Sashe 60
Dabiar Zuciya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Wacce nutsuwa kuma?,bazai wuce kuce siyayyar kaya ba,yo ku basu kudin kayan mana,sayi siyayyarsu su siya abinda ransu keso,kabar yaro ya dauki matarsa,daga baya maje muga waje" .
A sannan inda ya lura da kyau wani kallo samir ke binsa dashi,ya yadda ya amince ya kuma yi imanin lallai yarinyar batayi sa'a da kuma dacen uba ba,yasan tsaf zai bata ran kamilin mutumin da ya shaida musu suna kawu ado,don haka ya shiga maganar
"Kawu,inaga a barta din kamar yadda kace,idan naje gida na dawo sainazo na dauketan" murmushin takaici kawu ado ya saki
"Babu komai malam samir.....bari amusu magana,ku tafi din,Allah ya tsare hanya,ya baku zaman lafiya" kafin ya dire wannan kalaman ma tuni malam amadu yayi ciki,ransa a bace yana mitar ana shiga gonarsa,shida iyalansa amma ana musu shishshigi?.
Yasan komai yana iya faruwa a cikin gidan,don haka da murmushi saman fuskarsa ya miqe
"Ina zuwa,kuyi haquri don Allah bari a fito da ita,kunsan sha'anin mata,kada suje su bata muku lokaci" a hankali amiru ya gyada wuyansa da yakeji kamar an sauke masa guduma,yayi alamar to,yabi kawu amadu da kallo sanda ya shige cikin gidan yana saba babbar rigarsa.
Sai daya shige ya maido dubansa ga samir,magana yakeson masa amma wanzuwar badaru a wajen ya hanashi magana,bashi kuma da tabbacin ko yaqinin baya jin turanci ko qanqani bare ya juya harshe,saboda ya ganshi fes dashi fiye da yanayin sauran samarin qauyen,yasan kuwa bazai rasa karatu a tattare dashi ba,sai shuru yaci gaba da sukwane musu lokacin,amiru cike da mamakin samir din daya ruguza duk wani abu da yace masa zai aiwatar,kuma ko sau daya bai kalleshi ba bare yayi masa nuni kan ya taso su kebe suyi magana kafin a kai ga fitowa da yarinyar.
Tana daga dakinsu,amma sallama guda daya tak ta mahaifinsu ta haifar mata da wata mummunar faduwar gaba data hanata zama,saita miqe tsaye cak ta tsaya sanda taji yana maganarsa gaba gadi a tsakar gida
"Ke zuwaira..…ku shirya yarinyar nan,mijinta yana waje yana jiranta zasu tafi,kuyi maza maza ku hanzarta" a hankali ta daga kai ta dubi mijin nata,tana jin yadda zallar rashina adalcinsa yakai mata ko ina ma rayuwarta,bazai sauya ba,babu abinda zai sauyashi,saidai ta sani cewa ta roqi Allah,koma meye zai shigo rayuwar kaltum din yazo mata da sauqin da babu wanda ya zata a cikinsu
"Dake fa nake magana,ku hanzarta da Alla kada kubar mutane suna jiranku" daga haka ya juya hankalinsa kwance ya nufi cikin dakinsa.
Tsam ta miqe daga durquson da tayo gaban murhu tana shirya itace,saboda girkin da takeson ta dora musu,sakamakon yadda kaltume din gaba daya ta koma bata iya tsinana komai,mayafinta dake kan igiya ta janyo ta sanya,sannan ta kutsa kai ta fito ainihin babban tsakar gidansu.
Tana niyyar zarcewa zuwa waje tanimu dan maqotansu daya fito daga sashen inna laure ya fito
"Yauwa tanimu,leqa daga waje qofar gida,idan kaga baqin fuska kace musu anason magana da mijin kaltume" tace da yaron
"Nama sanhi ai,ogan ginin makarantar mai tafasa ne"ya amsa mata,saita dafa kansa
"Yauwa,yi maza ka kiramin shi" ya cilla kuwa da gudunsa yayi waje,yayin daya barta da juya maganar tasa,indai hakane kenan yana nufin uban gidan su bilalu ne?,ya akayi har yaje ya karbi auren kaltume da hannunsa da kuma amincewarsa?,tambayar data tsaya mata kenan a rai.
Dan jim samir yayi yana juya kiran da aka masa daga cikin gidan,yana kuma jinjina kalmar mijin kaltume da aka kirashi dashi,sai yaji kalmar shi kansa tayi masa nauyi qwarai,sai kuma ya miqe yana zura takalmansa,cikin tafiya ta nutsuwa ya kutsa kai cikin soron,yana kallon zaizayayyar katangar gidan,yana sake girmama ubangiji da yayo mu mabambanta,hakanan ya bambanta mu cikin rayuwa wadata da samu da kuma jin dadi.
Tunda ya doso soron ta zuba mishi idanu a fakaice,tabbas shi dinne,duk da gani daya tak ta taba yi masa amma ta shaidashi,duk wani karatu irin na hankali nazari da kuma lissafi daya kamata kayi akan mutum tayi namijin qoqarin yi a kansa kafin ya cimmata.
A zahiri bata ga wata siffa ta tawaya ko siffar da zata nuna maka cewa akwai wani matsala dangane da dabi'a da kuma halayyar mutum ba,duk da kuwa cewa bawai ta sanshi bane sani na dabi'a da halayya ba,to amma kuma....data dauko wanna nazarin ta hada da labarai da bilal je basu a lokacin da yake raye dangane da halayya da dabi'unsa,sai taji wani sashe na zuciyarta yana mata sanyi da haske,duk dadai ta hangi tarin tazara da kuma bambanci a tsakaninsu,ta kasa jin nutsuwar cewa shida kansa ya zabi diyarta kaltume,ba zata bari ta yaudari kanta ba,wannan sam baiyi zubi ko suffar irin mutanensu ba,akwai alamun tazara da bambancin duniyar rayuwa a tsakaninsu.
Shuru ne ya ratsa tsakaninsu bayan gaisuwar data gilma,umman ta tattara dukkan kalaman bakinta sannan ta motsa cikin yanayi na nutsuwa irin na uwa
"Duk da cewa babu wanda ya gayamin ko mukayi maganar dashi,amma zuciyata ta kasa yarda gasgatawa ko kuma gamsuwa akan cewa kaine da kanka ka zabi kaltume na amatsayin matar da zaka aura,banbamcin yanayi da kuma yadda aka bada tallanta ko ince sadakarta ya gayamin haka,zuciyata tafi gayamin cewa......ka karba auren kaltum ne saboda wala'alla tausayi taimako ko kuma wani abu daya shafi hakan,toh....koma meye,nidai zan roqeka,koda ka auri kaltum ne don ka nesantata da rayuwarmu zuwa wani lokaci,zan gode maka,aqalla zata samu wani sukuni na taqaitaccen lokaci da muka gasa samar mata....zan kuma roqi alfarmarka akan ka riqemin ita amana,ka kulamin da rayuwarta,nayi yaqini da kuma imani da Allah,tunda har na roqeshi,na kuma nemi zabinsa,toba shakka abinda ya aiwatar a yanzu akan kaltum dai dai ne,kuma ina saka ran alkhairi ne ga rayuwarta,ban damu ba,koma daga ina kake?,koma daga ina ka fito,nasan cewa ubangiji baiyi koma meye ba domin wofantar da addu'ata ba,ALQAWARIN ALLAH NE cewa,bawansa bazai taba daga hannunsa ya roqeshi ba,shi kuma ya dawo masa da hannunsa haka ba tare daya amsa masa ba,ko a kusa,ko a nesa,kaje da kaltum amma bisa ruqo na amana".
Kowanne gefe idan ya juya sai yaji ya kasa amayar musu da dalilin xuwansa,baizo don ya tafi da diyarsu ba,yazo ne saboda ya warware igiyar data dauru a kanta dalilin amiru,amirun dashi kansa ya aiwatar da komai bisa wasa,wasan da yayi kama da ganganci sak!.
A hankali umma ta yaye labulen dakin,zuwa sannan ta jima ta suman tsaye,fuskarta tayi sharkaf da hawaye,tamaqale jikin bango sai kace mai shirin tsagashi ta wuce ta ciki.
Tun umman bata qaraso ba ita ta isa gareta a sukwane ta fada jikinta
"Ummanmu...ummanmu" sai kuma ta kasa furta komai,cikin wata irin dakiya tace
"Ya isa,a ko ina kike Allah yana tare dake,hakanan kina tare da addu'ata da izinin ubangiji" data daga kai ta kalli ummantata,sai dakiyar umman ta bata tsoro da mamaki,ta bita da kallo sanda take isa inda take tara kayan sawarta ta fara hada mata waje daya
"Ummanmu,bamuyi sallama da habi ba" ta fada hawaye yana sulmiyo mata
"Indai da rai da rabo,watarana zaku gana" kalaman umman da sukazo mata kenan,suka kuma fi yi mata kama da kalaman wanda ke sallamar bankwana izuwa qiyama idan anayi.
Idanunta qyar bisa ga mahaifinta sanda yake sallamata izuwa ga hannun baquwar fuskar da bata taba koda magagin cewa wata alaqa zata hadasu ba,riqe da qullin kayanta da ummansu ta hada mata
"Muje ko?" Ta tsinkayi baquwar murya tana bada umarni a gareta,saita daga jiqaqqun idanuwanta ta dubeshi,ta sauke a hakali ta maida ga bigiren da mahaifinta ya wanzu ashi dazu,wayam yake babu kowa,ta sake duban hanyar da ummanta ta rakota,itama babu kowa sai takun sawayenta,saita sake dubansa karo na biyu,karo nabiyun da zuciyarta ta buga mata da wani irin qarfi,saboda yadda taga fuskarsa a tsuke,cike da wani irin kwarjini da bata taba katarin ganinsa a fuskar wani ba.
A hankali ta fara daga qafafunta tana jefasu zuwa gaba,tana fatan dagasun da takeyi yayi da dai da sunan tafiya,zasu turata zuwa gaba kamar yadda ya buqata,tana iya ji da ganin sanda suka zartata a tafiya,shida amirun da a sannan batasan ko waye ba,taga dai ya qara sauri ya kuma cimma wanda aka kira da sunan mijinta,taga ya kama hannunsa da alama magana yakeasa,saidai bata damu da jin me suke tattaunawa ba,idanuwanta sunfi hango mata zaizayayyen gidansu,da ummanta dake cikin dakinta tana kuka.
35
D/Z
*Littafin kudi ne,don girman Allah idan kin gani karki mana sharing,biya naki ta wadan nan numbers din ki karanta cikin aminci*
08184017082
Ko kuma
09134848107
"Saraki....wai me kake shirin aikatawa ne?,are you in your sense?" Aamir daya riqo samir a rude ya furta yana duban qwayar idanun samir din.
Hannunsa ya zame daga cikin ma Aamir yana dubansa shima
"So kake nace bazan karbeta ba?,so kake nace musu na saketa?,so kake na gayawa wannan rarraunar uwar cewa na saki diyarta kwana daya tal da daura mata aure?,wannan uwar data karbi dukkan qaddarar auren diyarta ga wanda bata san ainihin koshi waye ba?,ko kuma so kake na gayawa wannan dattijon kawun cewa na saki 'yar 'yar uwarsa?,aurenta baya nufin komai...hakanan bazai sauya komai ba"
"Duk da haka.....ta yaya zaia fuskanci daddy prof ka gaya masa ka daura aure ba tare da sani ko yardarsa ba?" Qaramin murmushin da iyakarsa lebe ya saki,don shi kansa yasan murmushin bai kai qasan zuciyarsa ba,shi da kansa yake gina tunanin abubuwan tashin hankalin da xasu biyo baya ya kuma yi musu fenti su fito radau kamar gaske,ciki kuwa harda sake tabarbarewar soyayya da fahimtar junan da yake tattali,wanda tayi qaranci tsakaninsa da mahaifinsa,sakamakon bambance banbamce na abubuwa masu yawa a tsakaninsu,wani sabanin ma baya sanin ainihin abinda ya haifar musu da shi,yakan zo ne haka siddan a wadansu lokutan
"Kada ka damu a abinda zan gaya masa, just wait and see what will happen". Kanshi amiru ya dafe
"Me yasa nayi coursing maka wannan matsalar?,why?" Gajeran murmushi ya sake fiddawa
"Bawa baya wucewa qaddararsa,dama qaddarar tawa ce" itace amsar daya bashi,kafin amirun ya juya zuwa bigiren da kaltume ta wanzu akai tana biye dasu,har yanzu fuskarta shafe da hawaye da qananun majina
"Tana bayanmu ne fa saraki"
"Garinsu ne,ba zata bata ba" ya amsa masa a gajarce.
A sannan inda ya lura da kyau wani kallo samir ke binsa dashi,ya yadda ya amince ya kuma yi imanin lallai yarinyar batayi sa'a da kuma dacen uba ba,yasan tsaf zai bata ran kamilin mutumin da ya shaida musu suna kawu ado,don haka ya shiga maganar
"Kawu,inaga a barta din kamar yadda kace,idan naje gida na dawo sainazo na dauketan" murmushin takaici kawu ado ya saki
"Babu komai malam samir.....bari amusu magana,ku tafi din,Allah ya tsare hanya,ya baku zaman lafiya" kafin ya dire wannan kalaman ma tuni malam amadu yayi ciki,ransa a bace yana mitar ana shiga gonarsa,shida iyalansa amma ana musu shishshigi?.
Yasan komai yana iya faruwa a cikin gidan,don haka da murmushi saman fuskarsa ya miqe
"Ina zuwa,kuyi haquri don Allah bari a fito da ita,kunsan sha'anin mata,kada suje su bata muku lokaci" a hankali amiru ya gyada wuyansa da yakeji kamar an sauke masa guduma,yayi alamar to,yabi kawu amadu da kallo sanda ya shige cikin gidan yana saba babbar rigarsa.
Sai daya shige ya maido dubansa ga samir,magana yakeson masa amma wanzuwar badaru a wajen ya hanashi magana,bashi kuma da tabbacin ko yaqinin baya jin turanci ko qanqani bare ya juya harshe,saboda ya ganshi fes dashi fiye da yanayin sauran samarin qauyen,yasan kuwa bazai rasa karatu a tattare dashi ba,sai shuru yaci gaba da sukwane musu lokacin,amiru cike da mamakin samir din daya ruguza duk wani abu da yace masa zai aiwatar,kuma ko sau daya bai kalleshi ba bare yayi masa nuni kan ya taso su kebe suyi magana kafin a kai ga fitowa da yarinyar.
Tana daga dakinsu,amma sallama guda daya tak ta mahaifinsu ta haifar mata da wata mummunar faduwar gaba data hanata zama,saita miqe tsaye cak ta tsaya sanda taji yana maganarsa gaba gadi a tsakar gida
"Ke zuwaira..…ku shirya yarinyar nan,mijinta yana waje yana jiranta zasu tafi,kuyi maza maza ku hanzarta" a hankali ta daga kai ta dubi mijin nata,tana jin yadda zallar rashina adalcinsa yakai mata ko ina ma rayuwarta,bazai sauya ba,babu abinda zai sauyashi,saidai ta sani cewa ta roqi Allah,koma meye zai shigo rayuwar kaltum din yazo mata da sauqin da babu wanda ya zata a cikinsu
"Dake fa nake magana,ku hanzarta da Alla kada kubar mutane suna jiranku" daga haka ya juya hankalinsa kwance ya nufi cikin dakinsa.
Tsam ta miqe daga durquson da tayo gaban murhu tana shirya itace,saboda girkin da takeson ta dora musu,sakamakon yadda kaltume din gaba daya ta koma bata iya tsinana komai,mayafinta dake kan igiya ta janyo ta sanya,sannan ta kutsa kai ta fito ainihin babban tsakar gidansu.
Tana niyyar zarcewa zuwa waje tanimu dan maqotansu daya fito daga sashen inna laure ya fito
"Yauwa tanimu,leqa daga waje qofar gida,idan kaga baqin fuska kace musu anason magana da mijin kaltume" tace da yaron
"Nama sanhi ai,ogan ginin makarantar mai tafasa ne"ya amsa mata,saita dafa kansa
"Yauwa,yi maza ka kiramin shi" ya cilla kuwa da gudunsa yayi waje,yayin daya barta da juya maganar tasa,indai hakane kenan yana nufin uban gidan su bilalu ne?,ya akayi har yaje ya karbi auren kaltume da hannunsa da kuma amincewarsa?,tambayar data tsaya mata kenan a rai.
Dan jim samir yayi yana juya kiran da aka masa daga cikin gidan,yana kuma jinjina kalmar mijin kaltume da aka kirashi dashi,sai yaji kalmar shi kansa tayi masa nauyi qwarai,sai kuma ya miqe yana zura takalmansa,cikin tafiya ta nutsuwa ya kutsa kai cikin soron,yana kallon zaizayayyar katangar gidan,yana sake girmama ubangiji da yayo mu mabambanta,hakanan ya bambanta mu cikin rayuwa wadata da samu da kuma jin dadi.
Tunda ya doso soron ta zuba mishi idanu a fakaice,tabbas shi dinne,duk da gani daya tak ta taba yi masa amma ta shaidashi,duk wani karatu irin na hankali nazari da kuma lissafi daya kamata kayi akan mutum tayi namijin qoqarin yi a kansa kafin ya cimmata.
A zahiri bata ga wata siffa ta tawaya ko siffar da zata nuna maka cewa akwai wani matsala dangane da dabi'a da kuma halayyar mutum ba,duk da kuwa cewa bawai ta sanshi bane sani na dabi'a da halayya ba,to amma kuma....data dauko wanna nazarin ta hada da labarai da bilal je basu a lokacin da yake raye dangane da halayya da dabi'unsa,sai taji wani sashe na zuciyarta yana mata sanyi da haske,duk dadai ta hangi tarin tazara da kuma bambanci a tsakaninsu,ta kasa jin nutsuwar cewa shida kansa ya zabi diyarta kaltume,ba zata bari ta yaudari kanta ba,wannan sam baiyi zubi ko suffar irin mutanensu ba,akwai alamun tazara da bambancin duniyar rayuwa a tsakaninsu.
Shuru ne ya ratsa tsakaninsu bayan gaisuwar data gilma,umman ta tattara dukkan kalaman bakinta sannan ta motsa cikin yanayi na nutsuwa irin na uwa
"Duk da cewa babu wanda ya gayamin ko mukayi maganar dashi,amma zuciyata ta kasa yarda gasgatawa ko kuma gamsuwa akan cewa kaine da kanka ka zabi kaltume na amatsayin matar da zaka aura,banbamcin yanayi da kuma yadda aka bada tallanta ko ince sadakarta ya gayamin haka,zuciyata tafi gayamin cewa......ka karba auren kaltum ne saboda wala'alla tausayi taimako ko kuma wani abu daya shafi hakan,toh....koma meye,nidai zan roqeka,koda ka auri kaltum ne don ka nesantata da rayuwarmu zuwa wani lokaci,zan gode maka,aqalla zata samu wani sukuni na taqaitaccen lokaci da muka gasa samar mata....zan kuma roqi alfarmarka akan ka riqemin ita amana,ka kulamin da rayuwarta,nayi yaqini da kuma imani da Allah,tunda har na roqeshi,na kuma nemi zabinsa,toba shakka abinda ya aiwatar a yanzu akan kaltum dai dai ne,kuma ina saka ran alkhairi ne ga rayuwarta,ban damu ba,koma daga ina kake?,koma daga ina ka fito,nasan cewa ubangiji baiyi koma meye ba domin wofantar da addu'ata ba,ALQAWARIN ALLAH NE cewa,bawansa bazai taba daga hannunsa ya roqeshi ba,shi kuma ya dawo masa da hannunsa haka ba tare daya amsa masa ba,ko a kusa,ko a nesa,kaje da kaltum amma bisa ruqo na amana".
Kowanne gefe idan ya juya sai yaji ya kasa amayar musu da dalilin xuwansa,baizo don ya tafi da diyarsu ba,yazo ne saboda ya warware igiyar data dauru a kanta dalilin amiru,amirun dashi kansa ya aiwatar da komai bisa wasa,wasan da yayi kama da ganganci sak!.
A hankali umma ta yaye labulen dakin,zuwa sannan ta jima ta suman tsaye,fuskarta tayi sharkaf da hawaye,tamaqale jikin bango sai kace mai shirin tsagashi ta wuce ta ciki.
Tun umman bata qaraso ba ita ta isa gareta a sukwane ta fada jikinta
"Ummanmu...ummanmu" sai kuma ta kasa furta komai,cikin wata irin dakiya tace
"Ya isa,a ko ina kike Allah yana tare dake,hakanan kina tare da addu'ata da izinin ubangiji" data daga kai ta kalli ummantata,sai dakiyar umman ta bata tsoro da mamaki,ta bita da kallo sanda take isa inda take tara kayan sawarta ta fara hada mata waje daya
"Ummanmu,bamuyi sallama da habi ba" ta fada hawaye yana sulmiyo mata
"Indai da rai da rabo,watarana zaku gana" kalaman umman da sukazo mata kenan,suka kuma fi yi mata kama da kalaman wanda ke sallamar bankwana izuwa qiyama idan anayi.
Idanunta qyar bisa ga mahaifinta sanda yake sallamata izuwa ga hannun baquwar fuskar da bata taba koda magagin cewa wata alaqa zata hadasu ba,riqe da qullin kayanta da ummansu ta hada mata
"Muje ko?" Ta tsinkayi baquwar murya tana bada umarni a gareta,saita daga jiqaqqun idanuwanta ta dubeshi,ta sauke a hakali ta maida ga bigiren da mahaifinta ya wanzu ashi dazu,wayam yake babu kowa,ta sake duban hanyar da ummanta ta rakota,itama babu kowa sai takun sawayenta,saita sake dubansa karo na biyu,karo nabiyun da zuciyarta ta buga mata da wani irin qarfi,saboda yadda taga fuskarsa a tsuke,cike da wani irin kwarjini da bata taba katarin ganinsa a fuskar wani ba.
A hankali ta fara daga qafafunta tana jefasu zuwa gaba,tana fatan dagasun da takeyi yayi da dai da sunan tafiya,zasu turata zuwa gaba kamar yadda ya buqata,tana iya ji da ganin sanda suka zartata a tafiya,shida amirun da a sannan batasan ko waye ba,taga dai ya qara sauri ya kuma cimma wanda aka kira da sunan mijinta,taga ya kama hannunsa da alama magana yakeasa,saidai bata damu da jin me suke tattaunawa ba,idanuwanta sunfi hango mata zaizayayyen gidansu,da ummanta dake cikin dakinta tana kuka.
35
D/Z
*Littafin kudi ne,don girman Allah idan kin gani karki mana sharing,biya naki ta wadan nan numbers din ki karanta cikin aminci*
08184017082
Ko kuma
09134848107
"Saraki....wai me kake shirin aikatawa ne?,are you in your sense?" Aamir daya riqo samir a rude ya furta yana duban qwayar idanun samir din.
Hannunsa ya zame daga cikin ma Aamir yana dubansa shima
"So kake nace bazan karbeta ba?,so kake nace musu na saketa?,so kake na gayawa wannan rarraunar uwar cewa na saki diyarta kwana daya tal da daura mata aure?,wannan uwar data karbi dukkan qaddarar auren diyarta ga wanda bata san ainihin koshi waye ba?,ko kuma so kake na gayawa wannan dattijon kawun cewa na saki 'yar 'yar uwarsa?,aurenta baya nufin komai...hakanan bazai sauya komai ba"
"Duk da haka.....ta yaya zaia fuskanci daddy prof ka gaya masa ka daura aure ba tare da sani ko yardarsa ba?" Qaramin murmushin da iyakarsa lebe ya saki,don shi kansa yasan murmushin bai kai qasan zuciyarsa ba,shi da kansa yake gina tunanin abubuwan tashin hankalin da xasu biyo baya ya kuma yi musu fenti su fito radau kamar gaske,ciki kuwa harda sake tabarbarewar soyayya da fahimtar junan da yake tattali,wanda tayi qaranci tsakaninsa da mahaifinsa,sakamakon bambance banbamce na abubuwa masu yawa a tsakaninsu,wani sabanin ma baya sanin ainihin abinda ya haifar musu da shi,yakan zo ne haka siddan a wadansu lokutan
"Kada ka damu a abinda zan gaya masa, just wait and see what will happen". Kanshi amiru ya dafe
"Me yasa nayi coursing maka wannan matsalar?,why?" Gajeran murmushi ya sake fiddawa
"Bawa baya wucewa qaddararsa,dama qaddarar tawa ce" itace amsar daya bashi,kafin amirun ya juya zuwa bigiren da kaltume ta wanzu akai tana biye dasu,har yanzu fuskarta shafe da hawaye da qananun majina
"Tana bayanmu ne fa saraki"
"Garinsu ne,ba zata bata ba" ya amsa masa a gajarce.