Sashe 31
Uwar Sadiku Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
‘Na sa plumber ya gyara wayar sai ka sake zagayawa ka yanketa tunda kaine ka ajiye ni.’
Ya haye saman ya barshi a nan tsaye yana fitar da kwalla saboda takaici; ya manta rabon da Abba ya daukeshi. Tun yana JS 1 da sukayi fada a makaranta Abban ya zaneshi, sai yanzu zai mareshi saboda wannan banzar matar tasa. Dama Mommy saida ta fada zuwa zatayi ta rabasu da Abba; ai dole ma ya koyawa matar nan hankali. Yayi kwafa ya shige daki ya mako kofa.
………
Duk abinda ya faru tsakaninsa da Sadiku tana jiyowa, don haka yana shiga falon tace
‘Sadik wani abun yayi ko?’
Ko kallonta bai yi ba sai da ya kusa shiga dakinsa ba tare da ya juyo ya kalleta ba yace
‘Kizo yanzu, ina jiranki.’
Kafin ta amsa ya shige dakin ya mako kofar, don haka ta tashi ta wuce dakinta ta kwantar da Sumayya wadda ta riga tayi bacci.
Ta fuskanci da fada ya shigo don haka itama ranta a bace ta shiga dakin, yana tsaye a gaban mudubi ya rungume hannayensa ita kuma ta wuce gefen gado ta zauna.
Sukayi shiru na dan lokaci, Jim kadan tace
‘Gani.’
Ya zuba mata ido har saida ta gaji da kallon da yake mata ta kawar da kai.
Yace
‘Zahra.’
Ta kalleshi, suna hada ido ta sunkuyar da kanta.
Ya cigaba
‘Ranar da na tafi Sadik yaje ya yanke waya wadda take kai ruwa tankin gidan Aisha, na barku a kan Malam Sule ya cigaba da kaita aiki tare da ‘yan makaranta amma tunda na tafi kika hana kika ce yara suna makara kuma basa makara. Na bar Rukayya ta tayata kwana amma ina tafiya kika turo aka kirawota kika barta ita kadai. Na ce a kai mata danyen naman sallah kika hana a bata, kuma waccan sallar ma haka kika sam mata naman shine wannan kika hanata gaba daya. Me yasa? Wanne irin wulakanci ne wannan Zahra? Kika barta tana yawo a motar haya kuma tana sayen ruwa, saboda me?’
Maganganun nashi duka sun shammaceta don haka tayi tsamo-tsamo a wajen, ta muskuta kadan ta gyara zama. Ta gagara bashi amsa sai wani muzurai kawai da takeyi, yace
‘Ni da gidana ban isa na fadi yanda nake so ayi ba kenan saboda kin ga ina kyaleki ko Zahra? Ba kya ma tsoron koyawa yara rashin kunya kiri-kiri kike aikata abubuwan da basu dace ba a gabansu saboda tsabar wulakanci da raini…'
A fusace ta katseshi
‘Kada fa ka zageni! Ai nima sai ka tambayeni kaji ta bakina amma daga dawowa ta gaya maka karya da gaskiya ka zo kana ta fada.’
‘To a cikin abubuwan da na lissafa wanne ne karyar ai gani ina sauraronki?’
Ta muskuta ta cigaba da muzurai tana zumbura baki, gaba daya ya shammaceta. Da ta san za ayi haka da ta tanadi karyar da zata tsara masa, sai dai batayi zaton yana dawowa haka zai gane komai ba. Duk wanda yayi mata wannan munafuncin ma dole ta dauki mataki a kansa don ba zata kyale ba.
Ya gaji da jira tai magana bata yi ba don haka ya cigaba
‘To shikenan kinyi yanda kike so nima zanyi yanda nake so, yara kuma ki cigaba da koya musu rashin mutunci. Amma ki sani, kin bani mamaki don a ya da nake dake na zata ko kare na ajiye nace ki tayani kula da shi zaki yi, balle na ajiye matar aure wadda ban ce ki kula da ita ba kawai hakkinta nace a bata amma kika haye Kai saboda hadama. Fice min daga daki.’
Ta kalleshi da mamaki kwakwalwarta tana nanata mata “fice min daga daki”, yau ita Yusuf yacewa ta fice masa daga daki saboda wata amarya.
Ta tashi cikin sanyin jiki tana kallonsa tana mamaki, sai yanzu ne ma taga tsananin fushin da yake ciki. Dole ta dauki matakin a kan duk wanda yake da hannu a cikin kulla mata wannan munafurcin.
Ta fice daga dakin ta rufe masa kofar.
Tana fita hawayen da take makalewa ya kwace, haka ta barshi yana zuba har ta karasa dakinta ta shige ta turo kofar. Ta zauna a gefen gado kamar wadda aka tunkuda, ta rufe fuskarta da tafukan hannunta tana fitar da hawaye masu zafi harda shesshekar.
Wai yau ita Yusuf yake kora daga dakinsa saboda tsabar wulakanci Kuma harda ce mata hadamammiya duk don yana da wata matar. Dole ta dauki matakin a kan Yusuf da wannan matar tasa don ba a isa a zo daga baya ba a rabata da mijinta.
Haka ta karasa wunin cikin kunci, ko da yara suka dawo daga islamiyya haka tace musu bata da lafiya don haka sukayi jugum-jugum.
Ta dafa abincin dare amma ko kallon table din bai yi ba har lokacin kwanciyar bacci.
Bata yi niyyar zuwa dakinsa ba don haka a dakinta ta kwanta, sai dai duk sata irin ta bacci kasa daukarta yayi. Juyi kawai take a kan gadon, zuciyarta sai kuna takeyi saboda takaici. Ga kayan matan da ta sha duk sun hadu sun birkita ta; tun saura sati daya ya dawo aka yi mata kaza ta cinye ga tsumi galan guda wanda shima tsaf ta shanye duk don shirin dawowarsa amma ga da abinda ya dawo mata da shi.
Haka ta kwana tana juyi tana tunanin mafita don dole ta dauki mataki.
UWAR SADDIKU
Written by
Sakina Yazid
(Innar su Amal)
19
Ko da gari ya waye haka Zahra ta tashi da idanuwanta a kumbure saboda rashin bacci, gashi ranar litinin ce don haka dole ta shirya yara zuwa makaranta. Haka ta goya Sumayya ta shiga hidima, da taimakon Yusra nan da nan suka gama.
Karfe bakwai da rabi Malam Sule ya juya mota yana jiransu a tsakar gidan.
Daidai lokacin Abba ya sauko bayan sun gaggaisa da yaran da kuma Malam Sule ya kunna tashi motar ya fice daga gidan. Yana fita daga gate din yaci karo da Rukayya ta fito a shirye, bayan ya amsa gaisuwar ta yace
‘Ina Antin suke ita da Amira.’
Tace
‘Basu gama shiryawa ba shine tace mu tafi.’
Yayi mata sallama ya wuce yayi parking a bakin gate din gidan Aisha, ya fito ya shiga ciki.
Amira ce a falo bayan ta gaisheshi ya shige daki inda ya sami Aisha a tsaye ta saka hijabinta ta dauko jakarta. Bayan sun gaisa yace
‘Muje na kai ku makarantar.’
Da mamaki tace
‘Kai da kanka?’
Yayi ‘yar dariya yace
‘To ya na iya, na zama direban matar Alhaji.’
Suka fito tare har bakin gate, ita da Amira suna cikin shiga motar Malam Sule ya zo wucesu da yara.
Saida Abba ya kai Amira makaranta ya dawo ya ajiye Aisha ya sanar da ita zai zo ya dauketa sai su dauko Amira in ya so sai ya kaita ta mayar da Amiran gidansu kamar yanda ta sanar masa.
Suka yi sallama ya dawo gida.
Duk da ta ajiye abincin safe amma bai ko kalli tebur din ba ya shirya ya fice ba tare da ya bi ta kanta ba.
Tunda take da shi bai taba fushi da ita har ya ki cin abincinta ba sai yau. Tsayawa kawai tayi tana kallon abincin a dinig table bayan ya fice; lallai an juya mata kan miji kuma dole ta dau mataki. Dole ta san yanda zata yi ta janyo hankalin mijinta ya dawo kanta kafin a saka shi ya koreta.
Abban bai dade da fita ba Jummai ta shigo gidan, don haka ta mikawa Jummai Sumayya tace mata ciwon kai yana damunta. Ta koma dakinta ta rufo kofa, ta zauna a gefen gado ta kafa tagumi.
Jimawa kadan ta tashi ta dauki wayarta ta fara lalube a ciki, har ta zo kan Yaya Murja sai kuma ta fasa dannan kiran. Idan dai Yaya Murja ce ta san hakuri kawai zata bata tace tayi addu’a , kuma ai kullum tana addu’a itama. Idan kuma ta kirawo Suwaiba itama hakurin zata bata don ita wannan bata ma san menene rayuwar ba.
Haka ta koma ta lalubo lambar Amina, kara daya wayar tayi aka dauka. Bayan sun gama gaisawa tace
‘Kawata ina son ganinki yanzun nan, gashi kuma ni bazan iya fitowa ba balle na zo.’
Tace
‘To nima dai gani a office amma bari mu gani watakila zan iya fitowa nan da minti ashirin haka sai na karaso gidan. Allah yasa dai lafiya.’
‘Ina fa lafiya, ke dai kawai ki hanzarta ki zo.’
Sukayi sallama suka ajiye wayar.
An dauki kamar awa daya domin har ta gaji da jiran Hajiya Amina kafin taji tsayuwar motarta a bakin gate. Cikin kankanin lokaci kuwa Jummai ta buga mata kofa ta sanar da ita isowar Aminan, nan take ta bada umarnin Aminan ta shigo ta sameta a dakin.
Tana shiga ta tura kofar ta karasa ta zauna a kusa da ita tana fadin
‘Yaya dai Uwar Sadiku? Ya zan ganki cikin duwa bayan kuma jiya maigida ya dawo? Me yake faruwa ne?’
Ta share kwallar da take kwarmin idonta tana ajiyar zuciya yayinda Aminan ta bita da kallon mamaki
‘Ni za ayiwa bura uba Aminoni? Tunda ya sauka a garin nan yake min wulakanci saboda wata banzar matarsa; wai ni Abban Sadik ya kalla yacewa hadamammiya yana wani korata daga dakinsa kamar kare.’
Ta zaro ido tana binta da kallo, sannan tace
‘Daga dawowa Zahra? Ke kuwa me kika yi masa?’
‘Me aka gaya masa dai zaki ce?’
‘Allah kawata? Yanzu wannan matar tasa mai kama da abun tausayi ta kai ta kulla wata tsiya haka?’
Nan ta karantowa Amina abubuwan da suka faru da yanda take jin janye hankalinsa akayi daga kanta aka saka shi ya zo yana yi mata wulakanci.
Aminan tace
‘Ikon Allah, lallai kishiya bata kadan. Shi yasa wallahi ba zan taba bari Habibi ya kara aure ba sai inda karfi na ya kare. Ka rayu da mutum tun bashi da komai amma yanzu yana jin yana da bakin kiranki hadamammaiya, kai maza basu da mutunci!’
‘Ni yanzu kin san me nake so? Duk inda kudi suke dole na nemosu don kin san munyi da Malam Hatimu zai raba min su gaba daya.’
‘Hakane. To yanzu ina zaki sami kudin bayan tuntuni kike cewa baki da su, kuma kinga dai nima bani da su.’
Ya haye saman ya barshi a nan tsaye yana fitar da kwalla saboda takaici; ya manta rabon da Abba ya daukeshi. Tun yana JS 1 da sukayi fada a makaranta Abban ya zaneshi, sai yanzu zai mareshi saboda wannan banzar matar tasa. Dama Mommy saida ta fada zuwa zatayi ta rabasu da Abba; ai dole ma ya koyawa matar nan hankali. Yayi kwafa ya shige daki ya mako kofa.
………
Duk abinda ya faru tsakaninsa da Sadiku tana jiyowa, don haka yana shiga falon tace
‘Sadik wani abun yayi ko?’
Ko kallonta bai yi ba sai da ya kusa shiga dakinsa ba tare da ya juyo ya kalleta ba yace
‘Kizo yanzu, ina jiranki.’
Kafin ta amsa ya shige dakin ya mako kofar, don haka ta tashi ta wuce dakinta ta kwantar da Sumayya wadda ta riga tayi bacci.
Ta fuskanci da fada ya shigo don haka itama ranta a bace ta shiga dakin, yana tsaye a gaban mudubi ya rungume hannayensa ita kuma ta wuce gefen gado ta zauna.
Sukayi shiru na dan lokaci, Jim kadan tace
‘Gani.’
Ya zuba mata ido har saida ta gaji da kallon da yake mata ta kawar da kai.
Yace
‘Zahra.’
Ta kalleshi, suna hada ido ta sunkuyar da kanta.
Ya cigaba
‘Ranar da na tafi Sadik yaje ya yanke waya wadda take kai ruwa tankin gidan Aisha, na barku a kan Malam Sule ya cigaba da kaita aiki tare da ‘yan makaranta amma tunda na tafi kika hana kika ce yara suna makara kuma basa makara. Na bar Rukayya ta tayata kwana amma ina tafiya kika turo aka kirawota kika barta ita kadai. Na ce a kai mata danyen naman sallah kika hana a bata, kuma waccan sallar ma haka kika sam mata naman shine wannan kika hanata gaba daya. Me yasa? Wanne irin wulakanci ne wannan Zahra? Kika barta tana yawo a motar haya kuma tana sayen ruwa, saboda me?’
Maganganun nashi duka sun shammaceta don haka tayi tsamo-tsamo a wajen, ta muskuta kadan ta gyara zama. Ta gagara bashi amsa sai wani muzurai kawai da takeyi, yace
‘Ni da gidana ban isa na fadi yanda nake so ayi ba kenan saboda kin ga ina kyaleki ko Zahra? Ba kya ma tsoron koyawa yara rashin kunya kiri-kiri kike aikata abubuwan da basu dace ba a gabansu saboda tsabar wulakanci da raini…'
A fusace ta katseshi
‘Kada fa ka zageni! Ai nima sai ka tambayeni kaji ta bakina amma daga dawowa ta gaya maka karya da gaskiya ka zo kana ta fada.’
‘To a cikin abubuwan da na lissafa wanne ne karyar ai gani ina sauraronki?’
Ta muskuta ta cigaba da muzurai tana zumbura baki, gaba daya ya shammaceta. Da ta san za ayi haka da ta tanadi karyar da zata tsara masa, sai dai batayi zaton yana dawowa haka zai gane komai ba. Duk wanda yayi mata wannan munafuncin ma dole ta dauki mataki a kansa don ba zata kyale ba.
Ya gaji da jira tai magana bata yi ba don haka ya cigaba
‘To shikenan kinyi yanda kike so nima zanyi yanda nake so, yara kuma ki cigaba da koya musu rashin mutunci. Amma ki sani, kin bani mamaki don a ya da nake dake na zata ko kare na ajiye nace ki tayani kula da shi zaki yi, balle na ajiye matar aure wadda ban ce ki kula da ita ba kawai hakkinta nace a bata amma kika haye Kai saboda hadama. Fice min daga daki.’
Ta kalleshi da mamaki kwakwalwarta tana nanata mata “fice min daga daki”, yau ita Yusuf yacewa ta fice masa daga daki saboda wata amarya.
Ta tashi cikin sanyin jiki tana kallonsa tana mamaki, sai yanzu ne ma taga tsananin fushin da yake ciki. Dole ta dauki matakin a kan duk wanda yake da hannu a cikin kulla mata wannan munafurcin.
Ta fice daga dakin ta rufe masa kofar.
Tana fita hawayen da take makalewa ya kwace, haka ta barshi yana zuba har ta karasa dakinta ta shige ta turo kofar. Ta zauna a gefen gado kamar wadda aka tunkuda, ta rufe fuskarta da tafukan hannunta tana fitar da hawaye masu zafi harda shesshekar.
Wai yau ita Yusuf yake kora daga dakinsa saboda tsabar wulakanci Kuma harda ce mata hadamammiya duk don yana da wata matar. Dole ta dauki matakin a kan Yusuf da wannan matar tasa don ba a isa a zo daga baya ba a rabata da mijinta.
Haka ta karasa wunin cikin kunci, ko da yara suka dawo daga islamiyya haka tace musu bata da lafiya don haka sukayi jugum-jugum.
Ta dafa abincin dare amma ko kallon table din bai yi ba har lokacin kwanciyar bacci.
Bata yi niyyar zuwa dakinsa ba don haka a dakinta ta kwanta, sai dai duk sata irin ta bacci kasa daukarta yayi. Juyi kawai take a kan gadon, zuciyarta sai kuna takeyi saboda takaici. Ga kayan matan da ta sha duk sun hadu sun birkita ta; tun saura sati daya ya dawo aka yi mata kaza ta cinye ga tsumi galan guda wanda shima tsaf ta shanye duk don shirin dawowarsa amma ga da abinda ya dawo mata da shi.
Haka ta kwana tana juyi tana tunanin mafita don dole ta dauki mataki.
UWAR SADDIKU
Written by
Sakina Yazid
(Innar su Amal)
19
Ko da gari ya waye haka Zahra ta tashi da idanuwanta a kumbure saboda rashin bacci, gashi ranar litinin ce don haka dole ta shirya yara zuwa makaranta. Haka ta goya Sumayya ta shiga hidima, da taimakon Yusra nan da nan suka gama.
Karfe bakwai da rabi Malam Sule ya juya mota yana jiransu a tsakar gidan.
Daidai lokacin Abba ya sauko bayan sun gaggaisa da yaran da kuma Malam Sule ya kunna tashi motar ya fice daga gidan. Yana fita daga gate din yaci karo da Rukayya ta fito a shirye, bayan ya amsa gaisuwar ta yace
‘Ina Antin suke ita da Amira.’
Tace
‘Basu gama shiryawa ba shine tace mu tafi.’
Yayi mata sallama ya wuce yayi parking a bakin gate din gidan Aisha, ya fito ya shiga ciki.
Amira ce a falo bayan ta gaisheshi ya shige daki inda ya sami Aisha a tsaye ta saka hijabinta ta dauko jakarta. Bayan sun gaisa yace
‘Muje na kai ku makarantar.’
Da mamaki tace
‘Kai da kanka?’
Yayi ‘yar dariya yace
‘To ya na iya, na zama direban matar Alhaji.’
Suka fito tare har bakin gate, ita da Amira suna cikin shiga motar Malam Sule ya zo wucesu da yara.
Saida Abba ya kai Amira makaranta ya dawo ya ajiye Aisha ya sanar da ita zai zo ya dauketa sai su dauko Amira in ya so sai ya kaita ta mayar da Amiran gidansu kamar yanda ta sanar masa.
Suka yi sallama ya dawo gida.
Duk da ta ajiye abincin safe amma bai ko kalli tebur din ba ya shirya ya fice ba tare da ya bi ta kanta ba.
Tunda take da shi bai taba fushi da ita har ya ki cin abincinta ba sai yau. Tsayawa kawai tayi tana kallon abincin a dinig table bayan ya fice; lallai an juya mata kan miji kuma dole ta dau mataki. Dole ta san yanda zata yi ta janyo hankalin mijinta ya dawo kanta kafin a saka shi ya koreta.
Abban bai dade da fita ba Jummai ta shigo gidan, don haka ta mikawa Jummai Sumayya tace mata ciwon kai yana damunta. Ta koma dakinta ta rufo kofa, ta zauna a gefen gado ta kafa tagumi.
Jimawa kadan ta tashi ta dauki wayarta ta fara lalube a ciki, har ta zo kan Yaya Murja sai kuma ta fasa dannan kiran. Idan dai Yaya Murja ce ta san hakuri kawai zata bata tace tayi addu’a , kuma ai kullum tana addu’a itama. Idan kuma ta kirawo Suwaiba itama hakurin zata bata don ita wannan bata ma san menene rayuwar ba.
Haka ta koma ta lalubo lambar Amina, kara daya wayar tayi aka dauka. Bayan sun gama gaisawa tace
‘Kawata ina son ganinki yanzun nan, gashi kuma ni bazan iya fitowa ba balle na zo.’
Tace
‘To nima dai gani a office amma bari mu gani watakila zan iya fitowa nan da minti ashirin haka sai na karaso gidan. Allah yasa dai lafiya.’
‘Ina fa lafiya, ke dai kawai ki hanzarta ki zo.’
Sukayi sallama suka ajiye wayar.
An dauki kamar awa daya domin har ta gaji da jiran Hajiya Amina kafin taji tsayuwar motarta a bakin gate. Cikin kankanin lokaci kuwa Jummai ta buga mata kofa ta sanar da ita isowar Aminan, nan take ta bada umarnin Aminan ta shigo ta sameta a dakin.
Tana shiga ta tura kofar ta karasa ta zauna a kusa da ita tana fadin
‘Yaya dai Uwar Sadiku? Ya zan ganki cikin duwa bayan kuma jiya maigida ya dawo? Me yake faruwa ne?’
Ta share kwallar da take kwarmin idonta tana ajiyar zuciya yayinda Aminan ta bita da kallon mamaki
‘Ni za ayiwa bura uba Aminoni? Tunda ya sauka a garin nan yake min wulakanci saboda wata banzar matarsa; wai ni Abban Sadik ya kalla yacewa hadamammiya yana wani korata daga dakinsa kamar kare.’
Ta zaro ido tana binta da kallo, sannan tace
‘Daga dawowa Zahra? Ke kuwa me kika yi masa?’
‘Me aka gaya masa dai zaki ce?’
‘Allah kawata? Yanzu wannan matar tasa mai kama da abun tausayi ta kai ta kulla wata tsiya haka?’
Nan ta karantowa Amina abubuwan da suka faru da yanda take jin janye hankalinsa akayi daga kanta aka saka shi ya zo yana yi mata wulakanci.
Aminan tace
‘Ikon Allah, lallai kishiya bata kadan. Shi yasa wallahi ba zan taba bari Habibi ya kara aure ba sai inda karfi na ya kare. Ka rayu da mutum tun bashi da komai amma yanzu yana jin yana da bakin kiranki hadamammaiya, kai maza basu da mutunci!’
‘Ni yanzu kin san me nake so? Duk inda kudi suke dole na nemosu don kin san munyi da Malam Hatimu zai raba min su gaba daya.’
‘Hakane. To yanzu ina zaki sami kudin bayan tuntuni kike cewa baki da su, kuma kinga dai nima bani da su.’