← Book details Zakin Saraki Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 40 OF 99

Sashe 40

Zakin Saraki Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Karbi nan, na ce dambulaninki Indi zo nan dan ubanki na gagaura make mari, so kike a shake mu muna ihu har mu daina? Zo nan" HINDU ta fada tana rarumar abu ta mike dan ta shako Yar...........

Mun shiga uku☹️☹️☹️☹️

*NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼*

°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°
```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.```
°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°

*https://www.facebook.com/106494781436168/*

🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻
*OUMOUGHLOUK ITIBEL*
_(ZAKIN SARAKAI)_
🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻

_FREE BOOK_

*Na*

*SAJIDA NIGER*

2️⃣7️⃣

Ba edditing

NADIRAH ta yi tsuru tana kallon Innarta, da Umma dake salalami ta kasa tsayuwa a waje daya

Innarta ta sake kallon Umma, sannan ta kallo NADIRAH ta ce" Yar gidan Habu makadi ki zo ko na zo?"

NADIRAH ta sake shagwagwabe fuskarta ta ce" Innata, gani na yi magariba ta shigo, kafin mu karasa ai ta yiwu kuma ya shiga barci dan ai baba baya jira barci na iya daukansa koda yaushe ko Innata?"

Hindu ta karra tafa hannu tana sumurtu, lokaci daya ta dage zanninta ta haura shi saman ciki sannan ta nemi tsalaka kujerar dake tsakaninta da Nadirah

Ido NADIRAH ta zarro, ta sake kallon innarta

Da gudu NADIRAH ta fala cikin dakinta ta rufo harda saka Ky sannan ta karasa wajen kujera ta zauna tana sauke numfashin gudun da ta sha sannan ta dan tsurawa waje daya ido tana dan balancing din kafafuwanta

Samun kanta ta yi da mikewa ta karasa gaban madubi ta dan rankwafa kadan tana daure gashin kanta a baya

Dan murmushi ta yi tana girgiza kanta kasa kasa ta ce" Amarya , Amarya ce, koda ta auren dole ce, koda ta karkara ce, in ba abinka ba baban su Inna ai mu mutanen karkara mun fi kowa riko da al'adu, a gida ba mace ke fara zuwa wajen miji ba, koda sarki ne, kasancewarka bako koda wanene kai ba shi zai saka a kwasheni a kaini gaisheka ba....., Duda ba maganar fahimtar junna ko tare yawun tsufa zan yi ba, ama a ji labarin nan a labba ai na fadi ba nauyi, Idan har da rabon mu gaisa zamu gaisa in la zo nan da kanka Babansu" ( kuturu🫢🫢🫢 abinda kike shiryawa kennan? Lalle kin traro match)

A falo kuwa zaman dabar Innarta ta yi tana salati tana sanar da ubangiji tana kallon Umma ta rasa me zata ce mata

Umma ta dafe kai itama da takaici ta ce" Ta kula, ta ajiye shirme da yarinta da wasan dake dawainiya da ita, ta ringa bambance baba da kuma dan gidan baba, ki fahintar da ita shi din baba ne, ba maganar wargi tsakaninsa da matarsa, ko waye ba zai rainashi ba, koda matarsa ce shi din sarkinta ne!"

Hindu sai ta samu kanta da jin maganar wata iri, ko matarsa ce shi din sarkinta ne? Toh mutane, yo ai itama da ta tsorata dan Indi bata riga ta zama matarsa a aikace bane, da hakan ta faru ai tana gannin abu ne daka iya faruwa tsakanin mata da miji ko? Ama yaya Umma ke dan so ta nuna kamar Indi ta yi sabo?

Umma ta dora da fadin" Bale a gaban kishiya take, matar da ta ci hakuri ta kora da ruwan zurra ido,matar nan ni na tabata hakurinta zai kasheta wata rana, kin kuma san maza na masifar son macen da sai yadda suka yi da ita ko?"

Hindu ta karra yin tsuru, ita Umma na magana ne ira tana aunawa a kankin kanta, Allah ta tuba ita din nan karan kanta maganar ba wata ji take yi ba, tsakaninta da Habu wani lokacin sai ta zo barci take lalabawa ta tashe shi a yi zaman tsakiyar dare a yi magana a yafewa junna, bama idan wata ya raba tsaka ya zama tulelen nan, takan ji komai a fili yake Alkur'an, takan bashi hakuri shi kuma yakan ce in bai yafe mata ba ai shi zai shiga uku dan idan ta tire daga yadda take yanzu ta yiwu a mata sarauniyar makada......., Gaskiya a nan tana iya cewa Umma kamar ta yi daya, wasu mazan ai a lokacin da kika zama sai yadda suka yi da ke din nema suke cin kaniyarki, Allah mun tuba a rayu da tunnanin za'a mutu kawai, in ba shi ba ai har a dambatu da makocin raba gado

Umma ta ci gaba da fadin" Mema ya hada fatarta da girki?, Ina ita ina aikin da aka zuba mata bayi dan su yi mata? Wanka kansa bai dace ta yi da kanta ba, ya dace ta dauki girman dake kanta fa, bana son abinda zai zamo tsegumi da tsuguri tsoma a cikin bayi, bana so kuma wancen ta yi tunanin ta samu hanyar da zata iya shiga tsakaninta da UMUGHLUK, uwa uba shi din da kansa idan ya fuskanci akoy maganar raini sai ya tsireta walahi!"

A zabure HINDU ta zarro ido , lokaci daya ta ce" In sha Allahu Bama za'a kai cen ba, yanzun ma sharin shedan ne, yar da bata cewa komai? Yar mai tsantsar biyaya? Na tabata rashin fahimta ne, yau zan kwana ina fada mata kuma zata dauka, a yafe mana ba zamu kuma ba"

Umma ta tabe baki tana sauke ajiyar zuciya, tabas yarinyar nan kamar ta mata ila ita din da kanta, a tunaninta yau da wata ce daban ta aikata haka ba wace take ji har kasan zuciyarta ba, da bata san abinda zai iya faruwa ba walahi!

Juyawa ta yi tana fadin" Zan koma bangarena kafin ya gama sallah na koma na bashi hakuri"

Inna ta gyada kai tana kallonta har ta bacewa ganninta

Tagumi ta rafka tana sake kiran sunnan yarta da fadin gwara ta bude kofar nan su fuskanci junna , ita kuma ta yi shiru ta ki fitowar, domin a muryar Innarta tana gane bata sauko ba, idan ta sauko sa yi maganar
Bayan sallar isha'i da kyar Umma ta samu komawaa domin baki ya yi a irin lokacin, sai dai tama zuwa ta sha mamakin gannin Auta har yanzu bata tashi ba

Zama ta yi ta shiga gabatar masa da lamarin ta fuskar rarashi da ban baki, ta karashe da fadin sakon sam na daga wajen sarauniya ya fito ba, wata kula kula ce, in sha Allah tana kan bincike dan ba zata yarda a fara kawo wargi a gaban danta ba

Murmushi ya yi yana basar da maganar, sannan yana karra gannin girman Umma a zuciyarsa, domin irin yadda take tsaye a kan lamarinsu ko iyayensa sai hakan, shi fa tausayinta yake ji baiwar Allah, ya tabata yakinta na ta kawo yarinyar cen gabaansa ba komai bame sai dan ta samu yan jikoki abinta, baban mafarkin Ummansu ta ga yan magadan sa, bata san shi bama zai kwatanta wani abu da yarinyar ba bale har ya dauki wani nauyim zuciyar, kai shi koda ya warke gaskiya da wahala ya tara zuri'a da yarinyar, dan sam bai ga tarbiya a tare da ita ba, irin yadda ta nuna din nan a saudiya ta bashi mamaki, bai taba tunanin akoy irin haka a hausa ba, abu kamar rainon arne? Sai da intacen bawansa ya daka mata tsawa fa a lokacin da ta ga dakinsa ido rufe ta nemi kutsawa da neman fado masa a jiki, bata san ba gidan ta samu ba, yanzu da wani lalatacen ne shikenan ta fado gidan sauki zai murjeta son ransa a bagas, ita a tunaninta soyaya ce sai ya bace mata batttt, kai shi yauma zai kunna wayarsa da ya bata layin, dama bai kunna bane saboda so yake ya huta sosai saboda abokan kasuwanci, layinsa ne sanane wa yan kasuwa kadai,

Umma ta yi murmushi tana kallon Auta ta ce" Babyna kin yi sallah kuwa?"

Auta ta dago a dan tsorace, dama tunda ta ga Ummar hankalinta ya kasa kwonciya ta tabata sai ta mata fadan ba ta hannata jimawa wajen Aba ba

Da sauri ta gyada kanta, sai kuma ta bude bakinta dake dan rawa ta ce" Dama harda ce zan yiwa Abah, shine, shine na jima"

Umma ta yi gagawar tareta dan karma ya saka wani abu a ransa ta ce" Aa ai karatu ba komai Auta, dama bana so kina jimawar ana ta hira kuma ki je baki samu isasshen barci ba , hakan na taba lafiyarki, idan kin gama yanzun tashi mu tafi na gyara maki komai ki sha maganinki ki kwonta"

Auta ta budi baki har tana dan hardewa ta ce" Ummah, ban gama ba, dama so nake na yin, kuma na sha maganin a gaban Aba yanzu ko Aba?"

Daga rubuce rubucen da yake ya dan dago ya gyada kansa, sai kuma a takaice ya ce" Zan rakata idan ta yi Umma"

Dan zuba masa ido ta yi ta ga hankalinsa ya dauku a abinda yake rubutawa
Wani irin harara ta watsawa Auta sannan ta yi kwafa ta mike ta yi masu sai da safe harda jadada a yiwa Auta addu'a fa idan zata kwonta

Bayan tafiyar Umma Auta ta jima tana kallon waje daya fuskarta na nuna alamun she is sad

Sai kuma ta sake tino maganar dazu

Ita abin ne ya sakata dariya ba dan komai ba sai tino maganar mahaifinsu da in dai yan tsokanarsa suka motsa ya kama adabar mhaifiyarsu da maganar kennan, a kan rikicin da suka sha tsakaninsa da ita dan aurwn hadi ne su a lokacin, kuma ita mahaifiyar tasu itace Auta, ya zamto tsaf take cewa ba zata je gaishe shi ba gaskiya ta gaji, shi kuma a lokacin eh lalle an bashi mata ne, ama farat daya ya ji du duniya ta masa iya yi, haka yake sabo babar rigarsa shi ya je ya gaishetan, ko ba komai ai halal ne, to mahaifin nasu ke anfani da haka ya yi ta tsokanar mahaifiyarsu ita kuma tana sinne kai tana dariya, summa sunna shaan dariya da mamakin wai du girman sarauta irin ta mahaifinsu dama zai iya aikata haka? Zai iya tashi da kansa ya tarda iyalinsa? Kwarai so wani abin ne mai girma

Kara sakin murmushi mai sauti ta yi, wanda ya saka yayanta dagowa da dan sauri ya tsura mata ido yana dan kallonta da byron dake hannunsa
Chapter 40 · 0% Book details