Sashe 58
Dabiar Zuciya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Zaka leqa kaga amaryar ne ko kuwa?" Kansa daya fara ciwo ya girgiza
"Zanzo baba daga baya"
"To...to saika shigo"
Baiko samu sararin amsa masa ba yayi gaba,amiru da bakinsa ke cike fal da tambayoyin da ya gaza samun amsarsu ya dafa masa baya...
Tunda suka fito yake jefa masa jerin gwanon tambayoyinsa amma bai kulashi ba,har sukayi nisa,suna haramar tadda gida
"Kace wani abu mana....waime ka shirya ne?" Ya sake tambayarsa wannan karon adan qage saboda yadda ya gaza samun amsar kowacce cikin tambayoyinsa.
Ba zato yaja cak ya tsaya,sannan ya waiwayo ya zubawa amirun idanu na wasu lokutta,har sai dashi amirun ya gaza daukar kallon samir din,gwani ne shi wajen iya hukunci da idanu,ya san da wannan tun ba yau ba
"Idan kai zaka dinga wasa da rayuwarka kana daukar hakan ba'a bakin komai ba....ni bazan dauki wannan ba,akanme zaka rakitowa kanka auren gangan amiru?,oh....da nufinka shine kayi yadda ka gayamin ko?,ka gama tsara hakan,me yasa?"
"Kai me yasa ka tare auren?,me yasa ka bari ya fada kanka?" Ya maida masa tashi tambayar cikin damuwa,don har ga Allah ya shiga damuwa,yace zai karba auren ne ba don wai yana nufin hakan ba har cikin ransa,ya fadi hakanne saboda yana ganin ba zasu bashi ba,kasancewarsa baqo kuma baquwar fuska a garesu,zasu qalubalanceshi akan hakan.
Ajiyar zuciya samir ya saki,shi dinma yace shi zai karba ne saboda shigen irin tunanun amiru,ta yaya zasu bawa mutumin da basusan waye ba auren diyarsu?,ashe wautarsu ta wuce duk inda yake tunani
"Na karba saboda na shirya sakinta ne da zarar kwadayin ubanta na aurar da ita ya fada,kuma hakan zai faru daga yanzu zuwa anjima,zuwa safiyar gobe da zan gama aikin daya kawoni garin na tattara na koma duniyata.....amma ka sani,kada ka sake gigin sake aikata wani kuskuren makamancin hakan,saboda idan kayi yanzu ka tsira,gaba zaka iya rasa wani abu da baka tsammata ba" daga wannan ya saki hannayensa da ada ya rungumesu a qirji ya soma takawa.
Sai amirun ya kasa cira qafarsa daga wajen,ya bishi da kallon mamaki,duka yayi wannan abun ne saboda shi,ya dauki wannaj risking ne saboda shi,saboda ya tunkudeshi daga fadawa wanan matsalar,shi yasa a rayuwa yayi amanna da qaunar da samir yake masa wadda babu na biyunta,baya ga qaunae mahaifiyarsa a gareshi,wannan tunaninnm ya bashi qwarin gwiwar cira qafarsa da hanzari yabi bayansa.
Yauma gidan akwai jama'a dake ta shigowa gaisuwar sadakar uku suna fita,sai kuma wasu daga cikin 'yan uwa na kusa sosai da suke tare da ummanmu,kamar su yakumbo indo,da umma altine habi sa sauransu.
A filin tsakar gidan suke zaune saman tabarmi,a yanxun sai iya su isu,habiba da kaltumee na saman tabarma daya su biyu suna hirarsu qasa qasa,wanda su kadai sukasan me suke tattaunawa.
Sallama yayi ya shigo,suka amsa masa,masu masa sannu da zuwa sukayi masa,ya gaisa dana gaisawa,sannan ya dubi kaltume
"Ki kiramin babarku,kuzo keda ita" sai ya qara gaba yana bude dakinsa.
Jikinta a matuqar sanyayen da batasan musabbabinsa ba tun dazu ta miqe,ta shiga dakin ummanmu ta shaida mata.
Tare suka fito da ita suka nufi dakin nasa,zuciyar kaltum na wani irin bugawa da saurin da bata taba jin irin hakan ba,har kamar ana dan matsa zuciyar tata ne.
Gefan gadonsa suka cimmasa a zaune,ya baza babbar rigar jikinsa yana dakon isowarsu,gefe daya ummansu ta zauna,sai kaltun din ta bita ta zauna a jikinta tanajin jikinta yayi wani irin laushi.
Gyaran murya yayi kamar me shirin fara karatu,sannan ya dubesu,kanshi tsaye yace dasu
"Kamar yadda nace,na kuma alqawarta,to na bada auren kaltum" a tare maganar ta bugi kowannensu,kaltum da batayi shirin kallonsa ba,batasan sanda ta daga kai ta dubeshi ba.
Ya fahimci irin kallon da suke binsa dashi,a karon farko kuma yaji yadan daburce
"Eh,yau dai nima na sauke nauyin da yake kaina,na aurar da sauran 'yata data ragemin,zanyi bacci kamar kowanne uba" mamaki mai girma ya kama umma,taci gaba da kallonsa kamar wani sakarai
"Waye ka aura mata?" Dubanta yayi yana matse fuska
"To meye na gaggawa?,koma waye na aura matan ai zaku ganshi,tunda kunqi auwalu ba shikenan ba an muku abinda kuke so?" Yayi maganar cikin fada fada,saboda baiso taci gaba da tambayarsa waye mijin?,don idan hakan ta faru bashi da amsar bata,shi kansa baisan waye ya aurawa kaltum din ba,amma koma waye yasan babu abinda zai faru bazai cinyeta ba,a iya nasa dan qaramin sanin da ya yiwa duniya kenan.
Can qasan ranta umman ta saki ajiyar zuciya,tana jin fiye da rabin tashin hankalinta na kwaranyewa,saidai kuma akwai sauran fargaba a tare da ita,don batasan waye ne ya dauko ya maqalawa kaltum din ba,taji ranta yana motsawa,tausayi da bacin rai suka cakude waje daya suna karafkiya cikin ranta,kamar ba zata tankashi ba saita kasa,duban fuskar kaltum kawai ya daga hankalinta
"A wannan zamanin?,a irin wannan lokacin zaka yiwa diyarka irin wannan auren na rashin siyar daraja da mutunci?"
Idanunsa ya bubbude sosai yana hura hanci,baya so kuma baya sha'awar tayi masa wata magana,kota kawo masa tarnaqi kan hukuncin daya yanke ko misqala zarratin,don baiga uban daya isa yasashi ya janye wannan hukuncin ba
"Ke zuwaira ki fita daga ido na,ita din uban wace da bazan zaba mata miji ba?,ina cewa yarinya budurwa uba ne dama yake da haqqin zaba mata miji,shine zaki hurewa yarinya kunne ki sakata ta bijiremin?,to wallahi ta gwada,bismillah,ga fili ga me doki nan,nida ku uban wanda ya fasa" da alamu jama'a yakeson tara mata,saita miqe tana riqe da hannun kaltum zuciyarta na quna
"Ko da wanne lokaci fa zan tattarata a miqa masa ita" ya bisu da kalmar sanda umman ta kama hannun kaltum da tuni hawaye ya jiqe mata fuska,tsantsar tashin hankali kuma ya cika zuciya har saman fuskarta.
Mamaki ya kuma kama umman,wanne irin abu ne kuma haka,a daura ma yarinyar aure ba tare da tasan mijin ba,sanna ace ta shirya kowanne lokaci zata iya barin gidansu?,babu wani shiri tanadi ko sakawa rai?,mema suke dashi da zasu kaita dashi?.
Kamar yasan tunanin da takeyi saiya fiddo sadakinta daga aljihunsa,wanda sai daga baya daya nutsu ya lissafa yaga dubu arba'in da daya harda dari biyar akai,yana da yaqinin zata yi ma yarinyar kayan daki,ya lissafa ya dauki dubu ashirin ya miqa mata
"Nasan dai tunanin da kike,gashinan ayi mata wani abu dasu wanda zata tafi dasu,daga baya aje ayi mata jere"
"Amma wannan wanne irin al'amarine fisabilillahi malam?,wannan abun fa kwata kwata baiyi dai dai ba,yadda kake da haqqi a wuyanta itama tana da nata haqqin....." Saiya zaburo ya fara maganganu,maganganun da suka sanyata dole ta janye kaltum,suka fice ranta a mugun bace.
Kasa riqe kukanta kaltum tayi sanda suka koma daki,su yakumbo suna tambayar lafiya?,ganin yadda yanayin fuskarsu ya nuna zallar tashin hankali.
A karon farko bayan dukka abindanya faru,qwalla ta subuce daga idanun umman sanda take gaya musu abinda ya faru,ran yakumbo a bace ta miqe
"Haba,wannan abun yayi yawa,bari naje na sameshi,yarinyar yar tsana ce ita da za'a bada ita sadaka?,batasan miji ba miji bai santa ba?,sannan ace a shirya kowanne lokaci za'a kaita?" Harta sanya kai kawu ado ya shigo gidan,ta dubi qofar dakin amadu a kulle,da alama ya fice abinsa
"Ke kuma lafiya kamar wadda aka koro" kawu ado ya fada yana kallon fuskar yakumbo indo data cika da bacin rai
"Shigo daga ciki yaya" ta fadi tana juyawa dakin umma,saiya sanya kai shima,ya samu kujera yaja ya zauna.
A taqaice yakumbo ta labarta masa komai,sai yayi shuru yana jinjina kai,tabbas lamarin ya bugeshi ya kuma bashi mamaki,hakanan tun a hanya daya taho aka bashi labarin,saidai bai gasgata ba,ganin labarin yayi kama dana qanzan kurege.
"Da farko mu soma aiki da hankali tukunna,dukkaninmu nan amadu ya fimu iko da diyarsa kattume,hakanan a cikinmu babu wanda ya isa yaja da hukuncin daya yanke akan diyarsa koda gaban alqali akaje kuwa....saidai idan ita yarinyar taja da kanta,idan akwai abinda zamu iya cikin wannan lamarin bai wuce mu bashi shawara,mu kuma nusashe da shi ba,idan ya dauka haka mukafi so,idan bai dauka ba kuma,mataki daya zamu dauka,mu binciki halayyar yaron sana'a gami da nasabarsa,idan muka tabbatar da bashi da matsala a dukka wadan nan,sai muyi haquri,mu bi auren da addu'ar sanyawar albarkar ubangiji" a hankali zukata suka soma sauka daga bayanan da kawu ado yayi,ga duk me nisan hankali a cikinsu idan ya yiwa kalaman kallo na tsanaki,zai hango ya kuma shanshano gaskiyar zancan kawu ado,saidai ko daya zuciyar kaltum bata rusuna ba,saima tashin hankali data sake shiga dajin zancan kawu adon,yana nufin kenan a haqura a miqata ga duk wanda baban nata ya bata aurensa?,saita sake fashewa da kuka cikin tashin hankali.
*******A nutse yake shiryawa duk da cewa yayi nisa a tunanin da yakeyi,har ya gama shirinsa tsaf,ya dawo a hankali ya zauna gefam katifa yana jan kayan breakfast dake saman wani babban tray da niyyar yin break aamiru na zaune saman wani stool yana dubanshi,hannayensa goye a qirijinsa.
Hannayen nasa ya saki yana sauke ajiyar zuciya,fuskarsa da alamun damuwa yace
"Am asking you since yesterday.....ya zakayi da auren nan,bakace min komai ba" kamar ko yaushe harara ya watsa masa yana hada tea din,sai daya kammala ya riqe kofin a hannunsa zaikai baki sannan yace cikin wani irin soft voice
"Da zaka dameni duk ba kaine ka jawo komai ba?,dana sani ma na qyaleka,idan yaso in ka koma hajiya qarama tayi banda da namanka" duk da tasirin damuwar dake tattare dashi amma sai daya daara,kana ya koma ya daidata zamansa sosai,cikin seriousness yace
"Am bother to ask you ne saboda hajiya qaraman da kuma boss professor,but u are feeling bossy,sai wani jamin aji kakeyi"
"An ja makan,idan kaji haushi ka barni da matsalata" kafada amirun ya dage
"Kome zakace zan dauka,saboda bamu saba hadiye damuwoyinmu mu kadai ba" qaramin murmushi ya subucewa saraki,saiya aje cup din a gabansa,ya hade yatsunsa waje guda yana kallon amirun
"Wani abun mamaki,ban dauki wannan abun daya faru a bakin komai ba,but amma sai naketa jin nauyinsa a kaina tun jiyan?" Shuru ya ratsa tsakani,amiru ya saki ajiyar zuciya,muryarsa tayi sanyi fiye da dazu
"Ni kaina gaba daya tunani na ya qare akan yadda wannan al'amarin zai warware....ni inaga.....me zai hana ka qara ko one week ne,ka more sadakinka kawai,daga nan ka rubuta masa takardarta kawai ka maidata gida?" Wanu banzan kallo ya jefa masa
"Zanzo baba daga baya"
"To...to saika shigo"
Baiko samu sararin amsa masa ba yayi gaba,amiru da bakinsa ke cike fal da tambayoyin da ya gaza samun amsarsu ya dafa masa baya...
Tunda suka fito yake jefa masa jerin gwanon tambayoyinsa amma bai kulashi ba,har sukayi nisa,suna haramar tadda gida
"Kace wani abu mana....waime ka shirya ne?" Ya sake tambayarsa wannan karon adan qage saboda yadda ya gaza samun amsar kowacce cikin tambayoyinsa.
Ba zato yaja cak ya tsaya,sannan ya waiwayo ya zubawa amirun idanu na wasu lokutta,har sai dashi amirun ya gaza daukar kallon samir din,gwani ne shi wajen iya hukunci da idanu,ya san da wannan tun ba yau ba
"Idan kai zaka dinga wasa da rayuwarka kana daukar hakan ba'a bakin komai ba....ni bazan dauki wannan ba,akanme zaka rakitowa kanka auren gangan amiru?,oh....da nufinka shine kayi yadda ka gayamin ko?,ka gama tsara hakan,me yasa?"
"Kai me yasa ka tare auren?,me yasa ka bari ya fada kanka?" Ya maida masa tashi tambayar cikin damuwa,don har ga Allah ya shiga damuwa,yace zai karba auren ne ba don wai yana nufin hakan ba har cikin ransa,ya fadi hakanne saboda yana ganin ba zasu bashi ba,kasancewarsa baqo kuma baquwar fuska a garesu,zasu qalubalanceshi akan hakan.
Ajiyar zuciya samir ya saki,shi dinma yace shi zai karba ne saboda shigen irin tunanun amiru,ta yaya zasu bawa mutumin da basusan waye ba auren diyarsu?,ashe wautarsu ta wuce duk inda yake tunani
"Na karba saboda na shirya sakinta ne da zarar kwadayin ubanta na aurar da ita ya fada,kuma hakan zai faru daga yanzu zuwa anjima,zuwa safiyar gobe da zan gama aikin daya kawoni garin na tattara na koma duniyata.....amma ka sani,kada ka sake gigin sake aikata wani kuskuren makamancin hakan,saboda idan kayi yanzu ka tsira,gaba zaka iya rasa wani abu da baka tsammata ba" daga wannan ya saki hannayensa da ada ya rungumesu a qirji ya soma takawa.
Sai amirun ya kasa cira qafarsa daga wajen,ya bishi da kallon mamaki,duka yayi wannan abun ne saboda shi,ya dauki wannaj risking ne saboda shi,saboda ya tunkudeshi daga fadawa wanan matsalar,shi yasa a rayuwa yayi amanna da qaunar da samir yake masa wadda babu na biyunta,baya ga qaunae mahaifiyarsa a gareshi,wannan tunaninnm ya bashi qwarin gwiwar cira qafarsa da hanzari yabi bayansa.
Yauma gidan akwai jama'a dake ta shigowa gaisuwar sadakar uku suna fita,sai kuma wasu daga cikin 'yan uwa na kusa sosai da suke tare da ummanmu,kamar su yakumbo indo,da umma altine habi sa sauransu.
A filin tsakar gidan suke zaune saman tabarmi,a yanxun sai iya su isu,habiba da kaltumee na saman tabarma daya su biyu suna hirarsu qasa qasa,wanda su kadai sukasan me suke tattaunawa.
Sallama yayi ya shigo,suka amsa masa,masu masa sannu da zuwa sukayi masa,ya gaisa dana gaisawa,sannan ya dubi kaltume
"Ki kiramin babarku,kuzo keda ita" sai ya qara gaba yana bude dakinsa.
Jikinta a matuqar sanyayen da batasan musabbabinsa ba tun dazu ta miqe,ta shiga dakin ummanmu ta shaida mata.
Tare suka fito da ita suka nufi dakin nasa,zuciyar kaltum na wani irin bugawa da saurin da bata taba jin irin hakan ba,har kamar ana dan matsa zuciyar tata ne.
Gefan gadonsa suka cimmasa a zaune,ya baza babbar rigar jikinsa yana dakon isowarsu,gefe daya ummansu ta zauna,sai kaltun din ta bita ta zauna a jikinta tanajin jikinta yayi wani irin laushi.
Gyaran murya yayi kamar me shirin fara karatu,sannan ya dubesu,kanshi tsaye yace dasu
"Kamar yadda nace,na kuma alqawarta,to na bada auren kaltum" a tare maganar ta bugi kowannensu,kaltum da batayi shirin kallonsa ba,batasan sanda ta daga kai ta dubeshi ba.
Ya fahimci irin kallon da suke binsa dashi,a karon farko kuma yaji yadan daburce
"Eh,yau dai nima na sauke nauyin da yake kaina,na aurar da sauran 'yata data ragemin,zanyi bacci kamar kowanne uba" mamaki mai girma ya kama umma,taci gaba da kallonsa kamar wani sakarai
"Waye ka aura mata?" Dubanta yayi yana matse fuska
"To meye na gaggawa?,koma waye na aura matan ai zaku ganshi,tunda kunqi auwalu ba shikenan ba an muku abinda kuke so?" Yayi maganar cikin fada fada,saboda baiso taci gaba da tambayarsa waye mijin?,don idan hakan ta faru bashi da amsar bata,shi kansa baisan waye ya aurawa kaltum din ba,amma koma waye yasan babu abinda zai faru bazai cinyeta ba,a iya nasa dan qaramin sanin da ya yiwa duniya kenan.
Can qasan ranta umman ta saki ajiyar zuciya,tana jin fiye da rabin tashin hankalinta na kwaranyewa,saidai kuma akwai sauran fargaba a tare da ita,don batasan waye ne ya dauko ya maqalawa kaltum din ba,taji ranta yana motsawa,tausayi da bacin rai suka cakude waje daya suna karafkiya cikin ranta,kamar ba zata tankashi ba saita kasa,duban fuskar kaltum kawai ya daga hankalinta
"A wannan zamanin?,a irin wannan lokacin zaka yiwa diyarka irin wannan auren na rashin siyar daraja da mutunci?"
Idanunsa ya bubbude sosai yana hura hanci,baya so kuma baya sha'awar tayi masa wata magana,kota kawo masa tarnaqi kan hukuncin daya yanke ko misqala zarratin,don baiga uban daya isa yasashi ya janye wannan hukuncin ba
"Ke zuwaira ki fita daga ido na,ita din uban wace da bazan zaba mata miji ba?,ina cewa yarinya budurwa uba ne dama yake da haqqin zaba mata miji,shine zaki hurewa yarinya kunne ki sakata ta bijiremin?,to wallahi ta gwada,bismillah,ga fili ga me doki nan,nida ku uban wanda ya fasa" da alamu jama'a yakeson tara mata,saita miqe tana riqe da hannun kaltum zuciyarta na quna
"Ko da wanne lokaci fa zan tattarata a miqa masa ita" ya bisu da kalmar sanda umman ta kama hannun kaltum da tuni hawaye ya jiqe mata fuska,tsantsar tashin hankali kuma ya cika zuciya har saman fuskarta.
Mamaki ya kuma kama umman,wanne irin abu ne kuma haka,a daura ma yarinyar aure ba tare da tasan mijin ba,sanna ace ta shirya kowanne lokaci zata iya barin gidansu?,babu wani shiri tanadi ko sakawa rai?,mema suke dashi da zasu kaita dashi?.
Kamar yasan tunanin da takeyi saiya fiddo sadakinta daga aljihunsa,wanda sai daga baya daya nutsu ya lissafa yaga dubu arba'in da daya harda dari biyar akai,yana da yaqinin zata yi ma yarinyar kayan daki,ya lissafa ya dauki dubu ashirin ya miqa mata
"Nasan dai tunanin da kike,gashinan ayi mata wani abu dasu wanda zata tafi dasu,daga baya aje ayi mata jere"
"Amma wannan wanne irin al'amarine fisabilillahi malam?,wannan abun fa kwata kwata baiyi dai dai ba,yadda kake da haqqi a wuyanta itama tana da nata haqqin....." Saiya zaburo ya fara maganganu,maganganun da suka sanyata dole ta janye kaltum,suka fice ranta a mugun bace.
Kasa riqe kukanta kaltum tayi sanda suka koma daki,su yakumbo suna tambayar lafiya?,ganin yadda yanayin fuskarsu ya nuna zallar tashin hankali.
A karon farko bayan dukka abindanya faru,qwalla ta subuce daga idanun umman sanda take gaya musu abinda ya faru,ran yakumbo a bace ta miqe
"Haba,wannan abun yayi yawa,bari naje na sameshi,yarinyar yar tsana ce ita da za'a bada ita sadaka?,batasan miji ba miji bai santa ba?,sannan ace a shirya kowanne lokaci za'a kaita?" Harta sanya kai kawu ado ya shigo gidan,ta dubi qofar dakin amadu a kulle,da alama ya fice abinsa
"Ke kuma lafiya kamar wadda aka koro" kawu ado ya fada yana kallon fuskar yakumbo indo data cika da bacin rai
"Shigo daga ciki yaya" ta fadi tana juyawa dakin umma,saiya sanya kai shima,ya samu kujera yaja ya zauna.
A taqaice yakumbo ta labarta masa komai,sai yayi shuru yana jinjina kai,tabbas lamarin ya bugeshi ya kuma bashi mamaki,hakanan tun a hanya daya taho aka bashi labarin,saidai bai gasgata ba,ganin labarin yayi kama dana qanzan kurege.
"Da farko mu soma aiki da hankali tukunna,dukkaninmu nan amadu ya fimu iko da diyarsa kattume,hakanan a cikinmu babu wanda ya isa yaja da hukuncin daya yanke akan diyarsa koda gaban alqali akaje kuwa....saidai idan ita yarinyar taja da kanta,idan akwai abinda zamu iya cikin wannan lamarin bai wuce mu bashi shawara,mu kuma nusashe da shi ba,idan ya dauka haka mukafi so,idan bai dauka ba kuma,mataki daya zamu dauka,mu binciki halayyar yaron sana'a gami da nasabarsa,idan muka tabbatar da bashi da matsala a dukka wadan nan,sai muyi haquri,mu bi auren da addu'ar sanyawar albarkar ubangiji" a hankali zukata suka soma sauka daga bayanan da kawu ado yayi,ga duk me nisan hankali a cikinsu idan ya yiwa kalaman kallo na tsanaki,zai hango ya kuma shanshano gaskiyar zancan kawu ado,saidai ko daya zuciyar kaltum bata rusuna ba,saima tashin hankali data sake shiga dajin zancan kawu adon,yana nufin kenan a haqura a miqata ga duk wanda baban nata ya bata aurensa?,saita sake fashewa da kuka cikin tashin hankali.
*******A nutse yake shiryawa duk da cewa yayi nisa a tunanin da yakeyi,har ya gama shirinsa tsaf,ya dawo a hankali ya zauna gefam katifa yana jan kayan breakfast dake saman wani babban tray da niyyar yin break aamiru na zaune saman wani stool yana dubanshi,hannayensa goye a qirijinsa.
Hannayen nasa ya saki yana sauke ajiyar zuciya,fuskarsa da alamun damuwa yace
"Am asking you since yesterday.....ya zakayi da auren nan,bakace min komai ba" kamar ko yaushe harara ya watsa masa yana hada tea din,sai daya kammala ya riqe kofin a hannunsa zaikai baki sannan yace cikin wani irin soft voice
"Da zaka dameni duk ba kaine ka jawo komai ba?,dana sani ma na qyaleka,idan yaso in ka koma hajiya qarama tayi banda da namanka" duk da tasirin damuwar dake tattare dashi amma sai daya daara,kana ya koma ya daidata zamansa sosai,cikin seriousness yace
"Am bother to ask you ne saboda hajiya qaraman da kuma boss professor,but u are feeling bossy,sai wani jamin aji kakeyi"
"An ja makan,idan kaji haushi ka barni da matsalata" kafada amirun ya dage
"Kome zakace zan dauka,saboda bamu saba hadiye damuwoyinmu mu kadai ba" qaramin murmushi ya subucewa saraki,saiya aje cup din a gabansa,ya hade yatsunsa waje guda yana kallon amirun
"Wani abun mamaki,ban dauki wannan abun daya faru a bakin komai ba,but amma sai naketa jin nauyinsa a kaina tun jiyan?" Shuru ya ratsa tsakani,amiru ya saki ajiyar zuciya,muryarsa tayi sanyi fiye da dazu
"Ni kaina gaba daya tunani na ya qare akan yadda wannan al'amarin zai warware....ni inaga.....me zai hana ka qara ko one week ne,ka more sadakinka kawai,daga nan ka rubuta masa takardarta kawai ka maidata gida?" Wanu banzan kallo ya jefa masa