Sashe 70
Uwar Sadiku Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
‘To gaskiya Alhaji wannan bayanin da kayi min ya fi kama da sihiri, Allah ne ma ya takaita abun. Watakila kai din kana da wata kariya ko kuma gidan naka na da makari shi yasa da suka shigo suka ga juna. Tunda idan ban manta ba lokacin da na yiwa Asma’u rukiyya na baka taimako kala-kala naka da na yaran.’
‘Hakane. To yanzu ya za ayi Malam? Na iya barinsu su koma gidan don ni gaskiya ina tsoron su koma su sake mantawa.’
Suka sake yin shiru na dan lokaci.
Jimawa kadan Malam Sama’ila yace
‘Akwai Malam Audurahmanu, kai ka san shi ai wanda yake zuwa mana limancin sallar dare da azumi. Sai dai shi a unguwar koki yake, shine ya kware a aikin sihiri ni dai ka barni da rukiyya idan aljani ya bayyana a jikin mutum.’
‘To ai sai mu tashi muje in dai zamu sameshi yanzun.’
‘Zamu sameshi tunda ko baya gida makarantarsu kusa da gidan ne’
Yaya Bello ya dubi Abban Sadik yace
‘To kaji ai sai ka tashi muje ko?’
Cikin sanyin murya ya amsa
‘To Yaya, yanda kace.’
Gaba daya suka mike suka fito, har sun kusan fita Yaya Bello ya koma yacewa Anti Karima
‘Ina ga ki dauko mayafi muje saboda ita Aisha din kya zauna da ita.’
Don haka ta saka hijabinta suka shiga motar Abban Sadik Yaya Bello ya tuka suka kama hanya.
A makaranta suka sami Malam Audurahmanu, babu dalibai don an tashi ‘yan islamiyya don haka ya nuna musu aji suka zauna.
Bayan Malam Sama’ila yayi masa bayani ya tambayi Aisha itama tayi nata bayanin, shi kuwa Abban Sadik da aka tambayeshi ma kasa bayanin yayi; abinda yake tunawa kawai shine ya dade bai ga Aishan ba kuma ya san bai saketa ba.
Malam Audurahmanu ya dubi Yaya Bello yace
‘Ina zuwa.’
Ya fita daga ajin.
Jimawa kadan ya dawo dauke da robar ruwa karama guda biyu da kuma wani mai a 'yar roba kamar ta Robb. Ya mikawa Aisha robar ruwan guda daya yace ta shanye, ta kalli Anti Karima ta daga mata kai don haka tayi Bismillah ta shanye. Ya mikawa Abban Sadik din dayan yace shima ya shanye, ba tare da wani musu ba ya shanye.
Ya dubi Yaya Bello yace
‘Ayoyin karya sihiri ne, sune matakin farko za a sha na kwana bakwai.’
Aisha tace
‘Ni dama tunda abun ya faru kullum sai na tofa ayoyin na sha sai dai a ruwan fanfo ne ba na zamzam ba.’
Malam yace
‘Ma Sha Allahu to shi ya sa ma abun baiyi wani tasiri sosai a kanki ba, karanta min ayoyin naji.’
Nan take ta karanta masa ayoyin ba tare da wani kuskure ba.
Yana murmushi yace
‘Ma sha Allah, in dai kika rike wannan babu wani sihiri da zai yi tasiri a kanki, ko yayi ma na dan lokaci ne tunda Allah yana jarraba bawa da abinda ya so.’
Ya mikawa Abban Sadik ‘yar robar hannunsa yace ka lakaci wannan ka shafa a kanka. Ya karbi robar ya rike amma ya kasa ko budewa, jujjuyata kawai yakeyi yana kallonta. Kafin yace wani abu Yaya Bello ya karba ya bude, ya lakaci man da yake ciki ya muttsike a hannunsa ya cire hular Abban Sadik din ya kama kan nasa ya shafe masa man tas. Nan da nan idonsa yayi ja ya fara neman birkicewa, Malam Sama’ila da yake gefensa ya dafe shi ya fara karatu.
Ba a fi minti biyar ba yayi atishawa ya dawo dai-dai. Ya goge gumin da yake fuskarsa, Yaya Bello ya mika masa hularsa ya saka yana ta faman satar kallon Aisha wadda suke zaune a gefe daya ita da Anti Karima.
Malam Audurahmanu ya mike yana fadin
‘Bismillah Malam Bello.’
Ya bi bayansa suka fice.
Sai da suka shiga ofishinsa suka zauna sannan Malam yayi gyaran murya ya dubeshi yace
‘Wato Malam Bello sihiri ne aka yiwa dan uwanka don a rabashi da mai dakinsa, aljanine aka saka masa wanda gaba daya yake hanashi tunawa da ita. Saboda yanda aljanine yake tare da shi kuma duk ma wanda ya so ya tuna masa ita to ba zai yarda su hadu ba. Amma Allah ya kawo makarin abun tunda ka ga wannanan man da ka shafa masa a kansa kamshin mutuwa yayiwa aljanin don haka ba zai sake dawowa ba. Sai dai da yake yana da wata matar kuma ga maganganun da ta gayawa wannan din za a iya cewa itace tayi wannan aika-aikar; duk da dai bai halatta a zargeta ba domin shaidanu makaryata ne. Amma yanzu idan kun tafi to a barshi ya cigaba da kwana gidan ita waccan din, zan bayar da ruwan tofi da zai dinga sha tsawon kwana bakwai kuma da addu’oi. Sannan a samu ko shi ko wani a dinga karanta bakara a dakin da yake kwana. In Sha Allah bayan kwana bakwai din sai ku dawo sannan sai ya koma rabon kwana kamar da.’
Yaya Bello ya jijjiga kai yana mamakin yanda Zahra zata yi haka, tunda yake bai taba jin matar da Hajiya take yabo kamar ita ba, don ko matarsa da ita aka fara aurowa Hajiya bata sonta kamar yanda take son Zahra.
Nan suka koma ajin, bayan sun koma ya sake yi musu bayani gaba daya kuma ya gaya musu kada su zargi kowa balle a sami wata sabuwar fitna don shaidanu haka suke so.
Ya basu umarni suje su cigaba da addu’a komai zai dawo dai-dai, ya sake bawa Aisha hakuri sannan sukayi sallama suka tafi.
Sai da suka fito sannan Aisha ta tuna da Amira, take ta buga mata waya tace ta zauna ko a library ne ta jirata nan da awa daya zata karaso.
Gidan Yaya Bellon suka koma inda sai da sukayi Sallah suka ci abinci sannan Aisha tayi musu sallama ta ja motarta ta tafi.
Duk yanda yake tsananin son magana da Aisha haka ya hakura ta tafi, sai dai ya bari kawai idan ya fito daga gidan Yaya Bello sai yayi mata waya ko yaya ne yaji muryarta tunda Malam yace kada yaje gidan da take.
--------
Saida ta dauki Amira sannan suka wuce gidan, tana shiga tayi wanka ta canza kaya sannan ta zauna ta kirawo Hajiya ta gaya mata abinda ake ciki. Nan take Hajiya ta bata shawarar ta yi sadaka kuma ta cigaba da addu’a. Haka tabi ‘yan uwanta da kira duk ta sanar da su su cigaba da tayata addu’a.
Duk da Malam yace kada ya zo gidanta sai an kwana bakwai wannan bai hanata walwala ba, tunda dai an warware matsalar. Haka ta kwana tana Sallah da addu’a cikin walwala.
---------
Tunda Aishan ta fita Abban Sadik yake kokarin cewa zai tafi amma Yaya Bello ya hanashi, ya kula gidan Aishan yake son zuwa kuma Malam yace kada yaje sai an gama addu’a. Nan ya rikeshi har saida sukayi Sallar Magriba kamar yanda ya saba. Ya jaddada masa addu’oi da kuma karatun kur’ani wanda Malam yace yayi sannan yace
‘Idan bakayi karatun kur’ani a dakin ba ni zan iya dauko Malam muzo muyi maka karatun ka dai sani don haka ka tabbatar kayi abinda Malam yace.’
Sukayi sallama ya kama hanyar gidan.
Saida suka kusa shiga unguwar sannan ya sami waje yayi parking, ya zaro wayarsa da nufin ya kirawo Aisha. Ga mamakinsa babu irin binciken da baiyi a wayar ba amma babu lambar Aisha, ya budo Whatsapp ma ya duba ko zai sami chats din ya dauki lambar daga nan amma bai samu ba. Gashi dama ya san bai taba haddace lambarta ba lambar Zahra kawai ya haddace kuma da kunya ya kirawo wani yace a bashi lambar Aisha bayan tana gidansa. Haka ya gaji ya hakura zuciyarsa babu dadi ya kama hanyar gidan.
Ta gaban gate din gidan da Aishan take ya wuce, sai da yayi slow ya karewa gidan kallo yana mamakin yanda ya dade bai ga gidan a wajen ba domin kullum ta nan yake bi idan ya dawo daga aiki. Haka ya wuce gidan Zahra yana mamakin wannan abun.
-------
Yanda ta saba taryarsa cikin walwala idan ya dawo haka tayi masa; Saida ya huta yayi sallar isha’i sannan ta kawo masa abincin dare. Binta kawai yakeyi da kallo domin abubuwan da suka faru yau tabbas sun haifar masa da wasi-wasi game da wacece Zahra; canza masa akayi ko kuwa dama can haka zuciyarta take. Baya jin zai iya tunkarar ta da wannan zancen a yanzu musamman da yake Malam yace kada su tada wata tarzoma kuma da dan sauran shakkarta a zuciyarsa. Don haka ya barwa tashi zuciyar wannan batun.
Haka tayi ta hidima da shi tana jansa da hira, domin tun da ta gane ba zata iya zuwa a raba shi da ‘yan uwansa yanzu ba sai ya zama duk lokacin da ya wuni wajensu idan ya dawo haka zatayi ta kokarin faranta masa rai domin ya gane ta fi su sonshi.
Bata ga alamar damuwa a tattare da shi ba sai dai ta kula da yanda tunaninsa yake yin nisa daga inda take, haka dai tayi ta fama. Ko da suka kwanta ma duk yanda ta kai ga dagewa haka ta hakura ta barshi domin gaba daya nuna mata yayi bacci yake ji ba zai iya ba. Bai fiya kin sauraron bukatarta a wannan lokacin ba don haka ta kwana cikin damuwa da fatan Allah ya sa ba wani abu Yaya Bellon yayi masa ba.
UWAR SADDIKU
Written by
Sakina Yazid
(Innar su Amal)
36
Tun bayan da suka dawo daga gidan Malam Aisha ta fara shirin tarbar Abba, tunda tana ji aka ce bayan kwana bakwai zai fara rabon kwana.
Duka labulayen gidan ta bayar aka wanke, suka share ko ina suka gyara ita da Amira. Ita kanta sai da gidan ya bata sha’awa saboda akwai abubuwa na gyaran gidan da ta dade bata yi ba.
Musamman ta sami lokaci suka je sayayya ita da Amira saboda kayan gyaran fatar ta duk sun kare bata sayi wasu ba.
Nan da nan gida ya dau kamshi.
Ranar Alhamis taje saloon aka yi mata gyaran jiki da kitso, tsaf aka goge mata fata ta fara sheki.
‘Hakane. To yanzu ya za ayi Malam? Na iya barinsu su koma gidan don ni gaskiya ina tsoron su koma su sake mantawa.’
Suka sake yin shiru na dan lokaci.
Jimawa kadan Malam Sama’ila yace
‘Akwai Malam Audurahmanu, kai ka san shi ai wanda yake zuwa mana limancin sallar dare da azumi. Sai dai shi a unguwar koki yake, shine ya kware a aikin sihiri ni dai ka barni da rukiyya idan aljani ya bayyana a jikin mutum.’
‘To ai sai mu tashi muje in dai zamu sameshi yanzun.’
‘Zamu sameshi tunda ko baya gida makarantarsu kusa da gidan ne’
Yaya Bello ya dubi Abban Sadik yace
‘To kaji ai sai ka tashi muje ko?’
Cikin sanyin murya ya amsa
‘To Yaya, yanda kace.’
Gaba daya suka mike suka fito, har sun kusan fita Yaya Bello ya koma yacewa Anti Karima
‘Ina ga ki dauko mayafi muje saboda ita Aisha din kya zauna da ita.’
Don haka ta saka hijabinta suka shiga motar Abban Sadik Yaya Bello ya tuka suka kama hanya.
A makaranta suka sami Malam Audurahmanu, babu dalibai don an tashi ‘yan islamiyya don haka ya nuna musu aji suka zauna.
Bayan Malam Sama’ila yayi masa bayani ya tambayi Aisha itama tayi nata bayanin, shi kuwa Abban Sadik da aka tambayeshi ma kasa bayanin yayi; abinda yake tunawa kawai shine ya dade bai ga Aishan ba kuma ya san bai saketa ba.
Malam Audurahmanu ya dubi Yaya Bello yace
‘Ina zuwa.’
Ya fita daga ajin.
Jimawa kadan ya dawo dauke da robar ruwa karama guda biyu da kuma wani mai a 'yar roba kamar ta Robb. Ya mikawa Aisha robar ruwan guda daya yace ta shanye, ta kalli Anti Karima ta daga mata kai don haka tayi Bismillah ta shanye. Ya mikawa Abban Sadik din dayan yace shima ya shanye, ba tare da wani musu ba ya shanye.
Ya dubi Yaya Bello yace
‘Ayoyin karya sihiri ne, sune matakin farko za a sha na kwana bakwai.’
Aisha tace
‘Ni dama tunda abun ya faru kullum sai na tofa ayoyin na sha sai dai a ruwan fanfo ne ba na zamzam ba.’
Malam yace
‘Ma Sha Allahu to shi ya sa ma abun baiyi wani tasiri sosai a kanki ba, karanta min ayoyin naji.’
Nan take ta karanta masa ayoyin ba tare da wani kuskure ba.
Yana murmushi yace
‘Ma sha Allah, in dai kika rike wannan babu wani sihiri da zai yi tasiri a kanki, ko yayi ma na dan lokaci ne tunda Allah yana jarraba bawa da abinda ya so.’
Ya mikawa Abban Sadik ‘yar robar hannunsa yace ka lakaci wannan ka shafa a kanka. Ya karbi robar ya rike amma ya kasa ko budewa, jujjuyata kawai yakeyi yana kallonta. Kafin yace wani abu Yaya Bello ya karba ya bude, ya lakaci man da yake ciki ya muttsike a hannunsa ya cire hular Abban Sadik din ya kama kan nasa ya shafe masa man tas. Nan da nan idonsa yayi ja ya fara neman birkicewa, Malam Sama’ila da yake gefensa ya dafe shi ya fara karatu.
Ba a fi minti biyar ba yayi atishawa ya dawo dai-dai. Ya goge gumin da yake fuskarsa, Yaya Bello ya mika masa hularsa ya saka yana ta faman satar kallon Aisha wadda suke zaune a gefe daya ita da Anti Karima.
Malam Audurahmanu ya mike yana fadin
‘Bismillah Malam Bello.’
Ya bi bayansa suka fice.
Sai da suka shiga ofishinsa suka zauna sannan Malam yayi gyaran murya ya dubeshi yace
‘Wato Malam Bello sihiri ne aka yiwa dan uwanka don a rabashi da mai dakinsa, aljanine aka saka masa wanda gaba daya yake hanashi tunawa da ita. Saboda yanda aljanine yake tare da shi kuma duk ma wanda ya so ya tuna masa ita to ba zai yarda su hadu ba. Amma Allah ya kawo makarin abun tunda ka ga wannanan man da ka shafa masa a kansa kamshin mutuwa yayiwa aljanin don haka ba zai sake dawowa ba. Sai dai da yake yana da wata matar kuma ga maganganun da ta gayawa wannan din za a iya cewa itace tayi wannan aika-aikar; duk da dai bai halatta a zargeta ba domin shaidanu makaryata ne. Amma yanzu idan kun tafi to a barshi ya cigaba da kwana gidan ita waccan din, zan bayar da ruwan tofi da zai dinga sha tsawon kwana bakwai kuma da addu’oi. Sannan a samu ko shi ko wani a dinga karanta bakara a dakin da yake kwana. In Sha Allah bayan kwana bakwai din sai ku dawo sannan sai ya koma rabon kwana kamar da.’
Yaya Bello ya jijjiga kai yana mamakin yanda Zahra zata yi haka, tunda yake bai taba jin matar da Hajiya take yabo kamar ita ba, don ko matarsa da ita aka fara aurowa Hajiya bata sonta kamar yanda take son Zahra.
Nan suka koma ajin, bayan sun koma ya sake yi musu bayani gaba daya kuma ya gaya musu kada su zargi kowa balle a sami wata sabuwar fitna don shaidanu haka suke so.
Ya basu umarni suje su cigaba da addu’a komai zai dawo dai-dai, ya sake bawa Aisha hakuri sannan sukayi sallama suka tafi.
Sai da suka fito sannan Aisha ta tuna da Amira, take ta buga mata waya tace ta zauna ko a library ne ta jirata nan da awa daya zata karaso.
Gidan Yaya Bellon suka koma inda sai da sukayi Sallah suka ci abinci sannan Aisha tayi musu sallama ta ja motarta ta tafi.
Duk yanda yake tsananin son magana da Aisha haka ya hakura ta tafi, sai dai ya bari kawai idan ya fito daga gidan Yaya Bello sai yayi mata waya ko yaya ne yaji muryarta tunda Malam yace kada yaje gidan da take.
--------
Saida ta dauki Amira sannan suka wuce gidan, tana shiga tayi wanka ta canza kaya sannan ta zauna ta kirawo Hajiya ta gaya mata abinda ake ciki. Nan take Hajiya ta bata shawarar ta yi sadaka kuma ta cigaba da addu’a. Haka tabi ‘yan uwanta da kira duk ta sanar da su su cigaba da tayata addu’a.
Duk da Malam yace kada ya zo gidanta sai an kwana bakwai wannan bai hanata walwala ba, tunda dai an warware matsalar. Haka ta kwana tana Sallah da addu’a cikin walwala.
---------
Tunda Aishan ta fita Abban Sadik yake kokarin cewa zai tafi amma Yaya Bello ya hanashi, ya kula gidan Aishan yake son zuwa kuma Malam yace kada yaje sai an gama addu’a. Nan ya rikeshi har saida sukayi Sallar Magriba kamar yanda ya saba. Ya jaddada masa addu’oi da kuma karatun kur’ani wanda Malam yace yayi sannan yace
‘Idan bakayi karatun kur’ani a dakin ba ni zan iya dauko Malam muzo muyi maka karatun ka dai sani don haka ka tabbatar kayi abinda Malam yace.’
Sukayi sallama ya kama hanyar gidan.
Saida suka kusa shiga unguwar sannan ya sami waje yayi parking, ya zaro wayarsa da nufin ya kirawo Aisha. Ga mamakinsa babu irin binciken da baiyi a wayar ba amma babu lambar Aisha, ya budo Whatsapp ma ya duba ko zai sami chats din ya dauki lambar daga nan amma bai samu ba. Gashi dama ya san bai taba haddace lambarta ba lambar Zahra kawai ya haddace kuma da kunya ya kirawo wani yace a bashi lambar Aisha bayan tana gidansa. Haka ya gaji ya hakura zuciyarsa babu dadi ya kama hanyar gidan.
Ta gaban gate din gidan da Aishan take ya wuce, sai da yayi slow ya karewa gidan kallo yana mamakin yanda ya dade bai ga gidan a wajen ba domin kullum ta nan yake bi idan ya dawo daga aiki. Haka ya wuce gidan Zahra yana mamakin wannan abun.
-------
Yanda ta saba taryarsa cikin walwala idan ya dawo haka tayi masa; Saida ya huta yayi sallar isha’i sannan ta kawo masa abincin dare. Binta kawai yakeyi da kallo domin abubuwan da suka faru yau tabbas sun haifar masa da wasi-wasi game da wacece Zahra; canza masa akayi ko kuwa dama can haka zuciyarta take. Baya jin zai iya tunkarar ta da wannan zancen a yanzu musamman da yake Malam yace kada su tada wata tarzoma kuma da dan sauran shakkarta a zuciyarsa. Don haka ya barwa tashi zuciyar wannan batun.
Haka tayi ta hidima da shi tana jansa da hira, domin tun da ta gane ba zata iya zuwa a raba shi da ‘yan uwansa yanzu ba sai ya zama duk lokacin da ya wuni wajensu idan ya dawo haka zatayi ta kokarin faranta masa rai domin ya gane ta fi su sonshi.
Bata ga alamar damuwa a tattare da shi ba sai dai ta kula da yanda tunaninsa yake yin nisa daga inda take, haka dai tayi ta fama. Ko da suka kwanta ma duk yanda ta kai ga dagewa haka ta hakura ta barshi domin gaba daya nuna mata yayi bacci yake ji ba zai iya ba. Bai fiya kin sauraron bukatarta a wannan lokacin ba don haka ta kwana cikin damuwa da fatan Allah ya sa ba wani abu Yaya Bellon yayi masa ba.
UWAR SADDIKU
Written by
Sakina Yazid
(Innar su Amal)
36
Tun bayan da suka dawo daga gidan Malam Aisha ta fara shirin tarbar Abba, tunda tana ji aka ce bayan kwana bakwai zai fara rabon kwana.
Duka labulayen gidan ta bayar aka wanke, suka share ko ina suka gyara ita da Amira. Ita kanta sai da gidan ya bata sha’awa saboda akwai abubuwa na gyaran gidan da ta dade bata yi ba.
Musamman ta sami lokaci suka je sayayya ita da Amira saboda kayan gyaran fatar ta duk sun kare bata sayi wasu ba.
Nan da nan gida ya dau kamshi.
Ranar Alhamis taje saloon aka yi mata gyaran jiki da kitso, tsaf aka goge mata fata ta fara sheki.