← Book details Zakin Saraki Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 84 OF 99

Sashe 84

Zakin Saraki Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Zuciyarta cike da zafi da kunna a sanyaye ainun ta ce" Allah zai saka maki, Allah zai sakawa Yayanki, ba ku kadai ba Allah zai saka mana muma da ta sako mu a layin ta'adanci, Allah zai sakawa du wani wanda ta cutar, koda ta samu tsiratar da kanta a wannan karron zata hadu da nata gamon , domin tana wasa da hakin da Allah baya yafewa, hakin wani a kanka Allah baya gafarta shi, idan kuwa sakankancewarta ya saka bata gane furfurar kanta da janyewar fatarta da da yanzu ba lalle a kireta mahaukaciya, bata da hankali, ta kuma tabe, wannan mata na ajiye makaman fadana da ita, wannan mata Allah ne zai yi maganinta, wannan mata bama tunanin mutuwama zata zamo mata aya, irinsu su rayu sunna gannin rayuwar ta zame masu ukuba ya fi, irinsu ya dace su jima sunna kallon lamarin ubangiji gannin idannuwansu, wannan mata sai ciwo ya koya mata hankali, wannan mata sai tsufa ya koya mata hankali, Allah ya sa wannan mata ta maimaita shekarun da ta yi a duniya sau biyyar ta yadda zata ringa ihun kiran mutuwa da tunanin shin ita mutuwar ta manta ne?, Ta yadda zata bar duniyar da abinda take cikinta ba tare da ta mutu ba! Tabas wannan matar la'ananiya ce wace bata jin tsoron Allah, munafuka ce ita kuma azaluma ce, ki yi hakuri AUTA, ko me ta yi maki Allah zai warware maki kin ji?"

Sosai Auta ta ji sanyi a zuciyarta, sosai ta ji bakinta ya bude, har zuciyarta ta cika da mamakin dama itama zata iya bude baki ta saki damuwarta haka wani ya saurara?

Kusan a nan suka wuni, abinci da sallah ke tashinsu, kiri kiri NADIRAH kuwa ta labe a daki ta ki fitowa, da farko kuka ta sha da tunane tunanen da ba zasu gyarata ba, daga baya ta rike carbi tana Adu'ar Allah ya bayana mata iyayenta cikin aminci da lafiya, in sha Allah zata zauna da shi idan ya nemeta dan ta ji yaya za'a yi ya barta ta je neman iyayenta, domin ba zata iya zama bata neme su ba fa, sai dai ya yi hakuri idan ta gansu ya yanke hukuncin dake gyara shi a kanta!

A bangarensama, sun cika dare sosai da SHEIK a bangarensa, domin a dawowarsu kusan magariba sai da ya bada damar shigowar UMMA , wace kana kallonta zaka ga bata tare da nutsuwa ko kadan, a yanzu ta saka alkyabar ama gaba daya tamkar an tonota daga cikin rami, domin kana ganninta zaka ga tsantsar tashin hankali da firgici a tatare da ita

Sosai ta gabatar da rainin wayonta, da su koke koken yanzu yaya za'a yi ba'a ga bafansa da gimbiya ba, shima ya nuna mata tsantsar tashin hankali da sheda mata yanzuma daga Tanut din suke an baza dukkan jami'an tsaro ana nemansa, sannan an dora Huzaifa kujera kafin a ganshi
A nan mamaki da tarin tambayoyi suka so zautata, me ya kawo HUZAIFA SOJA saman karagar mulki bayan ga ya'yansa maza manya? Ita fa, haukacewar da ta kusan yi wai jin an sace su, waye ya sace su? Ina suke? Ta zata abin wasa ne kamar yadda suka tsara ne sai ta nemi wayoyinsu ta rasa, karshema baban yaronsa ya sheda mata hankali tashe cewar an fa sace su, kamar ledar piya wata jama'a?, Mutane uku rigis kuma ba'a ga wanda ya dauke su ba? A haka ta koma tana tsantsamce da kowa, domin tana tafe tana waige waige da kame kanta dan kar aje itama a ritsa da itan, wanda ya sace sarki da matarsa da yarsa ta yiwu harda ita a layi, tana shiga bangarenta ta garkame ta kori kowa, sai a lokacin ta yi arba da madarar UMUGHLUK ITIBEL, wace ta yi baki kirin sakamakon maganin gubar da ta sauye baki daya
Hankalinta ne ya sake tashi, ta je garin neman rarumar jug din ta barar da shi ya fadi kasa, ji kake tartsatsa ya fashe gaba daya madarar da maganin suka bare nan kasa
A wajen ta zauna tana hade jikinta tamkar wata karamar yarinta tana yarfe hannayenta bayan ta tuge dan kwalin kanta tana ta wani abu kamar sabin kamu a rikice gaba dayanta ta ce" Na shiga uku, na barar da maganin gana daya, yanzu wa zai samo min wani?, Kai kuma dan Allah ka taimaka ka kirayeni ka ce min kun buyan ne ya sa ake tunanin sace ku aka yi, idan ba haka ba ina zan shiga da faduwar gaba da tsoro a cikin masarauta?, Waye ya sace ku? Me kuka yi masa? Idan ASADEEK ya gane ba ku kuka haifi wancen yar banzar ba yana iya tisoni a gaba fa?, Idan ya tambayeni me zan ce masa bayan ya san na san yarku? Wayo na shiga uku menene wannan tashin hankalin dake nufo ni, komai na kasa ganewa gaba daya komai sai shige min yake yi a cikin junna?, Wayo na shiga uku ..................."

Da wannan suka cika dare shi da SHEIK sunna sake tataunawa a kan hanyoyin da zai bilowa wasu abubuwan

*NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼*

°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°
```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.```
°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°

*https://www.facebook.com/106494781436168/*

🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻
*OUMOUGHLOUK ITIBEL*
_(ZAKIN SARAKAI)_
🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻

_FREE BOOK_

*Na*

*SAJIDA NIGER*

6️⃣1️⃣

Sai kusan karfe tara da wani abu SHEIK ya tafi, shima ba dan sun gama ba, sai dan su hau kan tsarinsu na gaba, wanda SHEIK din ne zai gabatar da binciken lokacin da zasu iya dauke babbar jakadiyarta a kwana kusa, dan basa so a firgicinta da faduwar gabanta ta samu sasauci ko na second daya

Alwallah ya daura bayan ya yi wanka ya haye salaya, so yake yi zuciyarsa ta yi sanyi, so yake yi ya samu nutsuwa irin wace babu wanda ya isa ya bashi sai ubangijinsa
Sai da ya kai kusan karfe biyun dare yana ibada, sannan ya mike ya karasa wajen kwonciyarsa, ya yi adu'ar barci ya kwonta yana rungume hannayensa a samn kirjinsa, a sanyaye ya lumshe idannuwansa yana jin nutsuwa da sabon tunani a kan matsalolinsa sunna ta shiga kwakwaluwarsa, a cikin tarin dacin da yake ciki sai ya ringa hango sauki , saukin nan kuwa ba komai bane face wani haske da ya shigo kwakwaluwarsa, hakan ya saka shi sakin dan murmushi yana jin abin har cen kasan zuciyarsa, har kamar abin na son ya saka shi jin babu dadi dan baya gefensa, ba komau bane face NADIRAH, zai iya cewa gwadama da suka bashi mace a lokacin da baya tunanin samu....... Zai iya cewa gwadama da suka cenza masa da Soul mai daraja, daya tak da bai hado irinta a kusa ba, idannuwansa ya lumshe a saman lebensa kadan kadan ya ce" TUZURUWAR kauye, ya dace a bar maraya ya huta, tunda ba za'a zo inda nake ba............a bar tunanina ya huta ko?"..................................................... Cike da begen nan a kasan zuciyarsa ya samu barci mai dadi, mai kuma nauyi, dan kuwa sai da kiran sallah kusan karewa ya jiyo a kunnayensa

____________________________________

Washe gari

A ranar wunin da aka yi, an yi shi ne cikin tarin taro na jama'a, ya wuni a fada ne cirrrrrr ba sasautawa, domin baki ya ringa samu ta ko'ina masu tafe da son sannin maganar da ake shelawa ko gaskiya ce?, Da jajantawa, asalima sakonsa na aiken da ya yiwa sarkin yanka sai da yamma suka kadaice ya sanar masa , sannan ya samu ya sake fita ta sirri ya je ya ga bakinsa da ya kilace idan har sun fara gane sun shiga uku ko da saura? Ai kam ya tarar da su ba yadfa suke, madubi ne da shi yana iya ganninsu tar tar, su kuwa basa gannin komai, a lokacin da ya je ya same su Bahija na zaune tana kallon waje daya, fuskarta ta yi jajajir tamkar wace ta sha duka, ita kuma kuka ne ta sha kamar ba gobe, iyayenta kuwa mahaifinta yana tsaye yana ta kallon wutacen dakin, ita kuma mahaifiyarta tana kwonce ta dukunkune cikin alkyabart , ga dukkan alamu ita rashin shayin tuni ya fara kaita makura

Bai ce komai ba ya yi tafiyarsa bayan ya sheda masu kar su rasa abinci ko abin sha, shayi kawai za'a hanna masu

Yana komawa bangarensa ya tarar da tsare tsare irin na mata masu daraja,
Watau aiki irin na mace mai kishin mijinta
An cenza masa su cafet labulaye, komai dai hajia uwar gida ran gida mai girma HUZNAH abincin ruhinsa tana kai kawo sai baza kanshi take yi ta kuma dauki kwaliya daidai gwargwado, duda tana fama da kayan alkyaba, ama kuma tsarin shigarta dake kasa tamatukar kawatar da idannuwansa ta tarbe shi da kula da kauna ta rakashi har dakinsa sannan ta koma falo cike da farin ciki, a zuciyarta tana ayyana ko me take tunani ta fi ta, domin ba zata taba gwada mata kula da mijinta ba, zata ga aikin soyaya ba nata na shirme ba, za kuma ta ga ko tana yar uwarsa ita din ta fita tunda soyaya ce tsakaninsu da aminci, du abinta bakuwa take a cikinsu ta yi biyaya ko ta gaza gane komai, ita dai babu Wanda ya isa ya fit sannin wanene mijinta!

Koda ya sauko cin abinci ya ringa binta ne da kallo mai cike da tausayi da tausasawa

A lokacin da take zuba masa abincin da ta bata lokaci tana daahuwarsa , a tausashe ya dora hannunsa saman nata ya sakar mata da murmushi a hankali ya ce" Ya isa haka HUZNAH ko so kike na gaza barci ciki ya cika sosai?"

Murmushin ta sakar masa itama tana sada kanta, a nutse ta ce" Allah ya taimakeka, idan ka gaza yin barci ai na bani, gwara na bari haka din"
Chapter 84 · 0% Book details