← Book details Bakar Masarauta Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 17 OF 79

Sashe 17

Bakar Masarauta Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Yawwa Bello ta, fatan kin fito lafiya." Mahaifiyar tata ta faɗa tana mai kallon ta fuskarta ɗauke da murmushi, domin kuwa ba Lamiɗo kaɗai kesan haɗin nan da za'ayi ba hatta ita tana so, sabo da aganin ta hakan shine zai sanya ɗiyar tata ta haƙura da soyayyar aljanin dake zuwar mata amafarki acewar su.

Jijjiga kai kawai Gimbiya Haddiyal tayi ba tare da tace komai ba, tukun daga bisani ta miƙe tsaye daga durƙushen da take tana mai faɗin.
"To Dadde ni zan huce."

"Tom shikenan ki tabbatar kinyi abun da ya dace, kar ki kuskura wani labari mara daÉ—in ji yazo wurin mu bayan tafiyar sa."
Mahaifiyar tata ta faÉ—a tana kallon ta.

Jijjiga kai kawai tayi tana mai jin ranta na mata wani irin suya da raɗaɗi, tukun ta juya tana mai dosar hanyar da zata sadata da waje Ƴammatan bayin nan na biye da ita abaya.

Acan kuwa ɓangaren Jauron Yamma ƙarfe shaɗaya dai dai suka ƙaraso cikin masarautar Fulɗe, da shi da mutanen sa akan dawakan su da sukaji uban Ado.
Koda suka iso kai tsaye aka zarce dasu zuwa fada suka kaiwa Lamiɗo gaisuwa, tukun daga bisani ya bada umarnin ayiwa Yarima jagora zuwa wurin da zasu haɗu da Gimbiya Haddiyal, sa'annan ya tura jakadiyar sa kan taje ta sanya afaɗawa Gimbiya Haddiyal cewar Yarima ya ƙaraso.

Dogo ne sosai mai ƙirar ƙarafan mutane, sanye yake da kayan fulani na maza, amma irin nasu na sarauta waƴan da sukayi matuƙar amsar jikin sa.
Yana da kyawun sa dai dai misali shima, yana da hasken fata duk da dai bai kasance irin farin nan tas ba. Yayin da fuskar sa kuma ta kasance aÉ—aure babu alamun annuri tattare da ita.
Tafe suke shi asaman doki, su kuma jama'ar sa da kuma waƴan da aka sa sukai sa wurin da zasu gana da Gimbiya akan ƙafafuwan su.

Wani tafkeken lambu mai cike da korayen ganyayyaki tare da ni'imtacciyar iska da inuwa acikin sa suka shiga.
Direct suka doshi inda wata shimfiɗar fata mai matuƙar taushi da kyawu take, yayin da saman shimfiɗar kuma aka ajiye tum-tum tum-tum daga kowace kusurwa, sai daga kan shimfiɗar kuma gaba ɗaya jere take da kayan itatuwa acikin wasu ƴan kwandinan kaba masu tsananin kyau, waƴan da suka haɗa dangin su ayaba, lemo, inibi, tufa, kankana, da dai sauran su, sai akusa dasu kuma wani rantsetstsen kofin silba ne ruwan zuma da yayi matuƙar haɗuwa cike danƙam da madarar shanu mai matuƙar dumi, ga kuma ɗan ƙaramin kofi na tsiyaya akife akan plate ɗin silban da babban yake akai, sai abu na gaba kuma da ya kasance dammamar fura da nono ɗauke acikin wata haɗaɗɗiyar ƙwaryar da aka sanya ludayin duma acikin ta, sai kuma fai-fain kaba da aka rufe ƙwaryar da shi, sai abu na karshe kuma da ya kasance naman kaji da ƴan shila banƙararru acikin wata ƙatuwar roba mai tsaninin kyau da ake yi mata murfi da fai-fai itama.

Riƙe dokin nasa akayi tukun ya sauko akai.
Kana wanda ya riƙe dokin yaja sa suna masu juyawa tare da sauran ƴan rakiyar duka suka bar wurin, yayin da shi kuma Yariman Yamma ya saɓule takaman fatar dake sanye aƙafafuwan sa, tukun ya hau kan shimfiɗar nan yana mai kishingiɗa akan tum-tum, kana ya ƙure hanyar da yake tsammanin tana nan zata ɓullo da idanuwa.

Zaman sa baifi da minti goma ba Gimbiya Haddiyal da tawagar ta suka ɓullo wurin.
Tunda suka bullo ya kafe ta da idanuwa daga nesa yana kallon ta bako ƙiftawa, wani irin kallo yake aika mata dashi tun daga nesa, wanda duk wanda ya gansa basai an faɗa masa ba zai san yayi nisa cikin kogin ƙaunar ta.

Cak ta tsaya a'inda take daga É—an nesa da shi ba tare da ta cigaba da takowa ba.
Tsaye suma Æ´ammatan bayin nan sukayi abayan ta cak, tukun daga bisani ta É—aga musu hannu ta sama ta baya ba tare da ta juya ta kalle su ba.

"Afuto lafiya Gimbiya." Suka faÉ—a suna masu juyawa suka doshi hanyar da suka biyo.
Ba ita ta cigaba da tafiya ba har sai da ta tabbatar da tabar jin motsin su tas, alamun sun bar cikin wurin, tukun ta fara ɗaga ƙafafuwan ta tana mai dosar kan shimfiɗar da Yariman Yamma yake kishingiɗe akai, idanuwan ta kafe ƙur akan fuskar sa kamar yacce shima ya kafe ta da nasa, sai dai ita kuma ba irin kallon da yake mata ba take masa, tana masa kallo ne na tsantsar -tsanar sa da take ji aranta tare da ƙin sa, ahaka har ta ƙarasa bakin shimfiɗar da yake kai.

Lumshe idanuwan sa yayi yana mai sake gyara kishingiɗar sa yayi balance ransa face, domin kuwa sai yanzu data matso wurin sa ya ƙara tabbatarwa da kansa lallai ba ƙaramun dace yayi ba, muddin ya mallaki wannan babbar kadarar aduniya amatsayin abokiyar rayuwar sa. Tukun daga bisani ya sake wara idanuwan sa akan fuskar ta da take cunkushe tsaye agaban sa, kana ya buɗe baki cikin yin ƙasa da murya yana mai faɗin.

"Barka da isowa Gimbiyar Jauron Yamma, Sarauniya kuma ga tsuntsaye da shanu na Masarautar FulÉ—e."
Ya faÉ—a fuskar sa É—auke da annuri.
Yayin da ita kuma taji saukar furucin sa na Gimbiyar Jauron Yamma da wani irin azabar raɗaɗi acikin ranta, tayarce har sai da ta rumtse idanuwan ta da ƙarfi tare da taune lower lips ɗin ta.
Tukun daga bisani ta warasu akan fuskar sa kamar yacce shima yake kallon ta gaba É—aya har sun fara canza launi suna yin ja.

Sannan ta tuɓe takalman da suke sanye aƙafar ta tana mai dosar kan shimfiɗar da yake kishingiɗe akai, zuciyar ta na tsantsar turiri.
Tsaye tayi agaban sa tana mai aika masa da wani irin matsiyacin kallo, tukun daga bisani ta ɗaga laɓɓan ta cikin kaushi, tana mai faɗin. "Shin wa...............✍

*HAK'IK'A INA GAB DA DAKATAWA GABA D'AYA MUDDIN BAZAKU DINGA YIN COMMENT BA.*

🐎 *BAƘAR MASARAUTA* 🐎
👑👑
🦋
🦅🕊🦆
🐍🎠🐄🏹

_*NA*_

UMAR FARUQ*D*

*BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHIM*

*PAGE 07*

"Shin waya sanar da kai wannan tatsuniyar da har kake shelantawa duniya cewar ni ɗin takace?" Ta faɗa cikin kaushi tana mai kafesa da dara-daran idanuwan ta, tukun daga bisani ta ɗora da faɗin. "To idan ma mafarki kake ina son kayi gaggawar farkwa, domin kuwa ni ɗin nan daka gani an hallice ni ne domin mutum ɗaya, haka kuma na daɗe da zamtowa mallakin sa, dan haka ina mai shawartar ka akan kayi gaggawar komawa wurin waƴan da suka aiko ka zuwa gare ni kasanar musu da cewar banyi ba, domin ko bazan taɓa yi maka ba har abada, kamar yacce kaima bakai mun ba, kuma baka da abubuwan da zanyi tinanin zakayi mun ko agaba!" Ta ƙarsahe maganar ƙasa-ƙasa tana mai jifan sa da wani irin matsayacin kallo, tukun daga bisani ta juya tana mai sauka daga kan shmfiɗar, sannan ta sanya takalmam ta, tukun ta fara ɗaga ƙafafuwan ta tana mai dosar hanyar da ta biyo ba tare da ta tsaya jin ta bakin sa ba.
Yayin da shi kuma Yariman Yamma lokaci ɗaya yana yin sa ya sauya, kana gaba ɗaya annurin dake kan fuskar sa ya ɓace ɓat, idanuwan sa kuma suka kaɗa sukai jajajir yana mai kallon ta, kafin daga bisani kuma ya buɗe baki cikin kaushi yana mai faɗin. "Shin waya baki izinin tafiya ne da har kika juya kika tafi?"

Cak Gimbiya Haddiyal ta tsaya daga inda take, sabo da furucin sa da taji ya daki dodon kunenn ta da ƙarfi, rumtse idanuwan ta tayi daga inda take ba tare da ta juyo ba, haka kuma bata cigaba da tafiya ba, sai zallar turiri kawai da take jin ranta na mata, tana mai tinanin kalar amsar da zata basa idan ta juyo.
Yayin da shi kuma ya miƙe daga kishingiɗen da yake yana mai zuwa ya sanya takalman sa, tukun ya fara ɗaga ƙafa cikin takun sa na isa yana mai dosar inda take.

Direct ya huce bayan ta yana mai zagayawa ya tsaya daga gaban ta gab da ita, tukun ya ranƙwafo da kansa yana mai rage tsayin sa ya zamto fuskar sa ta dawo saitin tata fuskar, tayarce har suke jin dirar numfashin junan su.

Kallon-kallo suka fara aikawa junan su da shi ba tare da wani daga cikin su yace tak ba, tukun daga bisani shi Yariman Yamma ya buɗe baki cikin kakkausar muryar sa yana mai faɗin. "Ke atinanin ki har akwai wani jarumin ne bayan ni aduk faɗin jahar nan da ƙetaren ta, ko ko azaton ki akwai wani mutum wanda zai iya jure raɗaɗin tsumagiya ta? Shin shi ɗin ɗan wace masarauta ne ma da farko?" Ya faɗa ƙasa-ƙasa tayarce ita kaɗai ce zata ji yana mai kafeta da idanuwan sa, kamar yacce itama ta kafesa da nata, tukun daga bisani ya saki wani shu'umin murmushin da yayi ai'nahin futo da kyawun sa, sannan ya ɗora da cewar. "Agaskiya nayi matuƙar jin daɗin sauraron wannan labarin daga bakin ki, domin ko ada ina tinanin bani da abokin karawa wanda zamu gwada ƙwanji tsakanin ni da shi wurin neman ki, amma sai gashi yau naji cewar akwai sa daga bakin ki, hakan kuwa ki sani ba ƙaramun farin ciki ya sanya ni ba, sai dai kuma ina son ki shaida masa cewar ni Yariman Yamma, tun farkon kafuwar ahalin mu ba'a taɓa yin wani wanda yay bugun shaɗi ba tare da yayi nasara ba, dan haka sai shima ya ƙara shiri akan wanda yake yi, domin kuwa ke ɗin tawace ni kaɗai, kuma an halkice kine domin n... "Dakata Malam!"
Ta faɗa da ƙarfi tana mai ɗaga masa hannu sama, tukun ta buɗe baki tana mai sakin wani irin wuci tare da faɗin. "Kar ka kuskura ka ƙara gigin furta kalmar cewar ni ɗin takace muddin baso kake na datse harshen ka ba kafun kabar wurin nan, domin kuwa wannan kalmar mutum ɗaya ne kawai ya halatta ya faɗe ta aduk faɗin duniya, kuma wallahi wallahi ni ɗin tasa ce kamar yacce shi ɗin yake nawa, bayan shi kuma babu wani agefen sa." Ta ƙarasa maganar tana mai juyawa daniyyar tafiya.
Chapter 17 · 0% Book details