Sashe 38
Uwar Sadiku Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tun saura kwana biyu ranar ta tanadi duk wasu abubuwa da take bukata wadanda zata shirya masa abinci.
Ranar ta kama ranar Talata sannan kuma ba kwananta ba don haka haka dai ta shirya ta fice wajen aiki da niyyar idan ta dawo sai ta zo ta fara shiri. Batayi niyyar rikeshi ba don haka ta shirya idan ma abun zai zama damuwa tunda ba kwananta bane to idan ya shigo ya kwasa yaje can gidan Zahra din yaci. Ita dai kawai tana so ta burgeshi a ranar.
Bata gane an shiga gidan ba data dawo daga aiki domin yaron da Amina ta turowa Zahran irin yaran nan ne na unguwa da suka saba haura gidajen mutane suna yin sata. Yanda suka tsara masa haka yayi kuma kafin ya fito saida ya tabbatar ya kawar da duk wata alama da zata sa a zargi wani abu. Inda ya binne abun kuwa ma tsaf ya baje wajen kuma da yake baya ne daga nesa kadan da tagar dakin maigidan babu ma wanda zai gane.
Don haka tana dawowa daga aiki ta fada kicin; ta gasa cake dinta dan karamin don haka kwalliya kawai tayi masa ta mayar da shi fridge, ta gasa kaza gashin larabawa sannan ta hada masa lafiyayyaen salad da kunun aya. Ta siyo masa agogo mai matukar kyau da turare mai i dankaren tsada ta hada ta ninke a takarda mai kyalli ta ajiye masa a kan mudubi tare da wata karamar farar takarda da aka rubuta
“Happy Birthday My Love”
Idan ba kwananta bane sai an idar da sallar Isha’i yake shigowa, in ya gama hirarsa shine in ya koma can sai ya dawo mata da Rukayya. Don haka tana idar da sallar Magriba ta fada wanka, doguwar riga kawai tasa irin ta zaman gida sai turaruka da ta feshe jikinta da su. Duk da kamshin da gidan yake sai da ta kawo turarukan wuta masu dadin kamshi ta kara kunnawa domin so take ya ji dadi kuma ya tafi kwana biyun nan da kewarta.
Nan da nan gidan ya dau kamshi ga sanyi, Kuma da yake da akwai wuta sai abun ya kara armashi.
Kamar yanda ta zata kuwa ana idar da sallar isha’i ya shigo gidan.
Da sallama ya shigo kafin ya karaso ciki ta mike ta tareshi kamar yanda ta saba, ta fada jikinsa tana fadin
‘Sannu da zuwa.’
Dif walwalar fuskarsa ta dauke, sabanin da da in ta rungumeshi yake riketa, sai ya dan cireta daga jikinsa yana karewa gidan kallo. Ta dan matsa gefe tana kallonsa cikin damuwa, tace
‘Akwai wata matsala ne Yallabai?’
Cikin yatsina fuska yana waige-waige yace
‘Wani wari nake ji wallahi kuma a cikin gidan nan ne, ko kinyi amfani da wani abun ne me wari?’
Mamakinta ya karu, ya wuceta ya zauna a kujerar zaman mutum daya yayinda tabi bayansa tana fadin
‘Wari ko dai kamshi?’
‘A’a, wari ne mai karfi wallahi don har kaina ya fara ciwo.’
Ta karaso ta zauna a kusa da shi, tana zama ya mike kamar wanda aka tsikara. Ya dubeta yace
‘Kuma babu abinda kika shafa a jikinki ko na magani.’
‘Babu.’
Ya fara karewa gidan kallo yana dafe goshi, tana tsaye tana kallonsa tana mamakin da ya fara komawa tsoro. Ya dan kara matsawa daga kusa da ita yace
‘Bari na tafi kaina har ya fara ciwo, dama zuwa nayi nayi miki sai da safe zan turo miki Rukayyan yanzu.’
Kafin ta amsa ya wuceta ya fice daga falon ba tare da ya dubi dining table din da ta jera abincin ba harda balloon da ta rataye.
Tabi bayansa da kallo tana mamaki, ta kara bude kofofin hancinta ko zata ji warin da yace yana ji amma ita kamshi kawai take ji kuma kamshi mai dadi. Ta shansahana jikinta nan ma kamshi taji, ta dai tabbatar babu wari a gidan. To me yake faruwa? Me yasa da can bai ji warin ba saida shigo gidan?
Ta kalli abincin da ta ajiye a dining table, take kwalla ta cicciko mata ido, ta sa hannu ta goge.
Ta kashe kudi gashi ba dadi take ji ba ta daure ta hada masa abincin kawai don ta burgeshi kuma ya shigo da wannan matsalar. Take wani bakin ciki ya tokare mata kirji, ta dafe kirjin tana Lahaula.
Tana nan a zaune ta ji shigowar Rukayya, ya bude mata gate ya turo ta shi ya koma.
Nan da nan tayi sauri ta tsige balloon din ta kai kicin ta Huda ta sa a shara, tana fitowa ta sa hannu ta shafe rubutun da yake kan cake din sannan ta budewa Rukayya kofar falon ta shigo.
Ta karfin tsiya ta danne damuwarta, ta yanka kazar ta bawa Rukayya tata sannan itama ta dan ci wanda zata iya. Ta hade kayan ta saka a fridge tana mamaki da takaici da fatan gobe kada ya shigo da wannan matsalar.
UWAR SADDIKU
Written by
Sakina Yazid
(Innar su Amal)
23
Yana leko da kansa bakin gate din gidan Aisha yaji kamar an dauke wani gungumemen dutse da aka dora masa a kirjinsa, nan da nan ya nemi ciwon kai ya rasa. Ya kalli gefe da gefe ya ya kara bude kofofin hancinsa ya shaki iska ya ji babu wani wari. Ya juya ya kalli gate din yana mamaki, ya jijjiga kai cikin damuwa sannan ya kama hanyar gidan Zahra.
To wannan warin da takurar da yaji a gidan Aishan me ya kawota? Yana zaton dai warin da yaji ne ya haifar masa da duk sauran damuwar, to amma bai taba jin wari irin wannan ba. Abinda yafi bashi tsoro shine yanda kamar warin yake fitowa daga jikin Aisha. Shi tunda ya auri Aisha ko warin gumi bai taba ji a jikinta ba tunda ita din gwanar shafa turare ce. To me ta shafa yau din? Ko wani maganin ne? Amma ai lafiyarta kalau sai laulayi wanda shima yayi sauki sosai.
Haka ya shiga gidan yana ta faman neman dalili a kwakwalwarsa amma bai samu ba, sai dai yana fatan Allah ya sa tayi wanka ta shafa turare kafin gobe domin goben ne zata karbi kwana.
………
Da yake jiya shinkafa dafa duka ta dafa da daddare bata samu tayi amfani da maganin kwarjinin da aka bata ba, sai yau ta shirya tuwo miyar kuka. Ta sami ‘yar karamar tukunya ta debar masa tashi miyar ta mayar wuta ta saka maganin, tsaf ya bace kamar ba a sa wani abu ba. Ta lashi kadan a harshenta taji babu abinda ya canza na dandanon miyar, cikin murna ta juye a flsak ta kawo ta jera a dining table.
Yana dawowa daga gidan Aisha ya zauna a table ya cinye tuwonsa tas, tana gefensa tana yi masa hira domin ita tace masa yunwa take ji shi yasa ana yin magriba ta ci nata tuwon.
……..
Duk matar da ba a wajenta ya kwana ba ya saba shiga gidanta da safe, tun asuba yake tunanin yanda zaiyi ya shiga gidan Aisha don yana tsoron ya shiga yanayin da ya shiga jiya.
Bai ankara ba har takwas da rabi ta wuce, ya riga ya san ta tafi aiki. Don haka kawai sai ya cigaba da shirinsa.
Sai da ya shirya tsaf ya kama hanyar office sannan ya kirawota.
Lafiya kalau suka gaisa, yanda yaji walwalarta shima ya saukar masa da walwala. Ya sanar da ita bai fito da wuri ba ya zo ya tarar ta fice don haka sai ya dawo zasu hadu.
Sukayi sallama kowa yana walwala. Itama Aishan tsoron da ta kwana da shi na abinda ya faru ya gushe, don haka cikin walwala ta cigaba da gudanar da aikinta.
……….
Kamar yanda ta saba kafin a idar da sallar Magriba ta shirya abincin dare, ta bi gidan da turare haka ma jikinta. Kamshine kawai yake tashi ko ta ina.
Bayan yayi sallama da Zahra ya nufo gidan,gaba daya ma ya manta da abinda ya faru jiya sauri kawai yake ya je ya ganta saboda bai gantaba da safe.
Yana shiga bakin gate yanayin ya fara canzawa, a fili yace
‘Subhanallahi.’
Ya karewa farfajiyar gidan kallo kamar mai neman wani abu. Ya daure ya karasa cikin gidan.
Yana shiga falon kamar a nan warin yake; ta taso daga inda take zaune da fara’arta ta nufi shi, sai dai kafin ta karaso inda yake ta kula da yanayin da fuskarsa ta shiga. Ta dan tsaya nesa da shi tana kallonsa, cikin sanyin murya tace
‘Sannu da zuwa.’
Kamar a fusace ya amsa
‘Yauwa, wai me kike shafawa ne ko kike sakawa a gidan nan mai wannan azabar wari?’
Ta sunkuyar da kai tana kokarin danne kwalla tace
‘Babu fa abinda na saka, turaren wuta na ne kawai wanda ka saba dashi kuma kaima kana yaba dadinsa.’
‘Kai! wannan ba turare bane. Gashi kaina har ya fara juyawa, bari naje daga waje na sha iska amma don Allah ki caje gidan nan ko mushen wani abun nema a ciki ba a sani ba.’
Kafin ta amsa yayi waje.
Yana fitowa ya tsaya a bakin gate yana shakar iska yana mamaki, wannan wace irin musiba ce? Ita kuwa Aisha me take sawa a gidan nan? Ya kama hanya ya nufi gidan Zahra, taku kadan sai kuma ya tsaya. Ya tuna ai daga can ya fito kuma a nan ya kamata ya kwana, to ya za ayi ya bar Aishan ita kadai?
Ya tsaya chak ya kasa gaba ya kasa baya; ba zai iya kwana a gidan Aisha ba a halin da ake ciki to amma idan ya koma gidan Zahra me zai ce mata? Har ya fara gajiya da tsayuwa bai sami wata amsa ba, don haka yaja jikinsa a hankali ya nufi gidan Zahra zuciyarsa cike da matsananciyar damuwa.
Tana zaune a falon sama tana jiransa domin yaron Malam ya tabbatar mata indai an binne wannan abun to Abban Sadik ba zai sake iya kwana a gidan ba.
Tana jiyo motsin bude gate ta kyalkyale da dariya saboda jin dadi, tana jiyo takunsa a bene ta gyara zama ta saita fuskarta.
Da sallama ya shigo, bayan ta amsa sallamar tace
‘Mantuwa kayi ne?’
Cikin yanayi na damuwa yace
Ranar ta kama ranar Talata sannan kuma ba kwananta ba don haka haka dai ta shirya ta fice wajen aiki da niyyar idan ta dawo sai ta zo ta fara shiri. Batayi niyyar rikeshi ba don haka ta shirya idan ma abun zai zama damuwa tunda ba kwananta bane to idan ya shigo ya kwasa yaje can gidan Zahra din yaci. Ita dai kawai tana so ta burgeshi a ranar.
Bata gane an shiga gidan ba data dawo daga aiki domin yaron da Amina ta turowa Zahran irin yaran nan ne na unguwa da suka saba haura gidajen mutane suna yin sata. Yanda suka tsara masa haka yayi kuma kafin ya fito saida ya tabbatar ya kawar da duk wata alama da zata sa a zargi wani abu. Inda ya binne abun kuwa ma tsaf ya baje wajen kuma da yake baya ne daga nesa kadan da tagar dakin maigidan babu ma wanda zai gane.
Don haka tana dawowa daga aiki ta fada kicin; ta gasa cake dinta dan karamin don haka kwalliya kawai tayi masa ta mayar da shi fridge, ta gasa kaza gashin larabawa sannan ta hada masa lafiyayyaen salad da kunun aya. Ta siyo masa agogo mai matukar kyau da turare mai i dankaren tsada ta hada ta ninke a takarda mai kyalli ta ajiye masa a kan mudubi tare da wata karamar farar takarda da aka rubuta
“Happy Birthday My Love”
Idan ba kwananta bane sai an idar da sallar Isha’i yake shigowa, in ya gama hirarsa shine in ya koma can sai ya dawo mata da Rukayya. Don haka tana idar da sallar Magriba ta fada wanka, doguwar riga kawai tasa irin ta zaman gida sai turaruka da ta feshe jikinta da su. Duk da kamshin da gidan yake sai da ta kawo turarukan wuta masu dadin kamshi ta kara kunnawa domin so take ya ji dadi kuma ya tafi kwana biyun nan da kewarta.
Nan da nan gidan ya dau kamshi ga sanyi, Kuma da yake da akwai wuta sai abun ya kara armashi.
Kamar yanda ta zata kuwa ana idar da sallar isha’i ya shigo gidan.
Da sallama ya shigo kafin ya karaso ciki ta mike ta tareshi kamar yanda ta saba, ta fada jikinsa tana fadin
‘Sannu da zuwa.’
Dif walwalar fuskarsa ta dauke, sabanin da da in ta rungumeshi yake riketa, sai ya dan cireta daga jikinsa yana karewa gidan kallo. Ta dan matsa gefe tana kallonsa cikin damuwa, tace
‘Akwai wata matsala ne Yallabai?’
Cikin yatsina fuska yana waige-waige yace
‘Wani wari nake ji wallahi kuma a cikin gidan nan ne, ko kinyi amfani da wani abun ne me wari?’
Mamakinta ya karu, ya wuceta ya zauna a kujerar zaman mutum daya yayinda tabi bayansa tana fadin
‘Wari ko dai kamshi?’
‘A’a, wari ne mai karfi wallahi don har kaina ya fara ciwo.’
Ta karaso ta zauna a kusa da shi, tana zama ya mike kamar wanda aka tsikara. Ya dubeta yace
‘Kuma babu abinda kika shafa a jikinki ko na magani.’
‘Babu.’
Ya fara karewa gidan kallo yana dafe goshi, tana tsaye tana kallonsa tana mamakin da ya fara komawa tsoro. Ya dan kara matsawa daga kusa da ita yace
‘Bari na tafi kaina har ya fara ciwo, dama zuwa nayi nayi miki sai da safe zan turo miki Rukayyan yanzu.’
Kafin ta amsa ya wuceta ya fice daga falon ba tare da ya dubi dining table din da ta jera abincin ba harda balloon da ta rataye.
Tabi bayansa da kallo tana mamaki, ta kara bude kofofin hancinta ko zata ji warin da yace yana ji amma ita kamshi kawai take ji kuma kamshi mai dadi. Ta shansahana jikinta nan ma kamshi taji, ta dai tabbatar babu wari a gidan. To me yake faruwa? Me yasa da can bai ji warin ba saida shigo gidan?
Ta kalli abincin da ta ajiye a dining table, take kwalla ta cicciko mata ido, ta sa hannu ta goge.
Ta kashe kudi gashi ba dadi take ji ba ta daure ta hada masa abincin kawai don ta burgeshi kuma ya shigo da wannan matsalar. Take wani bakin ciki ya tokare mata kirji, ta dafe kirjin tana Lahaula.
Tana nan a zaune ta ji shigowar Rukayya, ya bude mata gate ya turo ta shi ya koma.
Nan da nan tayi sauri ta tsige balloon din ta kai kicin ta Huda ta sa a shara, tana fitowa ta sa hannu ta shafe rubutun da yake kan cake din sannan ta budewa Rukayya kofar falon ta shigo.
Ta karfin tsiya ta danne damuwarta, ta yanka kazar ta bawa Rukayya tata sannan itama ta dan ci wanda zata iya. Ta hade kayan ta saka a fridge tana mamaki da takaici da fatan gobe kada ya shigo da wannan matsalar.
UWAR SADDIKU
Written by
Sakina Yazid
(Innar su Amal)
23
Yana leko da kansa bakin gate din gidan Aisha yaji kamar an dauke wani gungumemen dutse da aka dora masa a kirjinsa, nan da nan ya nemi ciwon kai ya rasa. Ya kalli gefe da gefe ya ya kara bude kofofin hancinsa ya shaki iska ya ji babu wani wari. Ya juya ya kalli gate din yana mamaki, ya jijjiga kai cikin damuwa sannan ya kama hanyar gidan Zahra.
To wannan warin da takurar da yaji a gidan Aishan me ya kawota? Yana zaton dai warin da yaji ne ya haifar masa da duk sauran damuwar, to amma bai taba jin wari irin wannan ba. Abinda yafi bashi tsoro shine yanda kamar warin yake fitowa daga jikin Aisha. Shi tunda ya auri Aisha ko warin gumi bai taba ji a jikinta ba tunda ita din gwanar shafa turare ce. To me ta shafa yau din? Ko wani maganin ne? Amma ai lafiyarta kalau sai laulayi wanda shima yayi sauki sosai.
Haka ya shiga gidan yana ta faman neman dalili a kwakwalwarsa amma bai samu ba, sai dai yana fatan Allah ya sa tayi wanka ta shafa turare kafin gobe domin goben ne zata karbi kwana.
………
Da yake jiya shinkafa dafa duka ta dafa da daddare bata samu tayi amfani da maganin kwarjinin da aka bata ba, sai yau ta shirya tuwo miyar kuka. Ta sami ‘yar karamar tukunya ta debar masa tashi miyar ta mayar wuta ta saka maganin, tsaf ya bace kamar ba a sa wani abu ba. Ta lashi kadan a harshenta taji babu abinda ya canza na dandanon miyar, cikin murna ta juye a flsak ta kawo ta jera a dining table.
Yana dawowa daga gidan Aisha ya zauna a table ya cinye tuwonsa tas, tana gefensa tana yi masa hira domin ita tace masa yunwa take ji shi yasa ana yin magriba ta ci nata tuwon.
……..
Duk matar da ba a wajenta ya kwana ba ya saba shiga gidanta da safe, tun asuba yake tunanin yanda zaiyi ya shiga gidan Aisha don yana tsoron ya shiga yanayin da ya shiga jiya.
Bai ankara ba har takwas da rabi ta wuce, ya riga ya san ta tafi aiki. Don haka kawai sai ya cigaba da shirinsa.
Sai da ya shirya tsaf ya kama hanyar office sannan ya kirawota.
Lafiya kalau suka gaisa, yanda yaji walwalarta shima ya saukar masa da walwala. Ya sanar da ita bai fito da wuri ba ya zo ya tarar ta fice don haka sai ya dawo zasu hadu.
Sukayi sallama kowa yana walwala. Itama Aishan tsoron da ta kwana da shi na abinda ya faru ya gushe, don haka cikin walwala ta cigaba da gudanar da aikinta.
……….
Kamar yanda ta saba kafin a idar da sallar Magriba ta shirya abincin dare, ta bi gidan da turare haka ma jikinta. Kamshine kawai yake tashi ko ta ina.
Bayan yayi sallama da Zahra ya nufo gidan,gaba daya ma ya manta da abinda ya faru jiya sauri kawai yake ya je ya ganta saboda bai gantaba da safe.
Yana shiga bakin gate yanayin ya fara canzawa, a fili yace
‘Subhanallahi.’
Ya karewa farfajiyar gidan kallo kamar mai neman wani abu. Ya daure ya karasa cikin gidan.
Yana shiga falon kamar a nan warin yake; ta taso daga inda take zaune da fara’arta ta nufi shi, sai dai kafin ta karaso inda yake ta kula da yanayin da fuskarsa ta shiga. Ta dan tsaya nesa da shi tana kallonsa, cikin sanyin murya tace
‘Sannu da zuwa.’
Kamar a fusace ya amsa
‘Yauwa, wai me kike shafawa ne ko kike sakawa a gidan nan mai wannan azabar wari?’
Ta sunkuyar da kai tana kokarin danne kwalla tace
‘Babu fa abinda na saka, turaren wuta na ne kawai wanda ka saba dashi kuma kaima kana yaba dadinsa.’
‘Kai! wannan ba turare bane. Gashi kaina har ya fara juyawa, bari naje daga waje na sha iska amma don Allah ki caje gidan nan ko mushen wani abun nema a ciki ba a sani ba.’
Kafin ta amsa yayi waje.
Yana fitowa ya tsaya a bakin gate yana shakar iska yana mamaki, wannan wace irin musiba ce? Ita kuwa Aisha me take sawa a gidan nan? Ya kama hanya ya nufi gidan Zahra, taku kadan sai kuma ya tsaya. Ya tuna ai daga can ya fito kuma a nan ya kamata ya kwana, to ya za ayi ya bar Aishan ita kadai?
Ya tsaya chak ya kasa gaba ya kasa baya; ba zai iya kwana a gidan Aisha ba a halin da ake ciki to amma idan ya koma gidan Zahra me zai ce mata? Har ya fara gajiya da tsayuwa bai sami wata amsa ba, don haka yaja jikinsa a hankali ya nufi gidan Zahra zuciyarsa cike da matsananciyar damuwa.
Tana zaune a falon sama tana jiransa domin yaron Malam ya tabbatar mata indai an binne wannan abun to Abban Sadik ba zai sake iya kwana a gidan ba.
Tana jiyo motsin bude gate ta kyalkyale da dariya saboda jin dadi, tana jiyo takunsa a bene ta gyara zama ta saita fuskarta.
Da sallama ya shigo, bayan ta amsa sallamar tace
‘Mantuwa kayi ne?’
Cikin yanayi na damuwa yace