← Book details Fulani Part 1 complete Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 54 OF 172

Sashe 54

Fulani Part 1 complete Complete Hausa Novel · about 8 min read

“Ana sakawa mutum ita ne saboda kar yai albarka, komai kike samu ko kika rika sai lalace, idan kana makota da maye ko kuma ya saka maka ido, to zai saka mata wutar ne tai ta binka tana cinye duk wani abu da ka mallaka, idan kuma be saka maka wutar ba zai saka maka ciwo har dukiyar dake tare da kai ta kare, shi ma idan ya gagara cinka ne, mayu suna da hassada basa son su ga wani yana samun wadata saboda mafi akasari su matalauta ne, masu siyar da kurwa ne kawai suke arziki wadanda basa ci sai dai su siyar ko kuma suna ci suna saidawa, ko baiwa ko basira maye ya gani a tare dake zai kwasheta ya jujuta miki kwakwalwa, idan maye ya ci mutum dubu sai ya zama sarkin mayu, daga lokacin ne mayen baya iya sake cin mutun sai dai su koma bada maganinsu saboda sun san lagonsu, mugun ya san makwancin mugu, idan kuma maita mutun ta gawurta, ko dabba ya kalla ya kwallafa rai zata mutu, ko gini kai idan maye baya so yana kallon ginin zai zube sai idan ka gagareshi, idan kurwarki tana gurin maye zai ta miki waibuwa yana saka ki kalar mafarkin da kike so, idan kuma suka aje miki aljani a daki to zasu rika jin inda kike neman magani da inda kike ajewa sai su bata shi ya gagara yi miki amfani�

Tun da ya fara bayani Fadime take masa kallon tsoro idonta a waje.

“Kai ma maye ne?�

Ya girgiza mata kai yana sake kai hannunsa ya shafa gashin kanta.

“Mu garin mu ba a maita, sai dai muna tsafi sosai, amman ba mu yarda da ayi maita ba, saboda ba ma yarda mu cutar da yan'uwanmu, idan mutum yai mata korarsa ake a garin ko da shi din sarkin garin ne, mayu har yayansu suke badawa saboda ana adashe tsakanin junansu, idan aka ci dan wannan idan za ayi kwasa na wani za a ci, duk irin son da kake ma dan dole ka bada, idan kuma aljanin maita ya bukaci ɗan ka da kansa dole ka cinye danka ko da kuwa kana kana son shi, mayu basa son tsagera, sun fi son matsoraci da mai yawan kyautata musu, matsoraci kurwarsa tana kwantawa ne guri daya har su samu nasarar kamawa babu wata hala, kama ma mai yawan kyautata kusu kullum yana tare da su, kamar kaza ne a cikin keji idan ka tashi yankawa cirota kawai zaka yi, tsarega kam yana musu wahalar kamu saboda kurwarsa bata zama a guri daya kuma baya shan inuwa daya da maye, wani mai aljanu ma wanda aljanunsa suka fi na maye a take zai tona musu asiri, sannan maye be son tsarguwa, idan kika matsa masa zai tashi ya bar miki guri, idan har makocinki ne, ko kuma ya baki maita ki ci a asirce bani sani ba ki kamu da ita, kowa kuma da yadda yake kama kurwa, wani lasowa yake, wani sai ya miki kyaface da hannu wani sai jikinsa na taba naki, wani sai ya baki abu kin ci, wani sai ya shiga innuwarki, wani sai ya baki abu kin karba ko kuma kin bashi a lokacin ne zai samu damar jan kurwarki izuwa gareshi, wani sai ya miki magana kin amsa, wani kuma da ido zai janyo kurwarki, akwai wadanda basa gashi, amana basa tsawa soyawa ko gasawa, irinsu sun fi hadari su da masu saidawa domin idan sun sayar yana da wahala wanda aka saidawa ya dawo da ita duk kuwa da irin azabar da za ayi ma wanda ya kama kurwar, wanda baya gashi kuma take daya kama yake yankewa ya cinye mutum ya mutum, irin su idan suka kama ba zaka wuce kwana daya ba ko wuni wani ma awanni zaka mutu�

Gaba daya jikin Fadime yai sanyi, tun dai tana gane bayanin nashi har kwakwalwar kanta ta fara kwancewa yanzu kam jinsa kawai take bata gane komai ba, sai dai abunda ya faru a dazun da Amo ya dawo mata a rai wata kila da gaske Amo mayya ce.

“To ni wa yake saka min wutar? Minayi?�

“Baki yi komai ba, ban fada miki maye yana da hassada ba? Idan ma suka gagara cin kurwarka suna mata duka su daddake ta mutun ya koma musaki ko mahaukaci ko wawa ko kuma ya koma kwance da rashin lafiya, amman daga yau ba za a sake saka miki wutar maitar ba, ba zan sake bari a cutar da ke ko yatsa ba zan bari wani ya nuna miki ba kowa kuwa�

Ya fada yana kallon cikin idonta fuskarsa na nuna alamar babu wasa a maganarsa. Juyawa yai baya ya kalli wata bakar mage dake labe cikin itatuwan masara tana kallonsu sai ya nufi inda take Fadime dai binsa kawai tai da kallo.
Amo na ganin ya nufota hankalinta ya tashi tana son ta gudu ta kasa, sai ta ji kamar ma yana kiranta yana nufota tana tunkararsa har ta kai kanta gurinsa ta duka ya kamata ya birkiceta ya nade hannunsa ya sakar mata kulli a ciki sannan ya saketa, kasa tashi magen tai a take ta fara aman jini Wasim na ganin haka ya juyo ya dawo inda Fadime take tsaye.

“Wannan magen ina ganinta idan ina kiwo tana bibiyata, har a mafarki wani lokaci ina ganinta�

Fadime ta fada tana nuna magen cikin wani irin tsoro har bata iya numfashi da kyau. Kafadunta ya fada ya kara matsowa da ita kusa da shi ya rumgumeta ya lumshe ido yana sauke ajiyar zuciya.

“Kin cika tsoro...�

Ya fada a hankali hana shafa kanta, kamar wacce ta tuna abu tai saurim dagowa daga kirjinsa ta leka mage sai ta hango babu magen a wajen, ta kalli Wasim

“Kai ma ai kana keta ka maida min murya katuwa kuma ka saka min maciji a tulu�

Murmushin yai ya risino kusa da fuskarta yana mata wani irin kallo kamar maye.

“Ai ke kika ce na miki dabon maciji kin tuna?�

“Amman ban ce ka maida min muryar katuwa ba�

Nan ma murmushi yai.

“Wannan kuma ra'ayina ne, amman ba zan sake maida miki murya katuwa ba na yi alkawari�

Yana gama fada mata haka jikinsa ya bashi cewar akwai wani mai nemansa a kuwa da shi, tafin hannunsa ya bude sai sunan Liya ya fito da sauri ya rufe hannun ya juya gurin wata karamar hanya ya fara tafiya.

“Zan tafi sai na sake zuwa nan�

Wannan karon bata daga masa hannu ba kamar yadda ta saba sai kawai ta bishi da kallo har ya haye saman dutse ya dago mata hannu ya juya ya sauka ta dayan bangaren. Sai ya wuce sannan ta juya ta koma gurin ruwa ta cigaba da cikonta tana tunanin wasu abubuwan daya fada mata, tana daga kai ta hango Liya tafe ta gefen gulbin, Fadime ta tsaya jiranta har ta kawo.

“Dan Allah ki taimaka ki dora min tulun nan a kai�

Kallonta Liya ta tsaya yi sannan ta karasa kusa da ita ta rika mata tulun ta dorata a kai, a nan Fadime ta hango gashin kazar dake kanta ta kai hannu ta cire mata.

“Gashin kaza a kanki�

Fadime ta fada bayan ta kai hannun ta cire gashin ta jefar, Liya bata tsaya komai ba ya kaiwa Fadime bugu a baki.

“Kam Bala'in nan�

Fadime bata san lokacin data jefawa Liya tulun kanta ba ta fara zaginta bakinta sai jini yake.

“Shegiya muguwa shegiya shegiya shegiya daga taimako, muguwa Azzamula, muguwa ban yafe ba Allah ya isa�

Liya ta duka ta dauki gashin ta maida a kanta ta ranta a na kare. Fadime ta fara daukar duwatsun dake gurin tana jifanta da su iya karfinta tana zaginta tana kuka a lokacin daya, domin ba karamin azaba ta ji ba, daman mutane garin Garuk indan suka daki wanda ba dan gari ba sai yaji zaba saboda dafin hannunsa domin su komai na su a tsafe yake, ko dangwarar mutun su kai indai sun yi da keta sai yaji ciwo.
Da gudu Liya ta haye saman dutsen tana dukewa dan kar jifar da Fadime take mata ta same ta, daman can neman Wasim ya biyo da ita ta nan kuma bata ganshi ta kwashi ruwan duwatsu a gurin Fadime.

*Littafin nan na kudi ne biya ki karanta cikin aminci. Pay 300 to 0314795884 Abubakar Hadiza Gt bank, then send the evidence to 08036126660*

Ina mata matan kwalisa Matan da suka ansa sunansu na Mata? Ina wadanda ke cewa mun yi mun yi bamu ga amfaninshiba? Hmmm to ku zo ga Yar gidan Maifata ta zo maku da Al ajabu, dan tsugunno, gumba da tsimi da Zuma daban daban, maganin sanyi na maza da Mata. Ga kuma garurruka irinsu mallakau sabuzu kuwa, sa bahaushe saibi, Dan hubbare kafi malam aiki, ke kadai ke da miji, dahuwar kaza, tattabara, ciccibi da dai sauransu. Ba anan kayanmu suka tsaya ba, muna hadin amare na musamman turaren sutura turaren tsugunno turaren wanka da na daki da na jiki duka 4amare nasu na musamman ne, amma ga tsuhuwar da ke son komawa yarinya itama zata iya zuwa ahadata kai abundai sai wanda ya gani, dan haka karkubari abaku labari, domin neman karin bayani zaku iua nemana ta wannan number 09029891757 ko 08169311410, muna aikawa ko'ina a fadin kasar nan har waje kasar nan muna aika kaya.
Address: Nasarawa Samaru Area gurin masallacin mai sola Gusau Zamfara state Nigeria.
03/12/2021, 09:23 - 🤐🤐🤐🤐: 24

*Littafin nan na kudi ne biya ki karanta cikin aminci. Pay 300 to 0314795884 Abubakar Hadiza Gt bank, then send the evidence to 08036126660*

Cikin natsuwa Sirleem ya shiga dakin mahaifiyarsa, tana ganinsa tai saurin aje wayar hannunta.

“Ya akai?�

Kai tsaye ta tambaye shi abun da bata saba ba. Mamaki ne ya bayyana a fuskarsa.

“Na ga kamar kina ciki damuwa ne�

“Aa ba komai ka je inda zaka je waya na ke son yi�

“Amman kin tabbatar da babu wata matsala?�

“Na fada maka ba komai mana Sirleem ka tafi inda zaka je�
Chapter 54 · 0% Book details