Sashe 13
Uwar Sadiku Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tana kwance a kan gado sanye da kayan bacci an kashe fitila da alama bacci takeyi, ya kunna fitlar tare da yin gyaran murya ya karasa ciki da sallama. Ta juyo ta dubeshi sannan ta tashi zaune a tsakiyar gadon, yayinda shi kuma ya zauna a gefen gadon.
‘Sannu da zuwa.’
Ta fada murya kasa-kasa.
Da murmushi ya amsa
‘Sannu. Ya gajiya? Ya taro?’
‘Alhamdulillah, kowa ya tafi makwancinsa.’
Yanayinta da kuma yanda take bashi amsa ya fahimci bata da walwala kuma idan yaja hirar zasuyi rigima, don haka ya ajiye ledar a kan durowar gefen gadonta yana fadin
‘Ga wannan ke da yara, sai dai naga duk kunyi bacci sai ki saka a fridge kwayi breakfast da shi.’
‘Mungode.’
Suka dan taba hira tana ta faman cijewa saboda kada tayi kuka a gabansa, shi din ma da yake yana sauri ya tafi wajen amarya kafin Zahran ta fara wata fitnar sai kawai yayi mata sallama yace ta rufe musu gidan.
Ta biyoshi a baya har suka zo bakin kofa sannan ta rufe musu kofar shi kuma ya wuce, ya dauki ledarsa a mota ya nufi gidan amarya.
……….
Kamshin da ya cika gidan shi ya fara yi masa maraba, ya riga ya san ita kadai ce a gidan don haka yana shiga ya mayar da kofar ya kulle. Ya karasa ya ajiye ledar hannusa a kan dining table, ya juyo ya karewa falon kallo yana murmushi.
Ya shige dakin yana rike da Babbar rigarsa, tun kafin ya karasa ciki ya hangota a kan gadon nade da laffayarta ta kashingide daga zaune a gefen gadon. Ya karasa ciki da sallama wadda ta farko da ita daga gyangyadin da takeyi, ta gyara zama tana amsa sallamar.
Ya karasa ya zauna a kusa da ita yana kallon fuskarta yana murmushi yayinda ta mayar masa da murmushinsa tana kokarin boye kwallar da take makale a idonta. Ya kama hannunta na hagu yana kallon lallenta, ta bi hannunsa da kallo yanda ya rike hannunta. A take hawayen da take boyewa ya kwace; Mustafa; ta kasa cire shi daga kwakwalwarta tunda aka ce an daura mata aure.
Ya matsa kusa da ita ya janyota jikinsa ya kwantar da kanta a kirjinsa; ya fahimci abinda yake saka ta kuka, ko bata gaya masa ya san tunanin tsohon mijinta takeyi. Yayiwa kansa alkawarin tabbas sai ya jiyar da ita dadi a rayuwarsu, sai ya so ta ya nuna mata soyayya fiye da yanda tsohon mijinta ya nuna mata. Sai ya jiyar da ita dadin da zata manta da duk wani namiji idan ba shi ba; domin shima yana sonta kuma ya tabbatar yana sonta fiye da yanda Mustafa ya sota.
Sai da ya dauki lokaci yana lallashinta sannan ta iya samu ta tsayar da hawayenta. Ya tayata ta warware laffayarta suka ci abinci sannan sukayi alwala sukayi Sallah.
Sai da yayi da gaske da ita sannan ta iya canza kayanta ta saka kayan bacci, yana ta yi mata dariya kamar wata budurwa saboda kunyar da take ji. Bayan sun gama ya kashe musu fitila suka kwanta, rungumeta kawai yayi saboda ya kula da yanda take cikin damuwa kuma ga bacci da take ji. Ya danne duk wata bukata tasa ya kyaleta zuwa gobe, kafin nan ta kara sakewa ta sami nutsuwa.
……
Kusan lokaci guda suka tashi da asuba, nan da nan sukayi wanka suka yi Sallah. Yayi zaton zata koma bacci don haka ya fice daga dakin ya komo falo ya fara kokarin hada TV. Bai jima da fitowa ba itama ta fito, suka zauna yana hada TV din suna hira, har ya gama suka zauna suna kallo.
Karfe takwas ta dan gota ta dubeshi tace
‘Nifa yunwa nake ji, bari na duba ko ruwan shayi na sama mana.’
Ta mike ta nufi kicin, yayinda shima ya nufi dining table inda ya ajiye ledar da ya shigo da ita jiya. Ya zazzage kayan shayin da burodin da ya siyo ya kwasa ya kai mata kicin din.
Yayi tunanin Zahra zata basu breakfast amma baya so yayi maganar don bai san yanda za su dauki abun ba. Nan da nan Aisha ta hada musu shayi da burodi ta dumama ragowar naman jiya suka zauna suna kallon TV suna cci
____
Tana zaune a falonsa ita kadai tana shan shayi, shayin kawai zata iya sha a halin yanzu domin kanta ciwo yake yi saboda yanda bata samu tayi bacci ba ko daya. Kwana tayi tana tunanin yanda za ayi Yusuf, nata ita kadai, yaje ya kwana da wata mace. Kuma haka ta tashi tana ta wannan tunanin tana tsaki.
Tun sassafe Jummai ta zo don haka ta barta da yaran a kasa ta dawo sama ta zauna. Koda Jumman ta shigo saida ta tambayeta ko za a yiwa amarya abinci amma tace a’a. Ta san ya kamata tayi amma bazata yi ba, domin da ana so ta bata abincin ai da a nan cikin gidan za a saka amaryar su zauna tare.
Karar wayarta ce ta katse tunaninta, ta daga wayar ta duba, Abban Sadik ne.
Saida taja tsaki sannan ta amsa wayar ta kara a kunnenta
‘Uwargida ran gida, kin tashi lafiya?’
Ta wurkila kwayar idonta cike da takaici sannan tayi yake ta amsa
‘Lafiya kalau, ya amarya?’
‘Alhamdulillah. Gamu nan shigowa yanzu zan kawo miki kanwar taki.’
‘To Allah ya kawo ku lafiya.’
Ta jiye wayar ta dubi agogon bangon dake falon, karfe goma da kwata. Ta ja tsaki ta kawar da kai, bata ma san lokacin ya tafi haka ba don ko wanka bata yi ba.
A take ta tuno abinda ya kamata ta fara yi, inda ta tashi da hanzari ta koma dakinta. Ta san dai inda suka boye layar nan jiya tabbas Abban Sadiku ta nan zai shigo falon don haka gara ta nemo layar taje ta mayar ayi ta ta kare kawai.
Tana shiga dakin ta nufi wardrobe inda ta rataye rigar da ta saka jiya a saman wardrobe din, ta zura hannunta a hankali cikin aljihun rigar ta laluba taji babu komai. Ta koma ta daya gefen ta zura hannunta a dayan aljihun ta laluba a hankali bata ji komai. Mamaki ya bayyana a fuskarta, ta fizge rigar daga saman wardrobe din ta karasa ta bajeta a kan gado ta sake lalube aljihun duka biyun bata ji komai ba. Ta daga rigar ta zazzage babu a binda ya fado, ta zauna a kan gado tana kallon rigar tana mamakin inda layar ta shiga.
Tabbas ba mantuwa tayi ba, a hannunta Amina ta bata layar kuma tabbas a aljihun rigar ta saka. Bata cire ba ta barta a kan da safe ta dauke; to a ina layar zata fadi?. Gashi tsaf aka share gidan jiya kuma yau ma Jummai har tayi shara.
Ta mike ta koma gaban wardrobe din ta sake dubawa ko a kasa layar ta fado, bata sami komai ba. Ta dawo ta zauna a gefen gadon tana tunani; to ina layar zata shiga?
‘Ikon Allah!’
Ta fada a fili.
Motsin taba kofar ne ya dawo da ita hayyacinta, Yusra ce ta shigo da sallama tace
‘Mommy Abba ya zo da matarsa.’
Taja tsaki
‘Mtsewwww! Kice masa ina wanka.’
‘Ai ba aiko ni yayi ba na san yanzu zai hawo nemanki.’
Ta mike tana fadin
‘To bari ki gani.’
Ta fada bandaki ita kuma Yusra ta juyo ta fito.Tana jin lokacin da Abban ya shigo dakin ya fita. Har ta gama wankan nan bata gano inda layar nan tayi ba don haka ta hakura tunda Aishan ta riga ta shigo ta zauna a falon. Haka ta fito ta zabo leshi mai kyau ta shirya tsaf ta fesa turarukanta masu kamshi sannan ta sauko.
Tun kan ta karasa saukowa ta hangosu; Aishan tana zaune a kan kujerar zaman mutum daya shi kuma Abban yana kan kujerar zaman mutum uku. Sadik da Yusra tunda suka gaisheta suka bar wajen, don Yusra ma tunda ta gaisheta ta haye sama bata sauko ba. Rukayya ce a zaune a kusa da Aishan sai Ummi da take ta faman yi mata surutu.
Ta karaso da sallama, ta wuce kai tsaye ta zauna a kusa da Abban Sadik. Tana murmushi ta dubeshi
‘Yallabi Ina kwana?’
Yaji dadin yanda ya ganta da fara’arta don haka shima tashi fara’ar ta karu
‘Lafiya kalau, ya kuka kwana?’
Bayan ta amsashi ta juya wajen Aisha tace
‘Amarya bakya laifi, barka da zuwa.’
Tana murmushi ta mayar mata da amsa
‘Yauwa, ina kwana.’
Suka gaisa cikin walwala, Zahra ta umarci Jummai ta kawo muta ruwa da lemo, ta dubi Abban Sadika tace
‘Ka san kasa tashi nayi saboda gajiya shi ya sa ban samu na dafa muku abincin safe ba, ko a kawo muku yanzu ku karya.’
‘A’a, mun karya ma sai dai ko kanwar taki zata kara.’
Tace
‘A’a na koshi.’
Sukayi shiru na dan lokaci, Abban Sadik yace
‘To Zahra ga kanwarki nan, naga ma kun riga kun saba kuma ban ga alamar matsala ba. Allah ya hada min kanku. Na gaya mata duk abinda take bukata ta nemeki, yara kuma yanzu sun zama masu gida biyu, duk inda suka shiga daya ne.’
Zahra tace
‘Hakane, Allah ya bada zaman lafiya. Ai ga uwata sarkin kaudi har ta makale mata.’
Suka yi dariya gaba daya. Abban ya mike yana fadin
‘Bari na hau sama, idan na sauko sai mu wuce.’
Ya Haye sama ya barsu a nan falon.
Yana wucewa Zahra ta sha kunu ta bata rai, suna hada ido da Aisha ta dauke nata kana saboda yanda taga sauyin yanayin.
Ta harari Rukayya wadda take zaune a kujerar kusa da ta Aisha tace
‘Ku kuma kowa ya bace kuna zaune kuna biya bakin mutane, tashi ki bani waje.’
Nan da nan suka fice daga falon ya zama daga Zahra sai Aishan, tana ta faman bata rai ita kuwa Aishan ta ma kasa hada ido da ita tunda ta kula da yanda yanayinta ya canza.
Jimawa kadan ta tashi ta kashe talabijin din dake kunne a falon ta haye sama ya zama Aishace ita kadai a falon.
Ta cika da mamakin yanda kiri-kiri Zahra tayi mata fuska biyu a cikin abinda bai fi minti ahsirin ba .
‘Sannu da zuwa.’
Ta fada murya kasa-kasa.
Da murmushi ya amsa
‘Sannu. Ya gajiya? Ya taro?’
‘Alhamdulillah, kowa ya tafi makwancinsa.’
Yanayinta da kuma yanda take bashi amsa ya fahimci bata da walwala kuma idan yaja hirar zasuyi rigima, don haka ya ajiye ledar a kan durowar gefen gadonta yana fadin
‘Ga wannan ke da yara, sai dai naga duk kunyi bacci sai ki saka a fridge kwayi breakfast da shi.’
‘Mungode.’
Suka dan taba hira tana ta faman cijewa saboda kada tayi kuka a gabansa, shi din ma da yake yana sauri ya tafi wajen amarya kafin Zahran ta fara wata fitnar sai kawai yayi mata sallama yace ta rufe musu gidan.
Ta biyoshi a baya har suka zo bakin kofa sannan ta rufe musu kofar shi kuma ya wuce, ya dauki ledarsa a mota ya nufi gidan amarya.
……….
Kamshin da ya cika gidan shi ya fara yi masa maraba, ya riga ya san ita kadai ce a gidan don haka yana shiga ya mayar da kofar ya kulle. Ya karasa ya ajiye ledar hannusa a kan dining table, ya juyo ya karewa falon kallo yana murmushi.
Ya shige dakin yana rike da Babbar rigarsa, tun kafin ya karasa ciki ya hangota a kan gadon nade da laffayarta ta kashingide daga zaune a gefen gadon. Ya karasa ciki da sallama wadda ta farko da ita daga gyangyadin da takeyi, ta gyara zama tana amsa sallamar.
Ya karasa ya zauna a kusa da ita yana kallon fuskarta yana murmushi yayinda ta mayar masa da murmushinsa tana kokarin boye kwallar da take makale a idonta. Ya kama hannunta na hagu yana kallon lallenta, ta bi hannunsa da kallo yanda ya rike hannunta. A take hawayen da take boyewa ya kwace; Mustafa; ta kasa cire shi daga kwakwalwarta tunda aka ce an daura mata aure.
Ya matsa kusa da ita ya janyota jikinsa ya kwantar da kanta a kirjinsa; ya fahimci abinda yake saka ta kuka, ko bata gaya masa ya san tunanin tsohon mijinta takeyi. Yayiwa kansa alkawarin tabbas sai ya jiyar da ita dadi a rayuwarsu, sai ya so ta ya nuna mata soyayya fiye da yanda tsohon mijinta ya nuna mata. Sai ya jiyar da ita dadin da zata manta da duk wani namiji idan ba shi ba; domin shima yana sonta kuma ya tabbatar yana sonta fiye da yanda Mustafa ya sota.
Sai da ya dauki lokaci yana lallashinta sannan ta iya samu ta tsayar da hawayenta. Ya tayata ta warware laffayarta suka ci abinci sannan sukayi alwala sukayi Sallah.
Sai da yayi da gaske da ita sannan ta iya canza kayanta ta saka kayan bacci, yana ta yi mata dariya kamar wata budurwa saboda kunyar da take ji. Bayan sun gama ya kashe musu fitila suka kwanta, rungumeta kawai yayi saboda ya kula da yanda take cikin damuwa kuma ga bacci da take ji. Ya danne duk wata bukata tasa ya kyaleta zuwa gobe, kafin nan ta kara sakewa ta sami nutsuwa.
……
Kusan lokaci guda suka tashi da asuba, nan da nan sukayi wanka suka yi Sallah. Yayi zaton zata koma bacci don haka ya fice daga dakin ya komo falo ya fara kokarin hada TV. Bai jima da fitowa ba itama ta fito, suka zauna yana hada TV din suna hira, har ya gama suka zauna suna kallo.
Karfe takwas ta dan gota ta dubeshi tace
‘Nifa yunwa nake ji, bari na duba ko ruwan shayi na sama mana.’
Ta mike ta nufi kicin, yayinda shima ya nufi dining table inda ya ajiye ledar da ya shigo da ita jiya. Ya zazzage kayan shayin da burodin da ya siyo ya kwasa ya kai mata kicin din.
Yayi tunanin Zahra zata basu breakfast amma baya so yayi maganar don bai san yanda za su dauki abun ba. Nan da nan Aisha ta hada musu shayi da burodi ta dumama ragowar naman jiya suka zauna suna kallon TV suna cci
____
Tana zaune a falonsa ita kadai tana shan shayi, shayin kawai zata iya sha a halin yanzu domin kanta ciwo yake yi saboda yanda bata samu tayi bacci ba ko daya. Kwana tayi tana tunanin yanda za ayi Yusuf, nata ita kadai, yaje ya kwana da wata mace. Kuma haka ta tashi tana ta wannan tunanin tana tsaki.
Tun sassafe Jummai ta zo don haka ta barta da yaran a kasa ta dawo sama ta zauna. Koda Jumman ta shigo saida ta tambayeta ko za a yiwa amarya abinci amma tace a’a. Ta san ya kamata tayi amma bazata yi ba, domin da ana so ta bata abincin ai da a nan cikin gidan za a saka amaryar su zauna tare.
Karar wayarta ce ta katse tunaninta, ta daga wayar ta duba, Abban Sadik ne.
Saida taja tsaki sannan ta amsa wayar ta kara a kunnenta
‘Uwargida ran gida, kin tashi lafiya?’
Ta wurkila kwayar idonta cike da takaici sannan tayi yake ta amsa
‘Lafiya kalau, ya amarya?’
‘Alhamdulillah. Gamu nan shigowa yanzu zan kawo miki kanwar taki.’
‘To Allah ya kawo ku lafiya.’
Ta jiye wayar ta dubi agogon bangon dake falon, karfe goma da kwata. Ta ja tsaki ta kawar da kai, bata ma san lokacin ya tafi haka ba don ko wanka bata yi ba.
A take ta tuno abinda ya kamata ta fara yi, inda ta tashi da hanzari ta koma dakinta. Ta san dai inda suka boye layar nan jiya tabbas Abban Sadiku ta nan zai shigo falon don haka gara ta nemo layar taje ta mayar ayi ta ta kare kawai.
Tana shiga dakin ta nufi wardrobe inda ta rataye rigar da ta saka jiya a saman wardrobe din, ta zura hannunta a hankali cikin aljihun rigar ta laluba taji babu komai. Ta koma ta daya gefen ta zura hannunta a dayan aljihun ta laluba a hankali bata ji komai. Mamaki ya bayyana a fuskarta, ta fizge rigar daga saman wardrobe din ta karasa ta bajeta a kan gado ta sake lalube aljihun duka biyun bata ji komai ba. Ta daga rigar ta zazzage babu a binda ya fado, ta zauna a kan gado tana kallon rigar tana mamakin inda layar ta shiga.
Tabbas ba mantuwa tayi ba, a hannunta Amina ta bata layar kuma tabbas a aljihun rigar ta saka. Bata cire ba ta barta a kan da safe ta dauke; to a ina layar zata fadi?. Gashi tsaf aka share gidan jiya kuma yau ma Jummai har tayi shara.
Ta mike ta koma gaban wardrobe din ta sake dubawa ko a kasa layar ta fado, bata sami komai ba. Ta dawo ta zauna a gefen gadon tana tunani; to ina layar zata shiga?
‘Ikon Allah!’
Ta fada a fili.
Motsin taba kofar ne ya dawo da ita hayyacinta, Yusra ce ta shigo da sallama tace
‘Mommy Abba ya zo da matarsa.’
Taja tsaki
‘Mtsewwww! Kice masa ina wanka.’
‘Ai ba aiko ni yayi ba na san yanzu zai hawo nemanki.’
Ta mike tana fadin
‘To bari ki gani.’
Ta fada bandaki ita kuma Yusra ta juyo ta fito.Tana jin lokacin da Abban ya shigo dakin ya fita. Har ta gama wankan nan bata gano inda layar nan tayi ba don haka ta hakura tunda Aishan ta riga ta shigo ta zauna a falon. Haka ta fito ta zabo leshi mai kyau ta shirya tsaf ta fesa turarukanta masu kamshi sannan ta sauko.
Tun kan ta karasa saukowa ta hangosu; Aishan tana zaune a kan kujerar zaman mutum daya shi kuma Abban yana kan kujerar zaman mutum uku. Sadik da Yusra tunda suka gaisheta suka bar wajen, don Yusra ma tunda ta gaisheta ta haye sama bata sauko ba. Rukayya ce a zaune a kusa da Aishan sai Ummi da take ta faman yi mata surutu.
Ta karaso da sallama, ta wuce kai tsaye ta zauna a kusa da Abban Sadik. Tana murmushi ta dubeshi
‘Yallabi Ina kwana?’
Yaji dadin yanda ya ganta da fara’arta don haka shima tashi fara’ar ta karu
‘Lafiya kalau, ya kuka kwana?’
Bayan ta amsashi ta juya wajen Aisha tace
‘Amarya bakya laifi, barka da zuwa.’
Tana murmushi ta mayar mata da amsa
‘Yauwa, ina kwana.’
Suka gaisa cikin walwala, Zahra ta umarci Jummai ta kawo muta ruwa da lemo, ta dubi Abban Sadika tace
‘Ka san kasa tashi nayi saboda gajiya shi ya sa ban samu na dafa muku abincin safe ba, ko a kawo muku yanzu ku karya.’
‘A’a, mun karya ma sai dai ko kanwar taki zata kara.’
Tace
‘A’a na koshi.’
Sukayi shiru na dan lokaci, Abban Sadik yace
‘To Zahra ga kanwarki nan, naga ma kun riga kun saba kuma ban ga alamar matsala ba. Allah ya hada min kanku. Na gaya mata duk abinda take bukata ta nemeki, yara kuma yanzu sun zama masu gida biyu, duk inda suka shiga daya ne.’
Zahra tace
‘Hakane, Allah ya bada zaman lafiya. Ai ga uwata sarkin kaudi har ta makale mata.’
Suka yi dariya gaba daya. Abban ya mike yana fadin
‘Bari na hau sama, idan na sauko sai mu wuce.’
Ya Haye sama ya barsu a nan falon.
Yana wucewa Zahra ta sha kunu ta bata rai, suna hada ido da Aisha ta dauke nata kana saboda yanda taga sauyin yanayin.
Ta harari Rukayya wadda take zaune a kujerar kusa da ta Aisha tace
‘Ku kuma kowa ya bace kuna zaune kuna biya bakin mutane, tashi ki bani waje.’
Nan da nan suka fice daga falon ya zama daga Zahra sai Aishan, tana ta faman bata rai ita kuwa Aishan ta ma kasa hada ido da ita tunda ta kula da yanda yanayinta ya canza.
Jimawa kadan ta tashi ta kashe talabijin din dake kunne a falon ta haye sama ya zama Aishace ita kadai a falon.
Ta cika da mamakin yanda kiri-kiri Zahra tayi mata fuska biyu a cikin abinda bai fi minti ahsirin ba .