Sashe 17
Dabiar Zuciya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Washewa fuskarsa tayi da wani murmushi mai aji,ya soma qoqarin jan kujera daya don yiwa kansa mazauni sannan ya amsa mata
"A'ah anna....bani da wani abu da zan aiwatar ne da safen....shi yasa na zabi na huta kafin na fita yau,don jiya ban samu zama yadda naso ba" ya qarashe maganar yana duqawa zuwa qasa gefan mahaifinsa,muryarsa cike da tsantsar ladabi ya furta
"Barka da asuba daddy" kallo daya yayi masa ya maida kansa ga abincinsa yana amsa masa da
"Ka tashi lafiya?"
"Lafiya alhmdlh" sai ya maida dubansa ga mommy wato hajiya jidda
"Barka da asuba mommy"
"Barka kadai yarona....da fatan ka tashi lafiya"
"lafiya qalau alhdmdlh"
"To ma sha Allah" ta amsa masa fuskarta na nuna jin dadin samunsa lafiya da tayi kamar kullum,saita miqe da kanta ta fara bude dukkan wani kwano dake saman teburin sanda qannensa ke gaisheshi daya bayan daya yana amsa musu,kamar yadda ta saba tanayi kullum kwanan duniya matuqar ya halarci wajen cin abinci,zata bude masa dukka ya zaba abinda yakeson ci,don wani lokaci ma abinda ya zaba yana so shi za'a dafa kowa da kowa,koda ba zabinka kenan ba,tun suna yiwa mommy mita da qorafi har ya zame musu jiki.
"Me zakaci a ciki samir?,Allah yasa akwai wanda ya dace da ra'ayinka" mommy ta fada tana murmushi kamar kullum,wanda baka rabata dashi saman fuskarta,sai a sannan alhj mukhtar yayi magana tun fitowar samir din,idanuwansa saman fuskar mommy,wani abu na yawo saman zuciyarsa,wani abu mai nauyin daya wuce a aunashi a mizani
"Ki kalleshi mana da kyau,ba yau ko jiya ko shekaran jiya aka haifeshi ba,amma kullum kina kallonshi ne kamar ranar nan da aka miqo miki shi cikin tsumman goyo,a qa'ida ya isa aure,a kuma qa'idance kamata yayi ace a gaban matarsa yake" kanta ta langabe tana duban professor
"Haba daddy.....kai kake ma samir kallon yayi girma har haka,ni kam a wajena har yanzu kamar yaron goye nake kallonsa.....bugu da qari ma daddy idan ba'a kula da samir ba...wa zamu kula dashi?,karka manta shi kadai Allah ya bamu...."
"Abbaaaa"sautin muryar jawahir tayi kutse cikin maganar mummy,sautin daya fito a narke,kamar me shirin sakin kuka,waiwayawa suka dukka suna kallonta,sai daddyn ya daga hannayensa duka biyun kafin yace
"You see.....su kuma daughters dina ki kaisu ina?" Murmushi ya saki,wani abu na lilo can qasan ranta da zuciyarta
"Dole dukkaninsu subi bayan samir a wajena" a nutse tsaf daddyn ya waiwaya ya dubi samir din sosai kuma kai tsaye,duk da idanun samir din na kai kawo ne tsakanin yan uwansa,fuskarsa tana fitar da wani murmushi me sanyi mai kuma cike da nutsuwa
"Gwara da kika ce a wajenki,ta ina yaronkin zai kama qafar yarana?,yaron naki da ba jin magana yake ba,wanda ya sarayar da alqiblarsa,babu wanda ya gane har yau inda yasa gaba" samir ya gama fahimtar qorafinsa na jiya da yaketa gujewa shi yakeson sokowa a yau din,saiya dan sunkui da kansa,kana ya daga kan nasa,yana muradun rushe wannan maganar,don baida sha'awar ci gaba da yinta,don haka cikin girmamawa yace da ita
"Kome akayi yau din zanci mommy,ki zauna ki huta....zan zuba da kaina,ina sauri ne ma,jiya akwai taron da zanyi da ma'aikata,ban samu zama ba nasa aka maidashi yau"ya fada yana miqa hannu zai hada tea.
jawahir ce ta miqe da hanzari ya dauka cup din ta soma hada masa,mummy tadan kalleta saita dauke kanta
"yi a hankali sarkin rawar kai,kada ki zuba masa a jiki"mummyn ta fadi sanda jawahir ke aje masa tea din,murmushi yayi ya dauka yana.kaiwa bakinsa,shi yasa yakeson autar tasu,sosai take nuna kumawa kan dukkan wani abu daya shefeshi,ba kamar 'yar uwarta ba,wadda har yanzu bai fuskanci inda ta sanya gaba ba,shegen sin jiki gayunbanza,izgili da yiwa.mutane kallon banza hadi da rashi iya magana dukka najwa ta hadasu,abu daya da yasa bata iya wani kyakkyawan abu a gabansa ko a kansa shine,baya daukar raini,kamar yadda baya raina kowa,tafi kowa sanin ainihin wayeshi,wannan shine ya ke mata waigi a kansa.
miqewa prof yayi yana yagar tissue
"idan ka dawo yau din bayan sallar isha'i,ka sameni zamuyi magana dakai"
"ok daddy"ya fada da muryarsa mai dadi,sannan yaci gaba da kurbar tea din a nutse.
cup din ya ajjiye bayan ya gama amsa wata waya,mummy ta dubeshi
"bakaci komai bafa samir?"
"mommy,am late"
"a maka packaging ka tafi dashi mana,ya zaka fita aiki babu cikakken abinci a cikinka"
"ba komai mommy,zan nemi wani abun naci idan na samu break"
"a'ah..,.najwa......maza,shiga kitchen ki cewa baraka ta baki warmers qanana"fuska tadan bata
"Mommy.....yace a barshi fa"idanu ta fitar mata gaba daya
"ni kuma nace ki dauko....."tuni ta miqe ma kafin mummyn ta qarasa bayani,saboda wani kallo da samir din ya jefeta dashi,harta soma takawa tajishi yana fadin
"dawo ki zauna,jawahir.....jeki dauko,guda daya ma is ok"taf tsoro ya cika cikinta,saboda ba kasafai yake bi takanta ba,tana tsoron irin wannan kallon nasa,saita ci gaba da tafiya ta miqe zuwa kitchen din,wata tsawa ya watsa.mata wadda ta sanyata tsaiwa,ta kuma kasa juyowa,har jawahir tazo ta wuceta da saurinta kuwa kamar yadda ya umarceta
bata motsa ba har sai dataji fitarsa yana cewa idan an zuba jawahir din ta miqa masa yana cikin mota.
koda ta koma harara Mommy ta bita da ita,sannan ta rufeta da fada,tana kallon fuskar jawahir,da alama taji dadin yadda mummyn ta balbaleta da fadan,sai tayi sakato,mamaki fal ranta,me yasa mummy ke mata fada da zafi har haka?,bata tanka ba har jawahir ta fice daga parlour din,saita dauki jakarta dake gefe wanda dama shirin makaranta tayi,kawai ta fice a falon.
yana daga zaune a driver seat ta buda gidan baya ta sanya warmer din sannan ta rufe,saita zagayo inda yake zaune din,fuskarta da murmushi
"a dawo lafya yaya"
"Allah yasa"ya amsa yana shirin rufe murfin motar,saidai jawahir din bata matsa ba tana tsaye still a wajen,kansa ya daga bayan ya sauke glass din motar yana dubanta
"ya akayi auta?"murmushi ta sakeyi
"kayi haquri yaya da abinda ya najwa keyi....ni kaina bansan meya canza ba"qawataccen murmushin gefan baki ya saki
"karki damu, she's still my sister.....ina tunanin tana da damuwa,but we will talk later"kaita gyada kawai kana taja baya,ya tada motar a nutse,ya qarasa bakin gate ya danna horn,idanunsa saman fuskar mai gadinsu da yaketa marmashe gyada yana zubawa cikin jiqaqqen garin kwaki,ya taso da hanzari ya durfafi qofar zai budeta,sai samir ya yafitoshi da hannu,don haka yabar bude qofar ya iskoshi da sauri ya iso bakin window inda samir ke zaune
"Allah ya taimaki saraki"
"an tashi lpy baba"
"lafiya qalau dana"
"abinda aka dafa ne yau baba bai maka ba,na ganka da garinka harda gyada?"samir ya tambayeshi yana dan murmushi,murmushin shima yayi,a ladabce yace
"ko daya mai gida,yau dai bamu samu abun karin bane"fuskarsa cike taf da mamaki bayan yadan yamutsata yace
"kamar yaya?,kune baku da sha'awar ci?"da sauri ya girgiza kai
"ko daya,Allah ya taimakeka wazaiqi abinci irin na gidan professor?,inajin dai yau da gobe ne irin ta bahaushe,wani lokaci ku samu,wani lokacin kuma saidai kowa ya siya abinda yake dashi"baice komai ba saiya duba agogon hannunsa,bashi da lokaci da cikin gidan zai koma,bai zaci wasu cikin gida dake rayuwa tare dasu ba'a basu abinci ba,saiya bude aljihun gaban motarsa ya aciro yan dubu dubu guda biyu ya miqa masa
"gashi,ka ajjiye wancan ka siya wani abun me dumi kaci"hannu bibbiyu yasa ya amsa kudin yana zabga masa godiya,sannan ya tafi qofar ya dage masa gate din,yaja motar da dan hanzari ya fice.
09
*zafafa biyar na kudine,tuntubi wadan nan numbers din don samun naki copy din ki karanta cikin aminci*
08184017082
Ko
09134848107
*_follow us @ instagram_*
https://www.instagram.com/invites/contact/?i=1h9y2qgfg67x5&utm_content=nj79azb
Or facebook
https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share
___________________________
cikin nutsuwar data zame masa jiki,kuma dabi'a yake tuqi,hankalinsa da kunnensa yana kan redion jikin motar daya kunna yana sauraren labaran safiya dake fita tar kamar yana wajen,yayin da wani sashe na hankalinsa ke jefo masa tunani iri daban daban kadan kadan,ciki harda sauyawar dabi'un qanwarsa,duk da cewa dama can halinta daban dana jawahir,ba zakayi tunanin ciki daya suka fito ba.
tafiyar minti kusan arba'in babu wani abu ta sadashi da inda kamfanin nashi yake,wato rukunin ma'aikatun dake sharada industrial area,ya sake rage gudun motar sosai,yana gangarawa sannu a hankali kan kwaltar dake shimfide tsakiyar hanyar,wanda hagunta da damanta dukka gine ginen masna'antu ne.
sa da yakai qarshe sannan ya karya wata kwana ya sake shiga wani titin,titine mai kyau,hakanan babu tarin gine gine barkatai kamae wanda ya baro,a hankali ya tsaya bakin wani babban katafaren gini,wanda yake dauke da bene hawa uku,iya ganinka gini ne daya amsa sunansa gini,wanda da gani ba tambaya kamfanine babba,wanda zaici jimillar ma'aikata masu dama,tako ina hasken gilasai da aka qawata benen me hawa biyu ne yake daukan hankali da idanun me kallo,yayin da manyan rubutun da akayi da manyan baqi can saman qololuwar ginin yake bada wani irin haske da kala me kyau,wannan shine M.S CONSTRUCTION COMPANY,kamfanin da ya shara yayi shuhura wajen karbar kwangilar gine ginen tituna,makarantu asibitoci ma'aikatu dama gidaje da suka amsa sunayensu,daga hannun mutane daban daban,kamfanine da ba'a taba samun kamarshi da yaro matashi ya mallakeshi ba,sannan kuma kamfanine da yayi suna ya danne sunan kowanne kamfani dake jin ya isa,hakan ya sanya yake da tarin abokan adawa da abokan takara bila adadin,saidai akwai wasu turaku dake riqe da kamfanin,wanda su wadancan sam basu san da wannan sirrin ba.
tsaiwar motarsa ba tare da ya dannan horn ba daya daga cikin securities dake tsare da katafariyar qofar shiga da fita ta kamfanin ya taso cikin gaggawa ya bude masa,yana rusunawa cikin girmamawa ya miqa gaisuwarsa,cike da kulawa ya amsa masa,sannan ya dage motar zuwa ciki.
kamar kowanne ma'aikaci,inda kowa yake aje abun hawansa nan shima ya aje tasa,ya kashe motar yana zare muqullin daga jiki,sannan ya waiwaya ya diba wayoyinsa tare da briefcase dinsa,ya dannan lock ya bude motar da niyyar zura qafarsa ya fita,saidai wata mota daga sako kai ta kuma faka da da tashi ya hanashi aiwatar da hakan,sai daya jira tsaiwar motar ta daidaita sannan ya bude ya fito,ba tare daya tsaya shaida waye a dayan motar ba.
"A'ah anna....bani da wani abu da zan aiwatar ne da safen....shi yasa na zabi na huta kafin na fita yau,don jiya ban samu zama yadda naso ba" ya qarashe maganar yana duqawa zuwa qasa gefan mahaifinsa,muryarsa cike da tsantsar ladabi ya furta
"Barka da asuba daddy" kallo daya yayi masa ya maida kansa ga abincinsa yana amsa masa da
"Ka tashi lafiya?"
"Lafiya alhmdlh" sai ya maida dubansa ga mommy wato hajiya jidda
"Barka da asuba mommy"
"Barka kadai yarona....da fatan ka tashi lafiya"
"lafiya qalau alhdmdlh"
"To ma sha Allah" ta amsa masa fuskarta na nuna jin dadin samunsa lafiya da tayi kamar kullum,saita miqe da kanta ta fara bude dukkan wani kwano dake saman teburin sanda qannensa ke gaisheshi daya bayan daya yana amsa musu,kamar yadda ta saba tanayi kullum kwanan duniya matuqar ya halarci wajen cin abinci,zata bude masa dukka ya zaba abinda yakeson ci,don wani lokaci ma abinda ya zaba yana so shi za'a dafa kowa da kowa,koda ba zabinka kenan ba,tun suna yiwa mommy mita da qorafi har ya zame musu jiki.
"Me zakaci a ciki samir?,Allah yasa akwai wanda ya dace da ra'ayinka" mommy ta fada tana murmushi kamar kullum,wanda baka rabata dashi saman fuskarta,sai a sannan alhj mukhtar yayi magana tun fitowar samir din,idanuwansa saman fuskar mommy,wani abu na yawo saman zuciyarsa,wani abu mai nauyin daya wuce a aunashi a mizani
"Ki kalleshi mana da kyau,ba yau ko jiya ko shekaran jiya aka haifeshi ba,amma kullum kina kallonshi ne kamar ranar nan da aka miqo miki shi cikin tsumman goyo,a qa'ida ya isa aure,a kuma qa'idance kamata yayi ace a gaban matarsa yake" kanta ta langabe tana duban professor
"Haba daddy.....kai kake ma samir kallon yayi girma har haka,ni kam a wajena har yanzu kamar yaron goye nake kallonsa.....bugu da qari ma daddy idan ba'a kula da samir ba...wa zamu kula dashi?,karka manta shi kadai Allah ya bamu...."
"Abbaaaa"sautin muryar jawahir tayi kutse cikin maganar mummy,sautin daya fito a narke,kamar me shirin sakin kuka,waiwayawa suka dukka suna kallonta,sai daddyn ya daga hannayensa duka biyun kafin yace
"You see.....su kuma daughters dina ki kaisu ina?" Murmushi ya saki,wani abu na lilo can qasan ranta da zuciyarta
"Dole dukkaninsu subi bayan samir a wajena" a nutse tsaf daddyn ya waiwaya ya dubi samir din sosai kuma kai tsaye,duk da idanun samir din na kai kawo ne tsakanin yan uwansa,fuskarsa tana fitar da wani murmushi me sanyi mai kuma cike da nutsuwa
"Gwara da kika ce a wajenki,ta ina yaronkin zai kama qafar yarana?,yaron naki da ba jin magana yake ba,wanda ya sarayar da alqiblarsa,babu wanda ya gane har yau inda yasa gaba" samir ya gama fahimtar qorafinsa na jiya da yaketa gujewa shi yakeson sokowa a yau din,saiya dan sunkui da kansa,kana ya daga kan nasa,yana muradun rushe wannan maganar,don baida sha'awar ci gaba da yinta,don haka cikin girmamawa yace da ita
"Kome akayi yau din zanci mommy,ki zauna ki huta....zan zuba da kaina,ina sauri ne ma,jiya akwai taron da zanyi da ma'aikata,ban samu zama ba nasa aka maidashi yau"ya fada yana miqa hannu zai hada tea.
jawahir ce ta miqe da hanzari ya dauka cup din ta soma hada masa,mummy tadan kalleta saita dauke kanta
"yi a hankali sarkin rawar kai,kada ki zuba masa a jiki"mummyn ta fadi sanda jawahir ke aje masa tea din,murmushi yayi ya dauka yana.kaiwa bakinsa,shi yasa yakeson autar tasu,sosai take nuna kumawa kan dukkan wani abu daya shefeshi,ba kamar 'yar uwarta ba,wadda har yanzu bai fuskanci inda ta sanya gaba ba,shegen sin jiki gayunbanza,izgili da yiwa.mutane kallon banza hadi da rashi iya magana dukka najwa ta hadasu,abu daya da yasa bata iya wani kyakkyawan abu a gabansa ko a kansa shine,baya daukar raini,kamar yadda baya raina kowa,tafi kowa sanin ainihin wayeshi,wannan shine ya ke mata waigi a kansa.
miqewa prof yayi yana yagar tissue
"idan ka dawo yau din bayan sallar isha'i,ka sameni zamuyi magana dakai"
"ok daddy"ya fada da muryarsa mai dadi,sannan yaci gaba da kurbar tea din a nutse.
cup din ya ajjiye bayan ya gama amsa wata waya,mummy ta dubeshi
"bakaci komai bafa samir?"
"mommy,am late"
"a maka packaging ka tafi dashi mana,ya zaka fita aiki babu cikakken abinci a cikinka"
"ba komai mommy,zan nemi wani abun naci idan na samu break"
"a'ah..,.najwa......maza,shiga kitchen ki cewa baraka ta baki warmers qanana"fuska tadan bata
"Mommy.....yace a barshi fa"idanu ta fitar mata gaba daya
"ni kuma nace ki dauko....."tuni ta miqe ma kafin mummyn ta qarasa bayani,saboda wani kallo da samir din ya jefeta dashi,harta soma takawa tajishi yana fadin
"dawo ki zauna,jawahir.....jeki dauko,guda daya ma is ok"taf tsoro ya cika cikinta,saboda ba kasafai yake bi takanta ba,tana tsoron irin wannan kallon nasa,saita ci gaba da tafiya ta miqe zuwa kitchen din,wata tsawa ya watsa.mata wadda ta sanyata tsaiwa,ta kuma kasa juyowa,har jawahir tazo ta wuceta da saurinta kuwa kamar yadda ya umarceta
bata motsa ba har sai dataji fitarsa yana cewa idan an zuba jawahir din ta miqa masa yana cikin mota.
koda ta koma harara Mommy ta bita da ita,sannan ta rufeta da fada,tana kallon fuskar jawahir,da alama taji dadin yadda mummyn ta balbaleta da fadan,sai tayi sakato,mamaki fal ranta,me yasa mummy ke mata fada da zafi har haka?,bata tanka ba har jawahir ta fice daga parlour din,saita dauki jakarta dake gefe wanda dama shirin makaranta tayi,kawai ta fice a falon.
yana daga zaune a driver seat ta buda gidan baya ta sanya warmer din sannan ta rufe,saita zagayo inda yake zaune din,fuskarta da murmushi
"a dawo lafya yaya"
"Allah yasa"ya amsa yana shirin rufe murfin motar,saidai jawahir din bata matsa ba tana tsaye still a wajen,kansa ya daga bayan ya sauke glass din motar yana dubanta
"ya akayi auta?"murmushi ta sakeyi
"kayi haquri yaya da abinda ya najwa keyi....ni kaina bansan meya canza ba"qawataccen murmushin gefan baki ya saki
"karki damu, she's still my sister.....ina tunanin tana da damuwa,but we will talk later"kaita gyada kawai kana taja baya,ya tada motar a nutse,ya qarasa bakin gate ya danna horn,idanunsa saman fuskar mai gadinsu da yaketa marmashe gyada yana zubawa cikin jiqaqqen garin kwaki,ya taso da hanzari ya durfafi qofar zai budeta,sai samir ya yafitoshi da hannu,don haka yabar bude qofar ya iskoshi da sauri ya iso bakin window inda samir ke zaune
"Allah ya taimaki saraki"
"an tashi lpy baba"
"lafiya qalau dana"
"abinda aka dafa ne yau baba bai maka ba,na ganka da garinka harda gyada?"samir ya tambayeshi yana dan murmushi,murmushin shima yayi,a ladabce yace
"ko daya mai gida,yau dai bamu samu abun karin bane"fuskarsa cike taf da mamaki bayan yadan yamutsata yace
"kamar yaya?,kune baku da sha'awar ci?"da sauri ya girgiza kai
"ko daya,Allah ya taimakeka wazaiqi abinci irin na gidan professor?,inajin dai yau da gobe ne irin ta bahaushe,wani lokaci ku samu,wani lokacin kuma saidai kowa ya siya abinda yake dashi"baice komai ba saiya duba agogon hannunsa,bashi da lokaci da cikin gidan zai koma,bai zaci wasu cikin gida dake rayuwa tare dasu ba'a basu abinci ba,saiya bude aljihun gaban motarsa ya aciro yan dubu dubu guda biyu ya miqa masa
"gashi,ka ajjiye wancan ka siya wani abun me dumi kaci"hannu bibbiyu yasa ya amsa kudin yana zabga masa godiya,sannan ya tafi qofar ya dage masa gate din,yaja motar da dan hanzari ya fice.
09
*zafafa biyar na kudine,tuntubi wadan nan numbers din don samun naki copy din ki karanta cikin aminci*
08184017082
Ko
09134848107
*_follow us @ instagram_*
https://www.instagram.com/invites/contact/?i=1h9y2qgfg67x5&utm_content=nj79azb
Or facebook
https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share
___________________________
cikin nutsuwar data zame masa jiki,kuma dabi'a yake tuqi,hankalinsa da kunnensa yana kan redion jikin motar daya kunna yana sauraren labaran safiya dake fita tar kamar yana wajen,yayin da wani sashe na hankalinsa ke jefo masa tunani iri daban daban kadan kadan,ciki harda sauyawar dabi'un qanwarsa,duk da cewa dama can halinta daban dana jawahir,ba zakayi tunanin ciki daya suka fito ba.
tafiyar minti kusan arba'in babu wani abu ta sadashi da inda kamfanin nashi yake,wato rukunin ma'aikatun dake sharada industrial area,ya sake rage gudun motar sosai,yana gangarawa sannu a hankali kan kwaltar dake shimfide tsakiyar hanyar,wanda hagunta da damanta dukka gine ginen masna'antu ne.
sa da yakai qarshe sannan ya karya wata kwana ya sake shiga wani titin,titine mai kyau,hakanan babu tarin gine gine barkatai kamae wanda ya baro,a hankali ya tsaya bakin wani babban katafaren gini,wanda yake dauke da bene hawa uku,iya ganinka gini ne daya amsa sunansa gini,wanda da gani ba tambaya kamfanine babba,wanda zaici jimillar ma'aikata masu dama,tako ina hasken gilasai da aka qawata benen me hawa biyu ne yake daukan hankali da idanun me kallo,yayin da manyan rubutun da akayi da manyan baqi can saman qololuwar ginin yake bada wani irin haske da kala me kyau,wannan shine M.S CONSTRUCTION COMPANY,kamfanin da ya shara yayi shuhura wajen karbar kwangilar gine ginen tituna,makarantu asibitoci ma'aikatu dama gidaje da suka amsa sunayensu,daga hannun mutane daban daban,kamfanine da ba'a taba samun kamarshi da yaro matashi ya mallakeshi ba,sannan kuma kamfanine da yayi suna ya danne sunan kowanne kamfani dake jin ya isa,hakan ya sanya yake da tarin abokan adawa da abokan takara bila adadin,saidai akwai wasu turaku dake riqe da kamfanin,wanda su wadancan sam basu san da wannan sirrin ba.
tsaiwar motarsa ba tare da ya dannan horn ba daya daga cikin securities dake tsare da katafariyar qofar shiga da fita ta kamfanin ya taso cikin gaggawa ya bude masa,yana rusunawa cikin girmamawa ya miqa gaisuwarsa,cike da kulawa ya amsa masa,sannan ya dage motar zuwa ciki.
kamar kowanne ma'aikaci,inda kowa yake aje abun hawansa nan shima ya aje tasa,ya kashe motar yana zare muqullin daga jiki,sannan ya waiwaya ya diba wayoyinsa tare da briefcase dinsa,ya dannan lock ya bude motar da niyyar zura qafarsa ya fita,saidai wata mota daga sako kai ta kuma faka da da tashi ya hanashi aiwatar da hakan,sai daya jira tsaiwar motar ta daidaita sannan ya bude ya fito,ba tare daya tsaya shaida waye a dayan motar ba.