Sashe 55
Uwar Sadiku Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
‘Um ni so nake kawai a rabata da mijina, su rabu har abada kuma kada ya sake auren wata mace.’
Aka kyalkyale da dariya wadda har dakin saida ya amsa, sai dai ko da suka kalli fuskar malamin da suke gabansa babu alamar shi yake dariyar.
Ya mika hannunsa baya ya zaro wata babbar tasa wadda kusan za a iya cewa hannu daya ba zai iya dauka ba. Ya dire tasar wadda take dauke da ruwa a gabansu, ya dauki wata bakar kwalba a gabansa ya diga wani mai a cikin tasar sannan ya fara motsi da baki kamar mai wuridi. Lokaci kadan ya gama sambatun ya busa a tasar sannan ya dubi Zahra yace
‘Duba min nan.’
Amina ta dan dungureta suka matsa gaban tasar suka leka; Aisha ce sanye da abaya suna tafiya tare da Abban Sadik a wani wajen kamar farfajiyar masallacin Madina. Sai dai ita Aishan wani abu kamar glass ya yi mata kawanya shi kuma Abban yana gefenta babu abinda yayi masa kawanya.
‘Sune wadannan ko?’
Da mamaki take gyada kai tana
‘Eh, sune, sune.’
Aka sake bushewa da dariyar nan da basu san wanda yake yinta ba, sannan mutumin mai kakkausar murya ya nuna Aisha a cikin tasar yace
‘Kinga wannan, ba zata tabu ba. Ko me za ayi mata ba zai yi tasiri sosai ba domin ta fi ki shiri.’
Dariyar nan ta sake karade dakin, bayan ta lafa ya nuna Abba yace
‘Wannan za muyi miki aiki a kansa amma sai ya baro wajen nan da yake, idan ya dawo gida sai ki sanar damu.’
Cikin in ina tace
‘To ba zasu rabu ba kenan?’
Dariyar ta sake karade dakin, bayan anyi shiru yace
‘Aikin da zamu yi miki shine; zamu shafe masa ita daga tunaninsa. Zai manta da ita ya manta ya sake aure, ke duk wani wanda zai iya fada a ji ma a auren zamu mantar dashi labarin Aisha. Idan aka yi haka to tabbas ita da danginta zasu raba auren don bazasu iya tuna masa da ita ba, don auren ma ba shi zai saki ba sai dai suje kotu alkali ya saki. Daga ranar da mukayi aikin ba zai sake tunawa da ita ba.’
Dakin ya kuma cika da dariyar.
Ita kanta saida tayi murmushi saboda wannan tsarin nashi yayi mata,tabbas idan Abba ya manta da Aisha zuwa wani lokaci ne ‘yanuwanta zasu raba auren. Shikenan ta huta da wannan alakakan.
Kamar daga sama aka jefo wata karamar bakar tasa gabansu, mutumin yace
‘Ku juye duk abinda kuka zo da shi a nan.’
Nan da nan Zahra ta bude jakarta ta fito da kudin da ta zo da shi naira dubu dari biyu ta saka a tasar, a take tasar ta bace.
Mutumin yace
‘Idan ya dawo a zo a sanar da mu, zuwa lokacin dan matsuruto zai sanar da ku kudin aikin da zaku ajiye masa kafin aiki ya fara. Ku tafi, ku tafi.’
Nan da nan suka mike, yaron da ya shigo da su ne ya sake shigowa ya wuce musu gaba. Ya bi da su ta wata kofar da ban da ba ta nan suka shigo ba, sai a lokacin Zahra taga sun fito ta kofar gaban gidan daidai inda suka ajiye mota. Motocin da suka tarar da safe basa wajen sai dai wata bakar mota wadda da alama bayan sun shiga ne masu ita suka zo.
Ba tare da bata lokaci ba suka shiga mota suka kama hanya, nan dinma hanyar da suka bi ba ta ita suka fito ba.
Babu wanda yayi magana sai da suka fito daga daji suka hau kwalta. Amina ta dubi Alele da yake tuki tace
‘Alele duk mai abun da ka gani ka tsaya mu siya mu dan sa wani abun a bakinmu, na manta ban yiwo mana guzuri ba yunwa muke ji.’
‘To Hajiya, mun kusa zuwa wajen masu mangoron nan ai.’
Ta dubi Zahra tace
‘Kawata kin ga inda za a magance miki matsalarki ko? Yanda yayi miki alkawarin haka zai yi miki aiki zaki sha mamaki.’
‘Hmmmn! Ai na ga alama.’
Suka yi shiru kowacce tana kora ruwan robar da suka taho da shi.
Jimawa kadan Zahra tace
‘Kawata naji yana maganar kudin aiki bayan kudin da na ajiye masa.’
‘Eh, ai in dai kin shiga da jaka wannan dakin sai kin ajiye duk kudin da yake jakar a wannan tasar ko an yi aiki ko ba ayi ba. Kudin aiki kuma da ban za a sanar dake. Kawai idan zamu dawo ki sake ciko jaka.’
‘Hmm!’
Suka sake yin shiru na dan lokaci, jimawa kadan Zahra tace
‘Ni abu daya ne yake bani haushi, duk inda naje sai ace wai mutuniyarki bazata tabu ba. Na rasa waye malaminta a garin nan da bamu san shi ba.’
Amina tace
‘To tunda dai an sami makarinta ba shike nan ba, duk ma wanda yake mata aiki su karata. Idan ta rabu da mijinki duk ma yanda tayi ba shikenan ba.’
‘hakane kam, a sauka lafiya.’
Sai daga baya suka sami masu rogo sun fito daga wani kauye, suka saya sukayi ta ci har suka rage yunwa.
Saida aka idar da Sallar Magriba sannan suka ajiye Zahra a gida suka wuce, a kan idan alhazai sun dawo zasu koma a gama aiki.
UWAR SADDIKU
Written by
Sakina Yazid
(Innar su Amal)
30
Tunda suka dawo daga Doguwa kuma sai Zahra ta cigaba da harkokinta cikin walwala, musamman da yake yanzu gidan yana hannunta. Abu daya ne kawai bata sami yanda take so ba; ta riga ta tsara yanda zata yi yawon Sallah a motar Abban, sai dai kawai ranar da zasu tafi da motar ya fita ya kaita gidan Yaya Bello ya ajiye a can sanna Ali ya wuce da su airport.
Da ya sanar da ita wannan tsarin nasa da wuri da tabbas ta hanashi don da ya saba tafiya ya bar motarsa a gidan, amma dai wannan zuwa Doguwa ya wanke mata duk wata damuwa.
Nan da nan ta cigaba da shirin babbar Sallah da lissafin yanda zata kasafta naman san da ya bari a yanka.
__
Tunda suka isa kasa mai tsarki Aisha ta dukufa addu’a; duk abinda take so saida ta roka kuma ta yiwa Abbanta addu’a sosai.
Tare da Abba suke a hotel don haka ma bata sake tayi wata kawa ba tunda yawancin ibada ma tare suke zuwa, don haka ko kasuwa ma bata tunanin zuwa.
Saura kwana biyu arfa suna zaune ita da Abban sun gama cin abinci suna hutawa a dakinsu na otel suna dan taba hira . Kamar wadda aka tunawa ta dubeshi tace
‘Uhm, Dubai din zamu wuce ko Yallabai don ka ga shi yasa ba zan yi tsaraba a nan ba sai na je can.’
Ya harareta yana jijjiga kai
‘Wannan mata bata da mantuwa.’
Ta dan zaro ido
‘Da mijin zan manta ko kuwa da kaina?’
‘To zamu wuce kin ji dadi?’
Zumbur ta mike tsaye
‘Allah, dadi kai! Ai bari ma kaga nayi Sallah na yiwa Allah godiya tukunna.’
Sai da ta gama murnar ta tambayeshi nawa zata turo a kudinta da tace zata biya, yace ta turo dubu dari biyu account dinsa ya isa shi sai ya cika sauran.
Sai bayan ya nuna mata visa dinta sanna taga kwana bakwai yayi musu booking, ta ji dadi sosai don haka ta fasa duk wata sayayya ta mayar da hankali wajen ibada da kuma addu’a.
…………
Tunda suka tafi Saudiyya kusan kullum wayoyin Abban suna kashe, sai lokacin da ya zaba sai ya kunna suyi waya ta Whatsapp don ya ji lafiyar iyali. Tayi mita har ta gaji, don haka ya zama kawai sai dai ta bar masa sako a WhatsApp idan ya gani sai ya kirawota.
Tunda suka tafi ya ke shawarar tafiya da Aisha Dubai kuma yake tunanin yanda zai yiwa Zahra bayani ya rasa. Bayan Sallah da kwana hudu ya kama ranar zasu wuce Dubai kuma har ranar bai gayawa Zahra ba.
Kaf suka shirya kayansu ana yin sallar Magriba suka bi jirgi sai Dubai.
Sai da suka sauka a hotel suka huta sannan ya bude data.
Yana bude data kuwa kiran Zahra ya shigo kamar tana jiransa, a lokacin Aisha tana wanka. Ya amsa wayar ya fice daga dakin, ya dawo falon kasa wato reception na hotel din ya sami kujera ya zauna.
Bayan sun gaisa ya tambayi yaran, duka suna kusa da ita don haka ta bashi suka gaisa da kowa har Saddiku. Bayan ta karbi wayar suka dan taba hira, jimawa kadan yace
‘Yauwa ban gaya miki ba na wuce Dubai din fa, itama Aishan muna tare da ita a nan din tare zamu dawo.’
A dan razane tace
‘Um ban gane ba. Kace ita nan gida zata wuto?’
‘Eh. Na canza shawara daga baya tunda itama ta biyawa kanta kudin zuwa Dubai din kawai sai muka wuce.’
‘Um, Allah ya bada sa’a.’
‘Amin.’
Yanda yaji muryarta ta canza nan take ya san da sauran bayani, ya san idan ta fara mita abun zai daukesu lokaci don haka nan take yayi mata sallama ya kashe wayar.
…………
Kwanki biyun farko da sukayi a Dubai shi kadai yake fita tare da wanda aka hadashi don ya raka shi kamfanin da zai yi sayayya. Yana fita Aisha take komawa bacci, domin dama ta tara bacci a Saudiyya. Haka ya kwana biyu yana yawo ita kuma tana hutawa, don ko abinci har dakin ake kawo mata.
Sun riga sun gama magana da Aisha a kan ya saya mata waya in ya so ita kuma sai tayi tsaraba da kudinta; don haka fitarsu ta farko ya sayo mata Samsung hadaddiya mai tsadar gaske.
Suna komawa daki ta kasa hakura, saida ta kunna wayar nan. Suka hadu sukayi launching sabuwar waya.
Wayar ta hadu sosai kuma camera tana fitar da hoto don haka sai ya zama duk inda suka je haka zasuyi ta hotuna.
Aka kyalkyale da dariya wadda har dakin saida ya amsa, sai dai ko da suka kalli fuskar malamin da suke gabansa babu alamar shi yake dariyar.
Ya mika hannunsa baya ya zaro wata babbar tasa wadda kusan za a iya cewa hannu daya ba zai iya dauka ba. Ya dire tasar wadda take dauke da ruwa a gabansu, ya dauki wata bakar kwalba a gabansa ya diga wani mai a cikin tasar sannan ya fara motsi da baki kamar mai wuridi. Lokaci kadan ya gama sambatun ya busa a tasar sannan ya dubi Zahra yace
‘Duba min nan.’
Amina ta dan dungureta suka matsa gaban tasar suka leka; Aisha ce sanye da abaya suna tafiya tare da Abban Sadik a wani wajen kamar farfajiyar masallacin Madina. Sai dai ita Aishan wani abu kamar glass ya yi mata kawanya shi kuma Abban yana gefenta babu abinda yayi masa kawanya.
‘Sune wadannan ko?’
Da mamaki take gyada kai tana
‘Eh, sune, sune.’
Aka sake bushewa da dariyar nan da basu san wanda yake yinta ba, sannan mutumin mai kakkausar murya ya nuna Aisha a cikin tasar yace
‘Kinga wannan, ba zata tabu ba. Ko me za ayi mata ba zai yi tasiri sosai ba domin ta fi ki shiri.’
Dariyar nan ta sake karade dakin, bayan ta lafa ya nuna Abba yace
‘Wannan za muyi miki aiki a kansa amma sai ya baro wajen nan da yake, idan ya dawo gida sai ki sanar damu.’
Cikin in ina tace
‘To ba zasu rabu ba kenan?’
Dariyar ta sake karade dakin, bayan anyi shiru yace
‘Aikin da zamu yi miki shine; zamu shafe masa ita daga tunaninsa. Zai manta da ita ya manta ya sake aure, ke duk wani wanda zai iya fada a ji ma a auren zamu mantar dashi labarin Aisha. Idan aka yi haka to tabbas ita da danginta zasu raba auren don bazasu iya tuna masa da ita ba, don auren ma ba shi zai saki ba sai dai suje kotu alkali ya saki. Daga ranar da mukayi aikin ba zai sake tunawa da ita ba.’
Dakin ya kuma cika da dariyar.
Ita kanta saida tayi murmushi saboda wannan tsarin nashi yayi mata,tabbas idan Abba ya manta da Aisha zuwa wani lokaci ne ‘yanuwanta zasu raba auren. Shikenan ta huta da wannan alakakan.
Kamar daga sama aka jefo wata karamar bakar tasa gabansu, mutumin yace
‘Ku juye duk abinda kuka zo da shi a nan.’
Nan da nan Zahra ta bude jakarta ta fito da kudin da ta zo da shi naira dubu dari biyu ta saka a tasar, a take tasar ta bace.
Mutumin yace
‘Idan ya dawo a zo a sanar da mu, zuwa lokacin dan matsuruto zai sanar da ku kudin aikin da zaku ajiye masa kafin aiki ya fara. Ku tafi, ku tafi.’
Nan da nan suka mike, yaron da ya shigo da su ne ya sake shigowa ya wuce musu gaba. Ya bi da su ta wata kofar da ban da ba ta nan suka shigo ba, sai a lokacin Zahra taga sun fito ta kofar gaban gidan daidai inda suka ajiye mota. Motocin da suka tarar da safe basa wajen sai dai wata bakar mota wadda da alama bayan sun shiga ne masu ita suka zo.
Ba tare da bata lokaci ba suka shiga mota suka kama hanya, nan dinma hanyar da suka bi ba ta ita suka fito ba.
Babu wanda yayi magana sai da suka fito daga daji suka hau kwalta. Amina ta dubi Alele da yake tuki tace
‘Alele duk mai abun da ka gani ka tsaya mu siya mu dan sa wani abun a bakinmu, na manta ban yiwo mana guzuri ba yunwa muke ji.’
‘To Hajiya, mun kusa zuwa wajen masu mangoron nan ai.’
Ta dubi Zahra tace
‘Kawata kin ga inda za a magance miki matsalarki ko? Yanda yayi miki alkawarin haka zai yi miki aiki zaki sha mamaki.’
‘Hmmmn! Ai na ga alama.’
Suka yi shiru kowacce tana kora ruwan robar da suka taho da shi.
Jimawa kadan Zahra tace
‘Kawata naji yana maganar kudin aiki bayan kudin da na ajiye masa.’
‘Eh, ai in dai kin shiga da jaka wannan dakin sai kin ajiye duk kudin da yake jakar a wannan tasar ko an yi aiki ko ba ayi ba. Kudin aiki kuma da ban za a sanar dake. Kawai idan zamu dawo ki sake ciko jaka.’
‘Hmm!’
Suka sake yin shiru na dan lokaci, jimawa kadan Zahra tace
‘Ni abu daya ne yake bani haushi, duk inda naje sai ace wai mutuniyarki bazata tabu ba. Na rasa waye malaminta a garin nan da bamu san shi ba.’
Amina tace
‘To tunda dai an sami makarinta ba shike nan ba, duk ma wanda yake mata aiki su karata. Idan ta rabu da mijinki duk ma yanda tayi ba shikenan ba.’
‘hakane kam, a sauka lafiya.’
Sai daga baya suka sami masu rogo sun fito daga wani kauye, suka saya sukayi ta ci har suka rage yunwa.
Saida aka idar da Sallar Magriba sannan suka ajiye Zahra a gida suka wuce, a kan idan alhazai sun dawo zasu koma a gama aiki.
UWAR SADDIKU
Written by
Sakina Yazid
(Innar su Amal)
30
Tunda suka dawo daga Doguwa kuma sai Zahra ta cigaba da harkokinta cikin walwala, musamman da yake yanzu gidan yana hannunta. Abu daya ne kawai bata sami yanda take so ba; ta riga ta tsara yanda zata yi yawon Sallah a motar Abban, sai dai kawai ranar da zasu tafi da motar ya fita ya kaita gidan Yaya Bello ya ajiye a can sanna Ali ya wuce da su airport.
Da ya sanar da ita wannan tsarin nasa da wuri da tabbas ta hanashi don da ya saba tafiya ya bar motarsa a gidan, amma dai wannan zuwa Doguwa ya wanke mata duk wata damuwa.
Nan da nan ta cigaba da shirin babbar Sallah da lissafin yanda zata kasafta naman san da ya bari a yanka.
__
Tunda suka isa kasa mai tsarki Aisha ta dukufa addu’a; duk abinda take so saida ta roka kuma ta yiwa Abbanta addu’a sosai.
Tare da Abba suke a hotel don haka ma bata sake tayi wata kawa ba tunda yawancin ibada ma tare suke zuwa, don haka ko kasuwa ma bata tunanin zuwa.
Saura kwana biyu arfa suna zaune ita da Abban sun gama cin abinci suna hutawa a dakinsu na otel suna dan taba hira . Kamar wadda aka tunawa ta dubeshi tace
‘Uhm, Dubai din zamu wuce ko Yallabai don ka ga shi yasa ba zan yi tsaraba a nan ba sai na je can.’
Ya harareta yana jijjiga kai
‘Wannan mata bata da mantuwa.’
Ta dan zaro ido
‘Da mijin zan manta ko kuwa da kaina?’
‘To zamu wuce kin ji dadi?’
Zumbur ta mike tsaye
‘Allah, dadi kai! Ai bari ma kaga nayi Sallah na yiwa Allah godiya tukunna.’
Sai da ta gama murnar ta tambayeshi nawa zata turo a kudinta da tace zata biya, yace ta turo dubu dari biyu account dinsa ya isa shi sai ya cika sauran.
Sai bayan ya nuna mata visa dinta sanna taga kwana bakwai yayi musu booking, ta ji dadi sosai don haka ta fasa duk wata sayayya ta mayar da hankali wajen ibada da kuma addu’a.
…………
Tunda suka tafi Saudiyya kusan kullum wayoyin Abban suna kashe, sai lokacin da ya zaba sai ya kunna suyi waya ta Whatsapp don ya ji lafiyar iyali. Tayi mita har ta gaji, don haka ya zama kawai sai dai ta bar masa sako a WhatsApp idan ya gani sai ya kirawota.
Tunda suka tafi ya ke shawarar tafiya da Aisha Dubai kuma yake tunanin yanda zai yiwa Zahra bayani ya rasa. Bayan Sallah da kwana hudu ya kama ranar zasu wuce Dubai kuma har ranar bai gayawa Zahra ba.
Kaf suka shirya kayansu ana yin sallar Magriba suka bi jirgi sai Dubai.
Sai da suka sauka a hotel suka huta sannan ya bude data.
Yana bude data kuwa kiran Zahra ya shigo kamar tana jiransa, a lokacin Aisha tana wanka. Ya amsa wayar ya fice daga dakin, ya dawo falon kasa wato reception na hotel din ya sami kujera ya zauna.
Bayan sun gaisa ya tambayi yaran, duka suna kusa da ita don haka ta bashi suka gaisa da kowa har Saddiku. Bayan ta karbi wayar suka dan taba hira, jimawa kadan yace
‘Yauwa ban gaya miki ba na wuce Dubai din fa, itama Aishan muna tare da ita a nan din tare zamu dawo.’
A dan razane tace
‘Um ban gane ba. Kace ita nan gida zata wuto?’
‘Eh. Na canza shawara daga baya tunda itama ta biyawa kanta kudin zuwa Dubai din kawai sai muka wuce.’
‘Um, Allah ya bada sa’a.’
‘Amin.’
Yanda yaji muryarta ta canza nan take ya san da sauran bayani, ya san idan ta fara mita abun zai daukesu lokaci don haka nan take yayi mata sallama ya kashe wayar.
…………
Kwanki biyun farko da sukayi a Dubai shi kadai yake fita tare da wanda aka hadashi don ya raka shi kamfanin da zai yi sayayya. Yana fita Aisha take komawa bacci, domin dama ta tara bacci a Saudiyya. Haka ya kwana biyu yana yawo ita kuma tana hutawa, don ko abinci har dakin ake kawo mata.
Sun riga sun gama magana da Aisha a kan ya saya mata waya in ya so ita kuma sai tayi tsaraba da kudinta; don haka fitarsu ta farko ya sayo mata Samsung hadaddiya mai tsadar gaske.
Suna komawa daki ta kasa hakura, saida ta kunna wayar nan. Suka hadu sukayi launching sabuwar waya.
Wayar ta hadu sosai kuma camera tana fitar da hoto don haka sai ya zama duk inda suka je haka zasuyi ta hotuna.