← Book details Abdul Nasser Alfah Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 54 OF 87

Sashe 54

Abdul Nasser Alfah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Zakiyya durkishewa tai awajen tana kuka mai cin rai,ashe daman fiyah yaudararta take soyayya suke da Abdoul amman ta rufeta baibai,Lallai ta yarda fiyah ta ci amanarta har tana tunanin zata iya barmata Abdoul,bata san cewa don ita aka hallicceshi ba itace first love dinsa kuma da ikon Allah itace takarshe muddin tana da rai bazata iya yarda wata tashigo rayuwar Abdoul ba.
Haka ta ringa kuka tana tafiya duk wanda yaganta saiyayita kallonta kamar wata zararra,har ta je bakin titi ta zauna dirshen tana kuka,nadamar sanar da fiyah sirrin dake boye take wanda shine yasa har Abdoul yaji yana sonta don ta na niyyar cetoshi,mema yasa tai saurin yarda fiyah tasan lokacin son kara saka Abdoul din cikin kwayar idonta duk ya rudeta yasa dandanan ta fayyacema fiyah komi,yazatai tagyara wannan barakar tana tsananin kishin Abdoul ko wata bata son taga ya kalla inhar sunan ta mace,to balle fiyah yarinyar da kallo guda zaka mata katabbatar da tsananin kyawunta,bata kwalliya afuska amman hakan bai hana ruwan kyanta bayyana ba.kodan wannan Dole Abdoul zai haukace akanta wai har tsawon yaushe haka tafaru.rushewa tai da kuka tana cewa"Allah ya isa fiyah,bazan yafe maki ba kin sace mun zuciyar Abdoul,to yakike son ninayi bacin na gaya maki bana iya rayuwa mai dadi muddin babu shi cikin rayuwata.........kamar ta haukace haka taita kuka abakin titin,mutane na kallonta kamar daga sama saiga malik yazo wucewa kamar ance yakalli gefen hanya idonsa akan zakiyya,zaro ido yayi yai saurin parking gefen hanya yafito.
"Zakiya!kina lafiya kuwa?mekike anan kekadai kuma kika zauna akasa bakin hanya kina kuka kanki guda kuwa?"
Kukan take tace"yaya malik kabarni nayi kukana don shine kurin abunda zan yi nasamu sauki,wallahi bansan safiyya munafuka bace sai yau,ta yaudareni bazan yafe mata ba tana shirin rabani da numfashina,yaya malik Andoul shine numfashina meyasa kuka sanyota cikin rayuwarku gashinan tayi dalilin rabani da rayuwata.........."
Kallonta yake cike da mamaki shi gabaki daya baima fahimci abunda take fada ba,jan hanunta yayi tana biyosa tana cigaba da kukanta,ya bude motar ya sata yarufe surutunta take tana kuka,bai sake mata magana ba don bama zata natsu tayi mashi bayanin abunda yake tambayarta ba,saida yaje gida ya sauketa yaga Abdoul baya nan,wayarsa ya lalubo sai lokacin yaga missed call dinsa har guda biyar,fitowa yayi yakirasa lokacin shi yana can har lokacin ba afito da fiyah ba daga dakin gaggawa.
Duk ya yamutse ya tashi hankalinsa daker ya iya daukar kiran.
"Malik ina kashiga na shiga halin taimako na kira baka dauka ba,ganinan *care life hospital* na kawo sofiyya."
Cike da tashin hankali malik yace"safiyya kuma?meyafaru badai wata matsala ko ganinan xuwa innalillahi wainna ilaihir raju,un."
Yakashe yashiga motar bai tsaya xuwa company ba duk da bakin dake jiransa kurin sai yanufi asibitin............duk ya rude wannan wace irin masiface daga wannan sai wannan,mekuma yafaru da ita Allah karka saka mummunan abu ya sameta.
Yanata wannan surutun har yaje asibitin,daker ya gano Abdoul din.
yadda yaganshi saida hankalinsa ya ninka tashi,duk ya rikice yariko hannun sa yace"Alfah meke faruwa?ina safiyyar me yasameta ka kwantar da hankalin ka babu abunda zai faru da ita."
Malik bai sake rudewa ba saida yaga Alfah yana fitar da kwalla muryarsa na rawa yace"malik,inajin tsoro inajin tsoron faruwar wani abu akanta,ta dalilina da zakiyya ta saka rayuwarta cikin hadari,dazun na kirata............ya zayyane mashi duk abunda yafaru yana hawaye,yace "tsorona kar ace sun mata injection,saboda hada yukurin fyade suka so yi mata Allah bai basu dama,yanzu haka suna can station sonake sainaga farkawarta kozan je"
Lallashinsa yake yana goge mashi kwalla lallai Alfah ya fara dawowa Alfah dinsa na ainahi,baya ma abu kuka duk tsananinsa tun bayan da bunda yafaru agidansu,amman yanxu akan mace duk ya gigice yafita daga natsuwarsa.
Yanxu ne yafahimci maganar zakiyya,kallon Alfah yayi yace"can na gamu da zakiyya bakin titi tana kuka sai surutu take wai safiyya ta yaudareta Allah ya isa bata yafe ba,meyafaru ne "
Dogon tsaki yaja yace"kyale wannan mahaukaciyar,wai da safiyya zatai kishi harta ikirarin inhar ita zata kaita asibiti wlh bata zuwa,Allah ya kyauta saidai ta mutu.ni bantaba ganin butulun mutun ba irinta,ubanwa yajefa safiyyar cikin wanna matsalar inba itaba,ba ta dalilin ceto zakiyyar suka ganta ba har haka ta kasance,to wallahi inbatai wasa ba zan bata mamaki,mahaukaciyar baza da batasan abun arxikiba"mtsss yaja tsaki malik yayi ajiyar xuciya yace "dole zanje na sanar agidansu,nasan suna can suna jajanta har magruba bata dawo ba,ko zaka zo muje"
Girgiza kai yayi yana shafa kanshi har lokacin baya cikin natsuwarsa shi xuciyarsa ma ciwo take"bazan je maitama ba ahalin yanxu,kaidai kaje din"
"Shikenan kakula da kanka,zan biya na sallami baki acan company"
Cikin yanayi marar dadi yace"kayi waya kace asalallamesu sun dawo gobe baka da lokacin zuwa company yanzu malik,"
Murmushi yayi yace"ok sir"yadda yayi harda sarawa yasa murmushi ya kubcewa Abdoul badan yashirya ba,fice wa yayi yatai wajen mota yana tunanin shiga unguwar,shekara shidda rabon dayaje ko kan titin unguwar balle bakin get din estate din.
Jan numfashi yayi ance ranar dole sai dole yaja motar yatai.

💞💞💞💞💞💞💞💞💞

Baba ne ya gama sallar magriba yace"nikau maman su kin kira uwata kinji inda ta tsaya hankalina ya kasa kwanciya tun dazu,"
Fitowa mama tai daga daki itama cikin yanayi marar dadi ta zauna gefen baba saman tabarma tace"wallahi babansu tun karfe shidda nake kiranta wayarta arufe,na kira jamila tace gaskiya bataje ba na kira balaraba tace ita rabonta da safiyha tun sunan jamila,shirun danai na dauka kafin kayi magana ta dawo,addua kurin nake tunda nashiga daki nai salla."
Juyowa baban yayi yana kallonta cike da damuwa yace"haba maman su,meyasa tun dazun baki fada ba da ban tura dalha yaje can akaramtar yaji abunda yafaru ba."
Sadda kai tai tace"kayi hkr babansu,na tura yesmin gidan su rafeea tunda tare suka tai data dawo tace mun ai rafeea can tabaro safiyyah basu gama ba wajen hudu da rabi,shine saina tura dalha nace yaje yagano mana ko lafiya,na boyene gudun tashin hankalinka."
Shiru yayi yana tunani sai kuma yaji ta bashi tausayi,mace mai kulawa da gidanta da iyalinta.duk abunda tasan zai daga mashi hankali kokari take ta kiyaye wannan dinma don yafi karfinta bata da wata mafita.
"Shikenan Allah yadawo da dalhan lafiya yasa kuma babu wata matsala,tunda bata kai har kamar yanxu inhar ba gidan jamila tabiya ba"
Shiru sukai yesmin sarkin kuka har tafara xubda hawaye mamace ke lallashi ta itama jitake kamar tayi kukan,gabanta ke faduwa bana jin safiyya ba lafiya ba.

Tunda ya shigo unguwar abubuwa dayawa suka ringa dawo mashi,unguwar ta canza sosai fiye da dacan,gine gine da abubuwan cigaba duk sun samu kasancewar unguwace ta yan siyasa da masu hannu da shuni,tafiya yake yana kallon gidajen daya bayan daya har idonsa yakai ga gidan da bazai taba mancewa dashi ba,gidan da ya canza mashi rayuwa ya fiddoshi daga cikin kangin talauci da kakanikaye.kwalla yaji ta fito mashi xuciyarsa ta karye abubuwan da suka faru ranar da ya dawi daga tafiya,ina ma ya bude idonsa yaga komi mafarki ne ba haka yake ba.amman ina wannan rayuwar tafi gaban mafarki.
Kallon gidan dake opposite da gidan su Alfah yayi yajima yana kallon gidan,kafin yayi parking kofar gidan unguwar babu kowa amman hansken fitilu ya haske ko ina kamar ba dare ba.
Tsaye yayi jingine jikin motar yana kallon gidan,ashe nan ne gidan su qanwarsa fiyah ko yaya iyayenta zasuji wannan labarin abun bazai masu dadi ba duba da jiya aka sallamo baban su daga asibiti.
Mashin yaji yatsaya bayansa ya waigo yaga wani matashin Saurayi ya sauko yana kallonsa,isowa yayi yaba malik hannu suka gaisa yace"kana neman wani agidan"
Malik yace"inadai son ayimun iso ciki zanyi magana da mutanen gidan"
Dalha yana kallonsa yace"bari nashiga to muje bismillah"
Gaba dalha yayi malik yana binsa abaya dalha yayi salama cikin gidan,dandanan mama da yesmin suka mike suna hada baki wajen tambayarsa.
"Ina take tare kuke?"
Yesmin kwalla suka cika idonta tace"yaya dalha ina Addata"
Sadda kai yayi yanajin banu dadi yace"wlh naje har makarantar,na duba nayi tambaya ansar dayace ko biyu wasu dasuka santa sukace ai tatafi gida,wasu suce su basu santa bama,bana nan naje duk inda nake tunani bansameta ba wayarta har yanzu kashe take"
Durkushewa yesmin tai tana kuka sosai mama da baba suna sallallami,dalha yace "ga bako nan yana son magana daku wata kila yasan wani bayani akan rashin dawowarta"
Yaje zaure ya shigo da malik yana sallama daker suke iya danne ransu suka ansa mashi saboda halin dasuke ciki.
Babane yace "matso nan yaro zauna ga tabarma,karka tugunna"
Baiyyi musuba ya zauna gefen baban yana gaidasu "lafiya ba lau ba yaro,Allah yasa lafiya daga wajenka"
Malik cikin natsuwa yace"am baba daman zuwa nai nasanar daku safiyya tana asibiti,yan garkuwa da mutane suka saceta to Allah yasa gaban wani dan uwana sukai hakan shine yabisu ya kuma sanar da yan sanda hakin da ake ciki,da taimakon Allah dana Dan uwana shida yan sandan akai nasarar samunta ankuma kama mutanen,amman dai yanzu safiyya na asibiti ana duba lafiyarta amman jikin ba tsananta wa yayi ba,shine na samu bayanin gidansu nace bari nazo n sanar daku don kar hakalinku ya rau gida biyu"
Mama hawaye suka.kece mata tana cewa"lahaula wala quwwata ialla billa ni y'arsu,Allah kadubemu saita duke tana hawaye"
Malik yace"kiyi hkr mama ai abun yazo da sauki da yanzu bamu san inda take ba,ku kwantar da hankalinku tana cikin kulawar likitoci insha Allah tana lafiya"
Baba yace "mungode ma Allah wadannan jarabawowi dayake mana ya kuma bamu ikon cinyewa,kaima yaro mun gode maka Allah yayi maka albarka kaida dan uwanka,tunda ni bazan iya zuwa ba kuje dasu don Allah suganta ko sun samu natsuwa,sai abar yesmin wajenta inhar sun riketa zuwa wani lokaci"
"To aba baby damuwa su shirya muje kaima kanena afito sai muje"
Yace ma dalha.

***********
Fiya ce kwance kan gadon asibiti an saka mata oxygen,Abdoul ne gefemta hannunsa cikin nata idonsa ker akanta,kamar ance mashi zata ruga yana tuno abunda likitocin suka gaya mashi dazun bayan fitowarsu.
Chapter 54 · 0% Book details