← Book details Zakin Saraki Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 80 OF 99

Sashe 80

Zakin Saraki Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Dan murmushi ya yi dan sarai ya gane so take ta ji BAHIJA yace ko NADIRAH, ya rab ya so ya jima yana tsokanarta da haka, sai dai gaba daya ji yake yi bashi da karfin yin haka kwata kwata, yayama zai iya yin haka dogon zango bayan kuka take yi da hawayenta? Bai ce ba zata iya yin kuka ba a rayuwa, ama ba zai so ace shine sanadiyar hakan ba, a tausashe, dan ya tabbatar mata eh ya san me ya fada ya sake maimaita sunnanta idannuwansa a cikin nata

Ido ta zarro, gudun zuciyarta ya dadu, da sauri ta nuna kanta da yaren bebanci ta ce" A san ice Indi?" (Ka san nice Indi?)
Ita da kanta bata san ta iya yaren bebaye ba sam

Murmushi ya yi ya gyada kai, a hankali ya ce" Na san ke ce Indi, na kuma san kece yar gidan INNA HINDU, da BABA HABU, da inar birni fa kuma Aban Birni"

Kirjinta ta dafe, sai kuma ta yi saurin zarro ido, da sauri ta silalo kaffafuwanta ta mike haihuwar Innar birni ta nufi bayi da gudu halitun bayanta na auka sittin saba'in, hakan ya saka shi zarro idannuwa ya sake zubawa kofar da ta bude ta bari a bude ido yana sauraron zubar fitsarinta a cikin WC har ta gama yana jiyo zubar ruwa da wankewarta ta gama ta fito yanzunma a kidime jama'a ta kasa tuna a yaya take tsaye a gabansa ta yi tsaye ta rike gugu, ko iskar sanyin AC bai ankarar da ita cewa mikowar ingozoma take ba, hankali kwonce ta masa tsaye da bindigun kirjinta ta shiga bayani tana kai kawo irin na oga a office , ko hamshakin da yake yin bayanin da yake so a fahimta, kuma a haka take so ya fahimta , ta yi ya kai sau uku tana masa zannen da ya jima da sani watau wacece imnar birni, waye aban birni da na kauye sannan ta juyo ta ce" Wata rana ne, muna zaman zamanmu, mun gama yin fada da Aminu fa innarsa , innarsa ta leta rantsuwar ba zata yarda da aurenmu ba, na cewa tawa innar ta yi hakuri zan hakura idan ta sheka lahira ko mun tsufa ne ba komai sai mu yi aurenmu, sai kawai innata ta ce zata zo birni da ni wajen bikin kawarta da ta haihu, nufinta kafin mu koma na huce sai mu yi zamanmu, ashe ashe harda nufinta ta ji kishi kishin din za'a yiwa Aminu suren dole da wata yar gidan ladan dake sonsa, kai dai wannan shine farkon shigarmu tashin hankali mai zaman kansa, domin a zuwanmu birni ashe marabinmu da kauyen LABBA kennan, muna zuwa muka tarar da ........"

"Ke, dakata min, idan kika kuma ambaton sunnan wani kato a gabana NADIRAH, zan karra nuna maki nima kato ne, kuma dukkan abinda yake iya baki ina iya baki shi , koma fiye da hakan malama!" Ya fada a kausashen da bata taba ganninsa ya yi ba, bayan ya mike daga saman gadon fuska a hade harda su nuno mata hannu, domin yana cikin binta da kallo ido na masa radadin tashin hankali ta wani katse masa farin ciki da sunnan wani kato, wollah kamar ta wanka masa mari ya ji

Ido ta zarro ta juya ta ce" Baka da sutura fa "

Goshinsa ya dafe dan takaici , jama'a ita tanada ita ne? Gaba daya so take yo ta caza masa kwakwaluwa bayan ana abun arziki
Muryarsa da amon bacin rai ya ce" Juyo min nan ki ji, a hirarki idan kika saki kika ringa sako min maganar wannan shedanin mai bin zuciyar mace gidan miji sai na babala maki du abinda na warto, kuma sai na wuni a kanki a dakin nan yau koda mayar da ke zan yi kamar tsohon zani sai dai a dinke ki kamar kwarya!, Aminun da kike hauka kansa yana cen mata biyu innar tasa ta aura masa har sun dauki ciki ni kina nan kina juyani kamar waina a cikin tanda, ki kuma min maganar Aminu ki gani!" Yana gama fadi ya juya a haka dinsa ya shige bayi, hakan ya sakata sake zarro ido tana kallonsa har ya bacewa ganninta

Bakin gadon ta zauna tana mamakin dama ya iya masifa da ihu wa mutane haka?, Dama ya iya fada murya a dage haka? Me ta masa? Ba ko tausayi? Ba zai tsaya ta gama masa maganar dan ya fahimci basu san komai ba? Innalilahi wai harda su cewa Aminu da mata biyu kuma da ciki, yo Aminu ko farcen mace ya kalla bayan nata ne? Hum za'a hadata da Aminu kiri kiri

Fitowarsa da tawul da karasowarsa bakin gadon ya zauna saman kujera ta bakin hado murya a hade ya ce" Ci gaba" ya sakata sada kai a ranta tana mamakin manyan gaban jikinsa da ginanen jiki irin nasa

Murya a tausashe ta ci gaba da sanar masa abinda ya faru dala dala, har zuwan su UMMA garin, wanda daga zuwansu ne aka saka aka kirawota, da kilaceta da aka yi, da irin gyaran da ake bata, a nan ne ya ringa yi mata tambayoyi a hankali, yannayin amon muryarsa kuwa na amayar da déception, yakan kawar da kansa gefe ya dauki dan lokaci yana fitar da huci sannan ya juyo inda take, ya sale bata damar idasa maganarta

Idannuwanta na kallon kirjinsa, wajen da ya fi bata sha'awa a jikinsa bama idan baya da riga, a sanyaye ta ce" Shi kadai ya zo ya daukeni, a gaban INNAR BIRNI, tana kuka tamkar ranta zai fita, a lokacin da zata sakani a motarma ta sake jadada min magana kamar haka NADIRAH, DUK RINTSI, KAR KI ZUBA MAGANIN DA ZA'A BAKI, KO KI FESA ABIN FESAWA, KO DUK WANI LAUNI NA HANYAR KASHE ABAN DATAWA, KAR KI CE BARI KAWAI KI AIWATAR KI DAWO KI SAMU YARON DA AKA RABAKI DA SHI, KI SANI SUNNAN HAKA KISA, A JAHILCIN DA AKE MAKI IKIRARI KUWA BOKO CE BAKI TSAYA KIN YI BA , INDIN HINDU KI RIKE AMANAR BAWAN ALLAH MARAYAN ALLAH KIN JI?"

Idannuwansa ya lumshe a sanyaye , yanzunma a sanyaye ya sake zuba idannuwansa a cikin nata yana kallonta
Haka kawai ta ji ba zata juri kallon ba, dan bata daba gannin idannuwansa da rauni ba, bata saba kallon idannuwansa na neman agaji ba, bata san haka a tatare da shi ba

Da kyar ya iya cijewa, ya sake bude bakinsa a sanyaye ya ce" Dan Allah, kar ki ce min a zuwanki gidan nan, a fahimtarki harda HUZNAH a cikin wannan rikici kin ji? Kin ga HUZNAH matata ce, matata ce wace ta nuna min sarki ko ba sarki ba tana so na, kuma na yarda da hakan Nadirah, nima ina son matatah, dan Allah kar ki ce min harda ita a cikin wa'inda zasu hadani da bugun zuciya?"

Haka kawai ta ji wani irin suka a daidai lokacin da ya yi furucinsa, haka kawai ta ji wani irin zafi a cikin kahon zuciyarta, har ta ji kamar wasu hawaye na cika cikin idannuwanta

A hankali ta ringa jin sanyin da bata ji a dazu, harma ta samu a sanyaye ta janyo abin rufar dake saman gadon ta dan raba a jikinta

Idannuwanta da suke ta yawo a tsakiyar tsadaden dakin ta maido sakan tsadadiyar kafarsa mai dauke da ni'imtatun kashin jiki luflufluf sun yi baki sidik sunna ta sheki, sannan ta ajiye a kan yan yatsun kafarsa masu tsayi summa samansu akoy gashikan nan
Kanta ne ya sara mata, lokaci daya ta ji wani irin zufa da zazabi na son keto mata

*HUZNAH* sunnan da mamalakin sunnan , halitar da bata taba kayar mata da gaba ko sakata a hali na jin kishi a da ba, me yasa ambatonta a cikin wasu kalamai na bakon rayuwarta a yanzu suka sakata jin sunnan gaba daya bashi da wani tsari ko dadi a baki? To ita me yasa iyayyenta suka saka mata wani wai HUZNAH? Filon cen filon kawai, sam bata da tsari kwata kwata fa sai kyan jaraba!

"NADIRAH" ya fada a sanyaye yana so ta yi masa bayani, duda irin faduwar masa da gaba da bayanin nata ke yi na yanzu, dan sam baya so wani abu mai zafi ya fito daga bakinta a kan HUZNAH, anya zai jure na HUZNHA kuwa? Huznah matar rufin asirinsa ce, ya kirta nata ba dadi ta dawo ta likun masa, a ransa yake ji Huznah matar da zata tarbi mashin da aka harbo masa ce ba ta labe a bayansa ba, idan kuwa ya ga akasin haka an shige shi sosai Walahi

Ita kuma da ta dago ta zubawa jajayen lebensa ido sai ta ji a nan fa gaskiya kamar sarki bai yi adalci ba, yo ta yaya zai ringa saka H a karshen sunnan HUZNAH yana wani karasa fada a sanyaye ita kuma ya wani ce NADIRA gatsau ba sakayawa? Oh wato shine namiji mai nuna ya fi son daya fite da daya ko? Irin wa'inda basa tsoron tashi da shanyayen jiki ko yayane?

Gannin ta kure shin nan ya daka shi lumshe idannuwansa yana ayana' shikenan, kasheni zasu yi, zuciyata ba zata jure ba'

Baki ta murguda tana sake rufe jikinta ta ce" Wannan kayanka ce, da ita ko ba ita duka lamarinka ne, ni ban sani ba gaskiya, na UMMARma ni ba komai na sani ba, kamar dai inaga harda kwartanci tana yi!"

Tana gama fada ta mike tana jan bargon hadi da neme nemen atamparta a ranta sai mitar abinda bata san dalilinsa take yi ba...........................................

*NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼*

°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°
```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.```
°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°

*https://www.facebook.com/106494781436168/*

🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻
*OUMOUGHLOUK ITIBEL*
_(ZAKIN SARAKAI)_
🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻

_FREE BOOK_

*Na*

*SAJIDA NIGER*

5️⃣8️⃣

"Wani irin kwartanci kuma?" Ya fada yana juyo da ita bayan ya mike

Lululu din da take ji ya sakata dan jinginuwa da jikinsa, muryarta cen ciki ta ce" Juwa nake ji ASADEEK, ina so na je kusa da Innata kafin hukuncinka ya same mu "
Chapter 80 · 0% Book details