take da qudurin yin a gabanta.
"Ki jirata ku wuce tare....uhmmm,ina jinki" samir ya fada duka lokaci daya.
Bai fasa cin abincinsa ba sanda take koro bayanta cike da kunya da kuma ɗar ɗar,saidai ya kafeta da manyan idanunsa,zuciyarsa cike fal da mamaki,yana kuma qoqarin danne mamakin da kuma dariyar data bashi har ta kammala bayananta.
Abincin ya aje gefe yana kallonta,ya karanci mata wani bin duka tunaninsu iri daya ne,basa kallon abubuwa a yadda suke,sau tari komai suna kallonsa a baibai a maimakon zahirin yadda yake
"Shekarunki nawa?" Tambayar data jita banbarakwai,saita tsargu,ta saci kallon kaltum,wadda tunda ta sunkui da kanta bata dagashi ba
"Sha....sha,ashirin" yadda ta bashi amsar ya tabbatar masa ta dan qara wani abu akan ainihin shekarunta,murmushin gefan baki ya saki
"Karki bari matata ta san ainihin abinda kike nufi ko fada a kaina,if not kuma.....saita zaneki,ku tashi kuje ku kwanta,gobe akwai tafiya a gabanmu" daga haka ya balle murfin ruwa ya soma sha a nutse.
Tuni kaltum takai qofa,saboda amsar daya bayar tamkar saqo ne zuwa ga mutum biyu kenan,wacece matarsa?,me kuma hake nufi da ita,mema maganarsa gaba daya ke nufi?,wadan nan sune ire iren tambayoyin data kwana tana yiwa kanta.
Tana iya jiyo kukan mubina bayan ta gama gayama kaltum din cewa
"Me yasa ya dauka abinda nake gaya masa bada wani muhimmanci ba?,bayan ni ina gaya masa saqo ne mai muhimmanci?" Ba zata iya cewa da ita komai ba,don itama ta kanta take,har ta gama maganganunta ta barke da kuka,tun tana jin kukan mubina har taji shuru,da alama tayi ta gaji,ko kuma bacci ya dauketa,saita sauka a hankali ta zura qafafunta qasa tayi bandaki.
Iska me zafi ya furzar daga bakinsa yana ture ayyukan dake gabansa,duk yadda yaso ya tilastawa kansa yin aikin abun ya gagareshi,fuskar kaltum din yake hangowa sanda mubinan ke isar mishi da saqon,yana sane ya zaunar da ita,akwai abinda yakeson gani da kuma karanta daga gareta,saidai kuma iya zamanta da tashinta taqi bashi damar komai.
Mirginawa yayi ya koma rub da ciki,yana tallafe fuskarsa da tafukan hannayensa,gami da lumshe idanunsa,yana jin yadda sukayi masa nauyi saboda baccin da ya cikasu,amma zuciya da qwaqwalwarsa sunqi bashi hadin kai.
Saidai shi bacci ba'a ci masa bashi,kamar yadda ba'a qayyade masa lokacin yinsa,a hankali idanunsa suka dinga rufewa har sukayi nauyin da bazai iya budesu ba,ya lula duniyar bacci.
*_DUNIYAR MAFARKI_*
A firgice ya farka,saidai bakinsa dauke da addu'a,a hankali yake karanto addu'o'in da ma'aiki ya bayar ga duk wanda yayi mafarki mara dadi,saiya miqe ya nufi bandaki,idanuwansa na haska masa fuskar mahaifiyarsa da yake gani tsugune a gefansa,tana kuma masa nuni da mahaifinsa dake tafiya zuwa wani wawakeken rami wanda wuta ce fal keci a cikinsa.
******Babu wani cikakken kuzari a jikinta take qarasa hada jakar kayanta,banda hajiya qarama da jawahir da suka damu da zuwan nata da babu inda zata.
"Ya na ganki a zaune?" Kaltum tayi qarfin halin yiwa mubina magana sanda ta dauki jakarta bayan samir ya aiko a shaida mata ta fito,kaita girgixa qwalla na sauko mata
"Bani da nutsuwar da zan iya binku,saikun dawo" bata iya ce mata komai ba ta soma takawa tana ficewa,mafarkinta na jiya na sake tsaya mata sosai a rai,duk kuwa da cewa kusan maimaici tayi na abinda ya faru a mafarkinta na wancan karon,amma abun sai ya tsaye mata a rai fiye da wancan.
Ga hoton matar har yanzu a wajenta,amma bata da wanda zai gaya mata wacece ita?,ta kasa fassara ma'anar yawan ganinta da takeyi cikin barcinta,saidai a yanzu zuciyarta ta karkata da zuwa gidan masu lalurar tabin hankali taje ta ziyarci matar data gani a gidan,wadda take mata kama da.matar dake zuwa mata a mafarki,duk da cewa waccar ta gida masu lalurar tabin hankalin shekarunta sunfi na wadda take cikin hoton da kuma wadda take gani a mafarkin tsufa........
52
D/Z
Tunda ta tunkaro wajen ya gaza dauke ganinsa daga kanta,karon farko daya soma ganinta cikin shiga irin wannan.
Abaya ce a jikinta baby pink mai sulbi mai kuma hawa biyu,wadda ta wadata da adon baqaqen duwatsu masu wani irin walwali da sheqi,duk da cewa shiya siyo kayan,amma ba tsammaci zasu karbeta har haka ba.
Yayi tayi rolling mayafin ya baiwa gaban gashinta mai santsi damar fitowa,idan ka kalleta zakayi tsammanin irin kyawawan Ethiopians din nan ne,saboda yadda kalar fatarta ya sake fes kamar bata shiga rana.
"Tohm" ta amsa mishi a tausashe,saiya juya yana niyyar barin kitchen din,da sauri mubina takai hannu xata karbi brief case dinsa
"Ya saraki....kawo na tayaka mana"
Batasan ta daga kai ta dubi sashen da suke ba saida suka kusa hada ido da samir,saita sauke kanta,tana jin wani abu na matsar zuciyarta,kunnuwanta naga amsar da xaya bata
"Nop,na gode" ya amsa mata yana yin gaba,binsa da kallo mubina tayi,saita koma da baya ta zauna jikinta na mata sanyi,kada fa ace sauqin kan da take hanga tattare dashi ba haka bane?.
Tun sanda suka baro kitchen din kowanne a cikinsu kuzarinsa ragagge ne,ga kaltum bata da tabbacin abinda ya sanya yanayin jikinta sauyawa,saidai tana jin zuciyarta da gangar jikinta duka babu dadi,hakanan ta kasa sakewa da mubina.
Mubina kuwa hasashenta daya ne,a yau din ta shirya ta kuma tattara dukkan wani qwarin gwiwarta na fuskantar samir din,a yau ta shirya shaida masa abinda yake cikin zuciyarta,durqusawa wada ba gajiyawa bace,matuqar zata samu samir a matsayin mijin aure zata iya aikata dukkan wani abu da bai taka kara ya karya ba irin wannan,bai kuma kasance kauce hanya mabayyaniya ba.
Tana saman abun salla bayan ta idar amma tayi nisa a tunani,maganganun saliha ke dawo mata tar a kwanya tun daxu,idan itace da miji irin samir kenan sai taga abinda ya turewa buzu nadi?,ita din zata iya itama kamar yadda saliha tace?,wannan tamkar tunkarar wani babban yaqi ne wanda batasan ya tsakiyarsa zata kaya ba,qarshensa dama nasara ce ko akasinta,batasan wanne matsayi take dashi ko ta taka a zuciyarsa ba bare ta dora daga nan,tafi kowa sanin yawan 'yamnatan dake qaunarsa suke kuma farautar soyayyarsa,tun kafin ta soma jin cewa itama ya kamata ta tabbatarwa da kanta matsayinta a wajensa,tana ji da ganin komai daga wajen jawahir,wani lokaci ita kanta jawahir din takan qi daga wayar wasu da dama daga cikinsu,wadanda ke kamun qafa da ita,to amma idan ta saddaqar.....hakan na nufin zai auri wata a gabanta kenan kamar yadda ta soma jin qishin qishin?,haka na nufin warwarewar igiyar aurensu kenan?, Ta koma ta auri wani?,idan kuma qudurinta ya tabbata fa?,ta yayq zai kalli idanun family dinsa ya shaida musu cewa ita din matarsa ce daya aurota a wani qauye waishi dinya ba tare da sanin magabatansa ba?,idan maganar ta fito waye da waye zai amsheta?,waye kuma zai mata mummunan kallo da mummunan fassara?.
Samun kanta tayi da runtse idanunta sanda sunan mommy da najwa ya darsu a ranta
"Hasbunallahu wa ni'imal wakil" labbanta suka motsa a hankali,kalmar ta kwarara cikin zuciyarta,sannu a hankali kuma hancinta ya cika da qamshin turaren data tabbatar a zahiri take iya jiyoshi,kafin kuma fa bude idanun nata muryar mubina ta cika kunnuwanta.
"Kaltum da magariba fa yace akai masa,nidai a ready,ki debo kayan na tayaki kaiwa,dama inason muyi magana dashi" a nutse ta daga kanta ta sauke ga mubina dake gaban mudubi tana sake fesa turare baya wancan data fesa,wani abu ya matse zuciyar kaltume,amma saita aro jarumta ta miqe tana nannade abun sallarta ba tare data cewa mubina komai ba ta fice izuwa kitchen.
Tana tsaka da harhada kayan abincin mubinan ta shigo,tayi shar cikin wani riga da skert da yadin material na mata me sulbi,sai baza qamshi take kamar tayi barin turare.
Ita tayi uwa tayi makarbiya ta amshe kwandon kayan abincin,kaltum din najin wani abu me kama da haushi yana son sauka a zuciyarta ta sakar mata kwandon,ko banza ita din macace,ya kamata kuma ta mutunta tare da martaba darajarta da mutuncinta na diya mace,bata tanka mata surutanta ba ta dauki flask na tea data hada masa ruwan zafin da bata da tabbacin zaisha tunda batasan zabinsa ba ta bita dashi.
Sanya yake da fara qal din long sleeves shirt,wandon jikinsa ash ne me turuwa,wanda iyakacinsa qauri,sun sameshi zaune da jibgin files a gabansa da alama aikin office ne ya deboshi zuwa gida,waya yake amsawa,amma idanunsa na kan qofar sanda suke shigowa.
Amsa sallamar mubinan yayi yana mamakin shigowarta sashen,saidai kafin ya dauke idanunsa ya hangi kaltum daga bayanta,sanye da madaidaicin hijabi light blue,wanda ya haska zagaggayar fuskarta,ya kuma qara fito da hasken qwayar idanunta.
Duk da amsa waya yake amma yana karantar sanyi cikin yanayinta,daga sanda yaji karatu akan girman amana gaba daya hankalinsa ya sake karkata a kanta,yana jin ashe wani babban nauyi ne akansa daya kamata ya bashi dukkan wata kulawa iyaka qarfinsa.
Ya gama wayar ya katseta yana ajjiyeta gefe,yana daga kai suna hada ido da mubina,saita saki murmushi tana sunkui da kai ita dole taji kunya.
Bai kula da wannan ba,ya fara janye hannun rigarshi zuwa baya tare da lanqwashe qafafunsa sanda take aje masa abincin a gabansa
"Sannu" ya furta can qasa,yanayin da sautin maganar ya fito ya tilasta mata daga kai ta dubeshi,saboda yayi maganar ne tamkar me rada.
Fridge ta nufa da niyyar dauko masa ruwa,sai yace
"Dawo nan ki zauna....jeki cikin gidaki daukomin ruwa mara sanyi" yace da mubina.
Dadi ne sosai ya rufeta,ta miqe da saurinta ta nufi qofar fita,saiya maida dubansa ga kaltum dake laluben wajen zama
"Dawo nan" ya fada yana nuna mata gabanshi,a sanyaye ta dawo ta zauna din inda yace mata,duk da cewa zaman kusa dashi irin haka ya mata nauyi amma ba zata iya kaucewa umarninsa ba
"Mene yake damunki?" Ya jefe mata tambayar yana bin fuskarta data dan cika ta murje da kallo kusan irin na qurilla,dan mitsitsin bakinta yana motsawa kadan kadan, Tambayar ta isketa a bazata,don bata zaci jin haka daga bakinsa ba,saita girgiza kanta
"Babu komai" ta amsa mishi,baice mata komai ba sai yaja abincinsa ya fara ci,ba jimawa mubina ta shigo da ruwan,hakan yasa kaltum miqewa tana neman izinin tafiya,don bata jin zata iya zama mubinan tayi maganar da take da qudurin yin a gabanta.
"Ki jirata ku wuce tare....uhmmm,ina jinki" samir ya fada duka lokaci daya.
Bai fasa cin abincinsa ba sanda take koro bayanta cike da kunya da kuma ɗar ɗar,saidai ya kafeta da manyan idanunsa,zuciyarsa cike fal da mamaki,yana kuma qoqarin danne mamakin da kuma dariyar data bashi har ta kammala bayananta.
Abincin ya aje gefe yana kallonta,ya karanci mata wani bin duka tunaninsu iri daya ne,basa kallon abubuwa a yadda suke,sau tari komai suna kallonsa a baibai a maimakon zahirin yadda yake
"Shekarunki nawa?" Tambayar data jita banbarakwai,saita tsargu,ta saci kallon kaltum,wadda tunda ta sunkui da kanta bata dagashi ba
"Sha....sha,ashirin" yadda ta bashi amsar ya tabbatar masa ta dan qara wani abu akan ainihin shekarunta,murmushin gefan baki ya saki
"Karki bari matata ta san ainihin abinda kike nufi ko fada a kaina,if not kuma.....saita zaneki,ku tashi kuje ku kwanta,gobe akwai tafiya a gabanmu" daga haka ya balle murfin ruwa ya soma sha a nutse.
Tuni kaltum takai qofa,saboda amsar daya bayar tamkar saqo ne zuwa ga mutum biyu kenan,wacece matarsa?,me kuma hake nufi da ita,mema maganarsa gaba daya ke nufi?,wadan nan sune ire iren tambayoyin data kwana tana yiwa kanta.
Tana iya jiyo kukan mubina bayan ta gama gayama kaltum din cewa
"Me yasa ya dauka abinda nake gaya masa bada wani muhimmanci ba?,bayan ni ina gaya masa saqo ne mai muhimmanci?" Ba zata iya cewa da ita komai ba,don itama ta kanta take,har ta gama maganganunta ta barke da kuka,tun tana jin kukan mubina har taji shuru,da alama tayi ta gaji,ko kuma bacci ya dauketa,saita sauka a hankali ta zura qafafunta qasa tayi bandaki.
Iska me zafi ya furzar daga bakinsa yana ture ayyukan dake gabansa,duk yadda yaso ya tilastawa kansa yin aikin abun ya gagareshi,fuskar kaltum din yake hangowa sanda mubinan ke isar mishi da saqon,yana sane ya zaunar da ita,akwai abinda yakeson gani da kuma karanta daga gareta,saidai kuma iya zamanta da tashinta taqi bashi damar komai.
Mirginawa yayi ya koma rub da ciki,yana tallafe fuskarsa da tafukan hannayensa,gami da lumshe idanunsa,yana jin yadda sukayi masa nauyi saboda baccin da ya cikasu,amma zuciya da qwaqwalwarsa sunqi bashi hadin kai.
Saidai shi bacci ba'a ci masa bashi,kamar yadda ba'a qayyade masa lokacin yinsa,a hankali idanunsa suka dinga rufewa har sukayi nauyin da bazai iya budesu ba,ya lula duniyar bacci.
*_DUNIYAR MAFARKI_*
A firgice ya farka,saidai bakinsa dauke da addu'a,a hankali yake karanto addu'o'in da ma'aiki ya bayar ga duk wanda yayi mafarki mara dadi,saiya miqe ya nufi bandaki,idanuwansa na haska masa fuskar mahaifiyarsa da yake gani tsugune a gefansa,tana kuma masa nuni da mahaifinsa dake tafiya zuwa wani wawakeken rami wanda wuta ce fal keci a cikinsa.
******Babu wani cikakken kuzari a jikinta take qarasa hada jakar kayanta,banda hajiya qarama da jawahir da suka damu da zuwan nata da babu inda zata.
"Ya na ganki a zaune?" Kaltum tayi qarfin halin yiwa mubina magana sanda ta dauki jakarta bayan samir ya aiko a shaida mata ta fito,kaita girgixa qwalla na sauko mata
"Bani da nutsuwar da zan iya binku,saikun dawo" bata iya ce mata komai ba ta soma takawa tana ficewa,mafarkinta na jiya na sake tsaya mata sosai a rai,duk kuwa da cewa kusan maimaici tayi na abinda ya faru a mafarkinta na wancan karon,amma abun sai ya tsaye mata a rai fiye da wancan.
Ga hoton matar har yanzu a wajenta,amma bata da wanda zai gaya mata wacece ita?,ta kasa fassara ma'anar yawan ganinta da takeyi cikin barcinta,saidai a yanzu zuciyarta ta karkata da zuwa gidan masu lalurar tabin hankali taje ta ziyarci matar data gani a gidan,wadda take mata kama da.matar dake zuwa mata a mafarki,duk da cewa waccar ta gida masu lalurar tabin hankalin shekarunta sunfi na wadda take cikin hoton da kuma wadda take gani a mafarkin tsufa........
52
D/Z
Tunda ta tunkaro wajen ya gaza dauke ganinsa daga kanta,karon farko daya soma ganinta cikin shiga irin wannan.
Abaya ce a jikinta baby pink mai sulbi mai kuma hawa biyu,wadda ta wadata da adon baqaqen duwatsu masu wani irin walwali da sheqi,duk da cewa shiya siyo kayan,amma ba tsammaci zasu karbeta har haka ba.
Yayi tayi rolling mayafin ya baiwa gaban gashinta mai santsi damar fitowa,idan ka kalleta zakayi tsammanin irin kyawawan Ethiopians din nan ne,saboda yadda kalar fatarta ya sake fes kamar bata shiga rana.