Sashe 82
Dabiar Zuciya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Da idanunsa ya kafeta sanda take budawa tana duba wanne ne kanwa ke a ciki,yabi hannayenta da kallo wanda ada basu da wani kaurin kirki,amma a yanzu sun ciko sosai,idanunsa suka sauka kan wani abun hannu guda uku dake daure a tsintsiyar hannunta,na dutsune irin dutsen shirin nan shigen na fulani,saidai wadan nan wasu irin masu garai garai da sheqi ne,butter colour ne masu dan girma circle shape.
Rubutune a dutsen tsakiya daya kaso hangowa,ya zuba idanu sosai amma bai gane me aka rubuta ba,har zuwa sanda tace
"Na gama" da siririyar muryarta,ya qarasa a hankali,saiya kama tsintsiyar hannunta,wanda hakan ya sanyata daga idanu ta dubeshi da sauri,sai taga dutsen yake kallo wanda aka rubuta i'm in love da qananun baqaqen rubutu.
Dazu dazu ta siya abun hannun a makaranta,an jima ana saidashi,duk da yadda kuma 'yan ajinsu keta siya bata taba marmarin siya ba,saboda akwai mai sunan samari a jiki da yawa,kowa yana siyan me sunan saurayinsa ne,sai dazu da aka kawo wadan nam design din sukayi mata saita dauka.
Yana gama karantawa ya dago suka hada idanu,tayi saurin dauke idonta tana jin bugun zuciyarta na sake ninkuwa fiye da da,wani irin maganadisu idanunsa ke dashi,ta dade da ganin haka,tun ranar daya tsaidata zai shigar da haladu wajenta,abinda ya janyo a sannan ta kasa maida masa maganganun da tayi niyya kenan.
Ya lura wanu nauyinsa da kuma kawaici take masa,sai yaqi sakin hannun nata,yaci gaba da kallon abun hannun,a hankali ya sakar mata hannun sannan ya fara diban containers din yana maidawa,hakan ya bata damar yin gaba da sauri ta jiqa kanwar,ta matsa gaban tukunyar ta bude ta zuba,ta juya miyar ta tattabatar komai yayi,saita kasa juyowa sanoda tana da tabbacin yana cikin kitchen din,baisan shi mugun nauyinsa takeji bane?,tanason ta qarasa aikinta ne tabar kitchen din,amma wanzuwarsa a nan ya hanata ci gaba da yin komai.
Littafinta na saman freezer din da zai dauki abu,bai kula ba ya bude sai littafin ya fado qasa,ya sunkuya a hankali ya dagashi,zai gyara mata alamar data saka na shaidar inda ta tsaya,saiya buda shafin,idanunsa ya sauka a inda ta saka alamar.
Layi hudu ne,amma suna dauke da wasu zafafan kalaman soyayya,da alama sun jima suna dakon soyayyar junansu,sai ranar jarumin ciki yake bayyanawa jarumar soyayar da yake mata.
Alamarta ya maida mata,ya rufe littafin ya dora mata a gefanta,sannan ya bude freezer din ya dauko fresh milk da basuyi sanyi sosai ba,yana da buqatar daukan cups,saidai kuma tana tsaye a wajen,hakan ya sakashi takawa,ya sake tsaiwa dab da bayanta,dyk da kusancun baikai na daxun ba amma saida numfashinta ya dauke na wucin gadi.
Dai dai sanda ya miqa hannu ta gefan wuyanta zai dauka cup din ya jefa mata tambayar data sanyata diriricewa
"Waya koya miki karanta litattafan soyayya?,bakisan koya maka soyayya suke ba?,ko kin shirya yinta a yanzun?" Kalmomin daya gaya mata kenan da suka shige deep inside her da wani irin sound me nauyin amo.
Tambayar tayi mata tsauri da yawa,hakanan batasan kalar amsar da zata bashi ba,saita zabi yin shuru
"Yaka dade ne,am starving fa,fuska kawai nayi" suka tsinci murya amiru tsakiyar kitchen din,abinda yasa samir ya janye baya a hankali hannayensa dauke da kofunan,ya dubi amiru wanda idanunsa suka hango masa kaltum dake tsaye bakin tukunya,taqi kuma juyowa
"Gasunan acici,ka fado waje babu sallama"
"Don zan shigo kitchen sai nayi sallama?,wanne sabon salo ne kuma hakan?" Ya amsa masa tana matsawa gaba tare da gocewa gefen saraki daya tsaya a gabansa ya kare masa abinda yakeson ganin
"Ashe mana,dole mu zauna da yunwa ashe jawahir ke girki" ya fada da salon tsokana irin wadda sukewa juna lokaci zuwa lokaci shi da jawahir din.
Dole ta juyo saboda batason yacu gaba da dauka jawahir din ce
"Ina yini" ta fada tana sake takurewa waje daya,tare da Allah wadan rashin fitowa da mayafinta da batayi ba
"Oh, sorry.......ashe ba ita bace,kamar kaltum ko?" Ya fada yana nunata da yatsa,saita daga kanta kawai
"Ma sha Allah,lafiya lau" ya amsa yana juyawa,saiya hangi samir tuni yayi gaba yama kusa ficewa daga kitchen din,don haka ya juya yabi bayansa,bakinsa fal da maganganu.
Tunda ya fito samir din ya karanci maganganu ne fal bakin amirun,don haka yaqi bashi damar cewa komai ma,ya maida hankalinsa ga hajiya qarama dake masa bayanin tanason suje azare qarshen watan nan,fada take musu sosai shi da amiru
"Dukkanku zuba muku idanu ai nayi,naji wanda zai fara maganar zuwa a cikinku amma ba'a samu ba,wasa wasa so kuke gaba daya a watsar da zuwa azare,bayan kunfi kowa sannin ammi tana da rai,kai koda bata da rai hakan bame yuwuwa bane,to ku shiga taitayinku da kyau na gaya muku,tunda shi yayan yana kallonku ya qyaleku,saboda haka ku shirya.....bikin salis za'ayi da farida,kuma dukkaninsu 'yan uwanku ne auren zumunci ne,saboda haka zuwa ya kamaku,kowanne ya kammala uzurinsa kafin sannan,ashirin da biyar ga wata nakeso mu wuce dukka harda su jawahir da najwa,uwarsu kuma idan taga zataje taje,wannan ba matsalata bace" can qasan rashi samir ke sakin murmushi yana kurbar fresh milk dinsa,har kwanan gobe dai hajiya qarama ba zata sauya ba,bai taba ganin wani abu data riqa ta kuma qi jininsa irin mummy jidda ba,taqi gaya masa dalili,kuma shima ya kasa ganowa,abu daya ya fahimta,tanayin komai ne akansa da mahaifiyarsa,mahaifiyar data gudu ta barshi,ta zabi ta shiga duniya ta barshi.
Jin zuciyarsa ta fara quntata da wannan tunanin yasa ya janyowa hajiyan wata hirar,tunani ne dake sanyashi yanzu yanzu ya burkice,shi yasa ba kasafai yake barin kansa yinsa ba.
Babu jimawa kaltum ta fito ya shirya komai,saidai wannan karon gaba daya jikinta lullube yake da wani cotton mayafi mai kyau baqi,ta gama shirya komai ta matso wajen hajiya qarama tana rusunawa
"Hajiya an gama" addu'a tayi mata sosai cikin kulawa da yabawa,har zuwa sanda kaltum din ta wuce daki bakin hajiya qarama baiyi shuru ba yaba mata take,mutum ce ita da bata raina ko manta alkhairi komai qanqantarsa
"Saraki.....wannan yarinyar....wankan engine akayi mata ne?,kasan rabona da ganinta kwana uku bayan zuwanta garin nan?"
"Wa ya sani ne?" Ya bashi amsa yana miqewa zuwa dining inda hajiya qarama ke kiran suzo ga abincin suci
"Anya kuwa kana kallonta da kyau samir?,kaga yadda ta canza? black skin din nan ta koma wani beautiful chocolate color?,ba sirantaka,komai nata moderate,baka gani ba wai?"
"Ban sani ba!,ba aikina bane wannan observation din, shut up your mouth kaci abinci malam" ya fada masa yana tsareshi da ido
Kai ya dauke ya fara zuba abincin,saidai bai iya yin shurun ba
"Saifa na fada malam,anya ba akwai abinda ka gano ba a sannan kayimin wuff ka amsha aurenta ba?" Haushi ya cika samir,ya rasa me zaiwa amiru ya huce,dama tun asali ya sanshi,mutum ne da yasa ainihin diri da halittar mace,aka haka yake da zabe zabe da ruwan idanu,a nan halinsu ya saba,kuma akan wannan suke fada,saiya dauka wani qaton saving spoon ya jefi amirun dashi,Allah yasa ua goce,don ba shakka daya sameshi saiyaji babu dadi
Kallonsu hajiya qarama data qaraso wajen kawai tayi ta tabe baki
"Har yau ku bakusan kun girma ba kenan" zuwanta ya yanke maganar,saidai duk sanda suka hada idanu da amiru saiya karanci maganar bata isheshi ba kenan.
Har suka gama cin abincin suka gama hirarsu bata sake fitowa ba,daga qarshe dai yadda amiru yaso kwana gidan bai yiwu ba,saboda daddy daya kira yanason ganinsu,dole tare suka tafi.
48
D/Z
Kwanakin da suka biyo baya ta maida hankalinta ne sosai ga jarrabawar da take gabanta,cikin ikon Allah kuma sai ta dinga zuwa mata da sauqi sosai kamar yadda jawahir ta gaya mata,sai abun yayi mata dadi qwarai a ranta.
Tafiya azare ta kama,kuma dukka kowa yayi amannar zuwa,har mummy da hajiya qarama bata damu da taje ko kar taje ba,sai gashi kamar ma tafi kowa damuwa da tafiyar,tun kafin ta isa garin kuma ta aika da tata gudummawar mai tsokar gaske ga bangaren gidansu amarya data ango,kamar dai yadda ta saba hidima kan jiki kan qarfi duk sanda wani sha'ani ya tashi daga dangin professor.
A satin da za'a tafi a zaren professor ya tako gidan da kansa wajen hajiya qarama,da alama kuma zuwan yana da alaqa da maganar auren samir da kuma bikin azaren.
Kaltum kusan itake kula da duk wani baqo da hajiya qaraman zatayi,tunda taji tace yaya rashid zaizo kaltum tayi abinci da abun sha na musamman saboda professor din,hatta hajiya qaraman bata sani ba,sai da yazo sannan taga kaltum din nata shirya masa kalolin abinci
"Kina wajen hajiya kenan?" Professor ya fada bayan ya gama amsa kasuwar kaltum dake duqe,hajiya ce ta karbi xancan ma tun kafin kaltum din tace komai
"Wallahi yaya,nace ina kuka samo haziqar yarinya haka,bason jiki ba ganda babu qyuya,na dade banji mutumin da naji dadin xama dashi ba kamar yarinyar nan" kada kai professor yayi,shi kansa yana yaba yadda yarinyar ke hidima da kowa cikin,duk da ba zama yake sosai ba amma yana lura da hakan,karon farko da zuciyarsa tayi sanyi da wuri kan wani abu da samir yayi gaban kansa ya aiwatar dashi ba tare da yarjewarsa ba
"Ki koma daki ki huta hakanan kinji,kya samu damar duba karatunki,zasu qarasa aikin"cewar hajiya qarama,tunda daya daga cikin masu aikinta ta dawo,dayar kuma ta kawo wadda zata riqe mata aikin kafin ta dawo. Kai ta gyada tana shigewa ciki.
Hira sukayi sosa irin ta zumunci ita da dan uwan nata,wanda dama duk sanda irin hakan ta faru yakan jima a gidanta,akwai shaquwa da qauna sosai tsakaninsa da hajiya qamar,daga qarshe ta fadi abinda take ganin ya kamata ya bayar kan hidimar bikin,ta kuma shaida masa ranar da ita zata tafi
"Ke kuma sai yaushe zaki tura taki gudunmawar hajjaju,naga jidda wannan karon ta rigaki bayarwa" ya fada yana saka hannunsa a aljihun babbar rigarsa yana ciro kudi.
Baki ta tabe tana duban wani barin
"Dama haka takeso ace,tayi qoqari,amma ni bana abu don a fada ko kuma saboda gasa,Allah sarki raihana.......har batason ace tayi wani aikin alkhairi,takan ce tayine saboda Allah,kuma shi take bida ya mata sakayya"
Wani kallo ya yiwa hajiya qaraman,tayi zaton abunda ya saba shi zaiyi a yanzun ma,saidai ga sabanin tunaninta sai taga ya dauke kai ba tare da yace komai ba,yaci gaba da irga kudaden daya debo din.
Miqewa yayi yana ajjiye mata kudin
Rubutune a dutsen tsakiya daya kaso hangowa,ya zuba idanu sosai amma bai gane me aka rubuta ba,har zuwa sanda tace
"Na gama" da siririyar muryarta,ya qarasa a hankali,saiya kama tsintsiyar hannunta,wanda hakan ya sanyata daga idanu ta dubeshi da sauri,sai taga dutsen yake kallo wanda aka rubuta i'm in love da qananun baqaqen rubutu.
Dazu dazu ta siya abun hannun a makaranta,an jima ana saidashi,duk da yadda kuma 'yan ajinsu keta siya bata taba marmarin siya ba,saboda akwai mai sunan samari a jiki da yawa,kowa yana siyan me sunan saurayinsa ne,sai dazu da aka kawo wadan nam design din sukayi mata saita dauka.
Yana gama karantawa ya dago suka hada idanu,tayi saurin dauke idonta tana jin bugun zuciyarta na sake ninkuwa fiye da da,wani irin maganadisu idanunsa ke dashi,ta dade da ganin haka,tun ranar daya tsaidata zai shigar da haladu wajenta,abinda ya janyo a sannan ta kasa maida masa maganganun da tayi niyya kenan.
Ya lura wanu nauyinsa da kuma kawaici take masa,sai yaqi sakin hannun nata,yaci gaba da kallon abun hannun,a hankali ya sakar mata hannun sannan ya fara diban containers din yana maidawa,hakan ya bata damar yin gaba da sauri ta jiqa kanwar,ta matsa gaban tukunyar ta bude ta zuba,ta juya miyar ta tattabatar komai yayi,saita kasa juyowa sanoda tana da tabbacin yana cikin kitchen din,baisan shi mugun nauyinsa takeji bane?,tanason ta qarasa aikinta ne tabar kitchen din,amma wanzuwarsa a nan ya hanata ci gaba da yin komai.
Littafinta na saman freezer din da zai dauki abu,bai kula ba ya bude sai littafin ya fado qasa,ya sunkuya a hankali ya dagashi,zai gyara mata alamar data saka na shaidar inda ta tsaya,saiya buda shafin,idanunsa ya sauka a inda ta saka alamar.
Layi hudu ne,amma suna dauke da wasu zafafan kalaman soyayya,da alama sun jima suna dakon soyayyar junansu,sai ranar jarumin ciki yake bayyanawa jarumar soyayar da yake mata.
Alamarta ya maida mata,ya rufe littafin ya dora mata a gefanta,sannan ya bude freezer din ya dauko fresh milk da basuyi sanyi sosai ba,yana da buqatar daukan cups,saidai kuma tana tsaye a wajen,hakan ya sakashi takawa,ya sake tsaiwa dab da bayanta,dyk da kusancun baikai na daxun ba amma saida numfashinta ya dauke na wucin gadi.
Dai dai sanda ya miqa hannu ta gefan wuyanta zai dauka cup din ya jefa mata tambayar data sanyata diriricewa
"Waya koya miki karanta litattafan soyayya?,bakisan koya maka soyayya suke ba?,ko kin shirya yinta a yanzun?" Kalmomin daya gaya mata kenan da suka shige deep inside her da wani irin sound me nauyin amo.
Tambayar tayi mata tsauri da yawa,hakanan batasan kalar amsar da zata bashi ba,saita zabi yin shuru
"Yaka dade ne,am starving fa,fuska kawai nayi" suka tsinci murya amiru tsakiyar kitchen din,abinda yasa samir ya janye baya a hankali hannayensa dauke da kofunan,ya dubi amiru wanda idanunsa suka hango masa kaltum dake tsaye bakin tukunya,taqi kuma juyowa
"Gasunan acici,ka fado waje babu sallama"
"Don zan shigo kitchen sai nayi sallama?,wanne sabon salo ne kuma hakan?" Ya amsa masa tana matsawa gaba tare da gocewa gefen saraki daya tsaya a gabansa ya kare masa abinda yakeson ganin
"Ashe mana,dole mu zauna da yunwa ashe jawahir ke girki" ya fada da salon tsokana irin wadda sukewa juna lokaci zuwa lokaci shi da jawahir din.
Dole ta juyo saboda batason yacu gaba da dauka jawahir din ce
"Ina yini" ta fada tana sake takurewa waje daya,tare da Allah wadan rashin fitowa da mayafinta da batayi ba
"Oh, sorry.......ashe ba ita bace,kamar kaltum ko?" Ya fada yana nunata da yatsa,saita daga kanta kawai
"Ma sha Allah,lafiya lau" ya amsa yana juyawa,saiya hangi samir tuni yayi gaba yama kusa ficewa daga kitchen din,don haka ya juya yabi bayansa,bakinsa fal da maganganu.
Tunda ya fito samir din ya karanci maganganu ne fal bakin amirun,don haka yaqi bashi damar cewa komai ma,ya maida hankalinsa ga hajiya qarama dake masa bayanin tanason suje azare qarshen watan nan,fada take musu sosai shi da amiru
"Dukkanku zuba muku idanu ai nayi,naji wanda zai fara maganar zuwa a cikinku amma ba'a samu ba,wasa wasa so kuke gaba daya a watsar da zuwa azare,bayan kunfi kowa sannin ammi tana da rai,kai koda bata da rai hakan bame yuwuwa bane,to ku shiga taitayinku da kyau na gaya muku,tunda shi yayan yana kallonku ya qyaleku,saboda haka ku shirya.....bikin salis za'ayi da farida,kuma dukkaninsu 'yan uwanku ne auren zumunci ne,saboda haka zuwa ya kamaku,kowanne ya kammala uzurinsa kafin sannan,ashirin da biyar ga wata nakeso mu wuce dukka harda su jawahir da najwa,uwarsu kuma idan taga zataje taje,wannan ba matsalata bace" can qasan rashi samir ke sakin murmushi yana kurbar fresh milk dinsa,har kwanan gobe dai hajiya qarama ba zata sauya ba,bai taba ganin wani abu data riqa ta kuma qi jininsa irin mummy jidda ba,taqi gaya masa dalili,kuma shima ya kasa ganowa,abu daya ya fahimta,tanayin komai ne akansa da mahaifiyarsa,mahaifiyar data gudu ta barshi,ta zabi ta shiga duniya ta barshi.
Jin zuciyarsa ta fara quntata da wannan tunanin yasa ya janyowa hajiyan wata hirar,tunani ne dake sanyashi yanzu yanzu ya burkice,shi yasa ba kasafai yake barin kansa yinsa ba.
Babu jimawa kaltum ta fito ya shirya komai,saidai wannan karon gaba daya jikinta lullube yake da wani cotton mayafi mai kyau baqi,ta gama shirya komai ta matso wajen hajiya qarama tana rusunawa
"Hajiya an gama" addu'a tayi mata sosai cikin kulawa da yabawa,har zuwa sanda kaltum din ta wuce daki bakin hajiya qarama baiyi shuru ba yaba mata take,mutum ce ita da bata raina ko manta alkhairi komai qanqantarsa
"Saraki.....wannan yarinyar....wankan engine akayi mata ne?,kasan rabona da ganinta kwana uku bayan zuwanta garin nan?"
"Wa ya sani ne?" Ya bashi amsa yana miqewa zuwa dining inda hajiya qarama ke kiran suzo ga abincin suci
"Anya kuwa kana kallonta da kyau samir?,kaga yadda ta canza? black skin din nan ta koma wani beautiful chocolate color?,ba sirantaka,komai nata moderate,baka gani ba wai?"
"Ban sani ba!,ba aikina bane wannan observation din, shut up your mouth kaci abinci malam" ya fada masa yana tsareshi da ido
Kai ya dauke ya fara zuba abincin,saidai bai iya yin shurun ba
"Saifa na fada malam,anya ba akwai abinda ka gano ba a sannan kayimin wuff ka amsha aurenta ba?" Haushi ya cika samir,ya rasa me zaiwa amiru ya huce,dama tun asali ya sanshi,mutum ne da yasa ainihin diri da halittar mace,aka haka yake da zabe zabe da ruwan idanu,a nan halinsu ya saba,kuma akan wannan suke fada,saiya dauka wani qaton saving spoon ya jefi amirun dashi,Allah yasa ua goce,don ba shakka daya sameshi saiyaji babu dadi
Kallonsu hajiya qarama data qaraso wajen kawai tayi ta tabe baki
"Har yau ku bakusan kun girma ba kenan" zuwanta ya yanke maganar,saidai duk sanda suka hada idanu da amiru saiya karanci maganar bata isheshi ba kenan.
Har suka gama cin abincin suka gama hirarsu bata sake fitowa ba,daga qarshe dai yadda amiru yaso kwana gidan bai yiwu ba,saboda daddy daya kira yanason ganinsu,dole tare suka tafi.
48
D/Z
Kwanakin da suka biyo baya ta maida hankalinta ne sosai ga jarrabawar da take gabanta,cikin ikon Allah kuma sai ta dinga zuwa mata da sauqi sosai kamar yadda jawahir ta gaya mata,sai abun yayi mata dadi qwarai a ranta.
Tafiya azare ta kama,kuma dukka kowa yayi amannar zuwa,har mummy da hajiya qarama bata damu da taje ko kar taje ba,sai gashi kamar ma tafi kowa damuwa da tafiyar,tun kafin ta isa garin kuma ta aika da tata gudummawar mai tsokar gaske ga bangaren gidansu amarya data ango,kamar dai yadda ta saba hidima kan jiki kan qarfi duk sanda wani sha'ani ya tashi daga dangin professor.
A satin da za'a tafi a zaren professor ya tako gidan da kansa wajen hajiya qarama,da alama kuma zuwan yana da alaqa da maganar auren samir da kuma bikin azaren.
Kaltum kusan itake kula da duk wani baqo da hajiya qaraman zatayi,tunda taji tace yaya rashid zaizo kaltum tayi abinci da abun sha na musamman saboda professor din,hatta hajiya qaraman bata sani ba,sai da yazo sannan taga kaltum din nata shirya masa kalolin abinci
"Kina wajen hajiya kenan?" Professor ya fada bayan ya gama amsa kasuwar kaltum dake duqe,hajiya ce ta karbi xancan ma tun kafin kaltum din tace komai
"Wallahi yaya,nace ina kuka samo haziqar yarinya haka,bason jiki ba ganda babu qyuya,na dade banji mutumin da naji dadin xama dashi ba kamar yarinyar nan" kada kai professor yayi,shi kansa yana yaba yadda yarinyar ke hidima da kowa cikin,duk da ba zama yake sosai ba amma yana lura da hakan,karon farko da zuciyarsa tayi sanyi da wuri kan wani abu da samir yayi gaban kansa ya aiwatar dashi ba tare da yarjewarsa ba
"Ki koma daki ki huta hakanan kinji,kya samu damar duba karatunki,zasu qarasa aikin"cewar hajiya qarama,tunda daya daga cikin masu aikinta ta dawo,dayar kuma ta kawo wadda zata riqe mata aikin kafin ta dawo. Kai ta gyada tana shigewa ciki.
Hira sukayi sosa irin ta zumunci ita da dan uwan nata,wanda dama duk sanda irin hakan ta faru yakan jima a gidanta,akwai shaquwa da qauna sosai tsakaninsa da hajiya qamar,daga qarshe ta fadi abinda take ganin ya kamata ya bayar kan hidimar bikin,ta kuma shaida masa ranar da ita zata tafi
"Ke kuma sai yaushe zaki tura taki gudunmawar hajjaju,naga jidda wannan karon ta rigaki bayarwa" ya fada yana saka hannunsa a aljihun babbar rigarsa yana ciro kudi.
Baki ta tabe tana duban wani barin
"Dama haka takeso ace,tayi qoqari,amma ni bana abu don a fada ko kuma saboda gasa,Allah sarki raihana.......har batason ace tayi wani aikin alkhairi,takan ce tayine saboda Allah,kuma shi take bida ya mata sakayya"
Wani kallo ya yiwa hajiya qaraman,tayi zaton abunda ya saba shi zaiyi a yanzun ma,saidai ga sabanin tunaninta sai taga ya dauke kai ba tare da yace komai ba,yaci gaba da irga kudaden daya debo din.
Miqewa yayi yana ajjiye mata kudin