Sashe 7
Uwar Sadiku Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
‘To Hajiya za ayi aiki, kuma in sha Allah yanzu kam babban aiki za ayi. Sai ki yi kokari zuwa gobe ki sanar damu lokacin da za a daura auren don mu san lokacin da muke da shi kada mu bata lokaci.’
Sukayi sallama da alkawarin zata kirawo shi gobe ta sanar da shi lokacin da yayi saura kafin auren.
Haka Hajiya Zahra’u Uwar Sadiku ta karasa wunin wannan ranar cikin damuwa.
……….
Tunda ya dawo gidan daga wajen aiki take tunanin ta yanda zata tambayeshi yaushe ne auren nasa, ta kasa nutsuwa ta jeranta kalamanta yanda ba zai iya karanta damuwarta ba. Har dare yayi bata sami wannan damar ba, ya gama cin abinci sa ya zauna a falon sama yayi kallon TV daga baya kuma ya koma dakinsa.
Yana zaune a kan gadonsa ya mike kafa yana aiki a kwanfutarsa ta shiga dakin sanye da kayan baccinta, bayan ya amsa sallamarta ta karasa ta kwanta a gefensa tace
‘Har yanzu aikin bai kare ba Yallabai.’
Ya kalleta yana murmushi
‘Saura kadan Madam, in zo ne ana nemana?’
Tayi ‘yar gajeriyar dariya
‘A’a gama a hankali abunka.’
Ya mayar da hankali kan kwamfutar ya cigaba da aikinsa yayinda ta muskuta ta gyara kwanciyarta. Jimawa kadan ta kirawo sunansa
‘Abban Sadik.’
Ya kauda idonsa daga kwamfutar ya dubeta alamar yana sauraronta, don haka ta cigaba
‘Yaushe ne auren naka da kace zakayi?’
Ba tare da ya bar aikin da yakeyi ba yace
‘Da sauran lokaci gaskiya tunda kin ga bamu gama daidatawa ba tukunnu, ba zan iya sanin lokacin ba yanzu.’
‘Uhmm!’
Taji dadin hakan don ta san hakan yana nufin tana da isasshen lokacin don karasa nata shirye-shiryen.
Ya cigaba da aikinsa ita kuma tana kwance, jimawa kadan ta sake kiransa
‘Abban Sadik.’
Ya kalleta sannan ya amsa
‘Um.’
Ta gyara kwanciyarta ta tokare kanta da hannunta ta bishi da kallo ta fara magana kamar tana nazarin kalmominta
‘Don Allah me ya sa kake son kara aure? Idan akwai wani abu da kake bukata ai gara kayi min magana na gyara ko?’
Ya ajiye kwamfutar a kan durowar gefen gado ya dan matsa kusa da ita ya fara wasa da gashin kanta wanda babu kitso amma dai ta daureshi guri daya da ribbon, ya dubeta suka hada ido sannan yace
‘Babu abinda nake bukata, kuma ke ma babu abinda kikayi min. Kawai dai mun hadu da Aishan ne kuma tunda ida damar auren mace hudu ai babu laifin don nayi biyu ko? Amma kada ki damu, babu abinda zai shafi son da nakeyi miki don ni din naki ne kuma ke din tawa ce kin ji. Ki kwantar da hankalinki.’
‘Hmm! Aisha sunanta ashe.’
‘Eh.’
‘Um.’
Ta zame ta gyara kwanciyarta tana fadin
‘Bari na kwanta bacci nake ji.’
Ya cigaba da aikinsa yayinda ita kuma ta juya masa baya ta rufe ido da sunan bacci, tunani kala-kala suna ta zarya a kwakwalwarta.
UWAR SADDIKU
Written by
Sakina Yazid
(Innar su Amal)
6
Tunda Abban Sadik ya tabbatar mata ba a kusa aurensa ba ta dan sami natsuwar, domin ta sanarwa Malam Hatimu shi kuma yayi mata alkawarin za ayi mata wani babban aiki wanda daga shi maigidanta ba zai sake aure ba har karshen rayuwarsa. Don haka ta saki ranta tana harkarta kamar bata da wata damuwa, kuma da bata ji yayi zancen kayan auren ba sai ta kara sakankancewa aikin Malam ne yake aiki.
…….
Sai bayan da ya sanar da Zahra aurensa sannan yaje gidansu ya sanar da mutanen gidan, mahaifiyarsu Hajiya Balaraba ta sawa abun albarka sosai duk da dai ta ja masa kunne a kan kada ya kuskura ya bata da uwargidansa. Ita kuwa yayarsa Yaya Saratu zancen bai yi mata dadi ba domin suna aminci sosai da Zahra’u; musamman da yake ita din mai kwadayi ce sosai ita kuma Zahra’un mai kyauta ce sosai. Inda Allah ya sawa abun ruwan sanyi don taga Yaya Bello shine gaba a wajen maganar, ta kuma san idan ta fiya rawar kai zai ci mutuncinta. Don haka itama tayi Allah ya sanya alkhairi kawai.
Yanda ya gayawa Zahra haka ya gaya musu, cewa ba a saka lokacin bikin ba, domin Yaya Bello ne da abokinsa suka kai kayan kuma ya san babu wanda zai gayawa musamman matarsa wadda suke shiri da Zahra. Itama Hajiya a haka suka barta.
Tunda taji labarin wannan auren Yaya Saratu ta kasa zaune ta kasa tsaye, a tunaninta ko Zahra bata sani ba. Domin wancan karon da ya fara maganar auren Hajiya ya fara gayawa kafin ya gayawa kowa don haka kafin shi ya gayawa Zahra Yaya Saratu ce ta fara gaya mata. Hakan yana daya daga cikin abubuwan da suka kara harzuka zuciyarta a lokacin, taga lallai idan ta bari akayi auren Yusuf ya rainata; don haka ne ma ta san yanda tayi aka fasa.
Yanzu ma sauri Yaya Saratun takeyi domin ta fara kawowa Zahra labari, don haka ranar da Yusuf ya sanar musu washegari ta shirya ta taho gidan Yusuf din.
Kamar yanda ta saba haka akayi mata tarba ta mutunci, kuma da yake da safe tazo harda shayi da burodi aka ajiye mata. Saida taci ta koshi sannan Zahra ta kwashe kwanukan ta zauna a kujerar zaman mutum daya wadda take kusa da wadda Yaya Saratun ta zauna.
Zahra ta dubeta tace
‘Kin kwana biyu baki leko mu ba Yaya Saratu, ya wajen Hajiya?’
Ta gyara zama
‘Hajiya tana nan lafiya wallahi, hidimace tayi min yawa shi yasa kika ji ni shiru.’
‘Allah Sarki.’
Sukayi shiru na dan lokaci, Yaya Saratu tace
‘Sai muka ji kuma wai Abban Sadik aure zai yi.’
Dama ta riga ta san zancen da ya kawota gidan kenan amma sai ta kauda kanta tana murmushi tace
‘Ai kuwa dai, abun ya zo.’
Ta kama haba alamar mamaki sannan ta bata amsa
‘Kin san na zata mutumin nan ya fasa auren nan amma ashe ba zai hakura ba.’
‘To ya za ayi, ai babu laifi sai dai kawai muyita addu’a Allah ya bamu zaman lafiya kawai.’
Wannan magana ta Zahra ta sage gwiwar Saratu, don haka cikin sanyin jiki tace
‘Uhm, ai maza sai a barsu, kedai Uwar Sadiku Allah ya kara miki hakuri don ko ta shigo ma babu abinda zata tsinta a gidan nan. Ba zata iya gasa dake ba don ba duk mutum ba wallahi.’
‘Uhm, Yaya kenan.’
Suka cigaba da hira tana tambayarta labarin inda amaryar zata zauna inda tace mata bata sani ba. Sai can wajen sha biyu na rana sannan tayi shirin tafiya; ai kuwa Zahra ta hada mata goma ta arziki kamar yanda ta saba sannan ta kawo naira dubu biyu ta bata kudin mota.
Sukayi sallama tana ta godiya ta kama hanya.
………
Sam batayi tunanin inda amaryar zata zauna ba sai yanzu da Yaya Saratu ta tuna mata, duk da ma tana ji a jikinta ba za ayi wannan auren ba tunda Malam yace ba za ayin ba. Amma dai zata so ta san tsarin da ya tanada don tayi shirin ko ta kwana.
Wancan lokacin dai da ya fara shirin auren akwai daki a falon kasa wanda yake a kasan dakinsa, nan yace za a gyara amarya ta tare; tunda ba a kwana a ciki ajiya kawai akeyi a ciki kamar store. Yanzun ma ta san bai wuce nan din ba, amma duk da haka zata tambayeshi taji idan ya dawo daga wajen aiki.
Sai bayan la’asar Abban Sadik din ya kirawota ya sanar da ita yau ba zai dawo da wuri ba, suna da meeting da mai girma gwamna kuma sai karfe takwas da rabi ma za a fara meeting din don haka zai yi dare. Don haka ta cigaba da harkarta ta san sai wajen sha daya na dare zai dawo kuma ba zai ci abincin dare ba.
Sai wajen goma da rabi ya dawo gidan, kusan tare suka shigo da Sadik wanda wanda yake zauna a kofar gida yana hira da abokai sai da ya hango motar Abban sannan yayi sauri ya shigo gidan da gudu.
Yana shiga falon tana saukowa daga bene wanda yake cikin falon, sanye take da doguwar rigar bacci ta yafa mayafin abaya. Ta fadada murmushinta ta karasa saukowa daga benen tana fadin
‘Sannu da zuwa Abba, ashe yau da wuri zaku gama meeting din ma.’
Ya sha kunu ya amsa
‘Yauwa. Ina Sadiku?’
Ta nuna alamar mamaki a fuskarta tace
‘Um ina jin ai yana bacci ko? Bari na duba yana dakinsu ai.’
Ta nufi dakin wanda yake can gefe guda a cikin falon, kafin ta karasa yace
‘Ba wani bacci da yakeyi, yanzu ya shigo gidan da ya hango ni.’
Ta tsaya ta juyo zatayi magana, kafin ta bude baki Abban ya daga murya ya kwalawa Sadik kira, ya bude baki zai yi masa kira na biyu Sadik din ya turo kofar dakin ya fito. Ya karaso a hankali yana shafa kai yana kallon kasa kamar mara gaskiya. Kafin ya karaso Abban yace
‘Me kakeyi a waje karfe goma da rabi na dare.’
Cikin rawar murya yace
‘Eh Abba dama Sulaiman na bawa wayarsa da ya kawo aka saka masa chaji.’
‘Shi yasa kake gudu da ka hangoni ko?’
Yayi shiru ya kara sunkuyar da kai don ya san an riga an kamashi.
Abban ya cigaba
‘Na hanaka wuce karfe tara a waje amma baka ji ko? So kake mu sa kafar wando daya da kai ko Sadik?’
Da sauri yace
‘A’a Abba, kayi hakuri ba zan sake ba.’
Ya jijjiga kai yayi kwafa ya wuce ta tsakanin Zahra da Sadik din ya haye sama ya nufi dakinsa.
Zahra ta harari Sadik tace
‘Allah ya shiryeka kai dai.’
‘Mommy wallahi Suleiman na bawa wayarsa.’
‘Tafi ka kwanta ni bana son shegiyar karyar tsiya.’
Ta haye sama itama ta bi Abban dakinsa.
Sai da yayi wanka sannan ta kawo masa shayi, ya zauna a kan kujera yana kurbar shayin yana duba wasu takardu yayinda ita kuma take kwance a kan gadon tana kallonsa. Jimawa kadan ya dubeta yace
‘Ki kwanta kiyi barcinki tunda na dawo, kinga gobe da wuri ‘yan makaranta zasu tashe ki.’
Tayi murmushi tace
‘Yanzu zaka ji munshari na kuwa.’
Shima yayi dariya.
Jimawa kadan tace
‘Abban Sadik.’
Sukayi sallama da alkawarin zata kirawo shi gobe ta sanar da shi lokacin da yayi saura kafin auren.
Haka Hajiya Zahra’u Uwar Sadiku ta karasa wunin wannan ranar cikin damuwa.
……….
Tunda ya dawo gidan daga wajen aiki take tunanin ta yanda zata tambayeshi yaushe ne auren nasa, ta kasa nutsuwa ta jeranta kalamanta yanda ba zai iya karanta damuwarta ba. Har dare yayi bata sami wannan damar ba, ya gama cin abinci sa ya zauna a falon sama yayi kallon TV daga baya kuma ya koma dakinsa.
Yana zaune a kan gadonsa ya mike kafa yana aiki a kwanfutarsa ta shiga dakin sanye da kayan baccinta, bayan ya amsa sallamarta ta karasa ta kwanta a gefensa tace
‘Har yanzu aikin bai kare ba Yallabai.’
Ya kalleta yana murmushi
‘Saura kadan Madam, in zo ne ana nemana?’
Tayi ‘yar gajeriyar dariya
‘A’a gama a hankali abunka.’
Ya mayar da hankali kan kwamfutar ya cigaba da aikinsa yayinda ta muskuta ta gyara kwanciyarta. Jimawa kadan ta kirawo sunansa
‘Abban Sadik.’
Ya kauda idonsa daga kwamfutar ya dubeta alamar yana sauraronta, don haka ta cigaba
‘Yaushe ne auren naka da kace zakayi?’
Ba tare da ya bar aikin da yakeyi ba yace
‘Da sauran lokaci gaskiya tunda kin ga bamu gama daidatawa ba tukunnu, ba zan iya sanin lokacin ba yanzu.’
‘Uhmm!’
Taji dadin hakan don ta san hakan yana nufin tana da isasshen lokacin don karasa nata shirye-shiryen.
Ya cigaba da aikinsa ita kuma tana kwance, jimawa kadan ta sake kiransa
‘Abban Sadik.’
Ya kalleta sannan ya amsa
‘Um.’
Ta gyara kwanciyarta ta tokare kanta da hannunta ta bishi da kallo ta fara magana kamar tana nazarin kalmominta
‘Don Allah me ya sa kake son kara aure? Idan akwai wani abu da kake bukata ai gara kayi min magana na gyara ko?’
Ya ajiye kwamfutar a kan durowar gefen gado ya dan matsa kusa da ita ya fara wasa da gashin kanta wanda babu kitso amma dai ta daureshi guri daya da ribbon, ya dubeta suka hada ido sannan yace
‘Babu abinda nake bukata, kuma ke ma babu abinda kikayi min. Kawai dai mun hadu da Aishan ne kuma tunda ida damar auren mace hudu ai babu laifin don nayi biyu ko? Amma kada ki damu, babu abinda zai shafi son da nakeyi miki don ni din naki ne kuma ke din tawa ce kin ji. Ki kwantar da hankalinki.’
‘Hmm! Aisha sunanta ashe.’
‘Eh.’
‘Um.’
Ta zame ta gyara kwanciyarta tana fadin
‘Bari na kwanta bacci nake ji.’
Ya cigaba da aikinsa yayinda ita kuma ta juya masa baya ta rufe ido da sunan bacci, tunani kala-kala suna ta zarya a kwakwalwarta.
UWAR SADDIKU
Written by
Sakina Yazid
(Innar su Amal)
6
Tunda Abban Sadik ya tabbatar mata ba a kusa aurensa ba ta dan sami natsuwar, domin ta sanarwa Malam Hatimu shi kuma yayi mata alkawarin za ayi mata wani babban aiki wanda daga shi maigidanta ba zai sake aure ba har karshen rayuwarsa. Don haka ta saki ranta tana harkarta kamar bata da wata damuwa, kuma da bata ji yayi zancen kayan auren ba sai ta kara sakankancewa aikin Malam ne yake aiki.
…….
Sai bayan da ya sanar da Zahra aurensa sannan yaje gidansu ya sanar da mutanen gidan, mahaifiyarsu Hajiya Balaraba ta sawa abun albarka sosai duk da dai ta ja masa kunne a kan kada ya kuskura ya bata da uwargidansa. Ita kuwa yayarsa Yaya Saratu zancen bai yi mata dadi ba domin suna aminci sosai da Zahra’u; musamman da yake ita din mai kwadayi ce sosai ita kuma Zahra’un mai kyauta ce sosai. Inda Allah ya sawa abun ruwan sanyi don taga Yaya Bello shine gaba a wajen maganar, ta kuma san idan ta fiya rawar kai zai ci mutuncinta. Don haka itama tayi Allah ya sanya alkhairi kawai.
Yanda ya gayawa Zahra haka ya gaya musu, cewa ba a saka lokacin bikin ba, domin Yaya Bello ne da abokinsa suka kai kayan kuma ya san babu wanda zai gayawa musamman matarsa wadda suke shiri da Zahra. Itama Hajiya a haka suka barta.
Tunda taji labarin wannan auren Yaya Saratu ta kasa zaune ta kasa tsaye, a tunaninta ko Zahra bata sani ba. Domin wancan karon da ya fara maganar auren Hajiya ya fara gayawa kafin ya gayawa kowa don haka kafin shi ya gayawa Zahra Yaya Saratu ce ta fara gaya mata. Hakan yana daya daga cikin abubuwan da suka kara harzuka zuciyarta a lokacin, taga lallai idan ta bari akayi auren Yusuf ya rainata; don haka ne ma ta san yanda tayi aka fasa.
Yanzu ma sauri Yaya Saratun takeyi domin ta fara kawowa Zahra labari, don haka ranar da Yusuf ya sanar musu washegari ta shirya ta taho gidan Yusuf din.
Kamar yanda ta saba haka akayi mata tarba ta mutunci, kuma da yake da safe tazo harda shayi da burodi aka ajiye mata. Saida taci ta koshi sannan Zahra ta kwashe kwanukan ta zauna a kujerar zaman mutum daya wadda take kusa da wadda Yaya Saratun ta zauna.
Zahra ta dubeta tace
‘Kin kwana biyu baki leko mu ba Yaya Saratu, ya wajen Hajiya?’
Ta gyara zama
‘Hajiya tana nan lafiya wallahi, hidimace tayi min yawa shi yasa kika ji ni shiru.’
‘Allah Sarki.’
Sukayi shiru na dan lokaci, Yaya Saratu tace
‘Sai muka ji kuma wai Abban Sadik aure zai yi.’
Dama ta riga ta san zancen da ya kawota gidan kenan amma sai ta kauda kanta tana murmushi tace
‘Ai kuwa dai, abun ya zo.’
Ta kama haba alamar mamaki sannan ta bata amsa
‘Kin san na zata mutumin nan ya fasa auren nan amma ashe ba zai hakura ba.’
‘To ya za ayi, ai babu laifi sai dai kawai muyita addu’a Allah ya bamu zaman lafiya kawai.’
Wannan magana ta Zahra ta sage gwiwar Saratu, don haka cikin sanyin jiki tace
‘Uhm, ai maza sai a barsu, kedai Uwar Sadiku Allah ya kara miki hakuri don ko ta shigo ma babu abinda zata tsinta a gidan nan. Ba zata iya gasa dake ba don ba duk mutum ba wallahi.’
‘Uhm, Yaya kenan.’
Suka cigaba da hira tana tambayarta labarin inda amaryar zata zauna inda tace mata bata sani ba. Sai can wajen sha biyu na rana sannan tayi shirin tafiya; ai kuwa Zahra ta hada mata goma ta arziki kamar yanda ta saba sannan ta kawo naira dubu biyu ta bata kudin mota.
Sukayi sallama tana ta godiya ta kama hanya.
………
Sam batayi tunanin inda amaryar zata zauna ba sai yanzu da Yaya Saratu ta tuna mata, duk da ma tana ji a jikinta ba za ayi wannan auren ba tunda Malam yace ba za ayin ba. Amma dai zata so ta san tsarin da ya tanada don tayi shirin ko ta kwana.
Wancan lokacin dai da ya fara shirin auren akwai daki a falon kasa wanda yake a kasan dakinsa, nan yace za a gyara amarya ta tare; tunda ba a kwana a ciki ajiya kawai akeyi a ciki kamar store. Yanzun ma ta san bai wuce nan din ba, amma duk da haka zata tambayeshi taji idan ya dawo daga wajen aiki.
Sai bayan la’asar Abban Sadik din ya kirawota ya sanar da ita yau ba zai dawo da wuri ba, suna da meeting da mai girma gwamna kuma sai karfe takwas da rabi ma za a fara meeting din don haka zai yi dare. Don haka ta cigaba da harkarta ta san sai wajen sha daya na dare zai dawo kuma ba zai ci abincin dare ba.
Sai wajen goma da rabi ya dawo gidan, kusan tare suka shigo da Sadik wanda wanda yake zauna a kofar gida yana hira da abokai sai da ya hango motar Abban sannan yayi sauri ya shigo gidan da gudu.
Yana shiga falon tana saukowa daga bene wanda yake cikin falon, sanye take da doguwar rigar bacci ta yafa mayafin abaya. Ta fadada murmushinta ta karasa saukowa daga benen tana fadin
‘Sannu da zuwa Abba, ashe yau da wuri zaku gama meeting din ma.’
Ya sha kunu ya amsa
‘Yauwa. Ina Sadiku?’
Ta nuna alamar mamaki a fuskarta tace
‘Um ina jin ai yana bacci ko? Bari na duba yana dakinsu ai.’
Ta nufi dakin wanda yake can gefe guda a cikin falon, kafin ta karasa yace
‘Ba wani bacci da yakeyi, yanzu ya shigo gidan da ya hango ni.’
Ta tsaya ta juyo zatayi magana, kafin ta bude baki Abban ya daga murya ya kwalawa Sadik kira, ya bude baki zai yi masa kira na biyu Sadik din ya turo kofar dakin ya fito. Ya karaso a hankali yana shafa kai yana kallon kasa kamar mara gaskiya. Kafin ya karaso Abban yace
‘Me kakeyi a waje karfe goma da rabi na dare.’
Cikin rawar murya yace
‘Eh Abba dama Sulaiman na bawa wayarsa da ya kawo aka saka masa chaji.’
‘Shi yasa kake gudu da ka hangoni ko?’
Yayi shiru ya kara sunkuyar da kai don ya san an riga an kamashi.
Abban ya cigaba
‘Na hanaka wuce karfe tara a waje amma baka ji ko? So kake mu sa kafar wando daya da kai ko Sadik?’
Da sauri yace
‘A’a Abba, kayi hakuri ba zan sake ba.’
Ya jijjiga kai yayi kwafa ya wuce ta tsakanin Zahra da Sadik din ya haye sama ya nufi dakinsa.
Zahra ta harari Sadik tace
‘Allah ya shiryeka kai dai.’
‘Mommy wallahi Suleiman na bawa wayarsa.’
‘Tafi ka kwanta ni bana son shegiyar karyar tsiya.’
Ta haye sama itama ta bi Abban dakinsa.
Sai da yayi wanka sannan ta kawo masa shayi, ya zauna a kan kujera yana kurbar shayin yana duba wasu takardu yayinda ita kuma take kwance a kan gadon tana kallonsa. Jimawa kadan ya dubeta yace
‘Ki kwanta kiyi barcinki tunda na dawo, kinga gobe da wuri ‘yan makaranta zasu tashe ki.’
Tayi murmushi tace
‘Yanzu zaka ji munshari na kuwa.’
Shima yayi dariya.
Jimawa kadan tace
‘Abban Sadik.’