Sashe 87
Zakin Saraki Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ya gamsu da hakan ya katse kiran sannan ya yi anfani da Ky din wajen ya bude ya shiga ta ciki ya rufo ya mayar da shi aljihunsa sai kuma ya ringa tahowa a hankali yana saurarawa dan a sanninsa a wajen nan akoy matar dake iya zama sarakuwarsa, watau INNA HINDU
Dariyar da kunnensa ke jiyowa da kuma hira hankali kwonce ya saka shi sake zuba idannuwansa a kanta, Auta hankalinta kwonce , dariya take yiwa Inna dake tambayar shin abinda ta yi mata kwontacen tuwo ne ko wani tashin hankali ne da galmi galmi a baki da kuma zakin madara, watau FLAN, fama take da Innar kan ta ci abinci , kwata kwata innar kwana biyu sai a hankali, ta cika damuwa a kan halin da yayarta take ciki, dan NADIRAH ba'a zancenta domin ita kiris take jira ta fashe da kuka ba kunyar kowa ta ringa haharba kafa tana fadin innar birni da aban birni
Dan murmushi ya ji yana taso masa daga kasan zuciyarsa, sai kuma ya dan koma kasa kasa ya yi salama ta yadda ya tabata zasu iya jiyo shi
Auta ce ta iya amsawa, inna kuwa ta nemi rikicewa a lokacin da ya bayana a gabansu ama ba wai ya shigo gaba dayansa bane, domin dakatawa ya yi yana kallon Auta da ta nufo shi fuskarta Kwonce da farin cikin ganninsa
A daburce Inna ta nemi dukawa kasa gaba dayanta, ta jimke hannayenta kamar dai yadda ta yi farkon haduwarsu, bakinta na neman hade kalma da kalma ta ce " Barka da warhaka Uban marayu......" Sai kuma ta kai dubanta kan NADIRAH wace tunda suka yi ido hudu da shi gabanta ya yanke ya fadi ta sada kanta tana wasa da yan yatsunta biyu tana jin yadda idannuwanta ke marmarmar sunna kokowar su sai sun kubce sun kalle shi, gangar jikinta kuwa ya kwashi wani irin kaikayin da bata san ko na meye ba, zuciyarta kuwa ta ringa wani irin dokawa har zufa ta nemi tsatsafo mata a gaban goshinta, hakan ya saka ta lumshe ido tana jin wani hawaye mai dumi yana son tarun mata a cikin idannuwanta
Inna kuwa nan da nan ta tuna da abinda suka aikata, su yan ta'ada, hakan ya saka hankalinta ya nemi tashi, kasa kasa sosai ta ce" Ke indi, kar dai hukuncin ne ya tardo mu yau laraba rana ta raba tsakiya gatse gatse za'a karmu ? Ba za'a yi hakuri a kaimu juma'a ba ko samu tsalakewaR tambayar kabari?"
A hankali ya janye idannuwansa daga fuskar Auta dake ta doka masa murmushi ya dan saci kallon Inna, a kalamanta babu abinda bai ji ba domin ba wani kwaramniya a dakin, TVma a kashe take gaba dayanta
Ba zato ya ji dariya na son fitowa daga bakinsa, a dole ya kai dubansa kan Auta ya ringa sakin dan murmushi mai sauti kadan sannan ya dauki wayar tasa ya latsa numbar Aban Birni ya karrta a kunnensa
A tausashe ya amsa salamar da Aban birni ya yi masa, sannan ya ce" Barka da warhaka Abah, ya gida, ya ibada"
Cike da jin kunya da mutunci Aban birni ya shiga gaishe shi, sai dai ASADEEK shima ya kasa amsa gaisuwar dan a ganninsa ta yi yawa, shine ya dace ya gaisar da shi haka, ama Abah ya gaza rage bashi girma har haka
Dan murmushi ya yi ya mikawa Auta wayar yana fadin" ki kai masu wayar"
Auta ba musu ta kawowa inna wayar wace ta yi tsuru tsuru baiwar Allah tana ta maimaita kalmatu shahada dan ta sabarwa harshe da fatan idan abin ya zo a fadeta dai-dai ta karbi wayar tana tambayar Aut waye? Sai dai Autar ta nuna itama bata sani ba, hakan ya sa Inna kara wayar a kunnenta a gajarce ta ce" Halo salama alaikum Hindu ce waye a ta dayan bangaren?"
Yana yar daria ya ce" Ta habu makadi kike uwar Indi ja gabar dukiyar kasan gadon karfe mai komai dozin"
Ido ta zarro, dan kuwa du duniya ta san mutun daya tak cilo yake yi mata irin kirarin nan face Aban birni, tsaye ta mike tana fadin" Ka rantse da Allah salihu ne? Wayo ni ta Habu maman Indi dama kana raye? Ina auntyn take dan girman Allah? Ina kuka shige? Kwai yana nan yana ta fashewa in fada maka Indi dai kafa ta kwasa ta je ta bude zare da abawa a gaban uban datawa, yanzu haka dai mu a hannu muke dumu dumu, ta yiwu a yanke hukunci yau......."
Sai kuma ta shiga rike harshen zani tana fyace majina da hawaye ta ce" Ko a ina kuka buya ka sanarwa Habu ni na yafe masa, ya yiwa Allah ya yafe min yan yawace yawacen da yake hannani nake yi, ina yi ne dan na dan saku da zaman da gida da kuma yiwa maneman Indi da rigima kashedin kar su taba min Ya ka ji SALIHU?"
Auta daria take yi bilhaki, ASADEEK kuwa jingina ya yi da garu ya kawar da kansa ya cije iya cijewa har sai da sansanyar muryarta ta ce" Innata wai Aban birni ne? Ce masa ga Indi bani shi mana "
A hankali ya juyo ya zuba mata lumsasun idannuwansa
Shigarta ba wata rikitaciya bace ba kuma mai kasaita bace, ama sai ta zama wata kasaitaciya a idannuwansa
Tana matukar son atampa, domin sket ne da riga na atampa a jikinta dinkin gaba daya ya bi halitar jikinta ya kawata sai daukan idannuwansa take yi
Hasken fatarta a cikin atampar mai ruwan ja ya matukar haskaka, harma kamar ta fi kulun haske ko dan ya kwana uku cir bai ganta ba?
Dariyar da Inna ke yi tana rike karkadaf da wayar a kunnenta tana sake tambayar wai Fatime ce? Ta rantse da Allah itace , NADIRAH na ja tana ja ya saka shi a hankali ya sauke dubansa a kan Auta
Murmushi ya saki yana kallon yadda Auta ke fara'a da fara'arsu , ta ce" Abahna ka raba rikicin cen fa, ba zata bata wayar nan ba, ka ga Mamah har ta dawo normal bayan kwana biyun nan ko abinci sai na yi da gaske take ci, bale Aunty sam take kin ci bayan yanzu bai dace ta ringa wasa da cikinta ba"
Bai gane manufarta ba, abinda ya fi tsaye masa a rai sunnan da ta kirayi inna da shi, Mamah..................., Sunnan ya fito daga cen kasan zuciyarta ne, kuma a saman lebenta yana bada amo ne kamar idan D'a zai kirayi mahaifiyarsa
Abinda Fatime ke sanar masu ya saka su zarro ido, sai kuma NADIRAH ta ringa tafa hannu ta juyo inda yake tsaye
Sosai magana ke saman lebenta, so ta yi ta ce da ka san inda suke, kaine ka dauke su ama ka kyale ni?, Sai dai tanaa saka idannuwanta a cikin nasa ta samu bakinta da yin nauyi, zuciyarta da bugawa, sai kuma haushin irin yadda yake bambanci da nuna mata yana sin matarsa ya taso mata, hakan ya sa ta turo baki, hadi da galawa bangon da yake jingine Harara kasa kasa ta furta" masu mata ko mema aka zo yi min dakina?"
Tsaf yake kallon lebenta, ta hakan ya gane furucin bakinta
A dole ya idasa sakin murmushinsa ya ringa neman sai sun hada ido, har dai hirar ta Inna ta ki karewa ta shige ciki tana bada bayanin abinda ya faru dala dala , wayaa kuwa kamar tana yiwa na nesa kugi du ta ware murya tana bada labarin gaba daya ta manta wayarma ta waye kuma a gaban wa take, ita dai farin cikinta ya samu da ta ji ahalinta
Shiru ne wajen ya dake dauka
A hankali Auta ta janyo hannun yayanta har falon tana nuna masa wajen zama ta ce" Abah zauna bara na kawo maka juid din da muka yi ni da Aunty"
Tana bada baya ya sake duban NADIRAH, wace ta yi saurin dauke nata idannuwan daga kansa, danma kar a wani ce kallon wani abin ne, kawai dai tana son gane kalar shadar jikinsa ne dan ta mata kyau a jikinsa sosai wollah, kamar majiya karfin filin din indiya
Murmushi ya yi ya miko hannunsa kasa kasa ya ce" Momyn Auta, asalamu alaiki"
Ido ta dan zarro, sai kuma ta dago ta zuba idannuwanta a saman hannun
Da sauri ta kallo hanyar da Auta ta bi, sai kuma ta sake kallonsa, kasa kasa tana dan matsawa kadan ta ce" Ka mayar da hannunka fan Allah kar Auta ta gani ta min wata fasarar, ba kyau gaisawa da kato fa.............."
Tahowar Auta ya saka NADIRAH saurin kara ja baya tana turo baki da kallon dariyar da ya faraa yi yana son dole sai ya bita sun yi musabaha , ita kuma tana neman labewa da sake bata fuska a dole ba zata gaisa da kato ba😌
Murmushi Auta ke yi, zuciyarta fara'a kamar zata fito ta fado daga kirjinta, sai kuma suka raka NADIRAH da kallo gaba dayansu dan a guje ta ruga ta nufi dakin da innarta ta shige tana haki
Dariya Auta ta saka tana ajiye abubuwan da ta jero ta zauna tana fadin" Abah ka korar min Auntyna....."
Shima fuskarsa yalwace da farin ciki ya ce" Ba ta hannaki cewa aunty ba? Momy ce fa?"
Ai kam Auta ta kara saka yar daria tana cewa" Abah, ai idan na ce maka aba ne take kishi, sai tace bafa ta sin bambanci, haka tace Abahna sam bata tunanin idan yana tsoron Allah, wai sai ya kirayi matarsaa a wani sanyaye ita kuma ya ce mata NADIRAH gatsau, abin nan yana bani dariya Aba, wai fa aunty kishi ne mai zafi ke fama da ita......"
A hankali ya tsare Auta da kallo, har sai da ta fahinci kallon ya yi dan yawa ta dan TAKAITA tana kallonsa
A nutse ya ce" Uman Aba, kina nufin ........., auta kina nufin wannan rigimar dan tana kishinaa ne?"
Auta na murmushi ta gyada kanta,
A hankali ya dan gyara zamansa yana dan cakude girairakinsa, kasa kasa ya ce" Ama, ana kishi idan ba'a son mutun?"
Auta ta tsayar da dubanta a saman fuskarsa, sai kuma ta dan girgiza kanta ta ce" Abah, a sanina ba kishi idan ba so"
Dariyar da kunnensa ke jiyowa da kuma hira hankali kwonce ya saka shi sake zuba idannuwansa a kanta, Auta hankalinta kwonce , dariya take yiwa Inna dake tambayar shin abinda ta yi mata kwontacen tuwo ne ko wani tashin hankali ne da galmi galmi a baki da kuma zakin madara, watau FLAN, fama take da Innar kan ta ci abinci , kwata kwata innar kwana biyu sai a hankali, ta cika damuwa a kan halin da yayarta take ciki, dan NADIRAH ba'a zancenta domin ita kiris take jira ta fashe da kuka ba kunyar kowa ta ringa haharba kafa tana fadin innar birni da aban birni
Dan murmushi ya ji yana taso masa daga kasan zuciyarsa, sai kuma ya dan koma kasa kasa ya yi salama ta yadda ya tabata zasu iya jiyo shi
Auta ce ta iya amsawa, inna kuwa ta nemi rikicewa a lokacin da ya bayana a gabansu ama ba wai ya shigo gaba dayansa bane, domin dakatawa ya yi yana kallon Auta da ta nufo shi fuskarta Kwonce da farin cikin ganninsa
A daburce Inna ta nemi dukawa kasa gaba dayanta, ta jimke hannayenta kamar dai yadda ta yi farkon haduwarsu, bakinta na neman hade kalma da kalma ta ce " Barka da warhaka Uban marayu......" Sai kuma ta kai dubanta kan NADIRAH wace tunda suka yi ido hudu da shi gabanta ya yanke ya fadi ta sada kanta tana wasa da yan yatsunta biyu tana jin yadda idannuwanta ke marmarmar sunna kokowar su sai sun kubce sun kalle shi, gangar jikinta kuwa ya kwashi wani irin kaikayin da bata san ko na meye ba, zuciyarta kuwa ta ringa wani irin dokawa har zufa ta nemi tsatsafo mata a gaban goshinta, hakan ya saka ta lumshe ido tana jin wani hawaye mai dumi yana son tarun mata a cikin idannuwanta
Inna kuwa nan da nan ta tuna da abinda suka aikata, su yan ta'ada, hakan ya saka hankalinta ya nemi tashi, kasa kasa sosai ta ce" Ke indi, kar dai hukuncin ne ya tardo mu yau laraba rana ta raba tsakiya gatse gatse za'a karmu ? Ba za'a yi hakuri a kaimu juma'a ba ko samu tsalakewaR tambayar kabari?"
A hankali ya janye idannuwansa daga fuskar Auta dake ta doka masa murmushi ya dan saci kallon Inna, a kalamanta babu abinda bai ji ba domin ba wani kwaramniya a dakin, TVma a kashe take gaba dayanta
Ba zato ya ji dariya na son fitowa daga bakinsa, a dole ya kai dubansa kan Auta ya ringa sakin dan murmushi mai sauti kadan sannan ya dauki wayar tasa ya latsa numbar Aban Birni ya karrta a kunnensa
A tausashe ya amsa salamar da Aban birni ya yi masa, sannan ya ce" Barka da warhaka Abah, ya gida, ya ibada"
Cike da jin kunya da mutunci Aban birni ya shiga gaishe shi, sai dai ASADEEK shima ya kasa amsa gaisuwar dan a ganninsa ta yi yawa, shine ya dace ya gaisar da shi haka, ama Abah ya gaza rage bashi girma har haka
Dan murmushi ya yi ya mikawa Auta wayar yana fadin" ki kai masu wayar"
Auta ba musu ta kawowa inna wayar wace ta yi tsuru tsuru baiwar Allah tana ta maimaita kalmatu shahada dan ta sabarwa harshe da fatan idan abin ya zo a fadeta dai-dai ta karbi wayar tana tambayar Aut waye? Sai dai Autar ta nuna itama bata sani ba, hakan ya sa Inna kara wayar a kunnenta a gajarce ta ce" Halo salama alaikum Hindu ce waye a ta dayan bangaren?"
Yana yar daria ya ce" Ta habu makadi kike uwar Indi ja gabar dukiyar kasan gadon karfe mai komai dozin"
Ido ta zarro, dan kuwa du duniya ta san mutun daya tak cilo yake yi mata irin kirarin nan face Aban birni, tsaye ta mike tana fadin" Ka rantse da Allah salihu ne? Wayo ni ta Habu maman Indi dama kana raye? Ina auntyn take dan girman Allah? Ina kuka shige? Kwai yana nan yana ta fashewa in fada maka Indi dai kafa ta kwasa ta je ta bude zare da abawa a gaban uban datawa, yanzu haka dai mu a hannu muke dumu dumu, ta yiwu a yanke hukunci yau......."
Sai kuma ta shiga rike harshen zani tana fyace majina da hawaye ta ce" Ko a ina kuka buya ka sanarwa Habu ni na yafe masa, ya yiwa Allah ya yafe min yan yawace yawacen da yake hannani nake yi, ina yi ne dan na dan saku da zaman da gida da kuma yiwa maneman Indi da rigima kashedin kar su taba min Ya ka ji SALIHU?"
Auta daria take yi bilhaki, ASADEEK kuwa jingina ya yi da garu ya kawar da kansa ya cije iya cijewa har sai da sansanyar muryarta ta ce" Innata wai Aban birni ne? Ce masa ga Indi bani shi mana "
A hankali ya juyo ya zuba mata lumsasun idannuwansa
Shigarta ba wata rikitaciya bace ba kuma mai kasaita bace, ama sai ta zama wata kasaitaciya a idannuwansa
Tana matukar son atampa, domin sket ne da riga na atampa a jikinta dinkin gaba daya ya bi halitar jikinta ya kawata sai daukan idannuwansa take yi
Hasken fatarta a cikin atampar mai ruwan ja ya matukar haskaka, harma kamar ta fi kulun haske ko dan ya kwana uku cir bai ganta ba?
Dariyar da Inna ke yi tana rike karkadaf da wayar a kunnenta tana sake tambayar wai Fatime ce? Ta rantse da Allah itace , NADIRAH na ja tana ja ya saka shi a hankali ya sauke dubansa a kan Auta
Murmushi ya saki yana kallon yadda Auta ke fara'a da fara'arsu , ta ce" Abahna ka raba rikicin cen fa, ba zata bata wayar nan ba, ka ga Mamah har ta dawo normal bayan kwana biyun nan ko abinci sai na yi da gaske take ci, bale Aunty sam take kin ci bayan yanzu bai dace ta ringa wasa da cikinta ba"
Bai gane manufarta ba, abinda ya fi tsaye masa a rai sunnan da ta kirayi inna da shi, Mamah..................., Sunnan ya fito daga cen kasan zuciyarta ne, kuma a saman lebenta yana bada amo ne kamar idan D'a zai kirayi mahaifiyarsa
Abinda Fatime ke sanar masu ya saka su zarro ido, sai kuma NADIRAH ta ringa tafa hannu ta juyo inda yake tsaye
Sosai magana ke saman lebenta, so ta yi ta ce da ka san inda suke, kaine ka dauke su ama ka kyale ni?, Sai dai tanaa saka idannuwanta a cikin nasa ta samu bakinta da yin nauyi, zuciyarta da bugawa, sai kuma haushin irin yadda yake bambanci da nuna mata yana sin matarsa ya taso mata, hakan ya sa ta turo baki, hadi da galawa bangon da yake jingine Harara kasa kasa ta furta" masu mata ko mema aka zo yi min dakina?"
Tsaf yake kallon lebenta, ta hakan ya gane furucin bakinta
A dole ya idasa sakin murmushinsa ya ringa neman sai sun hada ido, har dai hirar ta Inna ta ki karewa ta shige ciki tana bada bayanin abinda ya faru dala dala , wayaa kuwa kamar tana yiwa na nesa kugi du ta ware murya tana bada labarin gaba daya ta manta wayarma ta waye kuma a gaban wa take, ita dai farin cikinta ya samu da ta ji ahalinta
Shiru ne wajen ya dake dauka
A hankali Auta ta janyo hannun yayanta har falon tana nuna masa wajen zama ta ce" Abah zauna bara na kawo maka juid din da muka yi ni da Aunty"
Tana bada baya ya sake duban NADIRAH, wace ta yi saurin dauke nata idannuwan daga kansa, danma kar a wani ce kallon wani abin ne, kawai dai tana son gane kalar shadar jikinsa ne dan ta mata kyau a jikinsa sosai wollah, kamar majiya karfin filin din indiya
Murmushi ya yi ya miko hannunsa kasa kasa ya ce" Momyn Auta, asalamu alaiki"
Ido ta dan zarro, sai kuma ta dago ta zuba idannuwanta a saman hannun
Da sauri ta kallo hanyar da Auta ta bi, sai kuma ta sake kallonsa, kasa kasa tana dan matsawa kadan ta ce" Ka mayar da hannunka fan Allah kar Auta ta gani ta min wata fasarar, ba kyau gaisawa da kato fa.............."
Tahowar Auta ya saka NADIRAH saurin kara ja baya tana turo baki da kallon dariyar da ya faraa yi yana son dole sai ya bita sun yi musabaha , ita kuma tana neman labewa da sake bata fuska a dole ba zata gaisa da kato ba😌
Murmushi Auta ke yi, zuciyarta fara'a kamar zata fito ta fado daga kirjinta, sai kuma suka raka NADIRAH da kallo gaba dayansu dan a guje ta ruga ta nufi dakin da innarta ta shige tana haki
Dariya Auta ta saka tana ajiye abubuwan da ta jero ta zauna tana fadin" Abah ka korar min Auntyna....."
Shima fuskarsa yalwace da farin ciki ya ce" Ba ta hannaki cewa aunty ba? Momy ce fa?"
Ai kam Auta ta kara saka yar daria tana cewa" Abah, ai idan na ce maka aba ne take kishi, sai tace bafa ta sin bambanci, haka tace Abahna sam bata tunanin idan yana tsoron Allah, wai sai ya kirayi matarsaa a wani sanyaye ita kuma ya ce mata NADIRAH gatsau, abin nan yana bani dariya Aba, wai fa aunty kishi ne mai zafi ke fama da ita......"
A hankali ya tsare Auta da kallo, har sai da ta fahinci kallon ya yi dan yawa ta dan TAKAITA tana kallonsa
A nutse ya ce" Uman Aba, kina nufin ........., auta kina nufin wannan rigimar dan tana kishinaa ne?"
Auta na murmushi ta gyada kanta,
A hankali ya dan gyara zamansa yana dan cakude girairakinsa, kasa kasa ya ce" Ama, ana kishi idan ba'a son mutun?"
Auta ta tsayar da dubanta a saman fuskarsa, sai kuma ta dan girgiza kanta ta ce" Abah, a sanina ba kishi idan ba so"