Sashe 6
Uwar Sadiku Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Yana wucewa ta bi bayansa da kallo tana murmushi; ta san akwai magana a bakinsa daman wannan lokacin take jira. Cikin sauri ta daga kofin shayinta ta kurbe ta bishi dakin don haka kusan a lokaci guda suka shiga.
Kujerar mutum daya dake dakin ya zauna don haka ta zauna a gefen gado tana fuskantarsa, ta kara fadada murmushinta tace
‘Gani Yallabai, me na samu? Ka san hausawa sunce idan ka ji kira samu ne.’
Yayi wani dan gajeran murmushi ya taso ya dawo kusa da ita, ya kama hannunta na dama ya rike yana shafawa yana duban fuskarta. Suka shiru na dan lokaci sannan ya dubeta yace
‘Kanwa kika samu Zahra, aure zanyi in sha Allahu shine nake so na sanar dake.’
Tuni ta bude baki tana binsa da kallo cike da mamaki. Ya sunkuyar da kansa a hankali yayinda ta zare hannunta daga cikin nasa. Ta hadiye wani malolo da ya tokare mata makogoro tana kokarin tokare kwallar da take neman kwace mata tace
‘Aure kuma Abban Sadik?’
Ya daga kai alamar e, yana kallonta yana mata murmushi.
Suka yi shiru na dan lokaci, yaji batayi magana ba yace
‘Ai bazawara ce ma ko da yake mijin nata rasuwa yayi ya barta da yara biyu kanana. Tana da hankali kuma sosai ga ilimi na san bazaku sami matsala ba in sha Allah.’
Tayi murmushin yake tace
‘Allah ya sa, Allah ya tabbatar mana da alkhairi.’
Da sauri ya amsa
‘Amin amin.’
Ya mike da sauri tunda dama so yake ya bar gidan kafin ta saka shi a gaba da korafi. Ya matsa gaban mudubi ya dauki hularsa ya saka yanayi yana lekenta ta mudubin, ya dauki mukullan motarsa ya juyo yana fadin
‘To sai na dawo.’
‘A dawo lafiya.’
Ta fada da murya kasa-kasa tana kokarin danne damuwar da ta shiga, ya fice ya ja mata kofar dakin.
Ta bi kofar dakin da kallo tana takaici da mamaki; ashe har yanzu bata wuce kishiya a wajen Yusuf ba? Tayi zaton ma ba zai taba yi mata kishiya ba da taga shekaru shida sun shude bai kuma kwaso maganar auren ba, tayi zaton da Mallam yace mata ya dauke hankali sa daga kan maganar aure shike nan.
Hawayen da take tokarewa ya gangaro kan fuskarta, ta sa hannu ta goge. Ta cije lebe data tuno kalamansa “tana da hankali sosai, ga ilimi” lallai namiji, wai yau ita Yusuf yake gayawa zai auro mai hankali da ilimi.
Ta mike kamar wadda aka tsikara ta fice daga dakin.
Ta shiga dakinta ta turo kofa, ta jingina a jikin kofar, nan zuciyarta ta fara tuna mata rayuwarsu a baya lokacin da Yusuf din bai yi kudi haka ba; lokacin da albashinsa na wata da kyar yake kaisu kwana goma, a lokacin haka zata zauna da dadi babu dadi amma duk ya manta.
Ta fara kaiwa da kawowa tana tunanin mafita don gaskiya bata son wannan auren nasa, ta ina zata fara zama da kishiya?
Ta karasa ta zauna a gefen gado ta kafa tagumi, jimawa kadan ta mika hannu ta dauko wayarta daga kan durowar gefen gado inda take ajiye. Har ta lalubo lambar yayarta Yaya Murja zata kirawota sai kuma ta fasa ta rike wayar kawai; kamata yayi taje gidan duk da ta san ba lallai Yaya Murja ta barta tayi yanda take so ba amma dai tana son ganinta.
Matsalarta daya bata gayawa Abban Sadik zata fita ba don da ta gaya masa zaice Sale direba ya dawo ya kaita.
Nan ta yanke shawara sauri zatayi taje ta dawo don idan ta gaya masa ya san me zata je yi gara kawai ta tafi in ya so tayi sauri ta dawo kawai.
Nan da nan ta mike, ta saka hijabi ta dau jakarta da wayarta. Har ta zo falo ta tsaya ta saka karamar jakarta a cikin hijabin ta mayar ta saki hijabinta. Ta rufo kofar falon ta nufi gate, tana daf da fita Bala megadi ya fito daga bayan gidan inda yake bawa fulawowi ruwa, yana ganinta ya karaso da gudu yana rage tsawo
‘Hajiya barka da fitowa.’
‘Yauwa Malam Bala, na shiga nan gidan Umman Haidar duk wanda yazo nemana kace ayi min waya sai na fito kawai.’
‘To Hajiya a dawo lafiya.’
Ta amsa ta wuce Malam Bala ya mayar da gate ya rufe.
Saida tayi nisa da gidan sannan ta tsaya ta hau mota, dayake shata ta dauka kai tsaye aka wuce da ita har gidan Yaya Murja.
Bayan sun gaisa da megadin da ya bude mata kofa ta wuce ta nufi cikin gidan.
Shafa’atu ce a falon wato abokiyar zaman Yaya Murja din wadda suke kira Anti Shafa; tana zaune tana bawa Arif abinci. Bayan tayi mata sannu da zuwa suka gaisa, kafin ma ta tambayeta tace
‘Umman tana samanta.’
Nan da nan kuwa ta wuce saman inda nan ne wajen Yaya Murja din wadda itace uwargida.
A falo ta sameta a kwance a kan doguwar kujera, ta kunna TV tashar Zee World yayinda take ta faman dube dube a wayarta.
Ta shiga da sallama, Yaya Murja ta amsa sallamarta yayinda ta tashi zaune. Ta karasa ta zauna kusa da ita.
‘Ikon Allah, daga ina haka babu notice ko wani wajen kika zo kika biyo.’
Yaya Murjan ta tambaya tana mamaki.
Ta danyi yake tace
‘A’a nan kawai na zo Yaya.’
Suka gaisa Yaya Murja ta tambayi lafiyar yaran. Ta dubi Zahra tace
‘Lafiya kuwa? na ga kamar da damuwa a fuskarki.’
Ta kawar da kai tana jijjiga kai, ta sake dubanta suka hada ido tace
‘Yaya wai aure Abban Sadik zai yi.’
Tayi ‘yar dariya tana tafa cinyar Zahra
‘Shine duk kika birkice haka? To ai naga ba yau ya fara maganar auren ba ko? Ai kawai sai kice Allah ya bada sa’a tunda bake za kiyi masa auren ba, tsuntsun da yaja ruwa ai shi ruwa zai doka.’
‘Yaya, shekararmu fa kusan ashirin da aure duk bai tashi kara auren ba sai yanzu? Duk yanda nake tattalinsa amma shi ba zai raga min ba? Yana wani gaya min wai mai hankali ce sosai mai ilimi, da yake ni bani da hankali.’
Dariya Murja ta sake yi
‘To meye bako a wajenki a cikin abinda yayi? Ai ki kwantar da hankalinki kawai kice Allah ya bada sa’a domin idan kika ce zakiyi wata hayaniya ma kanki zaki dorawa hawan jini. Ni ba gani ba, me ta rage min, rayuwarta takeyi ina tawa bani ma da lokacinta. Kiyita addu’a kawai tunda ko bai yi yanzu ba ma nan gaba sai ya kara.’
Ta kau da kai, dama ta san haka Yaya Murja zata ce domin ita din hakurinta da ban ne. Ta san ba zata sami mafita ba ta dai zo ne saboda kawai ta fada taji sanyi a ranta tunda ita take gani kamar uwarta tun bayan rasuwar iyayensu.
Ta gyara zamanta tana kokarin kawar da damuwar, Yaya Murja ta katse mata tunani
‘Idan dai namiji ne babu yanda zakiyi dashi, idan kika ce ba zai yi miki kishiya ba to kanki zaki dorawa damuwa sai yayi, ki roki Allah ya hadaki da ta gari wadda ba zata cutar da ku ba gaba daya.’
‘Hakane Yaya.’
Ta dan daki cinyarta
‘Yauwa Uwar Saddiku, ko ke fa. Bari na samo miki lemon ki kora, kina sallah kina salati babu macen da zata baki tsoro.’
Har ta mike Zahra ta riketa
‘Ai barshi kawai Yaya, wallahi ko tambaya banyi ba na fito saboda takaici.’
Ta mike kafin Murja ta zauna suka nufi kasa tare, sukayi sallama tana sake bata hakuri tare da yi mata alkawarin gobe da yamma zata zo gidan nata.
Haka ta koma gida zuciyarta a jagule; tabbas zatayi duk yanda zata yi taga an fasa auren nan idan haka bai samu ba kuma to tafi so ta zama itace kan gida sai yanda ta tsara.
Tana shiga gidan ta tarar da mai aikinta Jummai wadda dama zuwa take tana tafiya idan ta gama aikinta, don haka tare suka shige cikin gidan Jummai ta kama aikinta ita kuma Zahra’u ta haye dakinta wanda yake sama ta rufe kofa.
Tana shiga ta ajiye hijabin da jakarta a kan kujera, ta karasa ta zauna a gafen gado ta kafa tagumi. Bata jima da zaman ba kuma ta mike ta lalubo wayarta a cikin jakarta ta koma ta zauna akan gadon ta shiga laluben lambar wayar Amina; kawarta ce ta aminci wadda zata iya cewa a yanzu bata da kawar da ta kaita.
Sau daya wayar tayi kara aka dauka, bayan sun gaisa Amina tace
‘Ya nake jinki kamar kinda damuwa ne Uwar Saddiku?’
Saida ta share kwallar da take kwarmin idonta sannan ta amsa
‘Ba zaki gane ba kawata, wallahi ina cikin damuwa. Abban Sadik aure zai yi.’
Da mamaki ta amsata
‘Ikon Allah, namiji dan babansa. Yanzu ashe dama bayan waccan maganar mutumin nan ba hakura yayi ba?’
‘Wallahi ko ni ma na zata ya hakura, amma yau da safen nan yake gaya min harda wani ce min wai mai hankali ce kuma tana da ilimi.’
‘Kiji dan rainin hankali!’
‘Wallahi kuwa kawata, na ma rasa abun yi.’
‘To ai ba wani abu bane kema kin san Abban Sadiku ba zai baki matsala ba, duk da dai maza basu da tabbas. Sai ka gama shan wahalarsu da sun sami duniya su auro wata suce da ita za a more.’
‘Kawata ni kawai na fi so yanda aka fasa wancan a fasa wannan ma gaskiya, na san idan aka fasa wannan ba lallai ya kara dauko wata ba tunda kinga kullum girma yake shima.’
‘Hakane kam, to ai sai ki kirawo Mallam kiji ko zai iya taimakawa tunda shi yayi wancan aikin idan kuma ya gagareshi akwai wani malamin a garin Babura sai mu sa rana muje.’
Tayi dan murmushi a karo na farko tun lokacin da Abban Sadiku yayi mata maganar kara aure, sukayi sallama da Hajiya Amina.
Tana tsinke wayar kuma ta kirawo Malam Hatimu mai almajirai ta sanar da shi abinda take so.
Bayan Mallam ya gama jin duk bayaninta yayi gyaran murya yace
Kujerar mutum daya dake dakin ya zauna don haka ta zauna a gefen gado tana fuskantarsa, ta kara fadada murmushinta tace
‘Gani Yallabai, me na samu? Ka san hausawa sunce idan ka ji kira samu ne.’
Yayi wani dan gajeran murmushi ya taso ya dawo kusa da ita, ya kama hannunta na dama ya rike yana shafawa yana duban fuskarta. Suka shiru na dan lokaci sannan ya dubeta yace
‘Kanwa kika samu Zahra, aure zanyi in sha Allahu shine nake so na sanar dake.’
Tuni ta bude baki tana binsa da kallo cike da mamaki. Ya sunkuyar da kansa a hankali yayinda ta zare hannunta daga cikin nasa. Ta hadiye wani malolo da ya tokare mata makogoro tana kokarin tokare kwallar da take neman kwace mata tace
‘Aure kuma Abban Sadik?’
Ya daga kai alamar e, yana kallonta yana mata murmushi.
Suka yi shiru na dan lokaci, yaji batayi magana ba yace
‘Ai bazawara ce ma ko da yake mijin nata rasuwa yayi ya barta da yara biyu kanana. Tana da hankali kuma sosai ga ilimi na san bazaku sami matsala ba in sha Allah.’
Tayi murmushin yake tace
‘Allah ya sa, Allah ya tabbatar mana da alkhairi.’
Da sauri ya amsa
‘Amin amin.’
Ya mike da sauri tunda dama so yake ya bar gidan kafin ta saka shi a gaba da korafi. Ya matsa gaban mudubi ya dauki hularsa ya saka yanayi yana lekenta ta mudubin, ya dauki mukullan motarsa ya juyo yana fadin
‘To sai na dawo.’
‘A dawo lafiya.’
Ta fada da murya kasa-kasa tana kokarin danne damuwar da ta shiga, ya fice ya ja mata kofar dakin.
Ta bi kofar dakin da kallo tana takaici da mamaki; ashe har yanzu bata wuce kishiya a wajen Yusuf ba? Tayi zaton ma ba zai taba yi mata kishiya ba da taga shekaru shida sun shude bai kuma kwaso maganar auren ba, tayi zaton da Mallam yace mata ya dauke hankali sa daga kan maganar aure shike nan.
Hawayen da take tokarewa ya gangaro kan fuskarta, ta sa hannu ta goge. Ta cije lebe data tuno kalamansa “tana da hankali sosai, ga ilimi” lallai namiji, wai yau ita Yusuf yake gayawa zai auro mai hankali da ilimi.
Ta mike kamar wadda aka tsikara ta fice daga dakin.
Ta shiga dakinta ta turo kofa, ta jingina a jikin kofar, nan zuciyarta ta fara tuna mata rayuwarsu a baya lokacin da Yusuf din bai yi kudi haka ba; lokacin da albashinsa na wata da kyar yake kaisu kwana goma, a lokacin haka zata zauna da dadi babu dadi amma duk ya manta.
Ta fara kaiwa da kawowa tana tunanin mafita don gaskiya bata son wannan auren nasa, ta ina zata fara zama da kishiya?
Ta karasa ta zauna a gefen gado ta kafa tagumi, jimawa kadan ta mika hannu ta dauko wayarta daga kan durowar gefen gado inda take ajiye. Har ta lalubo lambar yayarta Yaya Murja zata kirawota sai kuma ta fasa ta rike wayar kawai; kamata yayi taje gidan duk da ta san ba lallai Yaya Murja ta barta tayi yanda take so ba amma dai tana son ganinta.
Matsalarta daya bata gayawa Abban Sadik zata fita ba don da ta gaya masa zaice Sale direba ya dawo ya kaita.
Nan ta yanke shawara sauri zatayi taje ta dawo don idan ta gaya masa ya san me zata je yi gara kawai ta tafi in ya so tayi sauri ta dawo kawai.
Nan da nan ta mike, ta saka hijabi ta dau jakarta da wayarta. Har ta zo falo ta tsaya ta saka karamar jakarta a cikin hijabin ta mayar ta saki hijabinta. Ta rufo kofar falon ta nufi gate, tana daf da fita Bala megadi ya fito daga bayan gidan inda yake bawa fulawowi ruwa, yana ganinta ya karaso da gudu yana rage tsawo
‘Hajiya barka da fitowa.’
‘Yauwa Malam Bala, na shiga nan gidan Umman Haidar duk wanda yazo nemana kace ayi min waya sai na fito kawai.’
‘To Hajiya a dawo lafiya.’
Ta amsa ta wuce Malam Bala ya mayar da gate ya rufe.
Saida tayi nisa da gidan sannan ta tsaya ta hau mota, dayake shata ta dauka kai tsaye aka wuce da ita har gidan Yaya Murja.
Bayan sun gaisa da megadin da ya bude mata kofa ta wuce ta nufi cikin gidan.
Shafa’atu ce a falon wato abokiyar zaman Yaya Murja din wadda suke kira Anti Shafa; tana zaune tana bawa Arif abinci. Bayan tayi mata sannu da zuwa suka gaisa, kafin ma ta tambayeta tace
‘Umman tana samanta.’
Nan da nan kuwa ta wuce saman inda nan ne wajen Yaya Murja din wadda itace uwargida.
A falo ta sameta a kwance a kan doguwar kujera, ta kunna TV tashar Zee World yayinda take ta faman dube dube a wayarta.
Ta shiga da sallama, Yaya Murja ta amsa sallamarta yayinda ta tashi zaune. Ta karasa ta zauna kusa da ita.
‘Ikon Allah, daga ina haka babu notice ko wani wajen kika zo kika biyo.’
Yaya Murjan ta tambaya tana mamaki.
Ta danyi yake tace
‘A’a nan kawai na zo Yaya.’
Suka gaisa Yaya Murja ta tambayi lafiyar yaran. Ta dubi Zahra tace
‘Lafiya kuwa? na ga kamar da damuwa a fuskarki.’
Ta kawar da kai tana jijjiga kai, ta sake dubanta suka hada ido tace
‘Yaya wai aure Abban Sadik zai yi.’
Tayi ‘yar dariya tana tafa cinyar Zahra
‘Shine duk kika birkice haka? To ai naga ba yau ya fara maganar auren ba ko? Ai kawai sai kice Allah ya bada sa’a tunda bake za kiyi masa auren ba, tsuntsun da yaja ruwa ai shi ruwa zai doka.’
‘Yaya, shekararmu fa kusan ashirin da aure duk bai tashi kara auren ba sai yanzu? Duk yanda nake tattalinsa amma shi ba zai raga min ba? Yana wani gaya min wai mai hankali ce sosai mai ilimi, da yake ni bani da hankali.’
Dariya Murja ta sake yi
‘To meye bako a wajenki a cikin abinda yayi? Ai ki kwantar da hankalinki kawai kice Allah ya bada sa’a domin idan kika ce zakiyi wata hayaniya ma kanki zaki dorawa hawan jini. Ni ba gani ba, me ta rage min, rayuwarta takeyi ina tawa bani ma da lokacinta. Kiyita addu’a kawai tunda ko bai yi yanzu ba ma nan gaba sai ya kara.’
Ta kau da kai, dama ta san haka Yaya Murja zata ce domin ita din hakurinta da ban ne. Ta san ba zata sami mafita ba ta dai zo ne saboda kawai ta fada taji sanyi a ranta tunda ita take gani kamar uwarta tun bayan rasuwar iyayensu.
Ta gyara zamanta tana kokarin kawar da damuwar, Yaya Murja ta katse mata tunani
‘Idan dai namiji ne babu yanda zakiyi dashi, idan kika ce ba zai yi miki kishiya ba to kanki zaki dorawa damuwa sai yayi, ki roki Allah ya hadaki da ta gari wadda ba zata cutar da ku ba gaba daya.’
‘Hakane Yaya.’
Ta dan daki cinyarta
‘Yauwa Uwar Saddiku, ko ke fa. Bari na samo miki lemon ki kora, kina sallah kina salati babu macen da zata baki tsoro.’
Har ta mike Zahra ta riketa
‘Ai barshi kawai Yaya, wallahi ko tambaya banyi ba na fito saboda takaici.’
Ta mike kafin Murja ta zauna suka nufi kasa tare, sukayi sallama tana sake bata hakuri tare da yi mata alkawarin gobe da yamma zata zo gidan nata.
Haka ta koma gida zuciyarta a jagule; tabbas zatayi duk yanda zata yi taga an fasa auren nan idan haka bai samu ba kuma to tafi so ta zama itace kan gida sai yanda ta tsara.
Tana shiga gidan ta tarar da mai aikinta Jummai wadda dama zuwa take tana tafiya idan ta gama aikinta, don haka tare suka shige cikin gidan Jummai ta kama aikinta ita kuma Zahra’u ta haye dakinta wanda yake sama ta rufe kofa.
Tana shiga ta ajiye hijabin da jakarta a kan kujera, ta karasa ta zauna a gafen gado ta kafa tagumi. Bata jima da zaman ba kuma ta mike ta lalubo wayarta a cikin jakarta ta koma ta zauna akan gadon ta shiga laluben lambar wayar Amina; kawarta ce ta aminci wadda zata iya cewa a yanzu bata da kawar da ta kaita.
Sau daya wayar tayi kara aka dauka, bayan sun gaisa Amina tace
‘Ya nake jinki kamar kinda damuwa ne Uwar Saddiku?’
Saida ta share kwallar da take kwarmin idonta sannan ta amsa
‘Ba zaki gane ba kawata, wallahi ina cikin damuwa. Abban Sadik aure zai yi.’
Da mamaki ta amsata
‘Ikon Allah, namiji dan babansa. Yanzu ashe dama bayan waccan maganar mutumin nan ba hakura yayi ba?’
‘Wallahi ko ni ma na zata ya hakura, amma yau da safen nan yake gaya min harda wani ce min wai mai hankali ce kuma tana da ilimi.’
‘Kiji dan rainin hankali!’
‘Wallahi kuwa kawata, na ma rasa abun yi.’
‘To ai ba wani abu bane kema kin san Abban Sadiku ba zai baki matsala ba, duk da dai maza basu da tabbas. Sai ka gama shan wahalarsu da sun sami duniya su auro wata suce da ita za a more.’
‘Kawata ni kawai na fi so yanda aka fasa wancan a fasa wannan ma gaskiya, na san idan aka fasa wannan ba lallai ya kara dauko wata ba tunda kinga kullum girma yake shima.’
‘Hakane kam, to ai sai ki kirawo Mallam kiji ko zai iya taimakawa tunda shi yayi wancan aikin idan kuma ya gagareshi akwai wani malamin a garin Babura sai mu sa rana muje.’
Tayi dan murmushi a karo na farko tun lokacin da Abban Sadiku yayi mata maganar kara aure, sukayi sallama da Hajiya Amina.
Tana tsinke wayar kuma ta kirawo Malam Hatimu mai almajirai ta sanar da shi abinda take so.
Bayan Mallam ya gama jin duk bayaninta yayi gyaran murya yace