Sashe 99
Uwar Sadiku Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Suna zuwa bayan likita yayi mata tambayoyi ya rubuta mata gwaje-gwaje yace taje tayi ta kawo sakamakon yanzu. Suka wuce suka nufi dakin gwajin da yake cikin asibitin.
Ba tare da bata lokaci ba aka dauki jinita aka yi gwajin aka miko musu takardun, ana mikowa ta karbe. Ta bude; guda daya gwajin malaria ne kuma binciken ya nuna akwai malaria din dayar kuma gwajin cikin kuma shima ya nuna akwai ciki. Dama tayi tunanin hakan sai dai ta riga ta cire rai da haihuwa musamman yanda taga shekarun Abban sun ja kuma itama yanzu tana jin kamar ta wuce haihuwa, shi yasa ma tafi karkata ga malaria din.
Yanayin yanda ta ninke takardun yasa Abban ya zare takardun daga hannunta ya bude ya karanta. Ya leka fuskarta yana dariya yace
'Haba, ni na san wannan aman ya fi karfin malaria. Alhamdulillah! Allah ya sa ‘yan biyu ne mata.’
Ta kalleshi yanda yake murna kamar wani yaro tace
'In sha Allahu daya ne.’
'In sha Allahu biyu ne tunda sau biyu kika karba.’
Ta jijjiga kai kawai suka shige office din likitan yana mata dariya.
Likitan ya kara yi musu bayani sannan ya canza mata magani ya sallamesu suka kama hanya.
Suna zama a mota ta dubeshi fuskarta da damuwa tace
'Yanzu don Allah yaushe za a gama aikin gidan nan na koma, ka ga ba sai Hajiya da Anti Uwani sun gane nayi ciki tun ban koma ba.’
Yanayin yanda take magana ya bashi dariya, ya kuwa kyalkyale da dariya yayinda ita kuma ta bishi da harara. Yace
'To menene? Ai ni na san ni nayi.’
'Ni dai gara na koma din.’
Ya gintse dariyarsa saboda ya kula da yanda take kara shan kunu
'Nan da sati biyu, ai Anti Uwani ma ta tayaki laulayin.’
Ta harareshi ta zumbura baki tace
‘Kuma ya ka kama hanyar gida bayan ka ce sayayya zamu je?’
'Mu bari sai zuwa gobe kafin nan kin kara samun sauki sai mu je.’
Ta sake hade fuska tace
'Yanzu zamu je don ko ka je gidan ma ba zan fita daga motar nan ba, muje kawai muyi sayayyara.’
Ya sake gintse dariya ya kalli gefen tagarsa, ya karya kan mota suka nufi kasuwa.
Ya fahimci so take suje suyi sayayyar don ta koma da wuri kafin a gane tana da ciki, shi kuwa yanda yaji dadin cikin nan bai ki aje gidan radio ma a fada ba. Haka suka karasa shagon kayan dakin inda ta nuna duk wadanda take so ya biya kudin sannan suka tafi bayan ya bada adireshin gidan da lambar Saddikun don idan sun gama loda kayan su kai.
Yana tsayar da motar a kofar gidan ta kalleshi tace
'Yaushe zasu gama kafa kayan?’
Har ya fara dariya ya gintse saboda yanda ta bata rai tana shirin fashewa da kuka, ta kama hannun motar zata fita yayi sauri ya riketa. Yace
'Tsaya kiji mana.’
Ta gyara zama ta kalli gaba tana kaucewa idonsa
'Kinga gobe ma ya isa su gama daurawa in ya so jibi sai nazo mu tafi ko?’
Kai kawai ta daga masa. Sukayi sallama a kan ta shirya kayanta zai zo jibin ya juya ya nufi gidan.
………
Kamar yanda yayi mata alkawari haka aka yi. Ya zo da kansa ya dauketa suka koma gidan. Cikin walwala tayi sallama da su Hajiya da su Abdallah; wadanda suma nan da sati biyu zasu koma gidan kanin babansu wato Baba Abba. Ta shiga mota suka kama hanya.
Tayi zaton zata tarar da su Rukayya a gidan sai dai ga mamakinta babu kowa daga ita sai shi. Haka suka zagaya ya nuna mata dakinta da nashi sannan ya nuna mata sauran sassan gidan. Bayan sun koma saman ne ta tambayeshi ina yaran, ya bata amsa
'Saddiku yana nan fita yayi, amma kafin magriba zaki ga ya dawo. Su Rukayya kuma sai next week Yaya zai dawo dasu kafin nan kin shirya gidan yanda kike so.’
'Allah ya kai mu.’
'Kayanki na can gidan ma sai muje gobe ki kwaso wadanda kike bukata sauran kuma ki fadi yanda za ayi miki dasu ko?’
'Allah ya kai mu.’
Ya fice yayinda ta cigaba da kintsa kayanta a dakin.
Ta ji dadin yanda yayi mata kofar shiga dakinsa ta cikin dakinta, yanda zata iya shiga dakinsa ba tare da yaransa sun san ina take ba; musamman matan da dakinsu yake saman a kusa da nata.
……….
Bayan sati daya da tarewarsu Yaya Bello ya kawo su Rukayya. Ya sake yiwa Aishan nasiha da kuma bata hakuri sannan yayi musu sallama ya tafi.
Nan da nan suka hau hidima anata baje kaya.
Rukayya ta fito da keken dinkinta ta cewa Abban ya kamata ayi masa table, nan take kuwa ya amsa da alkawari zuwa wani satin za a yi mata table tunda ta kusa candy kafin admission ya fito sai ta samu ta koyi dinkin.
Haka suka cigaba da rayuwarsu cikin walwala.
_
Tunda suka je gidan Yaya Bello yake faman yiwa Yusra nasiha a kan ta samu ta bawa Aisha hakuri amma sam ta ki. Idan akayi magana sai tace wai ai ta kirawota itace taki saurararta.
Kafin ya mayar da su Rukayya ma sai da ya sa Umman Muhammad tayi mata magana amma da aka tambayeta sai tace ta yiwa Aishan waya wai Aishan ce ba zata fadi gaskiya ba saboda bata son Yusran. Haka suka kyaleta saboda Umman su Muhammad din ta gane karya takeyi kuma tana jinta a lokuta daban-daban tana gayawa yaran cewa idan dai sai ta bawa Aisha hakuri zata zauna a gidan to sai dai ta hakura da zaman gidan ta san Abbanta ya zabi matarsa a kanta. Don haka Yaya Bello yace a barta a nan din kawai don ya kula idan ma ta koma can din ba zata yiwa Aishan biyayya ba.
___
Satinsu uku da tarewa a gidan aka fara azumin Ramadan. Cikin walwala suka gabatar da azuminsu, inda kullum Jummai da yaran suke taya Aisha hada abincin shan ruwa.
Ranar Juma'a ya kama ranar Sallah, don haka washegarin Sallah ranar asabar Yaya Bello da kansa ya kawo su Yusra da Nana tare da nasa yaran, yayi musu sallama a kan zai dawo ya daukesu da magriba.
Cikin walwala Aishan ta karbesu don dama bata da niyyar yanke musu zumuncinsu, sai dai ko gaisuwa Yusra tayi mata ne albarkar idon Yaya Bello. Yana fita ta ja su Sumayya suka shige dakinsu na kasa.
Ita kuwa Aisha sai ta hau saman ta sa mukulli ta kulle duk dakunan da suke saman ta sauko da mukullin. Ya zama dakin su Rukayya na sama ne kawai yake a bude. Ta dawo ta zauna a falon kasa cikin yaran suna ta raha ana ciye-ciye. Suna nan zaune Yusra ta fito daga dakinsu rike da hannun Sumayya suka haye saman, a hankali ta dinga hawa benen ko Aishan zata ce wani abu sai dai har ta haye bata ko kalli wajen ba.
Bayan ta gama ganin dakin kannenta ta fito a gadarance ta nufi dakin Aisha, sai dai tana kama hannun kofar dakin taji a rufe. Haka ta bi duk dakunan har kicin ta jisu a rufe don haka tayi kwafa suka sauko, ta koma dakinsu na kasan ba tare da ta cewa kowa komai ba yayinda ita kuma Sumayya ta kwace ta koma cikin ‘yan uwanta suka cigaba da wasansu da Hanan ‘yar wajen Yaya Bello.
Sai bayan da suka idar da sallar la'asar sannan Nana ta samu taja Rukayya suka fito tsakar gidan, ta dubeta idonta ya ciko da kwalla tace
'Yaya Rukayya ni na fi so na zauna a gidan nan don Allah ki cewa Abba ko Anti nima a dawo dani.'
Rukayyan tace
'Wani abun ake miki a gidan Baban?’
'Kema kin san dai babu abinda za a yi min amma dai ai nan ne gidan mu ko? Kawai na fi son nan.’
'To kije ki cewa Anti Aisha kina so ki zauna, da kanta zata gayawa Abban sai kawai a barki a kawo miki kayan.’
Ta sunkuyar da kai tayi shiru na dan lokaci, ta dago ta share kwalla tace
'Yaya Yusra tace kada mu bata hakuri zata raina mu kuma cutar damu zatayi, amma ni dai ina son zama a nan.’
Rukayya tayi dariya tace
'To ki biyewa Yaya Yusra kiyi ta shan wahala a banza, baki gaji da wahala bane.’
Nan Yaya; Yar wajen Yaya Bello yayar Hanan ta fito ta samesu don itama duk da sa'ar Yusra ce amma ta fi kusanci da Rukayya saboda ta fi saukin mu'amala. Rukayya ta dafa Nana tace
‘Kije ina nan.’
Ta shigo falon jikinta a sanyaye. Babu kowa a falon sai Saddiku da yake zaune a kan dining table yana karatu a computer dinsa don yanzu ya sami gurbin karatu a BUK inda yake karantar Computer Engineering. Ya kalli Nanan tana tafiya kamar wadda kwai ya fashe mata a ciki, yace
'Ke, zo nan.’
Ta karasa ta tsaya a kusa dashi.
'Menene haka kike sanda kamar wata mara gaskiya.’
'Yaya so nake na zauna a nan shine Yaya Rukayya tace naje na gayawa Anti.'
Ya harareta
'Kina so ki zauna saboda Yusra ta dinga aikoki kina mata rashin kunya ko?’
'Wallahi Yaya ba haka bane, ita Yaya Yusra ma bata san zan zauna ba don tace kada na kuskura na bata hakuri na bari ita zata sa a koreta a dawo damu.’
Ya yi mata fada sosai tare da gargadin kada ta kuskura ta sake sauraren Yusra in ba haka ba da kanshi zai mayar da ita gidan Baban, sannan yace
'Antin tana kicin, kije ki gaya mata.’
Ta juya ta wuce kicin din inda Aisha da Jummai suke kokarin dora tuwon dare.
Har ta shiga kicin din Aishan bata ce mata komai ba don ta zata wajen Jummai ta shigo, sai da ta tsaya a gefenta ta kirawota cikin sanyin murya
'Anti.'
Ta juyo tace
'Na'am Nana. Ya akayi?’
'Anti don Allah ki cewa Abba a barni a nan gidan ni gaskiya na fi so na yi zamana a nan.’
Ta bita da kallo na dan lokaci sannan tayi murmushi tace
'To Nana zan gaya masa.’
Da mamaki ta dago idonta kalleta don bata zata zata amsa da sauri haka ba, tace
Ba tare da bata lokaci ba aka dauki jinita aka yi gwajin aka miko musu takardun, ana mikowa ta karbe. Ta bude; guda daya gwajin malaria ne kuma binciken ya nuna akwai malaria din dayar kuma gwajin cikin kuma shima ya nuna akwai ciki. Dama tayi tunanin hakan sai dai ta riga ta cire rai da haihuwa musamman yanda taga shekarun Abban sun ja kuma itama yanzu tana jin kamar ta wuce haihuwa, shi yasa ma tafi karkata ga malaria din.
Yanayin yanda ta ninke takardun yasa Abban ya zare takardun daga hannunta ya bude ya karanta. Ya leka fuskarta yana dariya yace
'Haba, ni na san wannan aman ya fi karfin malaria. Alhamdulillah! Allah ya sa ‘yan biyu ne mata.’
Ta kalleshi yanda yake murna kamar wani yaro tace
'In sha Allahu daya ne.’
'In sha Allahu biyu ne tunda sau biyu kika karba.’
Ta jijjiga kai kawai suka shige office din likitan yana mata dariya.
Likitan ya kara yi musu bayani sannan ya canza mata magani ya sallamesu suka kama hanya.
Suna zama a mota ta dubeshi fuskarta da damuwa tace
'Yanzu don Allah yaushe za a gama aikin gidan nan na koma, ka ga ba sai Hajiya da Anti Uwani sun gane nayi ciki tun ban koma ba.’
Yanayin yanda take magana ya bashi dariya, ya kuwa kyalkyale da dariya yayinda ita kuma ta bishi da harara. Yace
'To menene? Ai ni na san ni nayi.’
'Ni dai gara na koma din.’
Ya gintse dariyarsa saboda ya kula da yanda take kara shan kunu
'Nan da sati biyu, ai Anti Uwani ma ta tayaki laulayin.’
Ta harareshi ta zumbura baki tace
‘Kuma ya ka kama hanyar gida bayan ka ce sayayya zamu je?’
'Mu bari sai zuwa gobe kafin nan kin kara samun sauki sai mu je.’
Ta sake hade fuska tace
'Yanzu zamu je don ko ka je gidan ma ba zan fita daga motar nan ba, muje kawai muyi sayayyara.’
Ya sake gintse dariya ya kalli gefen tagarsa, ya karya kan mota suka nufi kasuwa.
Ya fahimci so take suje suyi sayayyar don ta koma da wuri kafin a gane tana da ciki, shi kuwa yanda yaji dadin cikin nan bai ki aje gidan radio ma a fada ba. Haka suka karasa shagon kayan dakin inda ta nuna duk wadanda take so ya biya kudin sannan suka tafi bayan ya bada adireshin gidan da lambar Saddikun don idan sun gama loda kayan su kai.
Yana tsayar da motar a kofar gidan ta kalleshi tace
'Yaushe zasu gama kafa kayan?’
Har ya fara dariya ya gintse saboda yanda ta bata rai tana shirin fashewa da kuka, ta kama hannun motar zata fita yayi sauri ya riketa. Yace
'Tsaya kiji mana.’
Ta gyara zama ta kalli gaba tana kaucewa idonsa
'Kinga gobe ma ya isa su gama daurawa in ya so jibi sai nazo mu tafi ko?’
Kai kawai ta daga masa. Sukayi sallama a kan ta shirya kayanta zai zo jibin ya juya ya nufi gidan.
………
Kamar yanda yayi mata alkawari haka aka yi. Ya zo da kansa ya dauketa suka koma gidan. Cikin walwala tayi sallama da su Hajiya da su Abdallah; wadanda suma nan da sati biyu zasu koma gidan kanin babansu wato Baba Abba. Ta shiga mota suka kama hanya.
Tayi zaton zata tarar da su Rukayya a gidan sai dai ga mamakinta babu kowa daga ita sai shi. Haka suka zagaya ya nuna mata dakinta da nashi sannan ya nuna mata sauran sassan gidan. Bayan sun koma saman ne ta tambayeshi ina yaran, ya bata amsa
'Saddiku yana nan fita yayi, amma kafin magriba zaki ga ya dawo. Su Rukayya kuma sai next week Yaya zai dawo dasu kafin nan kin shirya gidan yanda kike so.’
'Allah ya kai mu.’
'Kayanki na can gidan ma sai muje gobe ki kwaso wadanda kike bukata sauran kuma ki fadi yanda za ayi miki dasu ko?’
'Allah ya kai mu.’
Ya fice yayinda ta cigaba da kintsa kayanta a dakin.
Ta ji dadin yanda yayi mata kofar shiga dakinsa ta cikin dakinta, yanda zata iya shiga dakinsa ba tare da yaransa sun san ina take ba; musamman matan da dakinsu yake saman a kusa da nata.
……….
Bayan sati daya da tarewarsu Yaya Bello ya kawo su Rukayya. Ya sake yiwa Aishan nasiha da kuma bata hakuri sannan yayi musu sallama ya tafi.
Nan da nan suka hau hidima anata baje kaya.
Rukayya ta fito da keken dinkinta ta cewa Abban ya kamata ayi masa table, nan take kuwa ya amsa da alkawari zuwa wani satin za a yi mata table tunda ta kusa candy kafin admission ya fito sai ta samu ta koyi dinkin.
Haka suka cigaba da rayuwarsu cikin walwala.
_
Tunda suka je gidan Yaya Bello yake faman yiwa Yusra nasiha a kan ta samu ta bawa Aisha hakuri amma sam ta ki. Idan akayi magana sai tace wai ai ta kirawota itace taki saurararta.
Kafin ya mayar da su Rukayya ma sai da ya sa Umman Muhammad tayi mata magana amma da aka tambayeta sai tace ta yiwa Aishan waya wai Aishan ce ba zata fadi gaskiya ba saboda bata son Yusran. Haka suka kyaleta saboda Umman su Muhammad din ta gane karya takeyi kuma tana jinta a lokuta daban-daban tana gayawa yaran cewa idan dai sai ta bawa Aisha hakuri zata zauna a gidan to sai dai ta hakura da zaman gidan ta san Abbanta ya zabi matarsa a kanta. Don haka Yaya Bello yace a barta a nan din kawai don ya kula idan ma ta koma can din ba zata yiwa Aishan biyayya ba.
___
Satinsu uku da tarewa a gidan aka fara azumin Ramadan. Cikin walwala suka gabatar da azuminsu, inda kullum Jummai da yaran suke taya Aisha hada abincin shan ruwa.
Ranar Juma'a ya kama ranar Sallah, don haka washegarin Sallah ranar asabar Yaya Bello da kansa ya kawo su Yusra da Nana tare da nasa yaran, yayi musu sallama a kan zai dawo ya daukesu da magriba.
Cikin walwala Aishan ta karbesu don dama bata da niyyar yanke musu zumuncinsu, sai dai ko gaisuwa Yusra tayi mata ne albarkar idon Yaya Bello. Yana fita ta ja su Sumayya suka shige dakinsu na kasa.
Ita kuwa Aisha sai ta hau saman ta sa mukulli ta kulle duk dakunan da suke saman ta sauko da mukullin. Ya zama dakin su Rukayya na sama ne kawai yake a bude. Ta dawo ta zauna a falon kasa cikin yaran suna ta raha ana ciye-ciye. Suna nan zaune Yusra ta fito daga dakinsu rike da hannun Sumayya suka haye saman, a hankali ta dinga hawa benen ko Aishan zata ce wani abu sai dai har ta haye bata ko kalli wajen ba.
Bayan ta gama ganin dakin kannenta ta fito a gadarance ta nufi dakin Aisha, sai dai tana kama hannun kofar dakin taji a rufe. Haka ta bi duk dakunan har kicin ta jisu a rufe don haka tayi kwafa suka sauko, ta koma dakinsu na kasan ba tare da ta cewa kowa komai ba yayinda ita kuma Sumayya ta kwace ta koma cikin ‘yan uwanta suka cigaba da wasansu da Hanan ‘yar wajen Yaya Bello.
Sai bayan da suka idar da sallar la'asar sannan Nana ta samu taja Rukayya suka fito tsakar gidan, ta dubeta idonta ya ciko da kwalla tace
'Yaya Rukayya ni na fi so na zauna a gidan nan don Allah ki cewa Abba ko Anti nima a dawo dani.'
Rukayyan tace
'Wani abun ake miki a gidan Baban?’
'Kema kin san dai babu abinda za a yi min amma dai ai nan ne gidan mu ko? Kawai na fi son nan.’
'To kije ki cewa Anti Aisha kina so ki zauna, da kanta zata gayawa Abban sai kawai a barki a kawo miki kayan.’
Ta sunkuyar da kai tayi shiru na dan lokaci, ta dago ta share kwalla tace
'Yaya Yusra tace kada mu bata hakuri zata raina mu kuma cutar damu zatayi, amma ni dai ina son zama a nan.’
Rukayya tayi dariya tace
'To ki biyewa Yaya Yusra kiyi ta shan wahala a banza, baki gaji da wahala bane.’
Nan Yaya; Yar wajen Yaya Bello yayar Hanan ta fito ta samesu don itama duk da sa'ar Yusra ce amma ta fi kusanci da Rukayya saboda ta fi saukin mu'amala. Rukayya ta dafa Nana tace
‘Kije ina nan.’
Ta shigo falon jikinta a sanyaye. Babu kowa a falon sai Saddiku da yake zaune a kan dining table yana karatu a computer dinsa don yanzu ya sami gurbin karatu a BUK inda yake karantar Computer Engineering. Ya kalli Nanan tana tafiya kamar wadda kwai ya fashe mata a ciki, yace
'Ke, zo nan.’
Ta karasa ta tsaya a kusa dashi.
'Menene haka kike sanda kamar wata mara gaskiya.’
'Yaya so nake na zauna a nan shine Yaya Rukayya tace naje na gayawa Anti.'
Ya harareta
'Kina so ki zauna saboda Yusra ta dinga aikoki kina mata rashin kunya ko?’
'Wallahi Yaya ba haka bane, ita Yaya Yusra ma bata san zan zauna ba don tace kada na kuskura na bata hakuri na bari ita zata sa a koreta a dawo damu.’
Ya yi mata fada sosai tare da gargadin kada ta kuskura ta sake sauraren Yusra in ba haka ba da kanshi zai mayar da ita gidan Baban, sannan yace
'Antin tana kicin, kije ki gaya mata.’
Ta juya ta wuce kicin din inda Aisha da Jummai suke kokarin dora tuwon dare.
Har ta shiga kicin din Aishan bata ce mata komai ba don ta zata wajen Jummai ta shigo, sai da ta tsaya a gefenta ta kirawota cikin sanyin murya
'Anti.'
Ta juyo tace
'Na'am Nana. Ya akayi?’
'Anti don Allah ki cewa Abba a barni a nan gidan ni gaskiya na fi so na yi zamana a nan.’
Ta bita da kallo na dan lokaci sannan tayi murmushi tace
'To Nana zan gaya masa.’
Da mamaki ta dago idonta kalleta don bata zata zata amsa da sauri haka ba, tace