Sashe 43
Uwar Sadiku Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ya jijjiga kai yana murmushi; Rukayya tana son Aisha kuma Aisha tana son Rukayya sai dai yana sane da yanda Zahra ta hana wannan alakar kulluwa.
Tunda Zahra ta tafi airport yake tunani ko yace Aishan ta dawo nan gidan don watakila nata gidan ne yake warin sai dai idan ya tuna da fitnar Zahra sai ya fasa, haka yayi ta tunani ba tare da ya samo mafita ba . Daga baya bacci ya kwashe shi a kan kujerar.
Ita kuwa Rukayya tana saukowa ta gayawa Anti Rahma Abba yace taje don zata dinga taya Anti Aisha kwana. Nan take kuwa ta hada kayanta ta fice daga gidan.
Duk yanda Rahma ta so Yusra ta sa hannu wajen hidimar gidan nan ta ki, ta fahimci Zahra ce kawai take saka Yusra abu tayi don haka ta kyaleta. Ita da Jummai suke duk aiki. Don haka a dole ta nemi Jummai da ta dinga bari bayan isha’i ta dinga tafiya.
Sai wajen goman na dare a lokacin Nigeria sannan Zahra ta sami layi ta kirawo mutanen gida.
Bayan sun gaisa da Abba ta sanar da shi abinda ake ciki ta nemi ya bata yaran. Nan take ya kirawo Yusra ya mika mata wayar yana fadin
‘Ga Mommy, idan kun gama ki kawo min wayar.’
Sai da Mommy ta gaisa da kowa har Rahama, har Sumayya ma saida tayi ta surutunta a waya, da suka gama Yusra ta karbi wayar. Tana karba Mommy tace
‘Ina Rukayya ne? Ko tana wajen Abba?’
Tace
‘Hmm! Mommy ai kina tafiya yace ta hada kayanta ta koma gidan matarsa.’
Take jikinta yayi matukar sanyi. Tsoronta daya kada yaje kafin ta dawo ya koma zuwa gidan Aisha. Ta tuna da alkawarin da Yaron Malam yayi mata; to amma gashi tana tafiya har ya tura Rukayya, lallai idan bata yi da gaske ba idan ta dawo sai an sake mata aiki a kan Abba.
Shirun yayi yawa don haka Yusra tace
‘Mommy kina ji na?’
‘Ina jinki Yusra, zan dawo na samesu ita da Abban.’
Sukayi sallama Yusra ta mayarwa da Abban wayarsa.
………..
Tunda Yusra ta gaya mata Rukayya ta koma gidan Aisha ta kasa sukuni, duka wani buri da ta ciwo a kan zata zo tayi ta tuba tana ibada a nan ta watsar . Hankalinta gaba daya ya taho gida; ita da yaron Malam yace mata ko shekara nawa zatayi a Saudi Abba ba zai nemi Aisha ba gashi har ya fara shinshine-shinshine?
Lallai tana da aiki a gabanta.
Tun a wannan lokacin ta fara Allah-Allah ta gama Umrar ta koma gida, haka dai ta kasa natsuwa tayi ibada yanda ya kamata.
Ta sanarwa Yusrar ta sa mata ido da zarar ta ga wani canji a wajen Abban idan ta bugo ta sanar da ita. Kasancewar ta san ta bar Yusran a gidan ya sa ta dan sami natsuwa don ta san duk abinda ya faru a gidan sai ta gaya mata kuma tana dawowa zata dauki matakin da ya dace.
---------
Lokacin Sahur ne, kowa ya sauko ya ci abincinsa amma har an kusa ayi assalatu bata ga Sadik ya shigo daukar nasa abincin ba kamar yanda ya saba. Don haka ta zuba masa abincin ta bude kofar gidan ta fito a wannan daren ta nufi boys quarters din.
Da akwai wuta don haka bata bukatar fitila, ta zagaya ta hau barandar boys quarters din a hankali, kofar dakin a bude take kuma da alama basu ji motsin shigowarta ba sai da ta karasa har bakin kofa.
Sadik din yana tsaye a gaban irin teburin robar nan, kwalbar magani ce a hannunsa wadda yake juyewa a cikin robar lemon coke babbar, kusa da robar kuma kwayoyin magani ne kanana guda hudu a kan takarda. Kafin ta karasa sallamar da ta fara yayi sauri ya dure maganin ya ajiye kwalbar ya gyara tsayuwarsa ya kare abinda yakeyi.
Abokinsa wanda yake kuryar dakin wanda bai hango me yake faruwa ba yace
‘Kana da matsala, kayi sauri ka hada mana kayan nan don wallahi ni ko an yi assalatu sai na sha don ba zan iya kai azumin ba idan ban chake ba wallahi.’
Saida ta karasa shigowa dakin sannan abokin nasa ya gane dalilin daga masa hannun da Sadik din yake faman yi. Ta ajiye flask din a gefen Sadik din tana fadin
‘Abincin Sahur ne ba kazo ka karba ba Sadiku shi yasa na kawo maka ka na ga an kusa assalatu.’
Ya shafa kai yana wani kifta ido yana fadin
‘Dama yanzu zan zo ai, makara muka dan yi ne.’
Har tayi kamar zata tafi tayi wuf ta shammaceshi ta dauke robar coke din, da kwalabar maganin da kwayoyin da bai riga ya dura a robar ba; ta fice daga dakin tana fadin
‘Wallahi shaye-shaye kakeyi Saddiku sai na nunawa Abbanka, har Mommy ma sai na nuna mata.’
Kafin yayi wani yunkuri ta fice da hanzari.
Tana fita shi da abokin nasa sukayi tsuru-tsuru; nan da nan dabara ta fadowa Sadikun. Ya sallami abokin nasa ya sa maigadi ya bude masa gate ya fice. Ya koma dakin ya dauki abincin ya juya kamar yaci sannan ya koma ya kwanta. Ya dauki waya ya kirawo Mommy, tana dauka yace
‘Mommy kinga Anti Rahma ko, haka kawai ban san me ya kawota dakina ba yanzun nan tana shigowa ta ga robobi a kan tebur tace wai Ina shaye-shaye. Kuma wallahi Mommy ba nawa bane Balele ne ya manta su da yake a nan ya Sha ruwa don ni ban ma san menene ba tunda a robar coke ne. Na gaya mata ba nawa bane amma ta tafi da su wai sai ta gayawa Abba ina shaye-shaye.’
‘Subhanallah! Bana son karya Saddiku, idan kana shan wani abu ka gaya min idan ma baka sha ka gaya min.’
‘Wallahi Mommy kema kin san babu abinda nake sha haka kawai dai take son yin min sharri. Kuma ina jin Jummai ce ta saka ta don itace me cewa ta ga murfin magani a bq din.’
‘Tabbasa biri yayi kama da mutum! Bari na kirawo Abban naka, su kuma duk zasu ji daga gareni. Na rasa me yasa suke nemana da sharri musamman ma Jummai.’
Motsin Abban ya jiyo ya taho dakin a fusace yayi sauri ya katse wayar ya kifeta, ya juya kamar yana bacci.
Da karfi ya bangaji kofar yana shiga dakin ya sa hannu ya kunna fitila.
‘Sadik.’
Ya kirawo sunanshi a fusace.
A tsaye Sadik din yake a kan katifarsa ya jingina da bango da alamar razana a fuskarsa.
‘Na’am.’
Ya amsa a firgice.
Ya karewa dakin kallo sannan yace
‘Ina abokin naka da kuke shaye-shayen tare?’
Ya zaro ido
‘Shaye-shaye Abba? Ai babu kowa ni kadai nake kwana, jiya ne ma da aka sha ruwa abokaina suka zo su uku kuma da muka tafi asham daga can suka wuce ni kadai nake kwana.’
Ya juyo ya kalli Rahma wadda take tsaye a bayansa, tace
‘Ai kuwa sai dai in yanzu yaron nan ya fita don yana nan har maganar da yake fada naji.’
‘Wallahi Abba ni ban san wa ta gani ba kuma ni kadai na kwana a dakin nan kuma ka gani.’
Ya nuna masa robar coke din da kwalbar maganin da ke hannunsa yace
‘Wannan fa ko suma ba a nan aka dauka ba.’
Ya mariraice
‘Ba nawa bane Abba. Balele ne ya sha ruwa a nan jiya shine ya mantasu, wallahi ban san ma menene ba kuma ba nawa bane shi yasa ban dauke ba.’
‘Sadik, Sadiku ka bi a hankali. Zan bincika idan na kamaka da wani laifi tamu ce ni da kai. Shi kuma Balelen zai zo ya sameni, gobe zai bar min gidana. Daman na san yaron nan yana shaye-shaye sai anyi magana Mommy tace ba haka bane, gobe zai bar min gidana.’
Ba tare da yayi magana ba ya fice daga dakin.
Rahama ta kalli Sadiku suka hada ido yayi mata wata gajeriyar dariya ya fada kan katifarsa ya kwanta yana dariya.
Jijjiga kai kawai tayi ta janyo kafarta ta fito daga dakin.
A falon kasa ta sami Abban, yace
‘Kada ki damu zan bincika, yaran nan sun iya karya da dabara a kan abinda suke so, zan yi maganinsu. Gobe Malam Sule zai dawo ya karbi aiki, Balele ba zai sake shigo min gida ba.’
Jijjiga kai kawai tayi ta shige kichin; duk da Balele yana kama da ‘yan shaye-shaye ta san wannan ba kayansa bane za dai a koreshi ne ba da hakkinsa ba. Har yanzu tana mamakin Sadiku, lallai yaraon yau sai a barshi.
An riga na gama assalatu har an tayar da sallar asuba, don haka ta wuce dakin baki inda a nan take kwana tare da Sumayya da Ummi. Tayi alwala ta tayar da Sallah.
Bayan ta idar da sallah ta gama azkar dinta ta dauki wayarta don taga lokaci, tana dubawa taga ashe Zahra ta kirawota wajen sai biyar. Tana da dan credit dinta don haka ta dannawa Zahran flashing. Jimawa kadan ta kirawo, bayan sun gaisa tace
‘Sadik yace min kin dauki abinda ba shi ya ajiye a dakinsa ba kin kaiwa Abbansa.’
‘Eh, dama rashin fahimta me amma ai ya yiwa Abban bayani ma shike nan.’
‘To don Allah dai ko menene yaran nan sukayi a yi hakuri a jira sai na dawo ko a yi min waya, a daina saurin hadasu da ubansu; ni na baki amanarsu in sunyi wani abu ni zaki gayawa ba wani ba.’
‘To in Sha Allahu. Babu ma abinda sukeyi muna zaune lafiya ai.’
Sukayi sallama.
Rahma ta bi wayar da kallo; wato warning Zahra take mata a kan kada ta hada Sadik da Ubansa; lallai! Da ba dan anyi abu cikin girma da arziki da ita ba ma da yau zata bar gidan nan, amma tabbas idan ta tafi ba zata sake zama a gidan nan ba. Wato kenan su yaran Zahra ba za suyi laifi; tabbas ita ta san abinda ta gani kuma shima Sadikun ya sani don haka ma har ya kirawo me kare ma sa ya tsara mata karya da gaskiya . Um!
___
Tunda Zahra ta tafi airport yake tunani ko yace Aishan ta dawo nan gidan don watakila nata gidan ne yake warin sai dai idan ya tuna da fitnar Zahra sai ya fasa, haka yayi ta tunani ba tare da ya samo mafita ba . Daga baya bacci ya kwashe shi a kan kujerar.
Ita kuwa Rukayya tana saukowa ta gayawa Anti Rahma Abba yace taje don zata dinga taya Anti Aisha kwana. Nan take kuwa ta hada kayanta ta fice daga gidan.
Duk yanda Rahma ta so Yusra ta sa hannu wajen hidimar gidan nan ta ki, ta fahimci Zahra ce kawai take saka Yusra abu tayi don haka ta kyaleta. Ita da Jummai suke duk aiki. Don haka a dole ta nemi Jummai da ta dinga bari bayan isha’i ta dinga tafiya.
Sai wajen goman na dare a lokacin Nigeria sannan Zahra ta sami layi ta kirawo mutanen gida.
Bayan sun gaisa da Abba ta sanar da shi abinda ake ciki ta nemi ya bata yaran. Nan take ya kirawo Yusra ya mika mata wayar yana fadin
‘Ga Mommy, idan kun gama ki kawo min wayar.’
Sai da Mommy ta gaisa da kowa har Rahama, har Sumayya ma saida tayi ta surutunta a waya, da suka gama Yusra ta karbi wayar. Tana karba Mommy tace
‘Ina Rukayya ne? Ko tana wajen Abba?’
Tace
‘Hmm! Mommy ai kina tafiya yace ta hada kayanta ta koma gidan matarsa.’
Take jikinta yayi matukar sanyi. Tsoronta daya kada yaje kafin ta dawo ya koma zuwa gidan Aisha. Ta tuna da alkawarin da Yaron Malam yayi mata; to amma gashi tana tafiya har ya tura Rukayya, lallai idan bata yi da gaske ba idan ta dawo sai an sake mata aiki a kan Abba.
Shirun yayi yawa don haka Yusra tace
‘Mommy kina ji na?’
‘Ina jinki Yusra, zan dawo na samesu ita da Abban.’
Sukayi sallama Yusra ta mayarwa da Abban wayarsa.
………..
Tunda Yusra ta gaya mata Rukayya ta koma gidan Aisha ta kasa sukuni, duka wani buri da ta ciwo a kan zata zo tayi ta tuba tana ibada a nan ta watsar . Hankalinta gaba daya ya taho gida; ita da yaron Malam yace mata ko shekara nawa zatayi a Saudi Abba ba zai nemi Aisha ba gashi har ya fara shinshine-shinshine?
Lallai tana da aiki a gabanta.
Tun a wannan lokacin ta fara Allah-Allah ta gama Umrar ta koma gida, haka dai ta kasa natsuwa tayi ibada yanda ya kamata.
Ta sanarwa Yusrar ta sa mata ido da zarar ta ga wani canji a wajen Abban idan ta bugo ta sanar da ita. Kasancewar ta san ta bar Yusran a gidan ya sa ta dan sami natsuwa don ta san duk abinda ya faru a gidan sai ta gaya mata kuma tana dawowa zata dauki matakin da ya dace.
---------
Lokacin Sahur ne, kowa ya sauko ya ci abincinsa amma har an kusa ayi assalatu bata ga Sadik ya shigo daukar nasa abincin ba kamar yanda ya saba. Don haka ta zuba masa abincin ta bude kofar gidan ta fito a wannan daren ta nufi boys quarters din.
Da akwai wuta don haka bata bukatar fitila, ta zagaya ta hau barandar boys quarters din a hankali, kofar dakin a bude take kuma da alama basu ji motsin shigowarta ba sai da ta karasa har bakin kofa.
Sadik din yana tsaye a gaban irin teburin robar nan, kwalbar magani ce a hannunsa wadda yake juyewa a cikin robar lemon coke babbar, kusa da robar kuma kwayoyin magani ne kanana guda hudu a kan takarda. Kafin ta karasa sallamar da ta fara yayi sauri ya dure maganin ya ajiye kwalbar ya gyara tsayuwarsa ya kare abinda yakeyi.
Abokinsa wanda yake kuryar dakin wanda bai hango me yake faruwa ba yace
‘Kana da matsala, kayi sauri ka hada mana kayan nan don wallahi ni ko an yi assalatu sai na sha don ba zan iya kai azumin ba idan ban chake ba wallahi.’
Saida ta karasa shigowa dakin sannan abokin nasa ya gane dalilin daga masa hannun da Sadik din yake faman yi. Ta ajiye flask din a gefen Sadik din tana fadin
‘Abincin Sahur ne ba kazo ka karba ba Sadiku shi yasa na kawo maka ka na ga an kusa assalatu.’
Ya shafa kai yana wani kifta ido yana fadin
‘Dama yanzu zan zo ai, makara muka dan yi ne.’
Har tayi kamar zata tafi tayi wuf ta shammaceshi ta dauke robar coke din, da kwalabar maganin da kwayoyin da bai riga ya dura a robar ba; ta fice daga dakin tana fadin
‘Wallahi shaye-shaye kakeyi Saddiku sai na nunawa Abbanka, har Mommy ma sai na nuna mata.’
Kafin yayi wani yunkuri ta fice da hanzari.
Tana fita shi da abokin nasa sukayi tsuru-tsuru; nan da nan dabara ta fadowa Sadikun. Ya sallami abokin nasa ya sa maigadi ya bude masa gate ya fice. Ya koma dakin ya dauki abincin ya juya kamar yaci sannan ya koma ya kwanta. Ya dauki waya ya kirawo Mommy, tana dauka yace
‘Mommy kinga Anti Rahma ko, haka kawai ban san me ya kawota dakina ba yanzun nan tana shigowa ta ga robobi a kan tebur tace wai Ina shaye-shaye. Kuma wallahi Mommy ba nawa bane Balele ne ya manta su da yake a nan ya Sha ruwa don ni ban ma san menene ba tunda a robar coke ne. Na gaya mata ba nawa bane amma ta tafi da su wai sai ta gayawa Abba ina shaye-shaye.’
‘Subhanallah! Bana son karya Saddiku, idan kana shan wani abu ka gaya min idan ma baka sha ka gaya min.’
‘Wallahi Mommy kema kin san babu abinda nake sha haka kawai dai take son yin min sharri. Kuma ina jin Jummai ce ta saka ta don itace me cewa ta ga murfin magani a bq din.’
‘Tabbasa biri yayi kama da mutum! Bari na kirawo Abban naka, su kuma duk zasu ji daga gareni. Na rasa me yasa suke nemana da sharri musamman ma Jummai.’
Motsin Abban ya jiyo ya taho dakin a fusace yayi sauri ya katse wayar ya kifeta, ya juya kamar yana bacci.
Da karfi ya bangaji kofar yana shiga dakin ya sa hannu ya kunna fitila.
‘Sadik.’
Ya kirawo sunanshi a fusace.
A tsaye Sadik din yake a kan katifarsa ya jingina da bango da alamar razana a fuskarsa.
‘Na’am.’
Ya amsa a firgice.
Ya karewa dakin kallo sannan yace
‘Ina abokin naka da kuke shaye-shayen tare?’
Ya zaro ido
‘Shaye-shaye Abba? Ai babu kowa ni kadai nake kwana, jiya ne ma da aka sha ruwa abokaina suka zo su uku kuma da muka tafi asham daga can suka wuce ni kadai nake kwana.’
Ya juyo ya kalli Rahma wadda take tsaye a bayansa, tace
‘Ai kuwa sai dai in yanzu yaron nan ya fita don yana nan har maganar da yake fada naji.’
‘Wallahi Abba ni ban san wa ta gani ba kuma ni kadai na kwana a dakin nan kuma ka gani.’
Ya nuna masa robar coke din da kwalbar maganin da ke hannunsa yace
‘Wannan fa ko suma ba a nan aka dauka ba.’
Ya mariraice
‘Ba nawa bane Abba. Balele ne ya sha ruwa a nan jiya shine ya mantasu, wallahi ban san ma menene ba kuma ba nawa bane shi yasa ban dauke ba.’
‘Sadik, Sadiku ka bi a hankali. Zan bincika idan na kamaka da wani laifi tamu ce ni da kai. Shi kuma Balelen zai zo ya sameni, gobe zai bar min gidana. Daman na san yaron nan yana shaye-shaye sai anyi magana Mommy tace ba haka bane, gobe zai bar min gidana.’
Ba tare da yayi magana ba ya fice daga dakin.
Rahama ta kalli Sadiku suka hada ido yayi mata wata gajeriyar dariya ya fada kan katifarsa ya kwanta yana dariya.
Jijjiga kai kawai tayi ta janyo kafarta ta fito daga dakin.
A falon kasa ta sami Abban, yace
‘Kada ki damu zan bincika, yaran nan sun iya karya da dabara a kan abinda suke so, zan yi maganinsu. Gobe Malam Sule zai dawo ya karbi aiki, Balele ba zai sake shigo min gida ba.’
Jijjiga kai kawai tayi ta shige kichin; duk da Balele yana kama da ‘yan shaye-shaye ta san wannan ba kayansa bane za dai a koreshi ne ba da hakkinsa ba. Har yanzu tana mamakin Sadiku, lallai yaraon yau sai a barshi.
An riga na gama assalatu har an tayar da sallar asuba, don haka ta wuce dakin baki inda a nan take kwana tare da Sumayya da Ummi. Tayi alwala ta tayar da Sallah.
Bayan ta idar da sallah ta gama azkar dinta ta dauki wayarta don taga lokaci, tana dubawa taga ashe Zahra ta kirawota wajen sai biyar. Tana da dan credit dinta don haka ta dannawa Zahran flashing. Jimawa kadan ta kirawo, bayan sun gaisa tace
‘Sadik yace min kin dauki abinda ba shi ya ajiye a dakinsa ba kin kaiwa Abbansa.’
‘Eh, dama rashin fahimta me amma ai ya yiwa Abban bayani ma shike nan.’
‘To don Allah dai ko menene yaran nan sukayi a yi hakuri a jira sai na dawo ko a yi min waya, a daina saurin hadasu da ubansu; ni na baki amanarsu in sunyi wani abu ni zaki gayawa ba wani ba.’
‘To in Sha Allahu. Babu ma abinda sukeyi muna zaune lafiya ai.’
Sukayi sallama.
Rahma ta bi wayar da kallo; wato warning Zahra take mata a kan kada ta hada Sadik da Ubansa; lallai! Da ba dan anyi abu cikin girma da arziki da ita ba ma da yau zata bar gidan nan, amma tabbas idan ta tafi ba zata sake zama a gidan nan ba. Wato kenan su yaran Zahra ba za suyi laifi; tabbas ita ta san abinda ta gani kuma shima Sadikun ya sani don haka ma har ya kirawo me kare ma sa ya tsara mata karya da gaskiya . Um!
___