← Book details Dabiar Zuciya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 108 OF 117

Sashe 108

Dabiar Zuciya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ja da baya yayi,hakanan yaji a daren nan gangar jikinsa tana buqatar jin duminta,sai ya bude ma'ajiyar kayansa,wadda taci cupboard guda,ya lalubo wasu pyjamas farare qal masu budadden qirji ya sanya,ya feshi jikinsa da lallausan turarensa na bacci,sanna ya zura wasu slippers na fata ya dauki wayarsa ya baro sashen.

A hankali ya tura qofar dakin nata,babu haske kwata kwata sia qamshin dake tashi,da alama ta jima da kwanciya,don lokacin da ya kunna fitilar wayarshi ya hangeta ne duqunqune cikin bargo,kyakkyawar fuskarta ta haska tarwai cikin milk din duvet din da take ciki,sai ya maida qofar,ya taka har zuwa bakin gadon.

Da qaramin haske yayi amfani ya kalli fuskarta son ranshi,murmushi kwance saman fuskar tasa,saboda tunawa da wasu abubuwa daya dinga yi a kanta,wamcan lokacin da ya fara ganinta,cikin qauyensu,a yanzun sai yake ganin kamar ba ita ba,komai dake tattare da ita ya canza.

Jan bargon yayi a hankali ya sauko zuwa saman cikinta,ta sake bayyana sosai cikin kayan baccin da suka kwantawa fatarta,sai ya kasa daurewa,ya raba ta bayanta ya kwanta a jikinta tare da sake jawota cikin jikinsa sosai yana sauke numfashi,abinda ya farkar da ita kenan a tsorace

"Shshshsh..... mijinki ne, keep calm sai tayi shuru tana sauraren bugun zuciyarss dake fita da sauri da sauri.

A hankali ya zura hannunsa saman fatar cikinta ta qasan rigarta,ya fara yawo dashi,abinda yaso tafiya da numfashinta kenan,ya kuma qara bugun zuciyarta,saita riqe hannun nasa jin yana son zarcewa zuwa sama,bayan ta tabbatar babu bra a jikinta,da ya gota din kuwa tasan koma meye zayaji shi.

Cikin kasala ya girgiza kansa

"No....dan kadan please....nima na dana,karki hanani,nafa yi qoqari,ba wani abu bane me yawa.... please" ga tsoro ga kunya,saidai cikij wani salo dake nuna qwarewa a iya tafiyar da tattausar soyayya mai narkar da xukata,ya dinga karantar da ita wasu darussa masu wuyar mantawa,ya kaita duniyoyi da babu komai cikinsu face zallar farinciki da masoya ke tsinta a cikinsa,sunyi musayar kalamai,yadda ya fallasa a sirin zuciyarsa a gareta,hakanan bai qyaleta ba itama sai da ta fidda masa dukkan wani sirri dake ranta,ya jita a jiki da zuciyarsa sosai a ranar,da quar ya iya qyaleta bau zarme ba zuwa next level ba,saidai kuma ya qare da ciwon mara sosai,wanda bai sakeshi ba sai gab da asuba.

Tunda ya fito daga wanka yake son su hada ido amma taqi,sbaoda wani nauyinsa da ya dora mata,ya kaita makarantar da bata taba leqawa ba,saidai ta samu tarin karatu da ilimi,ya kuma sake loda mata soyayyarsa ninkin baninkin.

Allah Allah take kawai ya fice daga dakin,kada wani cikin jama'ar gidan ya ganshi ya gane a nan ya kwana,amma sai ta lura shi kam ko a jikinsa,sabgarsa yake hankalinsa kwance

"Ki daura alwala muyi sallah" ya fada yana shimfida abun salla tare da cije dariyarsa,saboda yana son yaga qarshen pretending dinta.

Baki tadan turo gaba,ta tsammaci xai fita ne ya barta,saboda maganar Allah tana kunya yaga tayi wanka a gabansa.

Daga kai yayi yana dubanta,sai tayi maza ra runtse idanunta,ya saki lallausan murmushin nan nasa,sai ya miqe daga sunkuyon da yayi,ya soma takawa zuwa inda take zaune ta nade dukka jikinta da duvet,saboda yadda ya yamutsa gaba daya kayanta.

Dan zabura tayi sanda ta jishi gab da ita,a dole ta juyo ta fuskanceshi,gashinta daya gama yamutsewa ya rufe fiye da rabin fuskarta

"Don Allah.....zan tashi,amma kaje......momma fa?" Murmushi ya sake,tana qara yi masa kyau,sai yakai hannunsa a hankali yana janye gashin nata zuwa baya,hakan ya baiwa fuskarta damar bayyana sosai,yakai idanunsa kan lips dinta wadanda suka danyi ja,yasan kuma hakan xafa faru,saboda ya tsotsesu son ransa

"Momma ma wajen daddy ta kwana,so kada ki wani damu.....ya kamata ki cire wannan kunyar kwata kwata idan kina tare dani,ni mijinki ne kamar yadda kike matata,halal muke ga juna,amma ban sani ba,ko sai ni da kaina na qarasa cire miki ita gaba daya a wuce wajen ne?" Yayi maganar yana sake matsota,abinda yasa taja baya da sauri,ba shire ta sauka daga gadon sai bandaki.

Bin bayanta yayi da kallo kamar wani zautacce,sai kuma murmushi ya subuce masa,yasa hannu saman kansa yana shafa sumarsa,idanunsa a lumshe yana tuna daren jiya,yana kuma jin yadda alwalarsa ke karyewa,saiya daura sabuwa kenan.

Tun bayan futarsa ya barta kwance cikin bargo bacci ya qauracewa idanunta,kamar yadda murmushi yaqi barin fuskarta,ashe haka soyayyar miji da mata take da dadi da kuma gardi?,duk inda ta juya a kaf fadin gadon qamshinsa ke tashi,ta rasa da wanne irin maye turare yake amfani,ya tafi ya bar mata qamshinsa,tasan kuma shine zai hanata sakewa.

Ajiyan ya dasa abubuwa masu matuqar qarfi cikin zuciyarta,saidai wasu guraren a jikinta radadi suke mata,saboda saqonnin data karba masu zafin gaske daga wajen sarakin,ashe a baya yadda take jinsa a ranta wasa ne farin girki inji hausawa.

Gyara kwanciyarta ta sakeyi a karo na barkatai,saidai saukar sautin kuka daga can waje ya sanyata tsaiwa cak,kafin ta samu kanta tana dirowa daga gadon ba tare data shirya ba,bata tsaya neman dankwali ko hijabi ba,daga ita sai doguwar rigar atamafar da sarakin ne ya zabo mata ita kafin ya fita tayo waje,saboda muryar jawahir takeji.

Kafin ta isa har samir hajiya qarama da momma sun rigata isa wajen,sai securities su biyu dake tsaye a can bakin qofa,daga gefe kuma yadikko ce da amiru.

Momma da hajiya qarama ke riqe jawahir din,wani irin kuka take mai ban tausayi,tana sulalewa qasa suna dagota,jiki da qafafuwan kaltum sukayi sanyi,hawaye ya balle mata,bisa dukkan alamu labari yaje kunnnesu,dama kuma zancan duniya baya buya,duk kuwa yadda kakai ga son boyeshi,sai ta kasa tsaiwa,ta nufi jawahir din da hanzari,tana ganinta itama ta nufota suka rungume juna,suka sake sakin sabon kuka.

Samir ne ya qaraso wajen a hankali ya rabasu,sannan ya kama hannun kaltum,zai kama na jawahir ya tuna a yanzun haramunne aikata hakan,sa ya yiwa hajiya qarama alama da ido,ta kamo jawahir din suka nufi falon gidan gaba daya,banda securities da sukaci gaba da kula da gidan.

Sun jima zaune cikin falon wanda yake shuru,bakajin sautin komai sai na kukan jawahir,babu wanda ya hanata kuka kamar yadda babu wanda ya hanata fadar dukkan abinda ke ranta,kalamai ne da suka sanya kowa kuka a wajen sosai,har da daddy da ya fito daga baya

"Ashe ni din ba kowa bace face wulaqantacciya wadda ta fito ta qazamar hanya,ashe bani da wani cikakken asali?,ashe ni da najwa ba mahaifinmu daya ba?,ashe ya saraki bamu hada alaqar komai dashi ba?,me yasa mommy bata tsaya ta haifemu wajen nagartaccen mutum irin daddy ba?,me yasa ta yiwa Allah shishshigi?,bata tsaya mun fito ta tsatson daddy ba?,tayi gaggawa taje ta haifemu daga wani tsatson na daban?,yanzu ace har bushewar zuciyar ya najwa yakai ta cakawa mahaifiyarta wuqa?,wannan wanne irin bala'i ne?" Sosai tausayinta ya cika zuciyar momma,ta matsa kusa da ita ta rungumeta sosai cikin jikinta,tana bata kalamai na ban haquri da yarda da qaddara

"Ni din ki daukeni tamkar mahaifiyarki,daddynku kuma har abada daddynku ne,babu me canza muku wannan" cike da mamaki ta daga ka daga jikin momma din ta dubeta

"Yanzu bayan dukka abinda mummy tayi miki har zaku iya ci gaba da riqeni?" Murmushi momma tayi,tausayin yarinyar na sake ratsata,saboda ta tabbatar nagartacciya ce saboda yadda kowa ke yabonta,tare da kaffa kaffar kada taji al'amarin

"Qwarai kuwa,ke din diyarmu ce halak malak" saita sake fashewa da kuka,wanda daga baya ta sassauta saboda kalaman ban baki data dinga samu daga wajen kowa,kukanta ya koma ajiyar zuciya.

A sannan samir ya miqa hannunsa ya matsa hannuwan kaltum,tadan dubeshi kadan,qasa qasa yace da ita

"Ya isa....kukan ya isa haka,ki adanashi,kada ki rasa na first night" kamar qasa ta tsage ta shige haka taji.

Ido suka hada da amiru,sai ya sakar masa wani kallon tsokana,dauke kansa yayi bayan ya maida masa da harara

"Idan kina fitowa irin haka,zuciyata zata iya bugawa" da sauri ta daga kai ta kalleshi,saiya wara mata idanunsa sosai yana gyada kai alamun tabbatar mata

"U have no idea how much I love you.....but the time will reveal,jeki nemo hijabi" abinda ya sanyata miqewa a kunyace zuwa daki,sai ya dubi jawahir

"Auta bita kuje,karki sake kuka,ki dauka kamar komai bai taba faruwa ba"
"To" ta amsa a matuqar karye

"Promise?" Ya sake cewa da ita,saita gyada kai tana qoqarin maida qwallarta,fuska yadan bata

"No,ki bude baki ki amsa min" murmushi ne ya taho mata mai hade da hawaye,har yanzu da gaske yana nan a matsayin yaya sarakinta,babu abinda ya canza

"Yes yaayaaa" ta amsa masa da yanayin da aca baya take amsa masa,abinda ya taba zukatansu gaba daya

"Good girl" ya fada yana qoqarin boye rauninsa,suka bita da kallo gaba daya sanda take tafiya zuwa dakin kaltum.

A nutse ya faka motarsa a harabar asibitin,wanda suka dauko jawahir da dukkansu sukayi amannar taje taga mahaifiyarta,shi da kaltum ne zaune a gaban,yayin da amiru da jawahir din suke baya.

Sai da yakashe motar sannan ya waiwaya yada dubeta

"Duk abinda ta aikata miki mahaifiyarki ce,she need your respect,sannan idan kika shiga kika zauna kina kuka?,ki tabbatar bazan sake barinki zuwa ba, understand?" Kai ta jinjina tana boye qwallarta

"Ok" ya fada,abinda yasa amiru bude side dinshi ya fito,itama jawahir din haka.

Caraf ya kama hannun kaltum itama dake qoqarin bude nata side ta fita,ya manne tafukan hannuwan nasu waje guda,dumin jikin kowannensu yana ratsa jikin dan uwansa

"Ina zaki madam?"

"Zan raka jawahir" wani narke mata yayi,tamkar dan yaye

"Haba madam.....wannan wata dama ce fa,da mun koma gida shikenan za'a sanya mana ido,don naji hajiya qarama daxun ta fara wasu maganganu....." Qasa yayi da muryarsa

"Please,abun jiya za'a dan sanmu na qara ɗanawa" idanu ta fitar waje gaba daya,amma ganin yadda ya tsareta da nasa idanun masu tsananin kaifi saita sauke nata qasa

"A waje muke fa" tana rufe baki taga motar ta soma duhu,saita daga kai da sauri,ashe danne madagar gilasan motar yayi gaba daya,saidai bai juya ba still ya tsareta da idanuwa ne,gilasan kuma sunayin sama har suka gama rufewa ruffff.

"Yanzu fa?" Ya jefe mata tambayar yana sake jifanta da wani tsumammen kallo,saidai kafin takai ga bashi amsa ma tuni ya hade tazarar dake tsakaninsu.
Chapter 108 · 0% Book details