Sashe 71
Fulani Part 1 complete Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tara da yan mintuna yaran su kai bachi amman tana zaune a dakin domin cika umarnin Shattima da jekadiya ta fada mata sai 10 zata tafi gida, ko kadan bata jidadin hakan ba, sai dai bata isa tai musa ba balle ta tsaba, ta sani suna mata haka ne saboda kawai bata da galihu, saboda tana aiki karkashinsu. Wannan abun kadai ya isa yasa ta kara kaunar Sirleem a ranta, ko ba komai ya tausaya mata, ya nuna mata kulawa kuma ya taimaketa. Sai da goma tai sannan Jekadiya ta shigo dakin.
“Za ki iya tafiya yanzu, direba na waje yana jiranki, daga gobe har kullum zai rika zuwa daukoki misalin 7am�
“Tau na gode�
Ta fada tana risinawa sannan ta mike tsaye ta fice daga dakin. A natse ta shigo falon Ammy, al'adar ta ce indai akwai mutane a falon ba zata fice ba sai ta taje ta gaishesu. Hakan yasa ta karasa gaban Ammy ta kwashi gaisuwa sannan ta risina gaban Yarima ta mika masa gaisuwa. Kara ma Ammy ta amsa shi kam ban da kallonta komai be yi ba, babu alamar amsar a tare da shi. Mikewa tai tsaye ta nufi kofar fita, fitarta da kamar minti daya ya mike tsaye ya nufi backyard din falon Ammy, tsaye a gurin yana kallon yadda ta nufi motar, da kuma Sirleem daya fito daga bangarensu ya doso inda take.
“Ina wuni, Malam dan Allah kai ne aka ce zaka kai ni gida?�
Falmata ta tambaya tana leken Baba Adamu dake gaban motar.
“Eh ni ne�
Ya amsa mata, sai ta matsar da kunnenta kusa da shi.
“Dan Allah sake fada bana ji sosai�
“Eh ni ne�
Ya fada da karfi.
“Tau na gode�
Ta mike tsaye tana jin alamar mutum a bayanta, da sauri ta juyo sai tai arba da Sirleem.
“Gida zaki je?�
Ya rada mata a kunne yana murmushi.
“Eh wannan zai kai ni gida�
“Ina maganinki yake?�
“Gashi�
Ta fada tana kokarin fiddo da hannunta cikin hijabin, bata karasa ba ya kai hannunsa cikin hijabin ya karbi maganin ya dora saman motar yana amsa gaisuwa da Baba Adamu ke masa, sai da ya fitar da maganin na digawa sannan ya rika fuskarta ya ja hijabinta baya ya fito da kunnuwanta ya kwantar da kanta ya diga mata maganin a kunne daya, ya saka mata kada sannan ya sake digawa a dayan kunne ya saka mata kada kana na rufe maganin.
“Karki yi wasa ki rika amfani da shi kullum, ta fada min magani ne mai tsada ta siya miki�
“Inshallah, na gode Allah ya saka da alheri�
“Never mind�
Ya fada yana fadada fuskarsa da murmushi sannan ya bude mata bayan motar, ta shiga ya rufe ya daga mata hannu, ita kuma ta juyo tana kallonsa ta bayan motar har suka fita daga harabar sannan ta juyo ta zauna daidai tana jin wani irin abu a zuciyarta mai wuyar fassara, abun da bata taba ji ba sai a yau, abun da ba zata iya fadar ga kalarsa ba balle yanayinsa, idanuwanta ne suka cika da kwalla sai ta rumgume hannayenta ta lumshe ido.
**
Sai da suka wuce sannan Shattima ya bar backyard din ya dawo cikin falon ya zauna kusa da Ammy.
“Ni kam sai nake ganin kamar Sirleem ba son Nana yake ba�
Ammy ta kalleshi.
“Kamar ya?�
Ya daga kafadunsa, alamar haka nan dai.
“Idan baya son ta ai ba zai nuna ba, tun da ba dole aka masa ba, ya dai rage kula ta ne kamar baya, saboda kun saka masa ido�
Be sake cewa komai ya ciro wayarsa dake aljihu, ganin Number Baba Waziri yasa ya mike tsaye ya fice daga falon. Kasa ya dauko gaba daya sannan ya kara wayar a kunnesa da sallama. Bayan sun gaisa Baba Waziri ya ce.
“Ban jika ba, tun da muka yi magana, idan Maijidda bata maka ka fada min wanda kake so, ba abu ne da zai dauki lokaci ba balle nai ta jiranka�
Shattima yayi shiru kamar ba Waziri ne a wayar ba, can kuma ya sauke ajiyar zuciya silently ya ce.
“Ina sonta Baba, amman dan Allah a tambaye ta idan ita ma tana so na, kar a mata dole�
“Mashallah, Allah ya hada kanku ya fada zaman lafiya sai ka fara shirye-shirye tun yanzu�
“Na gode Baba�
Ya furta sannan ya sauke wayar tare da sauke wani dogon numfashi. Data kunna ya shiga wani side ya siye ticket din jirgin da zai tashi zuwa Katsina a gobe.
**
Shattima na fita falon, Iya ta shigo lullube da zane, tana shigowa ta fadi gaban Ammy tana zuba mata kirari bakin nan cike da goro, sai da ta kalli ko'ina a falon ta ga Jekadiya ce kadai a falon sai Ammy sannan ta kara matsawa kusa da Ammy tana wasar hakora.
“Ranki ya dade, ina da magana�
Da gangan Ammy ta ki kallonta ba dan wulakanci ba sai dan nuna isa, daman can Allah ba hada jinin Ammy da Iya saboda Iya ta fiye shiga hanci da kuddudumi ga salo irin na tsofin mayu, Ammy kuma bata son haka.
“Tau ina jinki�
Ta kalli Jekadiya tana dariya, kamin ta sake kallon Ammy.
“Daman wata yar shawara ce na zo da ita�
Sai kuma tai shiru kamar mai tsoron fada. Ganin hakan yasa jekadiya ta ce.
“Iya ki bude baki ki yi magana, Ammy na saurarenki�
Iya ta juyo gurin Jekadiya tana yar dariya kamar ta kunya.
“Daman na ce wai akan Babban Mutum ne, na ce mi zai sa sai an tafi nesa�
Ammy ta kalleta domin ta fahimci inda zancenta ya dosa tun kamin ta karasa, Jekadiya kuma gabanta ya fadi duk da ta san ba wai ta fada ne ta siffar gulma sai dai ta san Ammy ba zata jidadi ba ta fada mata abu kuma aji shi gurin wani.
“Wannan lauye lauyen da kike ba zai fitar da ke ba, da kin fito kin fadi maganarki a fili da Ammy ta fahimta�
Iya ta shafa zanenta tana murmushi.
“Daman cewa nai me zai hana a hada Babban Mutum da yar'uwarsa? Ai ba sai an je can nesa ba an dauko bare tun da ga abu a ciki gidan�
Jekadiya makis tai a gurin kamar an kama munafuki, ta rasa abun cewa. Ammy ta juyo da kyau tana kallon Iya.
“Eh lallai haka, jindadi yayi muku yawa ke da yarki, har hauka take raya muku wannan, shine dalilin shigewa Shattima da Zainab take? To ai kalar zaren ba kalar yadin ba ne, kuma lalacewar takalmin sarki yafi karfin sakawa kafar bafade, Maijidda ce bare? Yar waziri ce nesa? Gata da sakin fuskar da ake muku a gidan nan ya muku yawa shiyasa har raini ya shiga ciki, har kike iya duban idona ki fada min wannan maganar, Iya wai ko kin manta waye ke?�
“Aa ina ya zan manta... A gafarce ni Hajiya salo na ne... Amin afuwa�
Iya ta fada da dariyar kunya, zuciyarta tab da tsanar Ammy sai kallon kurwarta take.
“To daga yau sai yau, ba ke ba ko Zainab kar na sake ganin kafarta a falon nan, idan kina bukatar wani abu ko yin wani abu ki nemi iso karki sake shigo min falo, idan kika yi wasa ba a masarautar ba a yola gaba daya ma sai na canja miki zama�
“To Ammy ba za a kara ba ayi min afuwa a gafarta min�
Ta farasa tana fashewa da kuka, ta mike tsaye rumgume da kunyarta ta fice daga falon, tana kuka kamar gaske.
Ammy ta kalli Jekadiya da duba na mamaki.
“Kin ba ni mamaki, ban yi zaton haka ba, amincewa da ke kuma farinciki abun da Waziri yai yasa na labarta miki taya zaki dauki sirri ki baza a kunne Iya?�
Jekadiya ta rasa inda zata saka kanta, a take ta hau rantsuwa, tana labartawa Ammy yadda akai ta Iya ta ji.
“Wallahi ranki ya dade ban yi hakan da nufin labarta mata komai ba, a gafarce ni, ni kaina murna ne yasa na fadi haka, ban yi zaton zata kawo wannan tunanin ba, Wallahi ba halina ba ne�
Ammy bata sake ce mata komai ba ta mike tsaye a fuce ta shige dakinta cikin mamakin yadda Iya ta iya karfin halin wannan tunanin, har ma ta iya furtawa.
***
Iya na shiga dakinta ta maida kofar dakin ta rufe.
“Idan ba yi da lala ba ayi da tsiya, tsaya mu gani ida ita ma Maijidda ta mutu sai wacce kuma? Wata rana da kanki za ki zo kina rokon na taya ki nemawa Shattima auren Zainab, ita kadai ce matarsa kuma da ita kadai zata haifa masa yaya, daga lokacin ne komai zai dawo na mu, ke kanki Ammy sai kin zama abar tausayi...�
Ta fada cikin wani irin zafin rai na jin zafin abun da Ammy tai mata.
“Tana jin kanta matar nan kamar ita ce sarkin, ke kuma bari na gani zaki taya ni yake ko kuma ta gawa za ki yi�
Ta karasa tana janyo wasu sabbin tufafin a cikin wardrobe dinta, atamfa mai kyau da tsada ya janyo ta dora saman gado domin bata son gobe ta tsaya jiran komai.
Haka ta kwana cikin bacin rai da sakesake kalakala a ranta, kamin garin Allah ya waye duk ta matsu, karfe tara ta shirya cikin atamfar data ciro jiya, ta dauki turare ta fesa sannan ta dauki jakar kudinta da makullin dakin ta fito, ta rufe dakin ta nufi kofar fita sai gaisawa take da hadimai kamar ta Allah, kowa sai bata girma yake har ta isa gate din. Sai da ta fita daga unguwar gaba daya sannan ta samu Napep ta shiga tana fadin.
“Malam Unguwar Waziri�
Ta shiga ta zauna har tana kwafa.
“Za ki iya tafiya yanzu, direba na waje yana jiranki, daga gobe har kullum zai rika zuwa daukoki misalin 7am�
“Tau na gode�
Ta fada tana risinawa sannan ta mike tsaye ta fice daga dakin. A natse ta shigo falon Ammy, al'adar ta ce indai akwai mutane a falon ba zata fice ba sai ta taje ta gaishesu. Hakan yasa ta karasa gaban Ammy ta kwashi gaisuwa sannan ta risina gaban Yarima ta mika masa gaisuwa. Kara ma Ammy ta amsa shi kam ban da kallonta komai be yi ba, babu alamar amsar a tare da shi. Mikewa tai tsaye ta nufi kofar fita, fitarta da kamar minti daya ya mike tsaye ya nufi backyard din falon Ammy, tsaye a gurin yana kallon yadda ta nufi motar, da kuma Sirleem daya fito daga bangarensu ya doso inda take.
“Ina wuni, Malam dan Allah kai ne aka ce zaka kai ni gida?�
Falmata ta tambaya tana leken Baba Adamu dake gaban motar.
“Eh ni ne�
Ya amsa mata, sai ta matsar da kunnenta kusa da shi.
“Dan Allah sake fada bana ji sosai�
“Eh ni ne�
Ya fada da karfi.
“Tau na gode�
Ta mike tsaye tana jin alamar mutum a bayanta, da sauri ta juyo sai tai arba da Sirleem.
“Gida zaki je?�
Ya rada mata a kunne yana murmushi.
“Eh wannan zai kai ni gida�
“Ina maganinki yake?�
“Gashi�
Ta fada tana kokarin fiddo da hannunta cikin hijabin, bata karasa ba ya kai hannunsa cikin hijabin ya karbi maganin ya dora saman motar yana amsa gaisuwa da Baba Adamu ke masa, sai da ya fitar da maganin na digawa sannan ya rika fuskarta ya ja hijabinta baya ya fito da kunnuwanta ya kwantar da kanta ya diga mata maganin a kunne daya, ya saka mata kada sannan ya sake digawa a dayan kunne ya saka mata kada kana na rufe maganin.
“Karki yi wasa ki rika amfani da shi kullum, ta fada min magani ne mai tsada ta siya miki�
“Inshallah, na gode Allah ya saka da alheri�
“Never mind�
Ya fada yana fadada fuskarsa da murmushi sannan ya bude mata bayan motar, ta shiga ya rufe ya daga mata hannu, ita kuma ta juyo tana kallonsa ta bayan motar har suka fita daga harabar sannan ta juyo ta zauna daidai tana jin wani irin abu a zuciyarta mai wuyar fassara, abun da bata taba ji ba sai a yau, abun da ba zata iya fadar ga kalarsa ba balle yanayinsa, idanuwanta ne suka cika da kwalla sai ta rumgume hannayenta ta lumshe ido.
**
Sai da suka wuce sannan Shattima ya bar backyard din ya dawo cikin falon ya zauna kusa da Ammy.
“Ni kam sai nake ganin kamar Sirleem ba son Nana yake ba�
Ammy ta kalleshi.
“Kamar ya?�
Ya daga kafadunsa, alamar haka nan dai.
“Idan baya son ta ai ba zai nuna ba, tun da ba dole aka masa ba, ya dai rage kula ta ne kamar baya, saboda kun saka masa ido�
Be sake cewa komai ya ciro wayarsa dake aljihu, ganin Number Baba Waziri yasa ya mike tsaye ya fice daga falon. Kasa ya dauko gaba daya sannan ya kara wayar a kunnesa da sallama. Bayan sun gaisa Baba Waziri ya ce.
“Ban jika ba, tun da muka yi magana, idan Maijidda bata maka ka fada min wanda kake so, ba abu ne da zai dauki lokaci ba balle nai ta jiranka�
Shattima yayi shiru kamar ba Waziri ne a wayar ba, can kuma ya sauke ajiyar zuciya silently ya ce.
“Ina sonta Baba, amman dan Allah a tambaye ta idan ita ma tana so na, kar a mata dole�
“Mashallah, Allah ya hada kanku ya fada zaman lafiya sai ka fara shirye-shirye tun yanzu�
“Na gode Baba�
Ya furta sannan ya sauke wayar tare da sauke wani dogon numfashi. Data kunna ya shiga wani side ya siye ticket din jirgin da zai tashi zuwa Katsina a gobe.
**
Shattima na fita falon, Iya ta shigo lullube da zane, tana shigowa ta fadi gaban Ammy tana zuba mata kirari bakin nan cike da goro, sai da ta kalli ko'ina a falon ta ga Jekadiya ce kadai a falon sai Ammy sannan ta kara matsawa kusa da Ammy tana wasar hakora.
“Ranki ya dade, ina da magana�
Da gangan Ammy ta ki kallonta ba dan wulakanci ba sai dan nuna isa, daman can Allah ba hada jinin Ammy da Iya saboda Iya ta fiye shiga hanci da kuddudumi ga salo irin na tsofin mayu, Ammy kuma bata son haka.
“Tau ina jinki�
Ta kalli Jekadiya tana dariya, kamin ta sake kallon Ammy.
“Daman wata yar shawara ce na zo da ita�
Sai kuma tai shiru kamar mai tsoron fada. Ganin hakan yasa jekadiya ta ce.
“Iya ki bude baki ki yi magana, Ammy na saurarenki�
Iya ta juyo gurin Jekadiya tana yar dariya kamar ta kunya.
“Daman na ce wai akan Babban Mutum ne, na ce mi zai sa sai an tafi nesa�
Ammy ta kalleta domin ta fahimci inda zancenta ya dosa tun kamin ta karasa, Jekadiya kuma gabanta ya fadi duk da ta san ba wai ta fada ne ta siffar gulma sai dai ta san Ammy ba zata jidadi ba ta fada mata abu kuma aji shi gurin wani.
“Wannan lauye lauyen da kike ba zai fitar da ke ba, da kin fito kin fadi maganarki a fili da Ammy ta fahimta�
Iya ta shafa zanenta tana murmushi.
“Daman cewa nai me zai hana a hada Babban Mutum da yar'uwarsa? Ai ba sai an je can nesa ba an dauko bare tun da ga abu a ciki gidan�
Jekadiya makis tai a gurin kamar an kama munafuki, ta rasa abun cewa. Ammy ta juyo da kyau tana kallon Iya.
“Eh lallai haka, jindadi yayi muku yawa ke da yarki, har hauka take raya muku wannan, shine dalilin shigewa Shattima da Zainab take? To ai kalar zaren ba kalar yadin ba ne, kuma lalacewar takalmin sarki yafi karfin sakawa kafar bafade, Maijidda ce bare? Yar waziri ce nesa? Gata da sakin fuskar da ake muku a gidan nan ya muku yawa shiyasa har raini ya shiga ciki, har kike iya duban idona ki fada min wannan maganar, Iya wai ko kin manta waye ke?�
“Aa ina ya zan manta... A gafarce ni Hajiya salo na ne... Amin afuwa�
Iya ta fada da dariyar kunya, zuciyarta tab da tsanar Ammy sai kallon kurwarta take.
“To daga yau sai yau, ba ke ba ko Zainab kar na sake ganin kafarta a falon nan, idan kina bukatar wani abu ko yin wani abu ki nemi iso karki sake shigo min falo, idan kika yi wasa ba a masarautar ba a yola gaba daya ma sai na canja miki zama�
“To Ammy ba za a kara ba ayi min afuwa a gafarta min�
Ta farasa tana fashewa da kuka, ta mike tsaye rumgume da kunyarta ta fice daga falon, tana kuka kamar gaske.
Ammy ta kalli Jekadiya da duba na mamaki.
“Kin ba ni mamaki, ban yi zaton haka ba, amincewa da ke kuma farinciki abun da Waziri yai yasa na labarta miki taya zaki dauki sirri ki baza a kunne Iya?�
Jekadiya ta rasa inda zata saka kanta, a take ta hau rantsuwa, tana labartawa Ammy yadda akai ta Iya ta ji.
“Wallahi ranki ya dade ban yi hakan da nufin labarta mata komai ba, a gafarce ni, ni kaina murna ne yasa na fadi haka, ban yi zaton zata kawo wannan tunanin ba, Wallahi ba halina ba ne�
Ammy bata sake ce mata komai ba ta mike tsaye a fuce ta shige dakinta cikin mamakin yadda Iya ta iya karfin halin wannan tunanin, har ma ta iya furtawa.
***
Iya na shiga dakinta ta maida kofar dakin ta rufe.
“Idan ba yi da lala ba ayi da tsiya, tsaya mu gani ida ita ma Maijidda ta mutu sai wacce kuma? Wata rana da kanki za ki zo kina rokon na taya ki nemawa Shattima auren Zainab, ita kadai ce matarsa kuma da ita kadai zata haifa masa yaya, daga lokacin ne komai zai dawo na mu, ke kanki Ammy sai kin zama abar tausayi...�
Ta fada cikin wani irin zafin rai na jin zafin abun da Ammy tai mata.
“Tana jin kanta matar nan kamar ita ce sarkin, ke kuma bari na gani zaki taya ni yake ko kuma ta gawa za ki yi�
Ta karasa tana janyo wasu sabbin tufafin a cikin wardrobe dinta, atamfa mai kyau da tsada ya janyo ta dora saman gado domin bata son gobe ta tsaya jiran komai.
Haka ta kwana cikin bacin rai da sakesake kalakala a ranta, kamin garin Allah ya waye duk ta matsu, karfe tara ta shirya cikin atamfar data ciro jiya, ta dauki turare ta fesa sannan ta dauki jakar kudinta da makullin dakin ta fito, ta rufe dakin ta nufi kofar fita sai gaisawa take da hadimai kamar ta Allah, kowa sai bata girma yake har ta isa gate din. Sai da ta fita daga unguwar gaba daya sannan ta samu Napep ta shiga tana fadin.
“Malam Unguwar Waziri�
Ta shiga ta zauna har tana kwafa.