Sashe 57
Dabiar Zuciya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Jama'a batun nan ba'an kawoshi don a tattauna ba,duk me buqata,malam amadu na cikin masallacin nan sai ya nemeshi su tattauna,ko ya iskeshi a gidansa,kowa yana iya tafiya"
"Nagodewa Allah da haladu baya nan" sukaji an fada daga bayansu,waiwayawa samir yayi,sai yaga abokin haladu ne,ya tuna abinda ya faru tsakaninsu a dandali,sannu sannu mutane suka fara yoyewa,wasu suka kafa sansani daga waje ana tattauna maganar,wasu na nuna sha'awarsu kan abun,amma sun gaza tunkarar malam amadu,sabida baqin fentin da aka yiwa kaltum din,yayin da wasu sukace zasu tsaya su kuwa suga tunqwal uwar daka.
Dariya amiru yake sosai sanda suke komawa gida akan hanya
"Gaskiya dole kaso zama a qauyen nan,abun dariya har gida,kaga yadda ake bada mace kyauta free babu ko sisin kwabonka?,anya kuwa master bani zan saka kaina ba?kasan Allah abun yayi min,kaga idan nadan more kona watanni ne,saina sallameta da abubuwan arziqi na qara gaba abina" Saraki wanda tunda suka taso baice komai ba ya juya ya dubi amiru,saiya sakar masa harara
"U r very stupid amiru,baka da hankali hala?" Fuskarsa ya gyara sosai gami da muryarsa ya koma serious
"Da gaske nake maka man.....wannan fa wata hanyace mai sauqi,aiba zina bace" qaqqarfan tsaki samir ya saki,sai kuma ya bushe da dariya
"Babu abinda zakayi da wannan yarinyar malam, infact ma babu abinda zaka tsinta a jikinta,bata da komai din da kake kwadayi" dariyar amiru ya tayashi
"Ka santa kenan?" Kafin yakai ga amsa masa saiga malam amadu kamar an jehoshi,cikin hanzari samir yayi gaba yana cewa
"Salamu alaikum" dakatawa yayi ya waiwayo yana duban samir kafin ya amsa masa,samir din ya miqa masa hannu suka gaisa sannan yace
"Sunana muhammadu,daya daga cikin masu ginin makarantar me tafasa"
"Toto...eh...anyi haka"
"Yauwa yaronka daya rasu bilal,akwai kudin sallama na aikinsa a wajenmu da zamu biyashi" wani farinciki ya saukarwa malam amadu,saiya fara matso hawaye
"Allah sarki,Allah sarki bilalu,yaro mai qoqarin neman na kai,ai nayi rashi,nayi rashi ba qarami ba" duk da cewa ba komai samir ya sani ba game da abinda ke wakana,amma a yadda yaga kulawarsa kan rayuwar yaron,a ganinsa wannan kukan baikai ko ina ba,tun daga kaishi asibiti,rasuwarsa da kawoshi da sukayi gida....
Kansa ya gayawa wannan ba huruminsa bane,huruminsa ya sauke nauyin dake kansu,don haka ya share wannan daga ransa,ya irgo kudaden da gumin bilal ha samar dasu ya miqawa malam amadun,yasa hannu ya cafke yana zabga godiya ya wuce suma suka wuce.
Ita kadai tana zaune amma cikin jikinta tana jin akwai abinda zai faru,tanajin tabbas babansu bai haqura ba,tunda ya fada din sai ya aikata,tunda ya quduri aniya sai yayi.
Bata sake samun yaqini ba saida qawayenta,tawaga daga wasila sukazo mata wai da niyyar gaisuwar,abunda ya bata mamaki ya kuma daure mata kai,wasilar dako a hanya bata nuna alamun ta santa bare wani abu ya hadasu?.
Bata nuna musu komai ba,tunda mutum ya nuna don kai yazo,sadai lantana dake tayata zama ko kallo basu isheta ba,har sai daga bisani sanda suka niyyaci tafiya sannan wasilar tace
"Lantana abunma harda 'yar shariya?,saboda zaku zama amaren gobe da asuba?,muna muku murna,shi auren sadaka ai falala gareshi,Allah ya sanya alkhairi yasa a daura a sa'a,idan auwalunne ta kwana gidan sauqi,idan bashi bane kuma sai munxo ganin wanda aka canka".
Idanunta ta daga tabi wasila da kallo,wadda ta kusa barin sassan nasu,wani birkicewa kwanyarta taji tana shirin yi,zancan ya fita kenan?,idan kuwa ya fita ba shakka babansu yakai maganar masallaci,idan taje masallaci da gaske auren zai mata a gobe da asuba?,ranar sadakar ukun dan uwanta?,lallai ummansu batasan da za can ba,saita daga idanu ta azasu akan ummanta.
Tana zaune cikin 'yan uwanta,tanata qoqarin yaqi da damuwoyin dake ranta,indai hakane ya kyautu takai mata wannan zancan ta qara mata damuwa?,baya tasan babu abinda ya isa ya canza qaddararta?,sai kawai ta lumshe idanunta,tana qoqarin ganin ta saisaita tunaninta.
Tabatan da akayi yasa ta bude dukka idanunta,lantana ce,fuskarta da idanunta cike fal da damuwa
"Don Allah kada ki dorawa kanki damuwa saboda zancansu,wani abunma zasu qireshi ne saboda su bata ranki" wani busashen murmushi ta sakarwa lantana,don ta gusar mata da tata damuwar itama
"Ban damu ba lantana,kawai ina tuna bilalu ne"
"In sha Allahu hutu ya samu"
"Muna fata" ta amsa mata,wani girma da qimar lantana take gani,ko meye zai faru da ita tana tsaiwa a gefanta,bata taba lissafa lantana cikin masoyanta ba saida wadan nan abubuwan suka faru,dama baka sanin masoyinka ko maqiyinka sai abu mara dadi ko mai dadi ya sameka,Allah kaci gaba da hadamu da masoyanmu na gaskiya,masu sonmu bilhaqqi amin.
*********Ƙarfe biyar saura na asubahi,amiru na daga tsaye yana dora lallausar sweeter dinsa saman jallabiyar jikinsa bayan ya gama alwala,ya dubi samir dake zaune saman abun salla bayan ya idar da raka'atanil fajr yana qarasa tasbihinsa da yatsun hannunsa
"Don Allah ka tashi haka mu tafi,kada mu rasa sahun gaba fa" sai da yakai sannan ya daga kai ya harareshi
"Wai yaushe ka zama magulmaci ne?,koda kaje da wuri fa baka da ladan zuwa da wurin,don ba manufarka kenan ba" dariya ya saki yana dora hular tashi ka fiya naci saman kansa da yake aje suma
"Allah so nake naga wannan dramer din ya zata kaya,sabon salon aurar da 'ya'ya mata,sai kace game?"
Tsaki samir ya saki,ya dauko salati adadin yadda zaiyi ya qarasa sannan ya miqe yana nade dardumar da yayi sallah akai,zuwa sannan har amiru yayi waje,ya zura slippers yabi bayan amirun wanda yaketa faman kiran ya fito su wuce don Allah.
*Duniya a yanzu ta cika da abubuwan da kake tunanin babu su,amma har wadanda baka taba kawowa akwai ba akwaisu*
Labarin rayuwar da umma ke ciki gaskiya ne,ya faru,ni ganauce ba jiyau ba,ranar da yarinyar ke bani labarin rayuwar da suke ciki na gaya mata cewa
"Banda ke da kanki kika gayamin zan qaryata ne!"
Ranar da naji labarin rayuwar auren wata mata cewa nayi
"Inda a novel ne cewa za'ayi DAMA AI SAIDAI A NOVEL DIN" saboda bamu rubuta koda kwatar rintsi tsanani da tashin hankalin data fuskanta ba
Yaron dana sauya sunanshi da bilal yayi mutuwa sak irin ta bilal
Na tsaya gaban gawarshi nayi kuka da idona
Tana zaune a gidan sabida bata da wani gata ko kuma tsayayye da zai tsaya mata
Idan tace zata koma gidansu gaban mahaifiyarta bata da wannan gurbin
Yaranta duka mata ne
Duka basuyi aure ba
Gwara umma anan ta aurar da habiba
Me yasa ko yaushe mukafi karkata ga zaqin labari
Soyayya
Dukiya
Kyau
Da jin dadi?
Me yasa bamason mutuwa ko jarrabawa cikin labaranmu?
Me yasa muke gudunsu bayan rayuwarmu a daure take da qalubalensu?
Irin wannan ke canza tunanin marubuta masuyin labarin da zai zama ilimi da izina zuwa rubuta baragada saboda faranta ran masu karatu!
Allah madaukakin sarki yana cewa
"Shin mutane suna tsammanin za'a barsu saboda sunce sunyi imani ba zamu jarabcesu?,haqiqa mun jarrabi wadanda suka gabacesu........"
33
D/Z
_ki tuntubi wadan nan numbers din don biyan naki ki karanta cikin aminci_
08184017082
Ko kuma
09134848107
Suna shiga masallacin ana shirin tada sallar,yau masallacin a cike yake saboda addu'ar ukun bilal,don haka basu samu sahun gaba ba,sai a can baya suka zauna.
Kamar ko yaushe aka idar da sallah,saidai yau mafi yawan mutane basu motsa ba aka fara gabatar da addu'o'i wa bilal,wanda aka dauki kusan minti talatin anayi kafin a kammala.
Niyyar tashi samir yayi,sai amiru ya danneshi,dubansa samir yayi
"Ka zauna malam,ai ba'a gama ba" kamar zaiyi magana saiya fasa,ya koma ya zauna,dai dai sanda malam amadu ya miqe
"Jama'a akwai wanda keda sha'awar auren diyata kaltume?,idan har babu zan bada ita yanzu ga dan uwanta auwalu" maganganu ne qasa qasa suka fara tashi,tsahon wani lokaci shuru sai qananun maganganu
"Akwai wanda ya shirya?" Malam amadu ya sake jefa tambayar ga mutane
"Akwai" babu zato bare tsammani muryar amiru ta sauka kunnen samir,da sauri ya waiwaya ya dubi amirun,suka hada ido,sai ya fuske masa,tsoron halin amiru daya sanshi dashi ya darsu a ransa,yasanshi sarai,komai yana daukarsa wasa ne koda gaske ne,hakanan yana iya fadar magana a cikin wasa ka ganta a zahiri a aikace
"To alhmdlh,yaro kaine zaka karba ko?" Malam amadu ya fada yana murmushin samun wanda zai baiwa kaltume din,kai amiru ya gyada
"Ni zan karba,nawa sadakin?"
"Aiko nawa kake dashi yaro ka bayar" mai gari ya amsa wannan karon.
Tun samir yana ganin abun a wasa,sai gashi ya tasamma zama gaske,mutane sun fara matsowa ana dai daita magana,har takai ana buqatar amiru ya miqo sadaki.
Aljihunsa ya shafa,bai fito da komai ba,amma kamar yaga samir yana zuba kudi a aljihunsa,wanda yace zai qarasa biyan ma'aikatan kudin gininsu,saboda a gobe yake son a bude makarantar
"Aramin dubu talatin mana"
"Baka da hankali amiru?" Ya tambayeshi qasa qasa yana zuba masa idanu a rikice
"Yaro miqo mana,ko ila ajalin za'ayi?" Mai gari ya tambaya amiru,bayan sun gama magana qasa qasa da malam amadu kan baqin fuska ne,shin ya aminta a daura auren diyarsu dasu yace ba komai,zai bincikesu daga baya.
"Gashi....shi ya karba min ne,za'a daura auren da sunan muhammad samir,shine waliyyi na" samier ya fada yana miqa kudin daya irgo.
Baki da hanci amiru ya sake,ya jima da sanin cewa samir ya fishi sanin takan tsiya,idan ya debo rigimarsa dama shi kadai ke iya solbata,wannan abun da samir yayi masa yasan da manufa a ciki,bai sake tabbatar da haka ba sai da suka hada idanu ya banka masa harara.
Cikin lokaci qanqani aka daura auren muhammad samir da ummu_kulsum kaltume,wanda ana gamawa mutane suka fara watsewa kowa ya tafi da lamarin a bakinsa,ta yaya malam amadu zai dauki diyarsa ya baiw baqo?,duk da an dan sanshi sakamakon aikin makarantar da sukeyi?.
Raguwar da jama'a sukayi ya basu damar ganawa da me gari,shi ya damu yadan yiwa su samir wasu tambayoyi,da suka shafi cikakken sunansa da kuma garinsu da sunan mahaifinsa,dukka ya gaya musu,saidai ta sigar da bazasu gane waye ba,me garin yadan masa nasiha kan ya riqe amana,shi kuma ya shaida masa an bashi umarnin gobe a bude aikin makarantar da aka gina daga mai gidansa,murnar wannan ya sanya zancan auren yadan lafa,har gari yayi haske suna tare da me gari,tuni samir yaji ya gaji,sai yace zashi gida akwai saqon da za'a kawo,a sannan ne malam amadu da shima ke shirin tafiya gida don ya shaida musu daurin auren kaltumen yace
"Nagodewa Allah da haladu baya nan" sukaji an fada daga bayansu,waiwayawa samir yayi,sai yaga abokin haladu ne,ya tuna abinda ya faru tsakaninsu a dandali,sannu sannu mutane suka fara yoyewa,wasu suka kafa sansani daga waje ana tattauna maganar,wasu na nuna sha'awarsu kan abun,amma sun gaza tunkarar malam amadu,sabida baqin fentin da aka yiwa kaltum din,yayin da wasu sukace zasu tsaya su kuwa suga tunqwal uwar daka.
Dariya amiru yake sosai sanda suke komawa gida akan hanya
"Gaskiya dole kaso zama a qauyen nan,abun dariya har gida,kaga yadda ake bada mace kyauta free babu ko sisin kwabonka?,anya kuwa master bani zan saka kaina ba?kasan Allah abun yayi min,kaga idan nadan more kona watanni ne,saina sallameta da abubuwan arziqi na qara gaba abina" Saraki wanda tunda suka taso baice komai ba ya juya ya dubi amiru,saiya sakar masa harara
"U r very stupid amiru,baka da hankali hala?" Fuskarsa ya gyara sosai gami da muryarsa ya koma serious
"Da gaske nake maka man.....wannan fa wata hanyace mai sauqi,aiba zina bace" qaqqarfan tsaki samir ya saki,sai kuma ya bushe da dariya
"Babu abinda zakayi da wannan yarinyar malam, infact ma babu abinda zaka tsinta a jikinta,bata da komai din da kake kwadayi" dariyar amiru ya tayashi
"Ka santa kenan?" Kafin yakai ga amsa masa saiga malam amadu kamar an jehoshi,cikin hanzari samir yayi gaba yana cewa
"Salamu alaikum" dakatawa yayi ya waiwayo yana duban samir kafin ya amsa masa,samir din ya miqa masa hannu suka gaisa sannan yace
"Sunana muhammadu,daya daga cikin masu ginin makarantar me tafasa"
"Toto...eh...anyi haka"
"Yauwa yaronka daya rasu bilal,akwai kudin sallama na aikinsa a wajenmu da zamu biyashi" wani farinciki ya saukarwa malam amadu,saiya fara matso hawaye
"Allah sarki,Allah sarki bilalu,yaro mai qoqarin neman na kai,ai nayi rashi,nayi rashi ba qarami ba" duk da cewa ba komai samir ya sani ba game da abinda ke wakana,amma a yadda yaga kulawarsa kan rayuwar yaron,a ganinsa wannan kukan baikai ko ina ba,tun daga kaishi asibiti,rasuwarsa da kawoshi da sukayi gida....
Kansa ya gayawa wannan ba huruminsa bane,huruminsa ya sauke nauyin dake kansu,don haka ya share wannan daga ransa,ya irgo kudaden da gumin bilal ha samar dasu ya miqawa malam amadun,yasa hannu ya cafke yana zabga godiya ya wuce suma suka wuce.
Ita kadai tana zaune amma cikin jikinta tana jin akwai abinda zai faru,tanajin tabbas babansu bai haqura ba,tunda ya fada din sai ya aikata,tunda ya quduri aniya sai yayi.
Bata sake samun yaqini ba saida qawayenta,tawaga daga wasila sukazo mata wai da niyyar gaisuwar,abunda ya bata mamaki ya kuma daure mata kai,wasilar dako a hanya bata nuna alamun ta santa bare wani abu ya hadasu?.
Bata nuna musu komai ba,tunda mutum ya nuna don kai yazo,sadai lantana dake tayata zama ko kallo basu isheta ba,har sai daga bisani sanda suka niyyaci tafiya sannan wasilar tace
"Lantana abunma harda 'yar shariya?,saboda zaku zama amaren gobe da asuba?,muna muku murna,shi auren sadaka ai falala gareshi,Allah ya sanya alkhairi yasa a daura a sa'a,idan auwalunne ta kwana gidan sauqi,idan bashi bane kuma sai munxo ganin wanda aka canka".
Idanunta ta daga tabi wasila da kallo,wadda ta kusa barin sassan nasu,wani birkicewa kwanyarta taji tana shirin yi,zancan ya fita kenan?,idan kuwa ya fita ba shakka babansu yakai maganar masallaci,idan taje masallaci da gaske auren zai mata a gobe da asuba?,ranar sadakar ukun dan uwanta?,lallai ummansu batasan da za can ba,saita daga idanu ta azasu akan ummanta.
Tana zaune cikin 'yan uwanta,tanata qoqarin yaqi da damuwoyin dake ranta,indai hakane ya kyautu takai mata wannan zancan ta qara mata damuwa?,baya tasan babu abinda ya isa ya canza qaddararta?,sai kawai ta lumshe idanunta,tana qoqarin ganin ta saisaita tunaninta.
Tabatan da akayi yasa ta bude dukka idanunta,lantana ce,fuskarta da idanunta cike fal da damuwa
"Don Allah kada ki dorawa kanki damuwa saboda zancansu,wani abunma zasu qireshi ne saboda su bata ranki" wani busashen murmushi ta sakarwa lantana,don ta gusar mata da tata damuwar itama
"Ban damu ba lantana,kawai ina tuna bilalu ne"
"In sha Allahu hutu ya samu"
"Muna fata" ta amsa mata,wani girma da qimar lantana take gani,ko meye zai faru da ita tana tsaiwa a gefanta,bata taba lissafa lantana cikin masoyanta ba saida wadan nan abubuwan suka faru,dama baka sanin masoyinka ko maqiyinka sai abu mara dadi ko mai dadi ya sameka,Allah kaci gaba da hadamu da masoyanmu na gaskiya,masu sonmu bilhaqqi amin.
*********Ƙarfe biyar saura na asubahi,amiru na daga tsaye yana dora lallausar sweeter dinsa saman jallabiyar jikinsa bayan ya gama alwala,ya dubi samir dake zaune saman abun salla bayan ya idar da raka'atanil fajr yana qarasa tasbihinsa da yatsun hannunsa
"Don Allah ka tashi haka mu tafi,kada mu rasa sahun gaba fa" sai da yakai sannan ya daga kai ya harareshi
"Wai yaushe ka zama magulmaci ne?,koda kaje da wuri fa baka da ladan zuwa da wurin,don ba manufarka kenan ba" dariya ya saki yana dora hular tashi ka fiya naci saman kansa da yake aje suma
"Allah so nake naga wannan dramer din ya zata kaya,sabon salon aurar da 'ya'ya mata,sai kace game?"
Tsaki samir ya saki,ya dauko salati adadin yadda zaiyi ya qarasa sannan ya miqe yana nade dardumar da yayi sallah akai,zuwa sannan har amiru yayi waje,ya zura slippers yabi bayan amirun wanda yaketa faman kiran ya fito su wuce don Allah.
*Duniya a yanzu ta cika da abubuwan da kake tunanin babu su,amma har wadanda baka taba kawowa akwai ba akwaisu*
Labarin rayuwar da umma ke ciki gaskiya ne,ya faru,ni ganauce ba jiyau ba,ranar da yarinyar ke bani labarin rayuwar da suke ciki na gaya mata cewa
"Banda ke da kanki kika gayamin zan qaryata ne!"
Ranar da naji labarin rayuwar auren wata mata cewa nayi
"Inda a novel ne cewa za'ayi DAMA AI SAIDAI A NOVEL DIN" saboda bamu rubuta koda kwatar rintsi tsanani da tashin hankalin data fuskanta ba
Yaron dana sauya sunanshi da bilal yayi mutuwa sak irin ta bilal
Na tsaya gaban gawarshi nayi kuka da idona
Tana zaune a gidan sabida bata da wani gata ko kuma tsayayye da zai tsaya mata
Idan tace zata koma gidansu gaban mahaifiyarta bata da wannan gurbin
Yaranta duka mata ne
Duka basuyi aure ba
Gwara umma anan ta aurar da habiba
Me yasa ko yaushe mukafi karkata ga zaqin labari
Soyayya
Dukiya
Kyau
Da jin dadi?
Me yasa bamason mutuwa ko jarrabawa cikin labaranmu?
Me yasa muke gudunsu bayan rayuwarmu a daure take da qalubalensu?
Irin wannan ke canza tunanin marubuta masuyin labarin da zai zama ilimi da izina zuwa rubuta baragada saboda faranta ran masu karatu!
Allah madaukakin sarki yana cewa
"Shin mutane suna tsammanin za'a barsu saboda sunce sunyi imani ba zamu jarabcesu?,haqiqa mun jarrabi wadanda suka gabacesu........"
33
D/Z
_ki tuntubi wadan nan numbers din don biyan naki ki karanta cikin aminci_
08184017082
Ko kuma
09134848107
Suna shiga masallacin ana shirin tada sallar,yau masallacin a cike yake saboda addu'ar ukun bilal,don haka basu samu sahun gaba ba,sai a can baya suka zauna.
Kamar ko yaushe aka idar da sallah,saidai yau mafi yawan mutane basu motsa ba aka fara gabatar da addu'o'i wa bilal,wanda aka dauki kusan minti talatin anayi kafin a kammala.
Niyyar tashi samir yayi,sai amiru ya danneshi,dubansa samir yayi
"Ka zauna malam,ai ba'a gama ba" kamar zaiyi magana saiya fasa,ya koma ya zauna,dai dai sanda malam amadu ya miqe
"Jama'a akwai wanda keda sha'awar auren diyata kaltume?,idan har babu zan bada ita yanzu ga dan uwanta auwalu" maganganu ne qasa qasa suka fara tashi,tsahon wani lokaci shuru sai qananun maganganu
"Akwai wanda ya shirya?" Malam amadu ya sake jefa tambayar ga mutane
"Akwai" babu zato bare tsammani muryar amiru ta sauka kunnen samir,da sauri ya waiwaya ya dubi amirun,suka hada ido,sai ya fuske masa,tsoron halin amiru daya sanshi dashi ya darsu a ransa,yasanshi sarai,komai yana daukarsa wasa ne koda gaske ne,hakanan yana iya fadar magana a cikin wasa ka ganta a zahiri a aikace
"To alhmdlh,yaro kaine zaka karba ko?" Malam amadu ya fada yana murmushin samun wanda zai baiwa kaltume din,kai amiru ya gyada
"Ni zan karba,nawa sadakin?"
"Aiko nawa kake dashi yaro ka bayar" mai gari ya amsa wannan karon.
Tun samir yana ganin abun a wasa,sai gashi ya tasamma zama gaske,mutane sun fara matsowa ana dai daita magana,har takai ana buqatar amiru ya miqo sadaki.
Aljihunsa ya shafa,bai fito da komai ba,amma kamar yaga samir yana zuba kudi a aljihunsa,wanda yace zai qarasa biyan ma'aikatan kudin gininsu,saboda a gobe yake son a bude makarantar
"Aramin dubu talatin mana"
"Baka da hankali amiru?" Ya tambayeshi qasa qasa yana zuba masa idanu a rikice
"Yaro miqo mana,ko ila ajalin za'ayi?" Mai gari ya tambaya amiru,bayan sun gama magana qasa qasa da malam amadu kan baqin fuska ne,shin ya aminta a daura auren diyarsu dasu yace ba komai,zai bincikesu daga baya.
"Gashi....shi ya karba min ne,za'a daura auren da sunan muhammad samir,shine waliyyi na" samier ya fada yana miqa kudin daya irgo.
Baki da hanci amiru ya sake,ya jima da sanin cewa samir ya fishi sanin takan tsiya,idan ya debo rigimarsa dama shi kadai ke iya solbata,wannan abun da samir yayi masa yasan da manufa a ciki,bai sake tabbatar da haka ba sai da suka hada idanu ya banka masa harara.
Cikin lokaci qanqani aka daura auren muhammad samir da ummu_kulsum kaltume,wanda ana gamawa mutane suka fara watsewa kowa ya tafi da lamarin a bakinsa,ta yaya malam amadu zai dauki diyarsa ya baiw baqo?,duk da an dan sanshi sakamakon aikin makarantar da sukeyi?.
Raguwar da jama'a sukayi ya basu damar ganawa da me gari,shi ya damu yadan yiwa su samir wasu tambayoyi,da suka shafi cikakken sunansa da kuma garinsu da sunan mahaifinsa,dukka ya gaya musu,saidai ta sigar da bazasu gane waye ba,me garin yadan masa nasiha kan ya riqe amana,shi kuma ya shaida masa an bashi umarnin gobe a bude aikin makarantar da aka gina daga mai gidansa,murnar wannan ya sanya zancan auren yadan lafa,har gari yayi haske suna tare da me gari,tuni samir yaji ya gaji,sai yace zashi gida akwai saqon da za'a kawo,a sannan ne malam amadu da shima ke shirin tafiya gida don ya shaida musu daurin auren kaltumen yace