Sashe 31
Bakar Masarauta Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Wani sanyi taji jikin ta duka ya mata lokaci ɗaya, yayin da ƙafafuwan ta kuma da suke akan kujera taji sun fara mata karkarawa, tayarce har ta kasa tashi daga kai duk da ƙoƙarin yin hakan da take yi.
Ganin hakan da Ishaƙ yayi ne ya sanya sa miƙewa tsaye cikin sanyi, yana mai yin wurin da take.
Ahankali ya miƙa hannuwan sa yana mai riƙo tafukan hannayen ta duka biyu da su, tukun daga bisani ya ɗagota yana mai miƙar da ita tsaye, sannan ya saki hannun ta ɗaya yana mai riƙe ɗaya sukayi gaba.
Zama yayi akan tabarmar dai dai wurin da ya tashi, yayin da ita kuma Aishatu ta zauna daga gaban sa kusa da Kaka, ya zamto suna facing É—in junan su da shi.
Sake miƙa hannuwan sa yayi ya riƙo nata da su, tukun daga bisani ya buɗe baki cin sanyi idanuwan sa akan ta yana mai faɗin. "Shin wane ke bayarwa Aishatu?" Ya jefo mata tambaya yana mai kallon ta.
Yayin da ita kuma ta lumshe idanuwan ta tana mai jin zuciyar ta na wata irin tsinkewa, tukun daga bisani ta wara su akan fuskar sa ahankali tana mai faɗin. "Allah mana." Ta faɗa ƙasa-ƙasa jikin ta na ƙara mutuwa.
Yayin da shi kuma Ishaƙ ya girgiza kansa alamar na'am, tukun daga bisani ya ɗora da faɗin. "Nasan dukan mu nan mun san mutuwa gaskiya ce, sannan kuma ko wane rai da yake cikin duniya sai ya ɗan ɗane ta, walau yaro, walau babba, tosho da tsohuwa, haka kuma babu wanda yasan lokacin da tasa zata riske sa, da...." "Haƙiƙa ni ɗin musulmace, wacce ta yadda da ƙaddara mai kyau da mara kyau, dan haka kawai faɗamun kai tsaye, insha Allah zan jure suraron koma mene ne, sannan kuma zan rungumi ƙaddara ta da hannu bibbiyu." Ta katse sa daga maganar da yake da faɗin haka jikin ta na tsantsar rawa, dan kuwa ji tai gaba ɗaya bazata iya jiran sa ba har zuwa lokacin da zai gama bayanin sa.
Lumshe idanuwna sa ya sake yi yana mai ƙara damƙar tafin hannun ta, tukun daga bisani ya buɗe su, sannan yayi gayaran murya, kana ya buɗe baki yana mai faɗin. "Allah yayiwa Baffah Rasuwa a shekaran jiya da daddare!" Ya faɗa yana mai yin shiru ba tare da yace komai ba, sai idanuwa kawai da ya bita da su yana mai kallon ta, kamar yacce itama take kallon sa idanuwan ta duka awaje, ba tare da tace masa komai ba, domin kuwa gaba ɗaya ma jitai duka natsuwar ta da komai nata sun ɗauke, ga wani irin dum da taji kunnuwan ta da kanta sun mata, ɗan cikin ta kuma na juyawa.
Yayin da Kaka kuma ta buɗe baki tana mai faɗin. "Innalillahi wa'inna ilahir raji'un. La'ilah Haillalahu Muhammadu Rasulullahi Sallalawu Alaihi Wassallam." Tukun daga bisani kuma wasu irin hawaye suka ɓalle daga cikin idanuwan ta da matuƙar gudu, kana ta sake buɗe baki cikin kuka tana mai faɗin. "Shin a'ina ka jiyo wannan labarin ne Ishaƙ?"
"Ɗazu nima ina zaune akasuwa, ɗaya daga cikin mutanen da suke can ƙasar tare yazo mun da labarin, domin kuwa yace ma tun a jiya da sassafe bayan anyi jana'izar sa ya tawo, wuri na ya fara sauka."
To yanzu yana ina ne shi É—in?" Cewar Kaka tana kallon sa.
"Na ajiye sa ne a shagon ƙofar gida, sabo da da haka yace ayau zai juyama nine na hana sa tafiya, nace ya bari zuwa gobe sai mu tafi tare."
Shiru sukai dukan su ba tare da sunce komai ba, sai uban tagumi da kaka ta buga tana kallon Aishatu data zamto tamkar mutun-mutumi awuirin da take, domin kuwa tun daga lokacin da taji furucin sa na farko bata sake iya motsawa daga yarce take ba, asalima gaba É—aya bata ji sauran bayanan nasa ba ko kaÉ—an.
Sai da ta ɗauki kimanin mintina kusan goma ahakan, tukun daga bisani ta ɗago afirgice tana mai kai idanuwan ta kan fuskar mijijn nata, sannan ta buɗe baki cikin rawar murya tana mai faɗin. "Shin dagaske ne Baffah na ya rasu Abban Ahmad?" Ta ƙarasa maganar wasu irin hawaye masu matuƙar gudu suna ɓallewa daga cikin idanuwan ta.
Miƙewa Kaka tayi tsaye tana mai nufar cikin ɗakin ta, hakan da ishak ya gani ne ya sanya sa miƙewa tsaye shima, tukun ya kamo hannun Aishatu yana mai janta sukayi part ɗin su.
ƘASAR MALIN, JAHAR KARFUZ CIKIN BAƘAR MASARAUTA.
Cikin tsantsar tashin hankali Sarki Barbaru ya doshi hanyar da zata kaisa wurin Boka mai hutar kasko.
Sai dai kuma tun kafin yayi nisa ya hango dan-dazon jama'a na ɓullowa hankali atsan-tsar tashe, ga kuma wani irin sauyawa da yaga sama nayi tana rikiɗewa kamar yacce Ƴammatan Bayin nan suka faɗa.
Hakan da ya ganine ya sanya sa juyawa baya da matuƙar sauri yana mai dosar wurin da dokunan su suke.
Ko daƙiƙa biyu ba baiyi ba daga wurin da yake zuwa ma'ajiyar dokunan.
Wani irin tsalle ya buga tun daga nesa, yarce kasan bashi bane jibge-gen mutumin nan, yana mai hayewa saman wani baƙin doki, tukun ya damiƙi linzamin sa da matuƙar ƙarfi yana mai sa hannu ya daki bayan sa da shi.
Wata irin haniniya dokin ya saki da ƙarfi, kana ya fara ɗaga ƙafafuwan sa yana mai fucewa daga cikin wurin da tsantsar gudu.
Gudu dokin yake yarce kasan zai tashi sama, yayin da jama'a ke cigaba da furfutowa bakunan su É—auke da ihu tare da kiran sunan Gargabilu.
Cikin daƙiƙun da basu zarta ukku ba duka dokin ya ɓulla kwanar da zata kai sa wurin Boka mai hutar kasko.
Da matuÆ™ar sauri Sarki Barbaru ya dire daga kan dokin ba tare da ya tsayar da shi ba, hankalin sa na sake matuÆ™ar tashi, sabo da yarce ya hango B.............âœ
By
UMAR FARUQ*D*
*BAƘAR MASARAUTA*
*NA*
UMAR FARUQ*D*
*PAGE 13*
Boka mai wutar kasko ya futo daga cikin ɗakin sa amatuƙar ruɗe, yana mai kallon sama, ga kuma yarce garin ke sake rikiɗewa yana yin duhu.
Da matuƙar sauri ya dire daga kan dokin, yana mai yin wurin da ya hangi Boka mai hutar kasko.
"Shin meke shirin faruwa damu n ya kai Boka?" Sarki Barbaru ya watsowa Boka mai hutar kasko tambaya cikin kakkausar muryar sa, hankalin sa atsantsar tashe.
Yayin da Boka Barbaru kuma ya cigaba da juyi yana kallon sama, ba tare da ya kalli ko inda Sarki Barbaru yake ba, ballan tana ya tanka masa.
"Na roƙeƙa da abun bauta Gargabilu ka tsaya kai mun bayanin ta inda mafuta take." Sarki Barbaru ya sake faɗa adai dai lokacin da ya ƙaraso gaban Boka mai hutar kasko.
"Ni kai na bansan ta inda zan fara ba, domin kuwa lamarin yazo mun alokacin da ban tsammace sa ba, sabo da ko kaɗan abun bauta Gargabilu bai sanar mun da faruwar hakan ba, gashi kuma afahimta ta ta yanzu naga kamar garin ake shirin rusawa tare da jama'a..." Dakata Boka!" Sarki Barbaru ya katse sa da faɗin haka cikin tsawa, hankalin sa na sake bala'in tashi, tukun daga bisani ya fara ɗaga ƙafafuwan sa yana mai ƙara matsawa kusa da Boka mai hutar kasko, sannan ya buɗe baki yana mai faɗin. "Mafuta nake son ka samar mana Boka, ba wai bayanin abun da yake shirin faruwa damu ba, domin ko tun lokacin da wannan labarin ya iso kunnuwa na na fahimce cewar mun aikata babban laifin ne ga Ubangiji Gargabilu, shiya sa har yake shirin hukun tamu ta wannan hanyar, dan haka duk yanzu ba lokacin dogon jawabi bane, kamata yayi ace ko da na ɓullo wurin nan in hangeka agaban Huta da Ƙasa kana ƙoƙarin nemar mana afuwa ba anan ba." Ya ƙarasa maganar da sakin huci.
Yayin da Boka mai Hutar kasko kuma ya buɗe baki cikin zafi shima yana mai faɗin. "Haƙiƙa al'amarin ya huce duk yarce kake.zato, domin kuwa cikin duka abubuwan daka lissafo ayanzu babu ɗaya da ya rage banyi sa ba, amma duk basuyi aiki ba, sabo da ita kanta Hutar kasko Bama ta koma, tana futar da jan hayaƙi, wanda hakan ke nuni da cewar kamar wasu al'ummar ne daga wani yankin suke shirin kawo mana farmaki, wannan dalilin shine ya sanya kazo ka sameni awurin nan, sabo da in duba ne dan na gano ta yadda zan ɓullowa al'amarin!" Boka mai hutar kasko ya ƙarasa maganar yana mai kallon cikin idanuwan Sarki Barbaru.
Yayin da shi kuma ya juya yana mai kaiwa iska naushi, tare da faxin. "Kai, kai, kai inaaa! Hakan ba zata taɓa faru dani ba wallahi." Ya faɗa da ƙarfi yana mai juyawa ya fara taku daga inda yake zuwa gaba cikin tsantsar sauri, tukun daga bisani kuma ya sake juyowa ahaukace yana mai dawowa gaban Boka Gargabilu, kana daga bisani ya buɗe baki yana mai faɗin. "To yanzu meye mafuta kenan Boka?"
"Zan koma ciki a yanzu domin nayi ƙoƙarin ganin mun sadu da ubangiji Gargabilu ayanzu-yanzu, duk da yau ɗin bata kasance ranar saduwar mu ba, amma sai dai kuma babu yarce zamuyi dole zanje nabi wata hanya, domin ganin na sadu da shi, sabo da ya samar mana da mafuta."
"To muje mana kawai kafara Boka, domin kuwa na sani ubangiji Gargabilu bazai taɓa barin mu mutaɓe ba, sabo da mun kasance masu ƙoƙarin yin duk wani abu da ya sanya mu muyi." Sarki Barbaru ya faɗa yana mai bin bayan Boka mai hutar kasko da yayi gaba.
Ganin hakan da Ishaƙ yayi ne ya sanya sa miƙewa tsaye cikin sanyi, yana mai yin wurin da take.
Ahankali ya miƙa hannuwan sa yana mai riƙo tafukan hannayen ta duka biyu da su, tukun daga bisani ya ɗagota yana mai miƙar da ita tsaye, sannan ya saki hannun ta ɗaya yana mai riƙe ɗaya sukayi gaba.
Zama yayi akan tabarmar dai dai wurin da ya tashi, yayin da ita kuma Aishatu ta zauna daga gaban sa kusa da Kaka, ya zamto suna facing É—in junan su da shi.
Sake miƙa hannuwan sa yayi ya riƙo nata da su, tukun daga bisani ya buɗe baki cin sanyi idanuwan sa akan ta yana mai faɗin. "Shin wane ke bayarwa Aishatu?" Ya jefo mata tambaya yana mai kallon ta.
Yayin da ita kuma ta lumshe idanuwan ta tana mai jin zuciyar ta na wata irin tsinkewa, tukun daga bisani ta wara su akan fuskar sa ahankali tana mai faɗin. "Allah mana." Ta faɗa ƙasa-ƙasa jikin ta na ƙara mutuwa.
Yayin da shi kuma Ishaƙ ya girgiza kansa alamar na'am, tukun daga bisani ya ɗora da faɗin. "Nasan dukan mu nan mun san mutuwa gaskiya ce, sannan kuma ko wane rai da yake cikin duniya sai ya ɗan ɗane ta, walau yaro, walau babba, tosho da tsohuwa, haka kuma babu wanda yasan lokacin da tasa zata riske sa, da...." "Haƙiƙa ni ɗin musulmace, wacce ta yadda da ƙaddara mai kyau da mara kyau, dan haka kawai faɗamun kai tsaye, insha Allah zan jure suraron koma mene ne, sannan kuma zan rungumi ƙaddara ta da hannu bibbiyu." Ta katse sa daga maganar da yake da faɗin haka jikin ta na tsantsar rawa, dan kuwa ji tai gaba ɗaya bazata iya jiran sa ba har zuwa lokacin da zai gama bayanin sa.
Lumshe idanuwna sa ya sake yi yana mai ƙara damƙar tafin hannun ta, tukun daga bisani ya buɗe su, sannan yayi gayaran murya, kana ya buɗe baki yana mai faɗin. "Allah yayiwa Baffah Rasuwa a shekaran jiya da daddare!" Ya faɗa yana mai yin shiru ba tare da yace komai ba, sai idanuwa kawai da ya bita da su yana mai kallon ta, kamar yacce itama take kallon sa idanuwan ta duka awaje, ba tare da tace masa komai ba, domin kuwa gaba ɗaya ma jitai duka natsuwar ta da komai nata sun ɗauke, ga wani irin dum da taji kunnuwan ta da kanta sun mata, ɗan cikin ta kuma na juyawa.
Yayin da Kaka kuma ta buɗe baki tana mai faɗin. "Innalillahi wa'inna ilahir raji'un. La'ilah Haillalahu Muhammadu Rasulullahi Sallalawu Alaihi Wassallam." Tukun daga bisani kuma wasu irin hawaye suka ɓalle daga cikin idanuwan ta da matuƙar gudu, kana ta sake buɗe baki cikin kuka tana mai faɗin. "Shin a'ina ka jiyo wannan labarin ne Ishaƙ?"
"Ɗazu nima ina zaune akasuwa, ɗaya daga cikin mutanen da suke can ƙasar tare yazo mun da labarin, domin kuwa yace ma tun a jiya da sassafe bayan anyi jana'izar sa ya tawo, wuri na ya fara sauka."
To yanzu yana ina ne shi É—in?" Cewar Kaka tana kallon sa.
"Na ajiye sa ne a shagon ƙofar gida, sabo da da haka yace ayau zai juyama nine na hana sa tafiya, nace ya bari zuwa gobe sai mu tafi tare."
Shiru sukai dukan su ba tare da sunce komai ba, sai uban tagumi da kaka ta buga tana kallon Aishatu data zamto tamkar mutun-mutumi awuirin da take, domin kuwa tun daga lokacin da taji furucin sa na farko bata sake iya motsawa daga yarce take ba, asalima gaba É—aya bata ji sauran bayanan nasa ba ko kaÉ—an.
Sai da ta ɗauki kimanin mintina kusan goma ahakan, tukun daga bisani ta ɗago afirgice tana mai kai idanuwan ta kan fuskar mijijn nata, sannan ta buɗe baki cikin rawar murya tana mai faɗin. "Shin dagaske ne Baffah na ya rasu Abban Ahmad?" Ta ƙarasa maganar wasu irin hawaye masu matuƙar gudu suna ɓallewa daga cikin idanuwan ta.
Miƙewa Kaka tayi tsaye tana mai nufar cikin ɗakin ta, hakan da ishak ya gani ne ya sanya sa miƙewa tsaye shima, tukun ya kamo hannun Aishatu yana mai janta sukayi part ɗin su.
ƘASAR MALIN, JAHAR KARFUZ CIKIN BAƘAR MASARAUTA.
Cikin tsantsar tashin hankali Sarki Barbaru ya doshi hanyar da zata kaisa wurin Boka mai hutar kasko.
Sai dai kuma tun kafin yayi nisa ya hango dan-dazon jama'a na ɓullowa hankali atsan-tsar tashe, ga kuma wani irin sauyawa da yaga sama nayi tana rikiɗewa kamar yacce Ƴammatan Bayin nan suka faɗa.
Hakan da ya ganine ya sanya sa juyawa baya da matuƙar sauri yana mai dosar wurin da dokunan su suke.
Ko daƙiƙa biyu ba baiyi ba daga wurin da yake zuwa ma'ajiyar dokunan.
Wani irin tsalle ya buga tun daga nesa, yarce kasan bashi bane jibge-gen mutumin nan, yana mai hayewa saman wani baƙin doki, tukun ya damiƙi linzamin sa da matuƙar ƙarfi yana mai sa hannu ya daki bayan sa da shi.
Wata irin haniniya dokin ya saki da ƙarfi, kana ya fara ɗaga ƙafafuwan sa yana mai fucewa daga cikin wurin da tsantsar gudu.
Gudu dokin yake yarce kasan zai tashi sama, yayin da jama'a ke cigaba da furfutowa bakunan su É—auke da ihu tare da kiran sunan Gargabilu.
Cikin daƙiƙun da basu zarta ukku ba duka dokin ya ɓulla kwanar da zata kai sa wurin Boka mai hutar kasko.
Da matuÆ™ar sauri Sarki Barbaru ya dire daga kan dokin ba tare da ya tsayar da shi ba, hankalin sa na sake matuÆ™ar tashi, sabo da yarce ya hango B.............âœ
By
UMAR FARUQ*D*
*BAƘAR MASARAUTA*
*NA*
UMAR FARUQ*D*
*PAGE 13*
Boka mai wutar kasko ya futo daga cikin ɗakin sa amatuƙar ruɗe, yana mai kallon sama, ga kuma yarce garin ke sake rikiɗewa yana yin duhu.
Da matuƙar sauri ya dire daga kan dokin, yana mai yin wurin da ya hangi Boka mai hutar kasko.
"Shin meke shirin faruwa damu n ya kai Boka?" Sarki Barbaru ya watsowa Boka mai hutar kasko tambaya cikin kakkausar muryar sa, hankalin sa atsantsar tashe.
Yayin da Boka Barbaru kuma ya cigaba da juyi yana kallon sama, ba tare da ya kalli ko inda Sarki Barbaru yake ba, ballan tana ya tanka masa.
"Na roƙeƙa da abun bauta Gargabilu ka tsaya kai mun bayanin ta inda mafuta take." Sarki Barbaru ya sake faɗa adai dai lokacin da ya ƙaraso gaban Boka mai hutar kasko.
"Ni kai na bansan ta inda zan fara ba, domin kuwa lamarin yazo mun alokacin da ban tsammace sa ba, sabo da ko kaɗan abun bauta Gargabilu bai sanar mun da faruwar hakan ba, gashi kuma afahimta ta ta yanzu naga kamar garin ake shirin rusawa tare da jama'a..." Dakata Boka!" Sarki Barbaru ya katse sa da faɗin haka cikin tsawa, hankalin sa na sake bala'in tashi, tukun daga bisani ya fara ɗaga ƙafafuwan sa yana mai ƙara matsawa kusa da Boka mai hutar kasko, sannan ya buɗe baki yana mai faɗin. "Mafuta nake son ka samar mana Boka, ba wai bayanin abun da yake shirin faruwa damu ba, domin ko tun lokacin da wannan labarin ya iso kunnuwa na na fahimce cewar mun aikata babban laifin ne ga Ubangiji Gargabilu, shiya sa har yake shirin hukun tamu ta wannan hanyar, dan haka duk yanzu ba lokacin dogon jawabi bane, kamata yayi ace ko da na ɓullo wurin nan in hangeka agaban Huta da Ƙasa kana ƙoƙarin nemar mana afuwa ba anan ba." Ya ƙarasa maganar da sakin huci.
Yayin da Boka mai Hutar kasko kuma ya buɗe baki cikin zafi shima yana mai faɗin. "Haƙiƙa al'amarin ya huce duk yarce kake.zato, domin kuwa cikin duka abubuwan daka lissafo ayanzu babu ɗaya da ya rage banyi sa ba, amma duk basuyi aiki ba, sabo da ita kanta Hutar kasko Bama ta koma, tana futar da jan hayaƙi, wanda hakan ke nuni da cewar kamar wasu al'ummar ne daga wani yankin suke shirin kawo mana farmaki, wannan dalilin shine ya sanya kazo ka sameni awurin nan, sabo da in duba ne dan na gano ta yadda zan ɓullowa al'amarin!" Boka mai hutar kasko ya ƙarasa maganar yana mai kallon cikin idanuwan Sarki Barbaru.
Yayin da shi kuma ya juya yana mai kaiwa iska naushi, tare da faxin. "Kai, kai, kai inaaa! Hakan ba zata taɓa faru dani ba wallahi." Ya faɗa da ƙarfi yana mai juyawa ya fara taku daga inda yake zuwa gaba cikin tsantsar sauri, tukun daga bisani kuma ya sake juyowa ahaukace yana mai dawowa gaban Boka Gargabilu, kana daga bisani ya buɗe baki yana mai faɗin. "To yanzu meye mafuta kenan Boka?"
"Zan koma ciki a yanzu domin nayi ƙoƙarin ganin mun sadu da ubangiji Gargabilu ayanzu-yanzu, duk da yau ɗin bata kasance ranar saduwar mu ba, amma sai dai kuma babu yarce zamuyi dole zanje nabi wata hanya, domin ganin na sadu da shi, sabo da ya samar mana da mafuta."
"To muje mana kawai kafara Boka, domin kuwa na sani ubangiji Gargabilu bazai taɓa barin mu mutaɓe ba, sabo da mun kasance masu ƙoƙarin yin duk wani abu da ya sanya mu muyi." Sarki Barbaru ya faɗa yana mai bin bayan Boka mai hutar kasko da yayi gaba.