← Book details Abdul Nasser Alfah Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 3 OF 87

Sashe 3

Abdul Nasser Alfah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Iya kar karfinta ta taka burkin,hankalinsu inyayi duba ya tashi.don sunyi tunanin sun banke shin,amman sadda ta bud'e idonta taganshi tsaye yana jiran motar tabi ta kanshi........daidai sadda su malik suka karaso wajen sai shashshekar gudun dasuka yi suke,da sauri suka fito daga cikin motar duk sun rud'e.don *FIYAH* tuni ta fara kwallah don gwanace wajen tsoro ........cikin sa,a Dr ya rik'esa gam yana kallonsa,idon nan nashi ya canza launi ya tausasa murya yace"plsss Alfah miye haka ya kakeyin abu irin na marasa hankali,meyayi zafi har haka ka tausayawa kanka kakuma ji tausayin wannan bawan Allahn abokin naka."
Rafeea duk ta tsure saboda tunaninta ta bankesa saboda yadda ta taka burkin daf da shi sosai.
"Assalamu alaikum,bawan Allah bakaji ciwo ba dai ko,kuyi hkr wlh ina saurine shikuma ya hau titi bai duba gabansa ba."
Wani kallon wulakanci yajefa mata ya fixge hannun sa daga na Dr yana dogon tsaki,fiyah na gefe tana goge kwallah ganin babu abunda ya same sa........ran rafeea ya b'aci ainun,da abunda Alfah yayi mata kallon shi tayi,cikin fushi tace"dallah malam miye nayi man tsaki,daga d'an kuskure kadan zaka wani yiman kallon wulakanci,kana jaman tsaki ni nace kahau kan titi babu kulawa, ko angaya maka titin dakin gyatumarka ne ehy,"taja dogon tsaki ta juyawa zata bar wajen.
Jitai kurun anfizgota kamar kwali omo cikin zafin nama,wani irin jan rik'o yayi mata baiyi wata wata ba ya saka tafinsa tare da iyakacin karfinsa ya kwalhe ta da kyakkywan mari. Ga baki d'aya wajen sun shiga shock,Rafeea jitayi ganinta ya d'auke da jinta.......idonta sun kada sunyi jajawur kamar gauta wata k'ara ta fasa tana dafe da wajen...........aguje fiyah ta karaso wajenta tana rikeda ita,jikinta rawa yake saboda yadda karar marin tafita. tabbas kasan wanda akai mashi ba karamar d'imuwa zai shigaba.cikin tsananin tashin hankali Rafeea ke kuka tana dafe da fuskarta,cikin kaushin murya yace"daga yau zakiyi gigin zagin wani bama niba,don ubanki yar iska da iyayenta basu bata tarbiyya ba."
Ya fizge daga hannun dr da malik,yajuya tari taxi zai shiga yajiyota tana cewa"shege d'an iska,azzalumi ban yafeba wlh saina yi silar zuwanka gidan yari mugu........azafafe yadawo wajen malik na rik'eshi yana cewa"haba Alfah karka biyeta macece zaka iya rauna ta tafa,wani irin juyowa yayi yana kallon malik yace"nasan da cewar macence ai shiyasa zan koya mata hankali yadda zata ji tsoron tunkarar namiji ko bani ba,don ubanki ba gidan yari ba kisaka akaini lahira inkikai hakan zan dawwama ina saka maki albarka jakar banza,"
Kuka take tana cewa"wlh sai babana yayi sanadin ajalinka,inhar yasan kaine ka mareni zaka gane kurenka mugu........k'afa yasa zai halbeta yaji anrik'e k'afar caraf cikin mamakin wanda yarik'e kafar sa yake kallon wajen........ *fiyah* ce tayi han zarin rik'e kafar tana hawaye duk sun wanke mata fuska,wani irin wurgi tayi da k'afar tana share kwallarta ta mik'e daga durk'ushen da take gaban Rafeea,cikin d'aurewar fuska kamar ba fiyah ba,cikin masifa da y'ar muryar ta kamar ta yan yara tace,
"Kar ka sake gangancin dukanta,kai baka da imanine ehy,bakasan kima da darajar mace ba,ana gaya maka cewa macece karka biye mata kaji mata ciwo,shine kake son sake kaimata duka,to kasani wlh muddin mahaifinta yaji bakaiba kaf danginka sai akulle tsinann..........cikin fita hayyaci Alfah ya yunk'uro zai kwasa mata nata marin,tai saurin ja baya Malik da dr suka rik'eshi......cikin zafin xuciya yace"kubarni na lahanta yan isaka.....janshi sukai har cikin taxi d'in daya tsayar d'azun suka shigar dashi daker, sadda xai shiga saida ya juyo idonsa cikin na Fiyah ya nunata da yatsa,yana girgizashi alamun worning.
Harara tabanka mashi tana mashi alama da hannu wuce kaidai.
Dr yace wa malik"abokina kaban no dinka pls don koda kai baka nemo niba nizan zo har gida induba jikin nashi,don zamanshi babu kulawar likita hadarine ga rayuwarsa."
Babu damuwa ya ansa wayar yasa mai sannan yayi mashi asauka lfy.

Lallashin Rafeea take tana cewa"kiyi hkr muje gida kinga dare yayi nasan sai nasha fad'a wajen baba da mama,tashi kiyi hkr inkinje gida kisanar da Abbanku nasan dole zai daukar maki mataki,dole ne ma wannan."
Tashi tayi tana share kwallarta don har ga Allah mari ya shigeta ba kadanba.
Dr ne ya iso wajen yana cewa"kiyi hkr Rafee,atu karki sanar da Alhaji kiyafe mashi bai cikin hayyacinsa hakan tafaru."
Cikin masifa tace "shine zai juye haukanta sa akaina wlh saina fad'a ai gabanka yayi man wannan zalincin ko kuma baka dauki mataki ba",ta nufi motarta tana masifa.

Tafiya suke zuwa gida fiyah tace"kinsan dr ne Rafeea."
Tsaki taja tace"likitan kakane shike zuwa har gida yana dubata duk karshen wata."
Jinjina kai tayi tace"amman baza kiyi hkr ba Rafeea kiyafe mai tun da kinji cewar baya cikin hayyacinsa hakan tafaru,don inkin lura hannunsa jini yake fitarwa,kuma sai yanzu na ganeshi shine wanda d'azun na taso makaranta aka bankeshi kan titin central park,na yarda da dr da yace bai cikin hayyacinsa ki yafe mai."

Tsaki taja tana kara gudun motar don tuni angama sallar mangaruba,
"Ki kyaleni fiyah,wlh saiya gane cewa ya tab'o yar gidan Alh muazzam Canji."
Shiru fiyah tayi don daman tasan za,ai hakan Rafeea na da fada aji wajen mahaifinta,don kuwa ita dayace mace wajensa,jida ita yake sosai duk abunda takeso yi mata yake,kuma duk wanda ya tab'ata yashiga uku don bazai kyaleshi ba.
Saboda haka mahaifin fiyah baison alakarsu,don dai kurun mahaifiyarta macece mai tsananin kirki da mutunci,shiyasa yake d'an barinta tana shiga gidan kuma take hudda da Rafeea,badan ransa yasoba.don yadda duk estate din suka kafa mashi k'ahon zuk'a akan zamanshi cikinsu,shiyasa yake iyakar yinsa don ganin ya kiyaye abunda zai saka suci mashi mutunci.

Har suka isa gida fiyah bata sake cewa komi ba godiya tayi mata da kuma saida safe kowace ta shige gidansu.

"Assalamu alaikum...........ina kika tsaya sofiyya badai kijin maganata ko,bance inkinga wannan yarinyar zata shiriritar dakeba ki kamo hanya kidawo gida,banson wannan alakar taki da ita ko kad'an kinsani,amman ina hakuri ne saboda mutuncin uwarta,amman inbacin haka bazan bari kina shigewa wadannan mutanen a da basu san mutuncin mu ba."
Duk Malam kabir El-ladan ne yake wannan fadan watau mahaifi ga sofiyya.
Sadda kai tayi tana idasa shigowa cikin gidan,durk'usawa tayi gabanshi cikin ladabi da biyayya tace"baba kayi hkr wlh akullum ina kokarin kiyaye duk abunda kake gaya man,matsala aka samu shiyasa amman dawuri muka taho."
Ta zayyane mashi duk abunda yafaru tacigaba da cewa"wlh baba dagaske Rafeea take zata iya fa da ma Abban su kuma har prison yana iya kaishi."
Baban yace "Allah ya kyauta,ni shiyasa banson kina shiga motarta yanzu dada tsotsai wani abu yafaru fa,ki kiyaye ba koda yaushe zaki ringa shiga motar ta ba kinjiko mamana."
D'aga kai tayi tace"insha Allah baba zan kiyaye kayi hkr."
"Shikenan,nayi tashi kije kiyi sallah Allah yayi maki albarka."
Tashi tayi tana ansawa da Ameen maman tace intayi sallar tazo ga abincinta nan ta d'auka,shigewa tayi d'akinsu tana magana da yesmin dake ta faman gugar uniform.
"Yaushe kika dawo yesmin."
Tace"Adda nah nima ban jima ba uncle yahya ya ka woni bajima wa,anty tace gobe inkin taso kibiya tana da magana dake."
Kayan ta ke cirewa tare da cewa"uhm ni wlh Anty zata matsaman kan wani kanen mijinta,ki kyaleta kawai yesmin ni 6allemun wannan abar."
Tana juya mata baya ta 6alle mata bra d'inta.

*************

Tunda suka dawo gidan malik baiyyi gigin sake mashi magana ba,don yasan yanzu zai sake burkicewa babu mai taimakonsa kuma,don unguwarsu ba sosai mutane ke shiga sabgar da batasu ba.
Malik ya dawo daga masallaci sallar isha,i ya samai falo shima ya gama tashi sallar agida yana d'auke praymate d'in.
Girgiza kai yayi kawai don baisan yadda zai yasa Alfah cigaba da yin sallah cikin jam,i ba,ko masallacin bai zuwa duk sallar dazai tofa cikin daki zaiyyita.fuskarnan kamar kullum tur6une babu walwala babu rahma kanta.
Zama yayi yana kallonsa kafin yace mashi.
"Me zakaci abokina"
Kallon banza ya wurga mai kurun yana cigaba da opreting system d'insa,xuwa can ya ajiye ya tashi yaje gaban frig ya bude win d'insa ya dauko ya cire hancin,ya bulbula ga cup ya koma mazauninsa yana kurb'a yana aikinsa,....kallon bakin ciki da takaici kawai malik kemashi,don baima san yazaiyyi da Alfah ba,idan akwai abunda yatsana cikin halayyarsa sabbi to bai wuce wannan shan win d'in da yake ba.
Kasa hakuri yayi yace mashi"Wai Alfah mai yasa kakeson kashe kanka,meyasa kai rayuwa baka daukar komi da sauki,duk abunda Allah ya kaddara maka baka hkr karok'esa sassauci,ina anfanin wannan halayyar daka k'irk'iro ma kanka...........cikin masifa dazafin zuciya ya jefar da cup din glass din dake hannunsa ya fashe kasa,yana huci.
Yanuna malik da hannu yace"kafita harkata malik,kadaina takurani da kalamanka,komi nake komi zanyi is not ur business."
Hawaye suka cika idon malik yace"komi zakace kuma kome zakayi man Alfah wlh saina gaya maka gaskiya,koda kuwa kasheni zakai wlh saina fad'a,don kuwa ina kaunarka inason rayuwarka idan kai bakason ta,ka taimakeni ka kulaman da ita,idan narasaka Alfah yakake son inyi,banfa da kowa saikai.Allahne gatana kaine gatana.plsss karage shan win d'inan koda baka bari dukaba dr ya sanar dani yadda tayi maka illah."
Kwallarsa suka silalo kan fuskara yaciga ba da cewa"Allah yasan da abunda yafaru baka da laifi,amman ya6oye gaskiyarsa saboda yana son jarabtarka yaga iyakar imanin ka,duk wannan ba daidai bane,kuma kaima kasani kake take sanin.....cikin sanyin murya ya katse malik da cewa"enough!and i'm sorry to hut u."
Tashi yayi yashige bedroom d'insa da system d'in sa ga hannu.

Murmushi malik yayi yace "thank god,yaushe rabon da naji irin wannan sweet voice d'in naka Alfah,ina maka fatan Allah ya sanyaya zuciyarka ya kuma kawo mani matai makin da zamu taru mudawo dakai cikin rayuwa mai kyau.

*sorry jiya banyi update ba in busy ne kuyi hkr.*

Mrs bbce
Mom muhseen😘
[9/17, 3:35 PM] Fauziya Madaki: 💞💞💞💞💞💞💞
*ABDOUL-NASSER*
*(ALFAH)*

WRITING BY.

MRS BB
MOM MUHSEEN.

WATTPAD NAME
HUMAIRA7531.

*DEDUCATED TO ZAUREN MRS BB AND ALFAH FANS*

🅿️.........4
Chapter 3 · 0% Book details