Sashe 13
Bakar Masarauta Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Yana futa ya ɗauki hanyar dake kallon kudu yana mai miƙar ta, tafe yake yana dingishi tare da cije lips ahanka har yayi tafiya mai nisa daga inda yake, tukun ya ɓulla wani huri wanda za'a iya kiran sa da daji sabo da bishiyun da suka kasance awurin masu matuƙar yawa ta koina, banda sautin kukan tsunysaye babu sautin da akeji yana tashi awurin.
Jingina yayi jikin wata bishiya yana mai ɗaga kansa sama tare da lumshe idanuwan sa. Kana ya ɗaga laɓɓan sa ahankali yana mai faɗin. "Iya tace ba'a taɓa yin nasara daga zaune, sannan kuma daɗi bai zuwa sai bayan ansha gumurzu, dan haka na ɗauri aniyar zama jarumi har zuwa lokacin da zancimma buri na, zan jure kowace kalar wahala daga gareki yake Gimbiyar BAƘAR MASARAUTA, zan ɗauki ko wane kalar wulaƙanci da ƙasƙanci muddin zan samu abun da zuciya ta take muradi agaba, zan tabbatarwa duniyar BAƘAR MASARAUTA cewa Iya batai ƙarya ba data kirani da suna JARUMI." Ya ƙarashe maganar yana mai buɗe idanuwan sa tare da sauke kansa ƙasa, tukun yakai duban sa kan tafin hannun sa da yake riƙe da kwari da gwafa, sannan ya matsa daga jikin bishiyar nan yana mai ɗaukar kwarin ya maƙala sa ajikin gwafar, tukun ya saita wata shirgegiya bishiya da take nesa dashi sosai, yana mai jan gwafar tukun ya sake ta.
Fit!!! Kake jin sautin futar tsinken daga jikin gwafar da matauƙar gudu yana mai zuwa ya cake cak ajikin bishiyar.
Cigaba da saki yayi baji ba gani yana yi yana tangaÉ—i tare da buÉ—e baki, sabo da yarce yake jin wata irin hajijiya na É—ibar sa, amma duk da haka ko kaÉ—an bashi da alamar zai tsaya.
Kallo ɗaya zakai nasa ka fahimci ba'a ƙaramun jigace yake ba, sabo da yarce gumi ke cigaba da tsiyaya daga jikin sa da yake tsantsar rawa, ga laɓɓan sa da sukayi matuƙar buahewa tare da yin baƙi, alamun ba ƙaramar ishirwa yake ji ba kenan!
"Kai Jarumi! Jarumi!! Jarumi!!! Shin meye hakan kake yi?" Sautin muryar iyar bayi ya daki dodon kunnen sa cikin firgici, amma duk da haka bai waiga ya kalli inda yajiyo sautin ba balle harya tsaya daga abun da yake, sai uban tangaÉ—i da yake yi kawai!
Da gudu Abokan nan nasa guda biyu da suka kai sa ɗaki suka ƙaraso inda yake suna masu sanya hannu suka rirriƙe sa, tukun Mauzum ya anshe kwari da gwafar daga hannun sa yana mai dire su aƙasa.
"Shin me yasa zaka baro ɗaki kayo nan, bayan kasan ɗauke kake da raunika ajikin ka Jarumi?" Cewar Iyar bayi tana mai durƙusawa ta aje ƙatuwar ƙwaryar dake rumgume ahannun ta agefe, tukun ta matsa inda su Mauzum suke zaune aƙasa, rungume da Bir da yake ta faman sakin numfarfshi idanuwan sa na kakafewa ahannun su.
Zama tayi tana mai tanƙwashe ƙafafuwan ta agaban sa, tukun ta tallabo kansa tana mai ɗora sa akan cinyar ta, kana ta buɗe tafin hannun ta tana mai ɗan marin fuskar sa sama-sama bakin ta na furta kalmar. "Kai Jarumi! Jarumi!! Jarumi na!!!" Amma sai dai ko kallon ta baiba sai idanuwan sa da suke cigaba da kakkafewa numfashin sa na fuzga da ƙarfi.
"Kai Mauzum maza yi sauri ka miƙo mun ƙwaryaccan." Iyar Bayi ta faɗa hankali tashe tana mai cigaba da marin fuskar Bir tare da faɗin Jarumi.
Dasauri suka mike su duka biyun har suna gware da juna wurin tashi, tukun Mauzum yay maza yaje ya ɗauko ƙwaryar da take cike da ruwa tare da kofi acikin ta yana mai zuwa ya ajeta agaban Iyar Bayi.
Dasauri ta sanya hannu ta É—auki moÉ—ar dake cikin ruwan tana mai kwaso ruwan da shi, tsiyaya sa tayi atafin hannun ta, tukun ta yarfawa Bir shi akan fuska tana mai cigaba da kiran sunan sa.
Ajiyar zuciya ya fara saukewa akai-akai yana mai lumshe idanuwan sa.
Hakan da Iyar Bayi ta gani ne yasan ya ta sa hannu ta ɗago kansa, tukun ta ɗora masa moɗar ruwan akan laɓɓa tana mai faɗin. "Sha ruwa Jarumi na."
Bai musa mata ba ya buÉ—e bakin sa ruwan ya fara wucewa da sauri da sauri.
Tas ya shanye ruwan yana mai buɗe idanuwan sa, sake maida moɗar ruwan tayi cikin ƙwaryar ta ƙara kamfato sa, tukun ta ƙara ɗora masa akan baki ya shanye sa tas.
Sannan ya sake maida kansa kan cinyar Iya yana mai lumshe idanuwan sa.
"Shin sai yaushe ne zake dena shigewa Gimbiya Jarumi? Kullum abun da nake gudar ma kenan amma ko kaɗan bakaji, to yanzu wagari ya waya kenan, gashi kuma kasan Jibi ne bikin ranar zagayowar godiya ga abun Bauta Gargabilu, amma kuma babu abun da ka tanada, ko iccen da zaka ɗauka baka tanada ba, kuma kasan ko awane irin hali kake ciki babu wanda zai yarje maka sai ka futo kaima." Iyar bayi ta faɗa tana mai bin fatar jikin sa da tayi wani irin dabbara-dabbaran baƙi da ja yarce kasan wanda ya ƙone da idanu. Yayin da shiko Bir har lokacin yake lumshe da idanuwan sa ba tare da yace mata komai ba.
Hannu tasa ahaɓar zanin ta tana mai ciro wani ƙullin tsuma, tukun ta fara kwance sa bayan ta sake matso da ƙwaryar ruwan nan gaban ta.
Ƙullikan wasu tsummokaran ne har guda biyu acikin babban ƙullin.
Ɗaukar na farkon tayi ta fara kwance sa. Gishiri ne ya bayyana acikin sa, buɗe tafin hannun ta tayi tana mai tsiyaya gishirin da yawa akan sa, tukun ta juye sa acikin ruwan ƙwaryar, sannan ta sake kwance ɗayan ɗaurin wanda yake ɗauke da garin magani acikin sa.
Shima ɗibar sa tayi ta zuba acikin ruwan, kana ta sake ƙulle su tana mai mai dasu jikin haɓar zanin ta ta ɗaure, tukun ta sanya hannun ta cikin ruwan tana mai jujjuya sa.
Kana ta tsunduma kofin nan tana mai kamfato ruwan da shi, tukun ta juye sa ajikin Bir.
Rumtse idanuwan sa yayi da ƙarfi yana mai taune leɓen sa na ƙasa, sabo da yarce ruwan yake ratsa ciwukan dake jikin sa yana kwanciya.
"Ina mai roƙon ka da abun bauta Gargabilu ka taimake ni ka kuma taimaki kan ka futa daga harkar Gimbiya, muddin baso kake muyi kukan rashin ka ba nan kusa." Iyar bayi ta faɗa tana mai cigaba da watsa masa ruwan ajiki.
Sai da ta gama sanya masa ruwan ta tabbatar da ya taɓa ko ina na jikin sa, tukun ta miƙe tsaye tana mai gyara ɗaurin baƙin ƙyallen da yake aƙugun ta, kana ta kalle su tana mai faɗin. "Yanzu ba zama zakuyi ba, ku tashi ku kama Jarumi kutaya sa yo nasa itacen ɗaukar shima, dan ko muddin bakuyi hakan ba to ni nasan wannan azabar tayau ba komai bace akan wacce Boka mai Hutar Kasko zai sa ayimasa aranar Biki." Ta ƙarasa maganar tana mai juyawa ta doshi hanyar data biyo.
"Shin har sai zuwa wane lokaci ne zaki cikan alk'warin da kika d'aukar mun ne Iya?" Bir ya fad'a da k'arfi yana mai mik'ewa tsaye, tukun ya fara d'aga k'afafuwan sa yana mai dosar inda iyar bayi take. Yayin da ita kuma Iyar Bayi ta tsaya cak ai'nda take jikin ta na matuk'ar rawa ba tare data iya furta komai ba, tukun daga bisani ta fara waige- waige tana mai duba gabas da yamma, kudu da arewa, domin taga ko akwai wani wanda yaji furucin Bir bayan su.
Sai da ta tabbatar da babu wani mahaluk'i dake wurin bayan su, tukun ta juyo inda Bir yake takowa da d'an gyashi jikin ta na tsantsar karkarwa.
"Shin mene zai sanya kayi irin wannan furucin awuri irin wannan jarumi?" Iyar Bayi ta fad'a k'asa k'asa tana mai matsawa inda Bir yake ta dafa kafad'ar sa.
"To iya s.... "Shiiiit!" Iya ta fad'a tana mai d'ora yatsa akan baki tare da zaro idanuwa, jikin ta na tsantsar rawa, yayin da shi kuma Bir ya bita da idanu yana kallon ta, tukun daga bisani ta janye yatsar ta daga kan la'b'ban ta tana mai bud'e baki ahankali tace. "Muddin baso kake in bak'unci k'asa ba ayau, to na rok'eka da abun bauta Gargabilu ka temakeni karna sake jin makamancin furuci irin wannan anan wurin."
"Amm..." "A'a Jarumi kawai kayi abun da na sanya ku, ka tafi, ka tafi kuje kufara samo icci na." Cewar iyar bayi jikin ta na tsantsar kyarma.
Yayin da shi kuma Bir ya rumtse idanuwan sa da matuk'ar k'arfi tare da taune leb'en sa na k'asa, tukun ya juya yana mai fara d'aga k'afafuwan sa ya doshi inda ya baro ba tare da ya sake cewa komai ba.
Wata irin nannauyar ajiyar zuciya Iyar bayi ta saki tana mi dafe k'irjin ta da hannu, tukun itama ta juya cikin tsantsar sauri tana mai dosar inda ta futo, har lokacin kuma jikin ta bai bar kyarmar da yake yiba.
Acan b'angaren Gimbiya Tsamir kuwa cikin zafin rai ta damk'i kan macijiyar nan da ke karkad'a harshen ta bayan ta durk'ushe agaban ta tare da rumtse idanuwan ta da k'arfi.
Tukun daga bisani ta bud'e baki cikin kaushi tana mai fad'in. "Shin meke shirin faruwa dani ce Shairama? Wane laifi nayiwa abun bauta Gargabilu da har yake shirin hukunta ni ta wannan hanyar? Kamar ni! Kamar ni!! Ni Gimbiya Tasmir har zan yiwa wani can k'as-k'antanccen bawa hukunci asa na sake sa! Shin ina k'arfin iko na ya tafi ne? Me Baba yake nufi dani ce akan wancan k'ask'antaccen banzan mara galihu Shairma?" Ta fad'a da k'araji tana mai sakin kan macjiyar ta mik'ewa tsaye.
Taku ta farayi daga inda take zuwa gaba, sai da tayi taku ya kai biyar, tukun taja tsaya tana mai sakin wasu irin numfar-fashi, kana daga bisani ta juyo tana mai dawowa wurin yashin da ta cake takobin ta ta funcike ta da matuk'ar k'arfi.
Jingina yayi jikin wata bishiya yana mai ɗaga kansa sama tare da lumshe idanuwan sa. Kana ya ɗaga laɓɓan sa ahankali yana mai faɗin. "Iya tace ba'a taɓa yin nasara daga zaune, sannan kuma daɗi bai zuwa sai bayan ansha gumurzu, dan haka na ɗauri aniyar zama jarumi har zuwa lokacin da zancimma buri na, zan jure kowace kalar wahala daga gareki yake Gimbiyar BAƘAR MASARAUTA, zan ɗauki ko wane kalar wulaƙanci da ƙasƙanci muddin zan samu abun da zuciya ta take muradi agaba, zan tabbatarwa duniyar BAƘAR MASARAUTA cewa Iya batai ƙarya ba data kirani da suna JARUMI." Ya ƙarashe maganar yana mai buɗe idanuwan sa tare da sauke kansa ƙasa, tukun yakai duban sa kan tafin hannun sa da yake riƙe da kwari da gwafa, sannan ya matsa daga jikin bishiyar nan yana mai ɗaukar kwarin ya maƙala sa ajikin gwafar, tukun ya saita wata shirgegiya bishiya da take nesa dashi sosai, yana mai jan gwafar tukun ya sake ta.
Fit!!! Kake jin sautin futar tsinken daga jikin gwafar da matauƙar gudu yana mai zuwa ya cake cak ajikin bishiyar.
Cigaba da saki yayi baji ba gani yana yi yana tangaÉ—i tare da buÉ—e baki, sabo da yarce yake jin wata irin hajijiya na É—ibar sa, amma duk da haka ko kaÉ—an bashi da alamar zai tsaya.
Kallo ɗaya zakai nasa ka fahimci ba'a ƙaramun jigace yake ba, sabo da yarce gumi ke cigaba da tsiyaya daga jikin sa da yake tsantsar rawa, ga laɓɓan sa da sukayi matuƙar buahewa tare da yin baƙi, alamun ba ƙaramar ishirwa yake ji ba kenan!
"Kai Jarumi! Jarumi!! Jarumi!!! Shin meye hakan kake yi?" Sautin muryar iyar bayi ya daki dodon kunnen sa cikin firgici, amma duk da haka bai waiga ya kalli inda yajiyo sautin ba balle harya tsaya daga abun da yake, sai uban tangaÉ—i da yake yi kawai!
Da gudu Abokan nan nasa guda biyu da suka kai sa ɗaki suka ƙaraso inda yake suna masu sanya hannu suka rirriƙe sa, tukun Mauzum ya anshe kwari da gwafar daga hannun sa yana mai dire su aƙasa.
"Shin me yasa zaka baro ɗaki kayo nan, bayan kasan ɗauke kake da raunika ajikin ka Jarumi?" Cewar Iyar bayi tana mai durƙusawa ta aje ƙatuwar ƙwaryar dake rumgume ahannun ta agefe, tukun ta matsa inda su Mauzum suke zaune aƙasa, rungume da Bir da yake ta faman sakin numfarfshi idanuwan sa na kakafewa ahannun su.
Zama tayi tana mai tanƙwashe ƙafafuwan ta agaban sa, tukun ta tallabo kansa tana mai ɗora sa akan cinyar ta, kana ta buɗe tafin hannun ta tana mai ɗan marin fuskar sa sama-sama bakin ta na furta kalmar. "Kai Jarumi! Jarumi!! Jarumi na!!!" Amma sai dai ko kallon ta baiba sai idanuwan sa da suke cigaba da kakkafewa numfashin sa na fuzga da ƙarfi.
"Kai Mauzum maza yi sauri ka miƙo mun ƙwaryaccan." Iyar Bayi ta faɗa hankali tashe tana mai cigaba da marin fuskar Bir tare da faɗin Jarumi.
Dasauri suka mike su duka biyun har suna gware da juna wurin tashi, tukun Mauzum yay maza yaje ya ɗauko ƙwaryar da take cike da ruwa tare da kofi acikin ta yana mai zuwa ya ajeta agaban Iyar Bayi.
Dasauri ta sanya hannu ta É—auki moÉ—ar dake cikin ruwan tana mai kwaso ruwan da shi, tsiyaya sa tayi atafin hannun ta, tukun ta yarfawa Bir shi akan fuska tana mai cigaba da kiran sunan sa.
Ajiyar zuciya ya fara saukewa akai-akai yana mai lumshe idanuwan sa.
Hakan da Iyar Bayi ta gani ne yasan ya ta sa hannu ta ɗago kansa, tukun ta ɗora masa moɗar ruwan akan laɓɓa tana mai faɗin. "Sha ruwa Jarumi na."
Bai musa mata ba ya buÉ—e bakin sa ruwan ya fara wucewa da sauri da sauri.
Tas ya shanye ruwan yana mai buɗe idanuwan sa, sake maida moɗar ruwan tayi cikin ƙwaryar ta ƙara kamfato sa, tukun ta ƙara ɗora masa akan baki ya shanye sa tas.
Sannan ya sake maida kansa kan cinyar Iya yana mai lumshe idanuwan sa.
"Shin sai yaushe ne zake dena shigewa Gimbiya Jarumi? Kullum abun da nake gudar ma kenan amma ko kaɗan bakaji, to yanzu wagari ya waya kenan, gashi kuma kasan Jibi ne bikin ranar zagayowar godiya ga abun Bauta Gargabilu, amma kuma babu abun da ka tanada, ko iccen da zaka ɗauka baka tanada ba, kuma kasan ko awane irin hali kake ciki babu wanda zai yarje maka sai ka futo kaima." Iyar bayi ta faɗa tana mai bin fatar jikin sa da tayi wani irin dabbara-dabbaran baƙi da ja yarce kasan wanda ya ƙone da idanu. Yayin da shiko Bir har lokacin yake lumshe da idanuwan sa ba tare da yace mata komai ba.
Hannu tasa ahaɓar zanin ta tana mai ciro wani ƙullin tsuma, tukun ta fara kwance sa bayan ta sake matso da ƙwaryar ruwan nan gaban ta.
Ƙullikan wasu tsummokaran ne har guda biyu acikin babban ƙullin.
Ɗaukar na farkon tayi ta fara kwance sa. Gishiri ne ya bayyana acikin sa, buɗe tafin hannun ta tayi tana mai tsiyaya gishirin da yawa akan sa, tukun ta juye sa acikin ruwan ƙwaryar, sannan ta sake kwance ɗayan ɗaurin wanda yake ɗauke da garin magani acikin sa.
Shima ɗibar sa tayi ta zuba acikin ruwan, kana ta sake ƙulle su tana mai mai dasu jikin haɓar zanin ta ta ɗaure, tukun ta sanya hannun ta cikin ruwan tana mai jujjuya sa.
Kana ta tsunduma kofin nan tana mai kamfato ruwan da shi, tukun ta juye sa ajikin Bir.
Rumtse idanuwan sa yayi da ƙarfi yana mai taune leɓen sa na ƙasa, sabo da yarce ruwan yake ratsa ciwukan dake jikin sa yana kwanciya.
"Ina mai roƙon ka da abun bauta Gargabilu ka taimake ni ka kuma taimaki kan ka futa daga harkar Gimbiya, muddin baso kake muyi kukan rashin ka ba nan kusa." Iyar bayi ta faɗa tana mai cigaba da watsa masa ruwan ajiki.
Sai da ta gama sanya masa ruwan ta tabbatar da ya taɓa ko ina na jikin sa, tukun ta miƙe tsaye tana mai gyara ɗaurin baƙin ƙyallen da yake aƙugun ta, kana ta kalle su tana mai faɗin. "Yanzu ba zama zakuyi ba, ku tashi ku kama Jarumi kutaya sa yo nasa itacen ɗaukar shima, dan ko muddin bakuyi hakan ba to ni nasan wannan azabar tayau ba komai bace akan wacce Boka mai Hutar Kasko zai sa ayimasa aranar Biki." Ta ƙarasa maganar tana mai juyawa ta doshi hanyar data biyo.
"Shin har sai zuwa wane lokaci ne zaki cikan alk'warin da kika d'aukar mun ne Iya?" Bir ya fad'a da k'arfi yana mai mik'ewa tsaye, tukun ya fara d'aga k'afafuwan sa yana mai dosar inda iyar bayi take. Yayin da ita kuma Iyar Bayi ta tsaya cak ai'nda take jikin ta na matuk'ar rawa ba tare data iya furta komai ba, tukun daga bisani ta fara waige- waige tana mai duba gabas da yamma, kudu da arewa, domin taga ko akwai wani wanda yaji furucin Bir bayan su.
Sai da ta tabbatar da babu wani mahaluk'i dake wurin bayan su, tukun ta juyo inda Bir yake takowa da d'an gyashi jikin ta na tsantsar karkarwa.
"Shin mene zai sanya kayi irin wannan furucin awuri irin wannan jarumi?" Iyar Bayi ta fad'a k'asa k'asa tana mai matsawa inda Bir yake ta dafa kafad'ar sa.
"To iya s.... "Shiiiit!" Iya ta fad'a tana mai d'ora yatsa akan baki tare da zaro idanuwa, jikin ta na tsantsar rawa, yayin da shi kuma Bir ya bita da idanu yana kallon ta, tukun daga bisani ta janye yatsar ta daga kan la'b'ban ta tana mai bud'e baki ahankali tace. "Muddin baso kake in bak'unci k'asa ba ayau, to na rok'eka da abun bauta Gargabilu ka temakeni karna sake jin makamancin furuci irin wannan anan wurin."
"Amm..." "A'a Jarumi kawai kayi abun da na sanya ku, ka tafi, ka tafi kuje kufara samo icci na." Cewar iyar bayi jikin ta na tsantsar kyarma.
Yayin da shi kuma Bir ya rumtse idanuwan sa da matuk'ar k'arfi tare da taune leb'en sa na k'asa, tukun ya juya yana mai fara d'aga k'afafuwan sa ya doshi inda ya baro ba tare da ya sake cewa komai ba.
Wata irin nannauyar ajiyar zuciya Iyar bayi ta saki tana mi dafe k'irjin ta da hannu, tukun itama ta juya cikin tsantsar sauri tana mai dosar inda ta futo, har lokacin kuma jikin ta bai bar kyarmar da yake yiba.
Acan b'angaren Gimbiya Tsamir kuwa cikin zafin rai ta damk'i kan macijiyar nan da ke karkad'a harshen ta bayan ta durk'ushe agaban ta tare da rumtse idanuwan ta da k'arfi.
Tukun daga bisani ta bud'e baki cikin kaushi tana mai fad'in. "Shin meke shirin faruwa dani ce Shairama? Wane laifi nayiwa abun bauta Gargabilu da har yake shirin hukunta ni ta wannan hanyar? Kamar ni! Kamar ni!! Ni Gimbiya Tasmir har zan yiwa wani can k'as-k'antanccen bawa hukunci asa na sake sa! Shin ina k'arfin iko na ya tafi ne? Me Baba yake nufi dani ce akan wancan k'ask'antaccen banzan mara galihu Shairma?" Ta fad'a da k'araji tana mai sakin kan macjiyar ta mik'ewa tsaye.
Taku ta farayi daga inda take zuwa gaba, sai da tayi taku ya kai biyar, tukun taja tsaya tana mai sakin wasu irin numfar-fashi, kana daga bisani ta juyo tana mai dawowa wurin yashin da ta cake takobin ta ta funcike ta da matuk'ar k'arfi.