Sashe 37
Uwar Sadiku Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ta shiga kicin ta dauko babban faranti ta juye musu kifin gaba daya da chips din kamar yanda suka saba, ta dauko ta dawo da shi tsakiyar falon kan kafet din ta ajiye musu; don in ya siyo irin wannan cimar basa zama a table a kasa ake bajewa. Bayan ta ajiye ta dauko ice cream din roba daya ta zauna ta fara sha.
Ya shigo falon da sallama ya karasa ya zauna a gaban tray din yana fadin
‘Ice cream din ai zai fi dadi idan kika gama cin kifin sarkin shan sanyi.’
Tace
‘Ka fara ci gani nan zuwa.’
Saida ya gaji ya fara cin kifin sannan ta ajiye robar ice cream din ta sauko, ta zauna a gaban farantin sai kuma ta dube shi tace
‘Wallahi kamar ma ba zan ci kifin ba, karninsa hawa kaina yake babu dadi.’
Da mamaki ya dubeta
‘Haba dai, ai ko yaya ne kya ci. Don ke fa na siyo kifin nan kuma kice ba zaki ci ba.’
‘Ba zaka gane ba.’
Ta fada tana kawar da kai.
Ya yago tsokar kifin ya nade yankan dankali guda biyu a ciki ya dora yankan albasa a kai ya nufo bakinta yana fadin
‘Naga kwana biyu laziness ya miki yawa bari kawai na baki a baki ki huta.’
Tana dariya ta bude bakin ya saka mata ba don tana so ba sai don bata so yaga kamar wani abune ya sa bata son ci don ta san duk cikin neman shiri ne kuma ita abun ya wuce a wajenta.
Da kyar ta hadiye lomar kifin nan, tana hadiyewa amai ya taso mata. Nan take ta mike ta fada bandaki da yake cikin falon, ba tare da bata lokaci ba ya bi bayanta. A gaban toilet ta tsuguna tayi ta amai yana mata sannu; har saida ta amayar da duk wani abu da yake cikinta. Tana mikewa zata fito daga bandakin kuma jiri ya fara dibanta, don haka nan da nan ya riketa suka dawo falo ya zaunar da ita.
‘Sannu Aisha, baki da lafiya ne ko yau kifin karni yake da yawa haka?’
A jigace tayi murmushi tace
‘Bana jin dadi dama kwana biyun nan jiri yana dan damuna.’
Duk yanda ta so ya kyaleta ta kwanta ki yayi saida ta tashi a daren suka tafi asibiti. Asibitin da yake zuwa nan ya kaita kuma da yake na kudine suna zuwa aka samu likita ya dubata.
Nan take aka tabbatar masa da Aisha tana dauke da ciki sati hudu, sai dai likita yace lallai ta dinga cin abinci kuma tana shan ruwa don yunwa ce take galabaitar da ita.
Tun a hanya yake tamabayarta ko da akwai wani abu da take son ci tace tuwo take so, don haka suna dawowa gidan ya zuba mata tuwon da ta dafa ya hada mata shayi ya sata a gaba saida taci. Bayan ya kwashe kwanukan ya dawo ya zauna ya dubeta yace
‘Sannu, ina jin ma dai wannan ‘yan biyu ne shi yasa ya zo da karfinsa.’
Ta harareshi ta bude baki a jigace tace
‘Tunda ba kai zaka haihu ba ai dole kace haka.’
Haka ya kare kwana biyun nan cikin tattalin Aisha, sosai kuma taji kwarin jikinta tunda baya barinta da yunwa. Sata yake a gaba duk mitarta sai taci abinci don yana ce mata yanzu haka wancan cikin ma yana tafiya Saudiya ta fara zama da yunwa shi yasa cikin ya zube.
………
Ko da ya dawo kwanan Zahra ma haka ya cigaba da zarya wajen Aisha, tun bai gaya mata ba har dai ya gaji da yanda take masa kallon zargi ya sanar da ita Aishan ce bata da lafiya. Tun daga wannan lokacin ta saka Rukayya a gaba da tambayoyi har saida ta gane ciki ne da ita.
Tana samun wannan tabbacin ta kirawo Malam ta sanar dashi; domin bata so Aisha ta haihu ko sau daya tunda akwai yiwuwar ta haifi namiji. Ita kuma yanda ta cika gidan da yara mata ba zata taba bari haka ta kasance ma. Auren Aishan ma da take fatan nan da wani lokaci ta kawo karshensa kuma bata so a fita a bar mata wani yaro don haka ma gara kawai kada Aishan ta haihu.
A nan Malam yayi mata alkawarin cewa Aisha bazata haifi wannan cikin ba amma dai ta bari zuwa lokacin da za a gama aikinta wanda akeyi yanzu sannan sai a san yanda za ayi da cikin.
Sai a lokacin ta samu natsuwa ta cigaba da harkokinta, duk wata rawar kai da Abban yakeyi ta daina damunta don ta san da an gama mata aiki gidan Aishan zai gagareshi shiga kamar yanda Malam ya gaya mata.
……….
Ranar da suka cika sati biyu da zuwa gaya Malam ya kirawota ya sanar da ita an gama aiki don haka ta zo ko ta turo a karba. Nan da nan ta kirawo Amina domin ita take so ta je ta karbo mata. Bayan ta gama yiwa Aminan bayani tace
‘Yanzu ya za ayi kawata, bana son tura wani ayi min wasa da aiken nan kuma wallahi ba lallai na samu ya barni komawa Gaya ba kwanan nan.’
Aminan tace
‘Kinga ma ni wallahi motata ta sami matsala, naira dubu hamsin makanike yake nema a wajena ta gagareni shi yasa ma kwana biyu bana fita da motar.’
‘kai kwata.’
‘Allah, kuma kinga ba zan iya zuwa Gaya a motar haya ba, ko kece ma zaki ba zan raka ki ba wallahi in dai a motar haya ne.’
Sukayi shiru na dan lokaci kowa da abinda yake tunani. Ragowar kudin Zahra ne a hannun Aminan wajen Naira dubu dari da sittin da tace ta cigaba da ajiye mata su zata hada na daya babban aikin a wajenta. Ta riga ta kashe kudin gaba daya don haka take neman hanyar da zata bi ba sai ta biya ba. Zahran ce ta katse mata tunani
‘To kawata ki dauka mana a cikin ragowar kudin nan, ko nawane ki dauka in dai za a samu a gyara motar zuwa gobe ki sami damar zuwa.’
Da fara’arta ta amsa
‘Ai kuwa nagode, yanzu zan kirawo makanike yaje gida ya dauki motar in sha Allah zaki jini idan na dawo.’
Sukayi sallama kowacce cikin walwala.
…………
Washegari sai can bayan la’asar sannan Amina ta kirawo Zahra ta sanar da ita ta dawo kuma yanzu zata zarto ta kai mata.
A bakar leda irin ta VIVA ta shiga gidan da sakon, nan da nan Mommy ta mikawa Jummai Sumayya suka shige dakin baki na nan kasa suk kullo kofa.
Suna zama Aminan tace
‘Kawata kin taro match, akwai aiki fa.’
Ta zaro ido
‘Allah kawata bana jin komai idan bukata zata biya, kinga kuwa yanda matar nan take kokarin mayar da ni kalar kwatance? Ai komai ma zan iya yi.’
Ta zura hannu a ledar ta zaro wata karamar farar roba irin ta man shafawa ta mika mata, ta bude tana kallo ita kuma tana yi mata bayani.
‘Yaron Malam yace wannan abun sunanshi kwarjini, kuma sai da kara masa dubu talatin ya bayar. Yace idan kika kusa sauke abincinsa zaki saka a ciki, narkewa yake kamar kitse kuma bashi da wari. An yi sa ne musamman da sunanki a jiki, in dai yaci wannan ba zai sake yi miki musu ba duk abinda kike so shi zai yi.’
Ta jijjiga kai cike da farin ciki ta mayar ta rufe tana fadin
‘Ina kuma babban?’
Amina ta sake zura hannu cikin ledar ta fito da wata buta irin ta alwala, amma da bakin karfe aka yi ta. Ta mika mata tana fadin
‘Kada ki bude don Malam yace azabar wari gareshi. Shi kuma binnewa zakiyi a tsakar gidanta, yace in dai kika binne wannan a gidan da take to ko yaje ba zai iya zama ba balle ayi wata mu’amalar aure. Yana shiga zai fito.’
Ta janyo ledra ta mayar da butar, ta dubi Amina ta dafa hannunta tace
‘Na gode kawata, Allah ya bar zumunci. Kin nuna min kauna kawata wallahi baki san yanda naji dadi ba.’
‘Babu komai ai yiwa kaine.’
Cikin damuwa Zahran tace
‘Yanzu inda matsalar take yanda za ayi na sami wanda zai shiga gidan ya binne min wannan abun, don kin san nifa ban taba shiga ba don ba zan iya kayan takaici ba.’
Sukayi shiru na dan lokaci kowa yana tunanin yanda za ayi. Jimawa kadan Aminan tace
‘Kinga tunda shi yana da mukullin ki faki ido ki dauki hotonsa yau da daddarem nan in ya so sai ki turo min hoton ni kuma zan sa a samo me kama da shi a kawo miki zuwa gobe da safe. Jibi da safe sai ki faki idonsa ki zare na wajensa ki musanya masa don kar ya gane, tunda tana zuwa aiki yaron da zai kawo miki zai jiri in ya so da zarar Abban ya fita sai kawai ki bashi yaje ya bude gate ya shiga ya nemi waje can gefe daya ya binne. Yana dawowa tunda wajenki yake fara zuwa sai ki yi sauri ki mayar masa da mukullin.’
Ta mika mata hannu suka tafa
‘kawata kin san kan tsiya wallahi, gaskiya ban ma san irin godiyar da zan yi miki ba. In Sha Allahu yana dawowa zan turo miki hoton.’
Nan da nan suka gama sukayi sallama Aminan ta kama hanya saboda magriba ta kusa, tana tafe tana jin dadin ribar dubu talatin din da ta ci. Yanzu kudin Zahra saura dubu saba’in kenan a hannunta kuma su din ma cinyesu zata yi.
--------
Yanda Abban yake kula da ita ya sa laulayin yana yi mata sauki, wani abun har da gangan ma yi take yana biye mata sai kace wanda ba a taba yiwa haihuwa ba. Ya na yawan gaya mata yana sonta shi yasa yake so ta haifa masa yara masu kama da ita kuma masu irin dabi’arta.
Tun shekarar da ta wuce taso tayi masa bikin zagayowar ranar haihuwa; duk da ba kowa zata gayyato ba iya su biyu kawai; sai kuma ya zama waccan shekarar bata sami dama ba a daidai lokacin. Don haka ta shiryawa wannan shekarar duk da laulayin nan yayi mata bazata.
Ya shigo falon da sallama ya karasa ya zauna a gaban tray din yana fadin
‘Ice cream din ai zai fi dadi idan kika gama cin kifin sarkin shan sanyi.’
Tace
‘Ka fara ci gani nan zuwa.’
Saida ya gaji ya fara cin kifin sannan ta ajiye robar ice cream din ta sauko, ta zauna a gaban farantin sai kuma ta dube shi tace
‘Wallahi kamar ma ba zan ci kifin ba, karninsa hawa kaina yake babu dadi.’
Da mamaki ya dubeta
‘Haba dai, ai ko yaya ne kya ci. Don ke fa na siyo kifin nan kuma kice ba zaki ci ba.’
‘Ba zaka gane ba.’
Ta fada tana kawar da kai.
Ya yago tsokar kifin ya nade yankan dankali guda biyu a ciki ya dora yankan albasa a kai ya nufo bakinta yana fadin
‘Naga kwana biyu laziness ya miki yawa bari kawai na baki a baki ki huta.’
Tana dariya ta bude bakin ya saka mata ba don tana so ba sai don bata so yaga kamar wani abune ya sa bata son ci don ta san duk cikin neman shiri ne kuma ita abun ya wuce a wajenta.
Da kyar ta hadiye lomar kifin nan, tana hadiyewa amai ya taso mata. Nan take ta mike ta fada bandaki da yake cikin falon, ba tare da bata lokaci ba ya bi bayanta. A gaban toilet ta tsuguna tayi ta amai yana mata sannu; har saida ta amayar da duk wani abu da yake cikinta. Tana mikewa zata fito daga bandakin kuma jiri ya fara dibanta, don haka nan da nan ya riketa suka dawo falo ya zaunar da ita.
‘Sannu Aisha, baki da lafiya ne ko yau kifin karni yake da yawa haka?’
A jigace tayi murmushi tace
‘Bana jin dadi dama kwana biyun nan jiri yana dan damuna.’
Duk yanda ta so ya kyaleta ta kwanta ki yayi saida ta tashi a daren suka tafi asibiti. Asibitin da yake zuwa nan ya kaita kuma da yake na kudine suna zuwa aka samu likita ya dubata.
Nan take aka tabbatar masa da Aisha tana dauke da ciki sati hudu, sai dai likita yace lallai ta dinga cin abinci kuma tana shan ruwa don yunwa ce take galabaitar da ita.
Tun a hanya yake tamabayarta ko da akwai wani abu da take son ci tace tuwo take so, don haka suna dawowa gidan ya zuba mata tuwon da ta dafa ya hada mata shayi ya sata a gaba saida taci. Bayan ya kwashe kwanukan ya dawo ya zauna ya dubeta yace
‘Sannu, ina jin ma dai wannan ‘yan biyu ne shi yasa ya zo da karfinsa.’
Ta harareshi ta bude baki a jigace tace
‘Tunda ba kai zaka haihu ba ai dole kace haka.’
Haka ya kare kwana biyun nan cikin tattalin Aisha, sosai kuma taji kwarin jikinta tunda baya barinta da yunwa. Sata yake a gaba duk mitarta sai taci abinci don yana ce mata yanzu haka wancan cikin ma yana tafiya Saudiya ta fara zama da yunwa shi yasa cikin ya zube.
………
Ko da ya dawo kwanan Zahra ma haka ya cigaba da zarya wajen Aisha, tun bai gaya mata ba har dai ya gaji da yanda take masa kallon zargi ya sanar da ita Aishan ce bata da lafiya. Tun daga wannan lokacin ta saka Rukayya a gaba da tambayoyi har saida ta gane ciki ne da ita.
Tana samun wannan tabbacin ta kirawo Malam ta sanar dashi; domin bata so Aisha ta haihu ko sau daya tunda akwai yiwuwar ta haifi namiji. Ita kuma yanda ta cika gidan da yara mata ba zata taba bari haka ta kasance ma. Auren Aishan ma da take fatan nan da wani lokaci ta kawo karshensa kuma bata so a fita a bar mata wani yaro don haka ma gara kawai kada Aishan ta haihu.
A nan Malam yayi mata alkawarin cewa Aisha bazata haifi wannan cikin ba amma dai ta bari zuwa lokacin da za a gama aikinta wanda akeyi yanzu sannan sai a san yanda za ayi da cikin.
Sai a lokacin ta samu natsuwa ta cigaba da harkokinta, duk wata rawar kai da Abban yakeyi ta daina damunta don ta san da an gama mata aiki gidan Aishan zai gagareshi shiga kamar yanda Malam ya gaya mata.
……….
Ranar da suka cika sati biyu da zuwa gaya Malam ya kirawota ya sanar da ita an gama aiki don haka ta zo ko ta turo a karba. Nan da nan ta kirawo Amina domin ita take so ta je ta karbo mata. Bayan ta gama yiwa Aminan bayani tace
‘Yanzu ya za ayi kawata, bana son tura wani ayi min wasa da aiken nan kuma wallahi ba lallai na samu ya barni komawa Gaya ba kwanan nan.’
Aminan tace
‘Kinga ma ni wallahi motata ta sami matsala, naira dubu hamsin makanike yake nema a wajena ta gagareni shi yasa ma kwana biyu bana fita da motar.’
‘kai kwata.’
‘Allah, kuma kinga ba zan iya zuwa Gaya a motar haya ba, ko kece ma zaki ba zan raka ki ba wallahi in dai a motar haya ne.’
Sukayi shiru na dan lokaci kowa da abinda yake tunani. Ragowar kudin Zahra ne a hannun Aminan wajen Naira dubu dari da sittin da tace ta cigaba da ajiye mata su zata hada na daya babban aikin a wajenta. Ta riga ta kashe kudin gaba daya don haka take neman hanyar da zata bi ba sai ta biya ba. Zahran ce ta katse mata tunani
‘To kawata ki dauka mana a cikin ragowar kudin nan, ko nawane ki dauka in dai za a samu a gyara motar zuwa gobe ki sami damar zuwa.’
Da fara’arta ta amsa
‘Ai kuwa nagode, yanzu zan kirawo makanike yaje gida ya dauki motar in sha Allah zaki jini idan na dawo.’
Sukayi sallama kowacce cikin walwala.
…………
Washegari sai can bayan la’asar sannan Amina ta kirawo Zahra ta sanar da ita ta dawo kuma yanzu zata zarto ta kai mata.
A bakar leda irin ta VIVA ta shiga gidan da sakon, nan da nan Mommy ta mikawa Jummai Sumayya suka shige dakin baki na nan kasa suk kullo kofa.
Suna zama Aminan tace
‘Kawata kin taro match, akwai aiki fa.’
Ta zaro ido
‘Allah kawata bana jin komai idan bukata zata biya, kinga kuwa yanda matar nan take kokarin mayar da ni kalar kwatance? Ai komai ma zan iya yi.’
Ta zura hannu a ledar ta zaro wata karamar farar roba irin ta man shafawa ta mika mata, ta bude tana kallo ita kuma tana yi mata bayani.
‘Yaron Malam yace wannan abun sunanshi kwarjini, kuma sai da kara masa dubu talatin ya bayar. Yace idan kika kusa sauke abincinsa zaki saka a ciki, narkewa yake kamar kitse kuma bashi da wari. An yi sa ne musamman da sunanki a jiki, in dai yaci wannan ba zai sake yi miki musu ba duk abinda kike so shi zai yi.’
Ta jijjiga kai cike da farin ciki ta mayar ta rufe tana fadin
‘Ina kuma babban?’
Amina ta sake zura hannu cikin ledar ta fito da wata buta irin ta alwala, amma da bakin karfe aka yi ta. Ta mika mata tana fadin
‘Kada ki bude don Malam yace azabar wari gareshi. Shi kuma binnewa zakiyi a tsakar gidanta, yace in dai kika binne wannan a gidan da take to ko yaje ba zai iya zama ba balle ayi wata mu’amalar aure. Yana shiga zai fito.’
Ta janyo ledra ta mayar da butar, ta dubi Amina ta dafa hannunta tace
‘Na gode kawata, Allah ya bar zumunci. Kin nuna min kauna kawata wallahi baki san yanda naji dadi ba.’
‘Babu komai ai yiwa kaine.’
Cikin damuwa Zahran tace
‘Yanzu inda matsalar take yanda za ayi na sami wanda zai shiga gidan ya binne min wannan abun, don kin san nifa ban taba shiga ba don ba zan iya kayan takaici ba.’
Sukayi shiru na dan lokaci kowa yana tunanin yanda za ayi. Jimawa kadan Aminan tace
‘Kinga tunda shi yana da mukullin ki faki ido ki dauki hotonsa yau da daddarem nan in ya so sai ki turo min hoton ni kuma zan sa a samo me kama da shi a kawo miki zuwa gobe da safe. Jibi da safe sai ki faki idonsa ki zare na wajensa ki musanya masa don kar ya gane, tunda tana zuwa aiki yaron da zai kawo miki zai jiri in ya so da zarar Abban ya fita sai kawai ki bashi yaje ya bude gate ya shiga ya nemi waje can gefe daya ya binne. Yana dawowa tunda wajenki yake fara zuwa sai ki yi sauri ki mayar masa da mukullin.’
Ta mika mata hannu suka tafa
‘kawata kin san kan tsiya wallahi, gaskiya ban ma san irin godiyar da zan yi miki ba. In Sha Allahu yana dawowa zan turo miki hoton.’
Nan da nan suka gama sukayi sallama Aminan ta kama hanya saboda magriba ta kusa, tana tafe tana jin dadin ribar dubu talatin din da ta ci. Yanzu kudin Zahra saura dubu saba’in kenan a hannunta kuma su din ma cinyesu zata yi.
--------
Yanda Abban yake kula da ita ya sa laulayin yana yi mata sauki, wani abun har da gangan ma yi take yana biye mata sai kace wanda ba a taba yiwa haihuwa ba. Ya na yawan gaya mata yana sonta shi yasa yake so ta haifa masa yara masu kama da ita kuma masu irin dabi’arta.
Tun shekarar da ta wuce taso tayi masa bikin zagayowar ranar haihuwa; duk da ba kowa zata gayyato ba iya su biyu kawai; sai kuma ya zama waccan shekarar bata sami dama ba a daidai lokacin. Don haka ta shiryawa wannan shekarar duk da laulayin nan yayi mata bazata.