Sashe 78
Bakar Masarauta Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Lumshe idanuwa Yarima Asad yayi, yana mai jin yadda tsigar jikin sa ke mimmik'ewa, ga kuma yadda yake ganin kyakkyawar fuskar ta a cikin idanuwansa, zai iya cewa tun da yake a rayuwa bai tab'a cin karo da mai kyawun ta ba ko a cikin larabawan da yayi rayuwa da su kuwa.
Lokaci d'aya yaji gaba d'aya komai nasa ya sauya a kanta, kayan da suke sanye a jikin ta da yake musu kallon na mahaukata a lokacin da suka shigo cikin masarautar yaga masu su, yanzu kuma sai yaga sunyi bala'in kyau a jikin ta ita.
Ko da ba a fad'a masa ba yasan ita d'in bagidajiya ce, duba da yadda yaga yanayin mutanen garin nasu suke, ga kuma kalar shigar da ya gani sanye a jikin ta.
To amma mai yasa ta kasa basa hak'uri bayan tasan itace tayi masa laifi.
Ya raya haka a cikin ransa yana mai sake d'aga idanuwansa yabi bayanta da kallo.
Kafin daga bisani kuma ya mik'e tsaye zumbur daga kan shimfid'ar da yake, yana mai shirin bin bayan ta.
Da sauri Al'amin ya mik'a hannun sa yana mai kamo tafin hannun Yarima Asad da shi.
Hakan da Yarima Asad yaji ne ya sanya sa dakatawa, yana mai juyowa ya watsa idanuwan sa akan fuskar Al'amin.
Girgiza masa kai Al'amin yayi yana mai masa alamar da ya dawo ya zauna da idanuwansa.
Yayin da a zuciyar sa kuma mamakin Asad ya gama rufe sa gaba d'aya, domin kuwa k'wayoyin idanuwan sa kawai ya kalla ya fahimci yanayin da yake a ciki.
Lumshe idanuwa Yarima Asad yayi ba tare da ya iya cewa Al'amin komai ba, tukun daga bisani ya dawo jiki a sanyaye yana mai komawa wurin da ya tashi ya zauna.
Kana ya k'ara bin hanyar da Gimbiya Haddiyal tabi da yanzu har an den hangon ta ma da idanuwan sa.
Sosai hoton kyakkyawar fuskar ta ya zauna daram a cikin idanuwan sa, ta yadda har yake jin tamkar har yanzu tana zaune ne a gaban sa.
A hankali ya durk'usar da kansa k'asa yana mai k'ara kallon madarar da take kwance akan sitirar jikinsa, kana ya d'an d'aga lab'b'ansa yana mai fesar da wata zazzafar iska daga cikin bakin sa.
Yayin da shi kansa yake mamakin abun da ya hanasa hukunta wannan bagidajiyar bak'auyiyar yarinyar, akan wannan laifin da tayi masa har ta juya ta ta tafi.
Wai yau shi Asad ne mace tayi masa laifi kuma ya barta ta juya ta tafi ba tare da ta basa ko hak'uri ba, laifi ma babban laifi ba k'arami ba.
Shi da mata suke hauka akan sa, suke kuka tare da kaff-kaffan abun da zai b'ata masa ransa, suke jin dad'i aduk lokacin da ya daga ido ya kalle su.
Mata masu aji masu ilimi, kana wa'yan da sukafi k'arfin kud'i, amma sai gashi yau wata can 'yar k'auye ta b'ata masa jiki ya kasa yin komai akan ta, asalima ko wani haushin ta baiji ba a ransa, sai zallar kyawun hallitar ta da ta tafi ta barsa da ita a cikin idanuwan sa.
Suna a cikin wannan yanayin Habu ya dawo fuskar sa d'auke da murmushi.
Amma sai dai kuma yana zuwa gaban shimfid'ar da suke zaune akai yaja ya tsaya cak, murmushin kan fuskar tasa na gushewa, yayin da idanuwan sa kuma suka kasance k'ur akan k'waryar madarar nan, tare da jikin Yarima Asad da ya gansa a b'ace.
"Shin meye hakan nake gani?
K'waryar madara ta kife a jikin ka?
Kar dai kuce mun ba Haddiyal bace ta kawo madarar nan da kanta, wata ta sanya ta kawo muku har tazo ta kifa maka ita a jiki."
Habu ya fad'a ransa a tsantsar b'ace.
Kafin daga bisani kuma ya fara k'ok'arin juyawa da sauri, da niyyar yaje ya samu Gimbiya Haddiyal dan yaji bayanin abun da ya faru.
Amma sai dai ko sauke k'afar sa d'aya da ya d'aga bai kaiga yiba Yarima Asad ya mik'a hannu da sauri yana mai cafko 'yan yatsun sa.
Hakan da Habu yaji ne ya sanya sa juyowa gare sa yana mai zuba masa idanuwan akan fuskar sa.
Shi kuwa Yarima Asad girgiza masa kai yayi yana mai d'an sakin murmushi, kana ya bud'e baki yana mai cewa.
"To yanzu da ka juya cikin fushi ina zaka kenan?"
"Zanje wurin ta ne, domin tamun bayanin yadda akai hakan ta faru, bayan ni da kaina nace mata ta amsa ta kawo muku da kanta."
Ya k'arasa maganar har lokacin ransa a b'ace, yana shirin zare yasun hannun sa daga cikin na Yarima Asad.
Ganin hakan da Yarima Asad yayi ne ya sanya sa sake damk'ar yastun nasa da k'arfi.
Tukun ya girgiza masa kansa fuskar sa d'auke da murmushi, kana ya d'aga lab'b'an sa yana mai fad'in.
"To idan ita d'in ce ta kawo da kanta kuma fa?"
"Ok kana nufin kace mun ita Haddiyal d'in ce ta kifo maka madarar da kanta tsabar tana hauka ko?"
Habu shima ya fad'a idanuwan sa akan Yarima Asad.
Yayin da shi kuma Yarima Asad ya lumshe nasa idanuwan, yana mai jin gaba d'aya yanayin sa na sauyawa.
Kana daga bisani ya sake wara idanuwan nasa akan fuskar Habu, sannan ya bud'e baki yana mai fad'in.
"To yanzu dai idan ma hukunci kake son kayi ba kowa ya kamata kayiwa ba face ni, domin kuwa ita har sai da ta juya ta tafi ma tukun na kifar da k'waryar madarar, ta hanyar zamewar da tayi a hannu na a lokacin da na d'auko ta domin nasha."
Yarima Asad ya samu kansa da fad'awa Habu haka, ba dan komai ba kuwa sai sabo da yadda yaga ransa ya b'aci, kuma ya fahimci muddin yaje wurin ta bazai mata da sauk'i ba.
Wanda sai bayan ya gama fad'ar hakan tukun mamakin abun da yasa sa yayi k'aryar akan waccan kucakar da tayi masa laifi ya lullub'e sa.
"To mema ya dameni ne ni, koda kashe ta ma zaiyi idan yaje d'in da har na rufa mata asiri?"
Yarima Asad ya fad'i haka a cikin ransa bayan ya gama yiwa Habu bayanin nan.
Yayin da Al'amin kuma yayi suman zaune a wurin da yake, idannwan sa akan fuskar Yarima Asad.
Gaba d'aya mamaki ya gama cikasa, ko a mafarki akace masa Yarima Asad zai aikata abun da ya aikata yau wallahi tallahi bazai tab'a yadda ba, amma sai gashi nan akan idanuwan sa komai ya faru.
Hakan ne yasa sa jinjina kan sa yana mai cigaba da bin Yarima Asad da idanuwa, wanda shi kuma zuwa yanzu ya saki yantsun Habu da ya rik'e yana mai lumshe idanuwan sa.
Shi kuwa Habu jinjina kansa yayi yana mai yadda da abun da Yarima Asad ya fad'a masa, domin kuwa ko kad'an dama shi da farko bai kawo k'anwar tasa ce ta kifar da madarar ba, sabo da yadda ya santa da tsantsar nutsuwa.
Hakan yasa ya d'an sakin murmushi, kana ya bud'e baki yana mai fad'in.
"To yanzu abun da za'ayi shine, tashi zakuyi mutafi part d'in mu sai kayi wanka ka canza kaya, in yaso sai akawo muku wata madarar bayan ka shirya kusha ko."
Ya fad'a yana mai rik'o hannun Al'amin.
Ba tare da Yarima Asad yace komai ba gaba d'ayan su suka mik'e suna masu bin bayan sa.
A b'angaren Gimbiya Haddiyal kuwa, cikin tsantsar k'unar rai ta k'arasa cikin d'akin ta.
Direct ta wuce bathroom d'in ta da yake a cikin d'akin.
Tana mai zuwa ta kunna ruwa, bayan ta shafe dai-dai saitin wurin da Yarima Asad ya rike na hannun ta da sabulu ta dinga dirzar sa.
Tana yi hawayen bak'in ciki na tsiyayowa daga cikin idanuwan ta suna wanke kaykkyawar fuskar ta.
Tabbas Yarima Asad ya shigo cikin sahun mutanen da tafi tsana a rayuwa ta sama da komai, ta yadda har ya zamto mutum na farko daga cikin su.
Yayin da shi kuma Yariman Yamma ya zamto na biyu.
Ba dan komai ba kuwa sai sabo da yadda gaba d'ayan su suka rik'e hannun ta, wanda ko kad'an basu cancanci su zamto wa'yan da zasu kalli ko da fuskar ta ba, hakan yasa take jin tamkar ba tayiwa Gid'ad'on ta adalici ba da ta bari hakan ta faru.
A yanzu tafi jin haushin Yarima Asad ma akan Yariman Yamma.
Sabo da shi kallo d'aya tayi masa ta fahimci gaba d'ayan sa zubin 'yan iskan samarin nan gare sa, duba da irin sitirar da ta gani sanye a jikin sa, wacce ko kad'an batayi kama da ta d'an musulmi ba, musulmin ma kuma wai hausa fulani, hausa fulanin ma wai d'an Sarki.
Wannan dalilin ne ya sanya ta k'arajin haushin sa fiye da yadda take jin na Yariman Yamma, domin kuwa ita ta tsani mu'amala da 'yan iskan mutane a rayuwar ta.
Ba ita ta bar dirzar hannun nata ba har sai da taji ya fara yi mata rad'ad'i, tukun ta hak'ura ta barsa haka tana mai juyawa ta doshi k'ofa, yayin da har lokacin kuma idanuwan ta suke cigaba da zubar hawaye.
Bata tsaya ba har sai da ta dangana da gaban dressing mirrow d'in ta, kana taja ta tsaya a gaban sa tana mai kallon kanta a cikin sa.
Kafin daga bisani kuma ta rumtse idanuwan ta da matuk'ar k'arfi, sannan ta bud'e su tana mai d'aga lab'b'an ta cikin sanyi tace.
"Shin har sai zuwa wane lokaci ne zaka bayyana a gareni Gid'ad'o am? Har tsawon wane lokaci zan cigaba da zaman jiran ka?
Ka taimake ni, ka taimaki rayuwa ta ka bayyanar mun a zahiri Gid'ad'o am, domin kuwa rashin ganin ka a zahiri tamkar barazana da rayuwata ce a gidan duniya, rashin bayyanar ka ya sanya har wasu mutane can suke k'ok'arin rik'e wani sassa daga jiki na, bayan kuma kai kad'ai ne mutumin da ya dace da rik'e su, domin kuwa kaine kad'ai mammalikin su.
Tabbas zuciya ta na gab da tarwasewa muddin rayuwa zata cigaba da had'ani da irin wa'yancan mutanen, wannan dalilin yasa naji na tsane su fiye da yadda na tsani mutuwa ta, domin kuwa ni d'in gaba d'aya na takace, tamkar yadda kaima ka zamto nawa ni kad'ai."
Lokaci d'aya yaji gaba d'aya komai nasa ya sauya a kanta, kayan da suke sanye a jikin ta da yake musu kallon na mahaukata a lokacin da suka shigo cikin masarautar yaga masu su, yanzu kuma sai yaga sunyi bala'in kyau a jikin ta ita.
Ko da ba a fad'a masa ba yasan ita d'in bagidajiya ce, duba da yadda yaga yanayin mutanen garin nasu suke, ga kuma kalar shigar da ya gani sanye a jikin ta.
To amma mai yasa ta kasa basa hak'uri bayan tasan itace tayi masa laifi.
Ya raya haka a cikin ransa yana mai sake d'aga idanuwansa yabi bayanta da kallo.
Kafin daga bisani kuma ya mik'e tsaye zumbur daga kan shimfid'ar da yake, yana mai shirin bin bayan ta.
Da sauri Al'amin ya mik'a hannun sa yana mai kamo tafin hannun Yarima Asad da shi.
Hakan da Yarima Asad yaji ne ya sanya sa dakatawa, yana mai juyowa ya watsa idanuwan sa akan fuskar Al'amin.
Girgiza masa kai Al'amin yayi yana mai masa alamar da ya dawo ya zauna da idanuwansa.
Yayin da a zuciyar sa kuma mamakin Asad ya gama rufe sa gaba d'aya, domin kuwa k'wayoyin idanuwan sa kawai ya kalla ya fahimci yanayin da yake a ciki.
Lumshe idanuwa Yarima Asad yayi ba tare da ya iya cewa Al'amin komai ba, tukun daga bisani ya dawo jiki a sanyaye yana mai komawa wurin da ya tashi ya zauna.
Kana ya k'ara bin hanyar da Gimbiya Haddiyal tabi da yanzu har an den hangon ta ma da idanuwan sa.
Sosai hoton kyakkyawar fuskar ta ya zauna daram a cikin idanuwan sa, ta yadda har yake jin tamkar har yanzu tana zaune ne a gaban sa.
A hankali ya durk'usar da kansa k'asa yana mai k'ara kallon madarar da take kwance akan sitirar jikinsa, kana ya d'an d'aga lab'b'ansa yana mai fesar da wata zazzafar iska daga cikin bakin sa.
Yayin da shi kansa yake mamakin abun da ya hanasa hukunta wannan bagidajiyar bak'auyiyar yarinyar, akan wannan laifin da tayi masa har ta juya ta ta tafi.
Wai yau shi Asad ne mace tayi masa laifi kuma ya barta ta juya ta tafi ba tare da ta basa ko hak'uri ba, laifi ma babban laifi ba k'arami ba.
Shi da mata suke hauka akan sa, suke kuka tare da kaff-kaffan abun da zai b'ata masa ransa, suke jin dad'i aduk lokacin da ya daga ido ya kalle su.
Mata masu aji masu ilimi, kana wa'yan da sukafi k'arfin kud'i, amma sai gashi yau wata can 'yar k'auye ta b'ata masa jiki ya kasa yin komai akan ta, asalima ko wani haushin ta baiji ba a ransa, sai zallar kyawun hallitar ta da ta tafi ta barsa da ita a cikin idanuwan sa.
Suna a cikin wannan yanayin Habu ya dawo fuskar sa d'auke da murmushi.
Amma sai dai kuma yana zuwa gaban shimfid'ar da suke zaune akai yaja ya tsaya cak, murmushin kan fuskar tasa na gushewa, yayin da idanuwan sa kuma suka kasance k'ur akan k'waryar madarar nan, tare da jikin Yarima Asad da ya gansa a b'ace.
"Shin meye hakan nake gani?
K'waryar madara ta kife a jikin ka?
Kar dai kuce mun ba Haddiyal bace ta kawo madarar nan da kanta, wata ta sanya ta kawo muku har tazo ta kifa maka ita a jiki."
Habu ya fad'a ransa a tsantsar b'ace.
Kafin daga bisani kuma ya fara k'ok'arin juyawa da sauri, da niyyar yaje ya samu Gimbiya Haddiyal dan yaji bayanin abun da ya faru.
Amma sai dai ko sauke k'afar sa d'aya da ya d'aga bai kaiga yiba Yarima Asad ya mik'a hannu da sauri yana mai cafko 'yan yatsun sa.
Hakan da Habu yaji ne ya sanya sa juyowa gare sa yana mai zuba masa idanuwan akan fuskar sa.
Shi kuwa Yarima Asad girgiza masa kai yayi yana mai d'an sakin murmushi, kana ya bud'e baki yana mai cewa.
"To yanzu da ka juya cikin fushi ina zaka kenan?"
"Zanje wurin ta ne, domin tamun bayanin yadda akai hakan ta faru, bayan ni da kaina nace mata ta amsa ta kawo muku da kanta."
Ya k'arasa maganar har lokacin ransa a b'ace, yana shirin zare yasun hannun sa daga cikin na Yarima Asad.
Ganin hakan da Yarima Asad yayi ne ya sanya sa sake damk'ar yastun nasa da k'arfi.
Tukun ya girgiza masa kansa fuskar sa d'auke da murmushi, kana ya d'aga lab'b'an sa yana mai fad'in.
"To idan ita d'in ce ta kawo da kanta kuma fa?"
"Ok kana nufin kace mun ita Haddiyal d'in ce ta kifo maka madarar da kanta tsabar tana hauka ko?"
Habu shima ya fad'a idanuwan sa akan Yarima Asad.
Yayin da shi kuma Yarima Asad ya lumshe nasa idanuwan, yana mai jin gaba d'aya yanayin sa na sauyawa.
Kana daga bisani ya sake wara idanuwan nasa akan fuskar Habu, sannan ya bud'e baki yana mai fad'in.
"To yanzu dai idan ma hukunci kake son kayi ba kowa ya kamata kayiwa ba face ni, domin kuwa ita har sai da ta juya ta tafi ma tukun na kifar da k'waryar madarar, ta hanyar zamewar da tayi a hannu na a lokacin da na d'auko ta domin nasha."
Yarima Asad ya samu kansa da fad'awa Habu haka, ba dan komai ba kuwa sai sabo da yadda yaga ransa ya b'aci, kuma ya fahimci muddin yaje wurin ta bazai mata da sauk'i ba.
Wanda sai bayan ya gama fad'ar hakan tukun mamakin abun da yasa sa yayi k'aryar akan waccan kucakar da tayi masa laifi ya lullub'e sa.
"To mema ya dameni ne ni, koda kashe ta ma zaiyi idan yaje d'in da har na rufa mata asiri?"
Yarima Asad ya fad'i haka a cikin ransa bayan ya gama yiwa Habu bayanin nan.
Yayin da Al'amin kuma yayi suman zaune a wurin da yake, idannwan sa akan fuskar Yarima Asad.
Gaba d'aya mamaki ya gama cikasa, ko a mafarki akace masa Yarima Asad zai aikata abun da ya aikata yau wallahi tallahi bazai tab'a yadda ba, amma sai gashi nan akan idanuwan sa komai ya faru.
Hakan ne yasa sa jinjina kan sa yana mai cigaba da bin Yarima Asad da idanuwa, wanda shi kuma zuwa yanzu ya saki yantsun Habu da ya rik'e yana mai lumshe idanuwan sa.
Shi kuwa Habu jinjina kansa yayi yana mai yadda da abun da Yarima Asad ya fad'a masa, domin kuwa ko kad'an dama shi da farko bai kawo k'anwar tasa ce ta kifar da madarar ba, sabo da yadda ya santa da tsantsar nutsuwa.
Hakan yasa ya d'an sakin murmushi, kana ya bud'e baki yana mai fad'in.
"To yanzu abun da za'ayi shine, tashi zakuyi mutafi part d'in mu sai kayi wanka ka canza kaya, in yaso sai akawo muku wata madarar bayan ka shirya kusha ko."
Ya fad'a yana mai rik'o hannun Al'amin.
Ba tare da Yarima Asad yace komai ba gaba d'ayan su suka mik'e suna masu bin bayan sa.
A b'angaren Gimbiya Haddiyal kuwa, cikin tsantsar k'unar rai ta k'arasa cikin d'akin ta.
Direct ta wuce bathroom d'in ta da yake a cikin d'akin.
Tana mai zuwa ta kunna ruwa, bayan ta shafe dai-dai saitin wurin da Yarima Asad ya rike na hannun ta da sabulu ta dinga dirzar sa.
Tana yi hawayen bak'in ciki na tsiyayowa daga cikin idanuwan ta suna wanke kaykkyawar fuskar ta.
Tabbas Yarima Asad ya shigo cikin sahun mutanen da tafi tsana a rayuwa ta sama da komai, ta yadda har ya zamto mutum na farko daga cikin su.
Yayin da shi kuma Yariman Yamma ya zamto na biyu.
Ba dan komai ba kuwa sai sabo da yadda gaba d'ayan su suka rik'e hannun ta, wanda ko kad'an basu cancanci su zamto wa'yan da zasu kalli ko da fuskar ta ba, hakan yasa take jin tamkar ba tayiwa Gid'ad'on ta adalici ba da ta bari hakan ta faru.
A yanzu tafi jin haushin Yarima Asad ma akan Yariman Yamma.
Sabo da shi kallo d'aya tayi masa ta fahimci gaba d'ayan sa zubin 'yan iskan samarin nan gare sa, duba da irin sitirar da ta gani sanye a jikin sa, wacce ko kad'an batayi kama da ta d'an musulmi ba, musulmin ma kuma wai hausa fulani, hausa fulanin ma wai d'an Sarki.
Wannan dalilin ne ya sanya ta k'arajin haushin sa fiye da yadda take jin na Yariman Yamma, domin kuwa ita ta tsani mu'amala da 'yan iskan mutane a rayuwar ta.
Ba ita ta bar dirzar hannun nata ba har sai da taji ya fara yi mata rad'ad'i, tukun ta hak'ura ta barsa haka tana mai juyawa ta doshi k'ofa, yayin da har lokacin kuma idanuwan ta suke cigaba da zubar hawaye.
Bata tsaya ba har sai da ta dangana da gaban dressing mirrow d'in ta, kana taja ta tsaya a gaban sa tana mai kallon kanta a cikin sa.
Kafin daga bisani kuma ta rumtse idanuwan ta da matuk'ar k'arfi, sannan ta bud'e su tana mai d'aga lab'b'an ta cikin sanyi tace.
"Shin har sai zuwa wane lokaci ne zaka bayyana a gareni Gid'ad'o am? Har tsawon wane lokaci zan cigaba da zaman jiran ka?
Ka taimake ni, ka taimaki rayuwa ta ka bayyanar mun a zahiri Gid'ad'o am, domin kuwa rashin ganin ka a zahiri tamkar barazana da rayuwata ce a gidan duniya, rashin bayyanar ka ya sanya har wasu mutane can suke k'ok'arin rik'e wani sassa daga jiki na, bayan kuma kai kad'ai ne mutumin da ya dace da rik'e su, domin kuwa kaine kad'ai mammalikin su.
Tabbas zuciya ta na gab da tarwasewa muddin rayuwa zata cigaba da had'ani da irin wa'yancan mutanen, wannan dalilin yasa naji na tsane su fiye da yadda na tsani mutuwa ta, domin kuwa ni d'in gaba d'aya na takace, tamkar yadda kaima ka zamto nawa ni kad'ai."