Sashe 56
Dabiar Zuciya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Sorry man,amma dai gaskiya ni bazan zauna na tasa aiki a gaba ba,kullum bani da abunyi saishi,tunda dai bashi zan aura ba ko?,bazan kuma biye maka ba,ya zamana daga ni har kai babu wani me qwaqwaran magana akansa,waima tsaya.....ina natun jauhar?" Yayi maganar yana zunkudawa gaba gami da tsare samir da ido.
Dubansa yayi da manyan idanunsa da gasken computer ke sake shiga ciki,sannan ya kauda idon nasa,kamar bazai amsa ba sai kuma yace
"Kaga malam,nifa bazan auri yarinyar nan ba"
"Saboda me?,look saraki,wasu lokutan fa kai kake sake haifar da sabin fahimta tsakaninka da daddy,yarinyar nan she has everything da akeson mace dashi, she's beautiful...tana da gata tana da ilimi...then...me kake buqata sama da haka?" Fuskar computer din ya rufe ba tare daya kasheta bama,ya tsare amiru da ido don ya gane cewa kome zai fada da gaske yake
"Duk abinda ka fada hakane,tana da komai,but....bazan aureta ba" daga haka yatsaya kawai,sai suka shiga kallon kallo shida amiru,wanda daga bisani amirun shiya dage kafadunsa kawai gami da tabe baki
"Well,da alama you are ready to face the consequences,any way......dazu kamar kana maganar zuwa qauye gobe ko?, right?"
"Dan rainin hankali,ashe ka jini" ya fada qasa qasa,kamar meyin mita,yana buda fuskar computer din da niyyar kasheta gaba daya,bai amsawa amiru ba har ya kashe,sannan ya dubeshi
"Haka nace,saboda ginin makarantar ya kammala,ya kamata a budeta,saboda a samu dama a fara karatu,sannan....."sai yayi shuru yana jan iska hunhunsa,a duk sanda zai tuna da yaron sai yaji babu dadi
"Akwai ragowar hakkin yaron nan,inason na kaiwa iyayensa" kai amiru ya jinjina,shi kansa daga yadda ya samir ya bashi labarin iya abinda ya sani game da rayuwarsu,da abinda yaji daga hannafi,da kuma abinda ya gani da idanunsa,sai ya tsinci kansa da tausayin yaron duk da ya tafi yayi nisan kiwo
"Hakan yayi,kace na shirya,am in love with garin fa?,nima yanayin qauyen yamin.....sai naji nayi kewar azare,duk daba qauye bane" murmushi samir ya saki,shikam ya soma jin dadin tafiye tafiyensa zuwa qauyukan da yakeyi,saboda ya zame masa tamkar wata makaranta ce daya bude ta qashin kansa,yana ganin salo da nau'in rayuwa iri daban daban,harda wadda mafarkinsa bai taba kawo masa ba,saiya soma baiwa amiru labarin garuruwan da ya jajje,ciki harda qauyen dinya,wanda a cikinsa ne ya soma kwana.
Wani abun yayi dariya wani abun yaja tsaki,amma dariyar da yakeyi din yafi yawa,bama kamar da yake bashi labarin yadda 'yammatan qauyen suke,da kuma yadda abokinsa haladu ya mato akan kaltum,daya fasaltawa amirun yadda kaltumen take harda fadowa qasa saboda dariya,don a ranar daya ganta ana cikin rudani da alhini ba wani kallonta yayi sosai ba
"Dole muje,nima nayi koda 'yammata biyu ne na kafa tarihi" harara samir ya jefa masa sanda ya miqe da niyyar zuwa toilet
"Kamar a kunnen khalisa"
"Dama dai kuna shiri" ya amsa masa,sanin cewa ba wani shiri suke sosai da samir din ba,saboda kowa tsarin dan uwansan bai masa ba.
********Tafe take a hankali tana ratsa 'yan zaman makoki,iskar sanyi na kadata yadda taga dama,kasancewar ta sake wani ramewa da bushewa tun daga wancan ranar,hannunta dauke da geron data auno,wanda yakumbo indo ce tace a auna din,za'a kai ayi gumbar sadakar uku a gobe.
"Yammataaaa" taji an fada,da muryar nan data tsani ji,har ta wuceshi yayu wuf yasha gabansa,ta daga kai ta dubeshi,itakam bataga amfanin rayuwa irin ta auwalu ba,koda yaushe ace mutum ba'a saitinsa yake ba,dai kaga yana gyangyadawa ko yana girgidi?.
Wani busashen murmushi ya sakar mata
"Yas......yaaa kuma wai qarun haqurinmu?,Allah ya jiqan bilale.....eh....ya kuma kyauta eh yane" tsaki taja tamkar xata tsinke harsheta,ta kuma maka masa harara sannan tayi gaba,tana jiyo lafazinsa na
"Zaki bayani eh.....gobe zaki zama tawa" daukar zancan nasa tayi a matsayin shirme da molanka da wadanda suka bugu suka sabayi,don haka koda ta shiga ciki,ci gaba tayi da sabgarta,bata ma sake tuna maganarsa ba bare ta dameta,gaba daya su da uwarsu sun sake fice mata akai,laure tunda aka gama hada bilal aka fita dashi bata sake takowa bangarensu ba,dama ba zatace taga asiya bama sam,duk da yake ita kanta uwarta yanzu ganin nata sai sa'i,sa'i,saboda ta fantsama gari da sunan makaranta,makarantar da babu wanda yasan taqamaimai dinta,amma saboda tsabar ƁABI'AR ZUCIYA na son rai,duka sunbi sun rufe idanunsu daga kallon abinda yake faruwa,da kuma abinda zai biyo baya.
Bayan sallar la'asar,suna zaune a dakin ummanmu ana hada 'yan tsummokaran bilal da za'a bada sadaka,idanun kaltum jiqe da hawaye,yayin da zuciyar ummanmu ke suya,jarumtar da tayi babu wanda ya zaceta,dai dai sannan babansu ya daga labule ya kirata ita da umman zuwa dakinsa.
Dukkansu a darare suka shiga,bama kamar ya kaltum,wanda ta manta ma yadda fasalin dakin yake da abinda ke cikinsa
"Ku qaraso ciki ku zauna" maganar data basu mamaki kenan,amma sanin cewa zukata a tausashe suke matuqa,cike da rauni saboda rashin da sukayi,sai mamakin nazu ya zama gajere,kowanne ya samu mazauni yana jiran ji daga bakinsa.
"Yauwa,na kiraku nan ne don na tuna muku keda kattume cewa,wa'adin dana deba mata na fidda miji ya cika....tun ranar da bilalu ya rasu,to saboda wannan rashin ya sanya na daga mata qafa,na qara mata wadan nan kwanakin,koda na qara dinma abinda na fuskanta shine babu wani data tsayar,wannan dalilin yasa ni da iliyasu da laure.....muka yanke shawarar zamu baiwa auwalu aurenta kawai,kowa ya huta,tuwona maina".
Wani irin kallo umman tayi masa,wani abu mai kama da bacin rai yana ratsata,laure?,iliyasu?,auwalu?,inda zata iya tambayarsa zatayi,shin laure ko iliya suka daukar mata cikin kattume har suka haife mata ita ko kuwa?,shin su ke da ahaqqu da ita da zasu dauki ragamar bada shawarar a hadata aure da lalataccen dansu?,wanda suma suka rasa yadda zasuyi dashi?,amma ba zata iya hakan ba gaban 'yarsu,zaidai bata jin zata iya shuru,saboda haka tace
"Ka aura mata koma waye,matuqar mutuncinsa dabi'arsa da addininsa sun cika amma banda iliya".
"Zuwaira me kike nufi?,wai ko abinda laure take fada naketa karewa ya tabbata gaskiya ne?" Kallon dake nuna ranta ya fara baci tayi masa,me yasa har kwanan gobe fifita laure yake a kanta?,kamar ma itace matarsa ba ita zuwaira ba?,kafin ta dire fadanta ya fara bambamin bala'i
"Indai zuwara bakison jinin iliya nima baki sona,saboda abinda yayishi shi yayini,kin daurewa yarinya qarqashi taci gaba da zama gandandan a gabanki tana abinda taga dama ko?to wallahi ni nafi qarfin gidana,ba macen data isa ta takani kona mata biyayya,saidai a bini"
Ranta yakai maqurar baci,saita kasa shuru
"Yaushe Allah yayi daren bare gari ya waye?,kwanan kaltum nawa duka a duniya?,banda al'ada a yanzun kaltum bata isa aure a wasu guraren ba,ba abinda zaisa naqi jinin iliya,saboda jinin 'ya'yana ne,abu daya nace....ka aura mata koma waye,ko daga ina yake,ko wanne jinsi yare ko qabila ne matuqar ya cika sharuddan da za'a bashi aure amma banda auwalu,saboda banga wani garanti qarko ko kwaliti da yake dashi ba".
Sai a sannan kaltum data kifa kai tana kuka ta daga kaibta dubi ummanta,karon farko kuma a kanta umman tasu ta maidawa babansu magana,abinda bata taba jin ko ganin ya faru ba tunda ta haifeta.
Wannan abun shi ya qara harzuqa malam amadu
"Ni kike maidawa magana zuwaira?,to wallahi wallahi ko ga waye saina aurar da kattume daga yau zuwa gobe,zabi guda uku,inma daga yanzu zuwa sallar magariba ta fitar da miji?,in bata kawo ba zanyi shelar bada sadakarta a sallar magariba ta anjima,idan ba'a samu me karba ba kuwa,babu uban daya isa ya hanani daura mata aure da auwalu a gobe wajen addu'ar uku koda sama da qasa zata hade.....ku tashi ku fitarmun daga daki zan kulle dakina" ya fada yana kadasu da hannu kamar wasu kaji.
Duqawa ummanmu tai ta kama hannun kaltum ta miqar da ita,tana jin qirjinta yana suya,kamar takai gejin da ta fara gaza daukar abubuwan da suketa afkowa cikin rayuwarta ne,tana jin haka cikin ranta.
Sannu a hankali suke takawa shi da amiru zuwa bakin masallacin da byan zuwan samir garin aka masa kwaskwarima aka gyarashi.
Dukkansu suna daure da alwalar sallar magariba kowannensu,saboda mintuna kadan suka rage lokacinta yashiga.
Suna tafe samir na nuna masa guraren da ya dan sani a zamansa a garin,abun sai yake qayatar da amiru,fuskokinsu kawai zaka kalla ka tabbatar da irin nishadin da suke ciki,duk da sunyi shiga ta baina baina,amma kana musu kallo daya zakasan cewa fatarsu da irin fresh da jikinsu yake dashi,basu saba rayuwa a irin wannan gurbin ba.
A haka har suka iso bakin masallacin,sanda liman yake qwala kiran sallar,sai suka shige masallacin gaba daya.
Sahu suka hada sannan suka zauna kafin lokacin da za'a tada iqama,yayin da hirarsu ta yanke,wannan dabi'a ce da suka samota tun asali daga wajen professor,tun suna qanana sanda suke zuwa masallaci salla.
Daga bayansu kadan ya hangi hannafi ya shigo,ya samu waje shima ya zauna,da kadan kadan masallacin ya fara cika,aka tada iqama sannan aka kabbara salla.
Minti biyar aka liman yayi sallama,masu azkar suka fara,masu gaggawar barin bigiren da sukayi sallah,ba tare da sunsan romon xama a inda mutum yayi sallah ba bayan ya idar suka fara gaggawar tashi
"Ah jama'a assalamu alaikum,kowa ya dakata a inda yake,akwai muhimmiyar sanarwa" malam amadu ya fada bayan ya miqe tsaye daga sahun gaba da yake yana fuskantar masallaci,hakan yasa masu niyyar fita suka tsaya cak,na zaune kuma suka bada hankalinsa akanshi,ciki harda samir da amir da suka bishi da kallo.
"Salamu alaikum jama'a a karo na biyu,kowa dai yasan sunana yasan waye ni,sanarwa nakeso na bayar na auren diyata kattume game buqata,inason aurar da ita a asubahin gobe idan Allah ya kaimu,ga duk wanda keso....na dauke masa nauyin komai,ya biya sadaki,shaidu su shaida a daura masa aure da ita" tsit masallacin yayi kafin daga bisaninya rude da hayaniya,kowa da abinda yake fada,wasu na fadin lallai ta tabbata yarinyar ta aikata abinda ta aikata shi yasa abinda ya faru ya faru din,yayin da wasu ke da sukasan ainihin rayuwar gidan malam amadu ke cike da mamakin abunda ya afku a yanzun,a iya saninsu wannan abun tsohuwar al'adace,wadda su kamsu qauyen duk da qarancin wayewa suka daina amfani da ita,cikin masu ganin baiken hakan harda hannafi,wanda yasan komai game da rayuwar gidan malam amadu.
Ganin abun zai zama cece kuce sai liman ya karbi lasifiqa yayi magana
Dubansa yayi da manyan idanunsa da gasken computer ke sake shiga ciki,sannan ya kauda idon nasa,kamar bazai amsa ba sai kuma yace
"Kaga malam,nifa bazan auri yarinyar nan ba"
"Saboda me?,look saraki,wasu lokutan fa kai kake sake haifar da sabin fahimta tsakaninka da daddy,yarinyar nan she has everything da akeson mace dashi, she's beautiful...tana da gata tana da ilimi...then...me kake buqata sama da haka?" Fuskar computer din ya rufe ba tare daya kasheta bama,ya tsare amiru da ido don ya gane cewa kome zai fada da gaske yake
"Duk abinda ka fada hakane,tana da komai,but....bazan aureta ba" daga haka yatsaya kawai,sai suka shiga kallon kallo shida amiru,wanda daga bisani amirun shiya dage kafadunsa kawai gami da tabe baki
"Well,da alama you are ready to face the consequences,any way......dazu kamar kana maganar zuwa qauye gobe ko?, right?"
"Dan rainin hankali,ashe ka jini" ya fada qasa qasa,kamar meyin mita,yana buda fuskar computer din da niyyar kasheta gaba daya,bai amsawa amiru ba har ya kashe,sannan ya dubeshi
"Haka nace,saboda ginin makarantar ya kammala,ya kamata a budeta,saboda a samu dama a fara karatu,sannan....."sai yayi shuru yana jan iska hunhunsa,a duk sanda zai tuna da yaron sai yaji babu dadi
"Akwai ragowar hakkin yaron nan,inason na kaiwa iyayensa" kai amiru ya jinjina,shi kansa daga yadda ya samir ya bashi labarin iya abinda ya sani game da rayuwarsu,da abinda yaji daga hannafi,da kuma abinda ya gani da idanunsa,sai ya tsinci kansa da tausayin yaron duk da ya tafi yayi nisan kiwo
"Hakan yayi,kace na shirya,am in love with garin fa?,nima yanayin qauyen yamin.....sai naji nayi kewar azare,duk daba qauye bane" murmushi samir ya saki,shikam ya soma jin dadin tafiye tafiyensa zuwa qauyukan da yakeyi,saboda ya zame masa tamkar wata makaranta ce daya bude ta qashin kansa,yana ganin salo da nau'in rayuwa iri daban daban,harda wadda mafarkinsa bai taba kawo masa ba,saiya soma baiwa amiru labarin garuruwan da ya jajje,ciki harda qauyen dinya,wanda a cikinsa ne ya soma kwana.
Wani abun yayi dariya wani abun yaja tsaki,amma dariyar da yakeyi din yafi yawa,bama kamar da yake bashi labarin yadda 'yammatan qauyen suke,da kuma yadda abokinsa haladu ya mato akan kaltum,daya fasaltawa amirun yadda kaltumen take harda fadowa qasa saboda dariya,don a ranar daya ganta ana cikin rudani da alhini ba wani kallonta yayi sosai ba
"Dole muje,nima nayi koda 'yammata biyu ne na kafa tarihi" harara samir ya jefa masa sanda ya miqe da niyyar zuwa toilet
"Kamar a kunnen khalisa"
"Dama dai kuna shiri" ya amsa masa,sanin cewa ba wani shiri suke sosai da samir din ba,saboda kowa tsarin dan uwansan bai masa ba.
********Tafe take a hankali tana ratsa 'yan zaman makoki,iskar sanyi na kadata yadda taga dama,kasancewar ta sake wani ramewa da bushewa tun daga wancan ranar,hannunta dauke da geron data auno,wanda yakumbo indo ce tace a auna din,za'a kai ayi gumbar sadakar uku a gobe.
"Yammataaaa" taji an fada,da muryar nan data tsani ji,har ta wuceshi yayu wuf yasha gabansa,ta daga kai ta dubeshi,itakam bataga amfanin rayuwa irin ta auwalu ba,koda yaushe ace mutum ba'a saitinsa yake ba,dai kaga yana gyangyadawa ko yana girgidi?.
Wani busashen murmushi ya sakar mata
"Yas......yaaa kuma wai qarun haqurinmu?,Allah ya jiqan bilale.....eh....ya kuma kyauta eh yane" tsaki taja tamkar xata tsinke harsheta,ta kuma maka masa harara sannan tayi gaba,tana jiyo lafazinsa na
"Zaki bayani eh.....gobe zaki zama tawa" daukar zancan nasa tayi a matsayin shirme da molanka da wadanda suka bugu suka sabayi,don haka koda ta shiga ciki,ci gaba tayi da sabgarta,bata ma sake tuna maganarsa ba bare ta dameta,gaba daya su da uwarsu sun sake fice mata akai,laure tunda aka gama hada bilal aka fita dashi bata sake takowa bangarensu ba,dama ba zatace taga asiya bama sam,duk da yake ita kanta uwarta yanzu ganin nata sai sa'i,sa'i,saboda ta fantsama gari da sunan makaranta,makarantar da babu wanda yasan taqamaimai dinta,amma saboda tsabar ƁABI'AR ZUCIYA na son rai,duka sunbi sun rufe idanunsu daga kallon abinda yake faruwa,da kuma abinda zai biyo baya.
Bayan sallar la'asar,suna zaune a dakin ummanmu ana hada 'yan tsummokaran bilal da za'a bada sadaka,idanun kaltum jiqe da hawaye,yayin da zuciyar ummanmu ke suya,jarumtar da tayi babu wanda ya zaceta,dai dai sannan babansu ya daga labule ya kirata ita da umman zuwa dakinsa.
Dukkansu a darare suka shiga,bama kamar ya kaltum,wanda ta manta ma yadda fasalin dakin yake da abinda ke cikinsa
"Ku qaraso ciki ku zauna" maganar data basu mamaki kenan,amma sanin cewa zukata a tausashe suke matuqa,cike da rauni saboda rashin da sukayi,sai mamakin nazu ya zama gajere,kowanne ya samu mazauni yana jiran ji daga bakinsa.
"Yauwa,na kiraku nan ne don na tuna muku keda kattume cewa,wa'adin dana deba mata na fidda miji ya cika....tun ranar da bilalu ya rasu,to saboda wannan rashin ya sanya na daga mata qafa,na qara mata wadan nan kwanakin,koda na qara dinma abinda na fuskanta shine babu wani data tsayar,wannan dalilin yasa ni da iliyasu da laure.....muka yanke shawarar zamu baiwa auwalu aurenta kawai,kowa ya huta,tuwona maina".
Wani irin kallo umman tayi masa,wani abu mai kama da bacin rai yana ratsata,laure?,iliyasu?,auwalu?,inda zata iya tambayarsa zatayi,shin laure ko iliya suka daukar mata cikin kattume har suka haife mata ita ko kuwa?,shin su ke da ahaqqu da ita da zasu dauki ragamar bada shawarar a hadata aure da lalataccen dansu?,wanda suma suka rasa yadda zasuyi dashi?,amma ba zata iya hakan ba gaban 'yarsu,zaidai bata jin zata iya shuru,saboda haka tace
"Ka aura mata koma waye,matuqar mutuncinsa dabi'arsa da addininsa sun cika amma banda iliya".
"Zuwaira me kike nufi?,wai ko abinda laure take fada naketa karewa ya tabbata gaskiya ne?" Kallon dake nuna ranta ya fara baci tayi masa,me yasa har kwanan gobe fifita laure yake a kanta?,kamar ma itace matarsa ba ita zuwaira ba?,kafin ta dire fadanta ya fara bambamin bala'i
"Indai zuwara bakison jinin iliya nima baki sona,saboda abinda yayishi shi yayini,kin daurewa yarinya qarqashi taci gaba da zama gandandan a gabanki tana abinda taga dama ko?to wallahi ni nafi qarfin gidana,ba macen data isa ta takani kona mata biyayya,saidai a bini"
Ranta yakai maqurar baci,saita kasa shuru
"Yaushe Allah yayi daren bare gari ya waye?,kwanan kaltum nawa duka a duniya?,banda al'ada a yanzun kaltum bata isa aure a wasu guraren ba,ba abinda zaisa naqi jinin iliya,saboda jinin 'ya'yana ne,abu daya nace....ka aura mata koma waye,ko daga ina yake,ko wanne jinsi yare ko qabila ne matuqar ya cika sharuddan da za'a bashi aure amma banda auwalu,saboda banga wani garanti qarko ko kwaliti da yake dashi ba".
Sai a sannan kaltum data kifa kai tana kuka ta daga kaibta dubi ummanta,karon farko kuma a kanta umman tasu ta maidawa babansu magana,abinda bata taba jin ko ganin ya faru ba tunda ta haifeta.
Wannan abun shi ya qara harzuqa malam amadu
"Ni kike maidawa magana zuwaira?,to wallahi wallahi ko ga waye saina aurar da kattume daga yau zuwa gobe,zabi guda uku,inma daga yanzu zuwa sallar magariba ta fitar da miji?,in bata kawo ba zanyi shelar bada sadakarta a sallar magariba ta anjima,idan ba'a samu me karba ba kuwa,babu uban daya isa ya hanani daura mata aure da auwalu a gobe wajen addu'ar uku koda sama da qasa zata hade.....ku tashi ku fitarmun daga daki zan kulle dakina" ya fada yana kadasu da hannu kamar wasu kaji.
Duqawa ummanmu tai ta kama hannun kaltum ta miqar da ita,tana jin qirjinta yana suya,kamar takai gejin da ta fara gaza daukar abubuwan da suketa afkowa cikin rayuwarta ne,tana jin haka cikin ranta.
Sannu a hankali suke takawa shi da amiru zuwa bakin masallacin da byan zuwan samir garin aka masa kwaskwarima aka gyarashi.
Dukkansu suna daure da alwalar sallar magariba kowannensu,saboda mintuna kadan suka rage lokacinta yashiga.
Suna tafe samir na nuna masa guraren da ya dan sani a zamansa a garin,abun sai yake qayatar da amiru,fuskokinsu kawai zaka kalla ka tabbatar da irin nishadin da suke ciki,duk da sunyi shiga ta baina baina,amma kana musu kallo daya zakasan cewa fatarsu da irin fresh da jikinsu yake dashi,basu saba rayuwa a irin wannan gurbin ba.
A haka har suka iso bakin masallacin,sanda liman yake qwala kiran sallar,sai suka shige masallacin gaba daya.
Sahu suka hada sannan suka zauna kafin lokacin da za'a tada iqama,yayin da hirarsu ta yanke,wannan dabi'a ce da suka samota tun asali daga wajen professor,tun suna qanana sanda suke zuwa masallaci salla.
Daga bayansu kadan ya hangi hannafi ya shigo,ya samu waje shima ya zauna,da kadan kadan masallacin ya fara cika,aka tada iqama sannan aka kabbara salla.
Minti biyar aka liman yayi sallama,masu azkar suka fara,masu gaggawar barin bigiren da sukayi sallah,ba tare da sunsan romon xama a inda mutum yayi sallah ba bayan ya idar suka fara gaggawar tashi
"Ah jama'a assalamu alaikum,kowa ya dakata a inda yake,akwai muhimmiyar sanarwa" malam amadu ya fada bayan ya miqe tsaye daga sahun gaba da yake yana fuskantar masallaci,hakan yasa masu niyyar fita suka tsaya cak,na zaune kuma suka bada hankalinsa akanshi,ciki harda samir da amir da suka bishi da kallo.
"Salamu alaikum jama'a a karo na biyu,kowa dai yasan sunana yasan waye ni,sanarwa nakeso na bayar na auren diyata kattume game buqata,inason aurar da ita a asubahin gobe idan Allah ya kaimu,ga duk wanda keso....na dauke masa nauyin komai,ya biya sadaki,shaidu su shaida a daura masa aure da ita" tsit masallacin yayi kafin daga bisaninya rude da hayaniya,kowa da abinda yake fada,wasu na fadin lallai ta tabbata yarinyar ta aikata abinda ta aikata shi yasa abinda ya faru ya faru din,yayin da wasu ke da sukasan ainihin rayuwar gidan malam amadu ke cike da mamakin abunda ya afku a yanzun,a iya saninsu wannan abun tsohuwar al'adace,wadda su kamsu qauyen duk da qarancin wayewa suka daina amfani da ita,cikin masu ganin baiken hakan harda hannafi,wanda yasan komai game da rayuwar gidan malam amadu.
Ganin abun zai zama cece kuce sai liman ya karbi lasifiqa yayi magana