Sashe 9
Uwar Sadiku Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Muryar Abban Sadik ta katse mata tunani yana ta wannan murmushin nasa da take ganin kamar da gayya yake yi.
Ta yi yake
‘To me zan ce? Wannan shirin aure da ba a saka da ni ba ai dole na koma cikin ‘yan kallo.’
Ya kalleta na dan lokaci
‘Ya zaki ce haka, ai na miki bayani ni kaina ba wai haka na shirya ba.’
‘Um, to ai nima ban ce komai ba. Allah ya bamu zaman lafiya.’
Ya kara fadada murmushinsa
‘Ko ke fa, ai ba wani abu bane.’
Sukayi shiru na dan lokaci, jimawa kadan yace
‘Ban sami lokaci na siyo miki kayan fadar kanwa ba amma da safe zan tura miki kudi naira dubu dari biyu sai ki sayi duk kayan da kike so da kuma sauran shirye-shiryenki.’
So take tace bata so amma ba zata iya ba domin ta san idan ta barsa to zai je ya karawa amaryar, don haka tace
‘Nagode, Allah ya kara budi.’
Sukayi shiru suka cigaba da kallon TV din da take gabansu, kowa da tunanin da yake ransa.
Jimawa kadan ta mike tana fadin
‘Bari naje na kwanta, bacci nake ji.’
‘To sai na shigo.’
Ta wuce ta nufi dakinta wanda yake kusa da nashi dakin, yayinda shi kuma ya bi bayanta da kallo yana mamakin abinda ya bata mata rai bayan wancan karon da zai yi aure bata nuna haka ba. Ya dubi katin gayyatar da ya bata yanda ta barsu a nan,ya kawar da kai. Allah yasa dai kada ta tayar masa da wata fitna kuma.
Ita kuwa Zahra tana shiga dakin ta turo kofa ta tsaya a bayan kofar, ta saki hawayen da take makalewa ya gangaro kan kumatunta.
Wato dai ta tabbata Yusuf aure zai yi, lallai namiji kanin ajali! Menene bata yi masa?
Ta tuno rayuwarsu lokacin yana malamin makarantar firamare; albashinsa baya isarsu, haka take hakura da abubuwa da yawa sannan kuma ‘yan uwanta suna yawan taimaka mata. Ko da ya sami sauyin aiki ya fara samun cigaba bata taba tsammanin zai yi mata kishiya ba, ta samu ta barar da wancan yanzu kuma ya dauko wannan; kuma harda munafurci don ta tabbatar zancen da ya gaya mata na dalilin da yasa aka matso da ranar auren kusa karya ne.
Tayi kwafa, ta bar bayan kofar ta wuce bandakin ta turo kofar, ta karasa gaban mudubin sink ta tsaya ta dafa sink din tana kallon fuskarta a mudubi.
Babu abinda take gani sai hawayen da ta kasa daina fitar dasu; idan ta tuna yiwuwar Yusuf dinta zai kwana da wata matar har wani daci take ji a bakinta.
Haka ta dauki lokaci tana hawaye tana kallon mudubin ba tare da ta san me take tunani ba, saida ta fara gajiya da tsaiwa sannan ta kunna fanfon sink din ta wanke fuskarta. Tana fitowa daga bandakin ta sami waje a gefen gado ta zauna ta cigaba da tunanin mafita.
Sai wajen sha daya da rabi na dare Abban Sadik ya gama abinda yake, har zai kwanta sai kuma ya fasa. Ya fito daga dakinsa ya nufo dakin Zahra; don bata saba barinsa ya kwana shi kadai ba ko da kuwa tana jego ko rashin lafiya. Duk da ya san yau din ya dan motsa kishinta amma dai gara ya lallabota su shirya.
A hankali ya tura kofar dakin ya shiga; tana kwance a gefen gadon a takure da kayan da ta wuni da su gashi ko fitila bata kashe ba. Ya kalleta yayi murmushi don ya san tabbas bacci ne ya kwasheta.
Ya karasa ya zauna a gefen gadon ya tabata a hankali, ta mutssike ido ta bishi da kallo sannan ta tashi zaune a hankali.
Bayan ta zauna yace
‘Bacci ya kwasheki baki ko canza kaya ba? Ko a nan zamu kwana ne?’
‘Um, ban ma san nayi bacci ba wallahi. Bari dai yanzu zan shirya na taho gara dai mu kwana a can din.’
Ya mike yana fadin
‘To ina jiranki.’
Ya fice ya barta a dakin inda ta shirya ta bishi daga baya.
……
Kwanciya kawai Zahra tayi amma duk yanda ta so tai bacci kasa daukanta yayi, sai bayan asuba sannan ta samu baccin ya kwasheta. Inda Allah ya taimaka mata ranar asabar ce yara babu makaranta don haka shima Abban Sadik da yaga tana bacci sai kawai ya fito daga dakin ya rufe mata kofa, ya zauna a falonsa yana karance-karancensa.
Sai wajen karfe goma sannan ta farka, nan da nan ta wanke fuska ta sako kaya ta fito falo. Ta kalleshi tayi yake sannan tace
‘Sorry Yallabai, na barka da shan shayi ba bread. Wallahi bacci ne ya kwasheni kuma ka ki tashi na.’
Yayi dariya
‘Na ji kinata minshari ne, nace bari na barki ki kai ragon.’
Ta harareshi sanna ta bashi amsa
‘Bari nayi sauri na hada mana breakfast, 'yan gidan ma na san sun tashi don ga muryarsu can a kasa.’
Ta wuce da hanzari ta nufo falon kasa.
Kafin ta karasa saukowa Ummi ta sheko da gudu ta rungumeta tana mita
‘Mommy, tun dazu nake nemanki Yaya Yusra ta hanani zuwa dakin Abba na kirawoki, muna tashi ta sauko da mu kasa ta hanamu komawa kuma ta hada mana shayi ba dadi. Ai zaki bani wani shayin ko?’
Ta riko hannunta suka karasa saukowa ta zauna a kan kujerar zaman mutum uku kusa da Rukayya da Khadija wadanda suke zaune suna kallon cartoon, ta dorata a cinyarta tana murmushi tana bata amsa
‘Uwata ta kaina, Yaya Yusra bata kyauta ba bari mu ci abinci sai nayi mata fada.’
Daya bayan daya yaran suka gaida Mommy, bayan ta amsa ta dubi Yusra tace
‘Ina Yayanki?’
‘Bai fito ba Mommy, kin san shi da baccin tsiya.’
‘Bari nayi sauri na dafa mana indomie, yau bacci ya daukeni duk an ji yunwa har an bawa Uwata shayi mara dadi.’
Yusra tayi dariya tace
‘Mommy kin san fa tsohuwar yarinyar nan ba a iya mata.’
Ta harareta
‘Nagode kin ji Yaya.’
Suka saka dariya gaba daya, ta mike ta nufi kicin Ummi tana biye da ita.
Nan da nan ta dafa musu indomie da kwai, ta jera a dining table sannan ta hau saman ta kirawo Abban Sadiku wanda suka sauko tare. Kafin ta sauko duk yaran sun zauna a table sai Sadiku wanda bai fito ba har wannan lokacin, ta wuce dakinsa ta tura kofar. Ta sameshi yana kwance rub da ciki a kan gadonsa daga shi sai gajeran wando, motsinta ya tasheshi ya juyo yana dubanta yana mutssike ido.
Ta harare shi tace
‘To sarkin lalaci, a tashi gari ya waye.’
‘Mommy na tashi fa.’
‘Da kaji shigowata ba, to ka fito ga abinci can indomie na dafa, idan ka bari tayi sanyi ba zaka dafa wata ba haka zaka ci.’
Ta juya ta fice ta wuce ta zubawa kowa abincinsa sannan itama ta zuba nata ta zauna suka fara ci; yara suna ta hira da Abbansu ita kuma tayu shiru kawai tana cin abincin. Hankalinta yana kan maganar aurensa, ta kasa nutsuwa.
Kafin su gama cinye abincin ita ta cinye nata tunda dama kadan ta zuba, ta mike ta dauki kwanonta ta shigar kicin ta ajiye. Tana fitowa ta wuce sama ta koma dakinta ta turo kofa ta cigaba da tunanin mafita.
Saida suka kusa gama cin abincin Sadik ya fito daga dakinsa, bayan ya gaida Abban ya zauna ya ja kwanonsa wanda Mommy ta riga ta zuba masa abinci. Haka ya hakura ya ci indomie wadda ta riga tayi sanyi saboda Abba yana zaune, da ya san Abban bai koma sama ba jira zaiyi sai ya tashi sannan ya fito ya dafa mai dumi; don ya san Mommy ba zata iya hanashi ba fada kawai takeyi.
Bayan sun gama karyawa nan suka zauna a falon kasa suna kallonsu, jimawa kadan wajen Sha biyu saura Jummai mai aikin Mommy tazo. Bayan sun gaisa da yaran ta kama aikinta, Yusra ta haye sama don ta sanar da Mommy zuwanta.
A hankali ta tura kofar ta shiga da sallama, tana daga kwance a gefen gado ta amsa sallamarta. Ta turo kofar ta karasa ta zauna a gefen gado kusa da kafar Mommy yayinda ita kuma ta fara kokarin mikewa zaune.
‘Mommy Jummai ta zo, ta ma fara aikinta.’
‘To.’
Ta amsa a gajiye kamar wadda batayi bacci ba
Yusra ta sake binta da kallo; har yanzu kayan bacci ne a jikinta wanda tabbas ba dabi’arta bane. Da kalau take da yanzu tayi wanka ta canza kaya tana tashin kamshi, tabbas ko dai bata lafiya ko kuma ciki ne da ita. Mommy ce ta katse shirun tana kallon Yusra
‘Lafiya dai kike kare min kallo kamar yau kika fara ganina Yaya?’
Ta kawar da kai tana murmushi
‘Mommy baki da lafiya ne?’
‘Lafiyata kalau Yusra, me kika gani?’
‘Kawai dai na ga kamar ba kya jin dadi.’
‘Babu komai.’
Sukayi shiru na dan lokaci; to me ma zata boye musu? Ai gara ma ta gaya musu ubansu zai yi aure su san zaman da zasuyi da shi. Ko babu komai Yusra dama ta zama abokiyar shawararta tunda ta ga tunaninsu ya zo daya. Da dai Rukayya ce da sai ta boye mata don wannan sak halin ubanta ta yiwo, ko kuma halin Yaya Murja; don wani lokacin tabbas tunaninta irin na Yaya Murja ne.
Ta danyi gyaran murya wanda ya janyo hankalin Yusra ta dubeta, ta kawar da kai tace
‘Yusra Abbanku aure zai yi.’
A dan razane tace
‘Aure Mommy!’
‘Um, ya sami wata bazawara wai mai yara biyu shine zai aureta. Next week ma za a daura auren.’
Ta kara zaro ido
‘Next week Mommy? To ya akayi ba wanda ya sani.’
‘Hmm! Munafurci mana irin na da namiji. Ko nima ban sani ba sai jiyan yake gaya min wai asabar mai zuwa za a daura masa aure saboda tsabar wulakanci.’
Ta fara kada kai
‘Hmmmn! Amma gaskiya bazawarar na ta wanki kan Abba. Tab! To yanzu kuma ina yace zai sakata tunda bai bamu notice ba ai ba lallai mu iya kwashe kayan dakin kasa zuwa next week ba.’
‘Wai ya kama hayar wannan gidan na kusa da gidan su Mashkur, a nan zata zauna.’
Mamakin Yusra ya karu, ta ce
Ta yi yake
‘To me zan ce? Wannan shirin aure da ba a saka da ni ba ai dole na koma cikin ‘yan kallo.’
Ya kalleta na dan lokaci
‘Ya zaki ce haka, ai na miki bayani ni kaina ba wai haka na shirya ba.’
‘Um, to ai nima ban ce komai ba. Allah ya bamu zaman lafiya.’
Ya kara fadada murmushinsa
‘Ko ke fa, ai ba wani abu bane.’
Sukayi shiru na dan lokaci, jimawa kadan yace
‘Ban sami lokaci na siyo miki kayan fadar kanwa ba amma da safe zan tura miki kudi naira dubu dari biyu sai ki sayi duk kayan da kike so da kuma sauran shirye-shiryenki.’
So take tace bata so amma ba zata iya ba domin ta san idan ta barsa to zai je ya karawa amaryar, don haka tace
‘Nagode, Allah ya kara budi.’
Sukayi shiru suka cigaba da kallon TV din da take gabansu, kowa da tunanin da yake ransa.
Jimawa kadan ta mike tana fadin
‘Bari naje na kwanta, bacci nake ji.’
‘To sai na shigo.’
Ta wuce ta nufi dakinta wanda yake kusa da nashi dakin, yayinda shi kuma ya bi bayanta da kallo yana mamakin abinda ya bata mata rai bayan wancan karon da zai yi aure bata nuna haka ba. Ya dubi katin gayyatar da ya bata yanda ta barsu a nan,ya kawar da kai. Allah yasa dai kada ta tayar masa da wata fitna kuma.
Ita kuwa Zahra tana shiga dakin ta turo kofa ta tsaya a bayan kofar, ta saki hawayen da take makalewa ya gangaro kan kumatunta.
Wato dai ta tabbata Yusuf aure zai yi, lallai namiji kanin ajali! Menene bata yi masa?
Ta tuno rayuwarsu lokacin yana malamin makarantar firamare; albashinsa baya isarsu, haka take hakura da abubuwa da yawa sannan kuma ‘yan uwanta suna yawan taimaka mata. Ko da ya sami sauyin aiki ya fara samun cigaba bata taba tsammanin zai yi mata kishiya ba, ta samu ta barar da wancan yanzu kuma ya dauko wannan; kuma harda munafurci don ta tabbatar zancen da ya gaya mata na dalilin da yasa aka matso da ranar auren kusa karya ne.
Tayi kwafa, ta bar bayan kofar ta wuce bandakin ta turo kofar, ta karasa gaban mudubin sink ta tsaya ta dafa sink din tana kallon fuskarta a mudubi.
Babu abinda take gani sai hawayen da ta kasa daina fitar dasu; idan ta tuna yiwuwar Yusuf dinta zai kwana da wata matar har wani daci take ji a bakinta.
Haka ta dauki lokaci tana hawaye tana kallon mudubin ba tare da ta san me take tunani ba, saida ta fara gajiya da tsaiwa sannan ta kunna fanfon sink din ta wanke fuskarta. Tana fitowa daga bandakin ta sami waje a gefen gado ta zauna ta cigaba da tunanin mafita.
Sai wajen sha daya da rabi na dare Abban Sadik ya gama abinda yake, har zai kwanta sai kuma ya fasa. Ya fito daga dakinsa ya nufo dakin Zahra; don bata saba barinsa ya kwana shi kadai ba ko da kuwa tana jego ko rashin lafiya. Duk da ya san yau din ya dan motsa kishinta amma dai gara ya lallabota su shirya.
A hankali ya tura kofar dakin ya shiga; tana kwance a gefen gadon a takure da kayan da ta wuni da su gashi ko fitila bata kashe ba. Ya kalleta yayi murmushi don ya san tabbas bacci ne ya kwasheta.
Ya karasa ya zauna a gefen gadon ya tabata a hankali, ta mutssike ido ta bishi da kallo sannan ta tashi zaune a hankali.
Bayan ta zauna yace
‘Bacci ya kwasheki baki ko canza kaya ba? Ko a nan zamu kwana ne?’
‘Um, ban ma san nayi bacci ba wallahi. Bari dai yanzu zan shirya na taho gara dai mu kwana a can din.’
Ya mike yana fadin
‘To ina jiranki.’
Ya fice ya barta a dakin inda ta shirya ta bishi daga baya.
……
Kwanciya kawai Zahra tayi amma duk yanda ta so tai bacci kasa daukanta yayi, sai bayan asuba sannan ta samu baccin ya kwasheta. Inda Allah ya taimaka mata ranar asabar ce yara babu makaranta don haka shima Abban Sadik da yaga tana bacci sai kawai ya fito daga dakin ya rufe mata kofa, ya zauna a falonsa yana karance-karancensa.
Sai wajen karfe goma sannan ta farka, nan da nan ta wanke fuska ta sako kaya ta fito falo. Ta kalleshi tayi yake sannan tace
‘Sorry Yallabai, na barka da shan shayi ba bread. Wallahi bacci ne ya kwasheni kuma ka ki tashi na.’
Yayi dariya
‘Na ji kinata minshari ne, nace bari na barki ki kai ragon.’
Ta harareshi sanna ta bashi amsa
‘Bari nayi sauri na hada mana breakfast, 'yan gidan ma na san sun tashi don ga muryarsu can a kasa.’
Ta wuce da hanzari ta nufo falon kasa.
Kafin ta karasa saukowa Ummi ta sheko da gudu ta rungumeta tana mita
‘Mommy, tun dazu nake nemanki Yaya Yusra ta hanani zuwa dakin Abba na kirawoki, muna tashi ta sauko da mu kasa ta hanamu komawa kuma ta hada mana shayi ba dadi. Ai zaki bani wani shayin ko?’
Ta riko hannunta suka karasa saukowa ta zauna a kan kujerar zaman mutum uku kusa da Rukayya da Khadija wadanda suke zaune suna kallon cartoon, ta dorata a cinyarta tana murmushi tana bata amsa
‘Uwata ta kaina, Yaya Yusra bata kyauta ba bari mu ci abinci sai nayi mata fada.’
Daya bayan daya yaran suka gaida Mommy, bayan ta amsa ta dubi Yusra tace
‘Ina Yayanki?’
‘Bai fito ba Mommy, kin san shi da baccin tsiya.’
‘Bari nayi sauri na dafa mana indomie, yau bacci ya daukeni duk an ji yunwa har an bawa Uwata shayi mara dadi.’
Yusra tayi dariya tace
‘Mommy kin san fa tsohuwar yarinyar nan ba a iya mata.’
Ta harareta
‘Nagode kin ji Yaya.’
Suka saka dariya gaba daya, ta mike ta nufi kicin Ummi tana biye da ita.
Nan da nan ta dafa musu indomie da kwai, ta jera a dining table sannan ta hau saman ta kirawo Abban Sadiku wanda suka sauko tare. Kafin ta sauko duk yaran sun zauna a table sai Sadiku wanda bai fito ba har wannan lokacin, ta wuce dakinsa ta tura kofar. Ta sameshi yana kwance rub da ciki a kan gadonsa daga shi sai gajeran wando, motsinta ya tasheshi ya juyo yana dubanta yana mutssike ido.
Ta harare shi tace
‘To sarkin lalaci, a tashi gari ya waye.’
‘Mommy na tashi fa.’
‘Da kaji shigowata ba, to ka fito ga abinci can indomie na dafa, idan ka bari tayi sanyi ba zaka dafa wata ba haka zaka ci.’
Ta juya ta fice ta wuce ta zubawa kowa abincinsa sannan itama ta zuba nata ta zauna suka fara ci; yara suna ta hira da Abbansu ita kuma tayu shiru kawai tana cin abincin. Hankalinta yana kan maganar aurensa, ta kasa nutsuwa.
Kafin su gama cinye abincin ita ta cinye nata tunda dama kadan ta zuba, ta mike ta dauki kwanonta ta shigar kicin ta ajiye. Tana fitowa ta wuce sama ta koma dakinta ta turo kofa ta cigaba da tunanin mafita.
Saida suka kusa gama cin abincin Sadik ya fito daga dakinsa, bayan ya gaida Abban ya zauna ya ja kwanonsa wanda Mommy ta riga ta zuba masa abinci. Haka ya hakura ya ci indomie wadda ta riga tayi sanyi saboda Abba yana zaune, da ya san Abban bai koma sama ba jira zaiyi sai ya tashi sannan ya fito ya dafa mai dumi; don ya san Mommy ba zata iya hanashi ba fada kawai takeyi.
Bayan sun gama karyawa nan suka zauna a falon kasa suna kallonsu, jimawa kadan wajen Sha biyu saura Jummai mai aikin Mommy tazo. Bayan sun gaisa da yaran ta kama aikinta, Yusra ta haye sama don ta sanar da Mommy zuwanta.
A hankali ta tura kofar ta shiga da sallama, tana daga kwance a gefen gado ta amsa sallamarta. Ta turo kofar ta karasa ta zauna a gefen gado kusa da kafar Mommy yayinda ita kuma ta fara kokarin mikewa zaune.
‘Mommy Jummai ta zo, ta ma fara aikinta.’
‘To.’
Ta amsa a gajiye kamar wadda batayi bacci ba
Yusra ta sake binta da kallo; har yanzu kayan bacci ne a jikinta wanda tabbas ba dabi’arta bane. Da kalau take da yanzu tayi wanka ta canza kaya tana tashin kamshi, tabbas ko dai bata lafiya ko kuma ciki ne da ita. Mommy ce ta katse shirun tana kallon Yusra
‘Lafiya dai kike kare min kallo kamar yau kika fara ganina Yaya?’
Ta kawar da kai tana murmushi
‘Mommy baki da lafiya ne?’
‘Lafiyata kalau Yusra, me kika gani?’
‘Kawai dai na ga kamar ba kya jin dadi.’
‘Babu komai.’
Sukayi shiru na dan lokaci; to me ma zata boye musu? Ai gara ma ta gaya musu ubansu zai yi aure su san zaman da zasuyi da shi. Ko babu komai Yusra dama ta zama abokiyar shawararta tunda ta ga tunaninsu ya zo daya. Da dai Rukayya ce da sai ta boye mata don wannan sak halin ubanta ta yiwo, ko kuma halin Yaya Murja; don wani lokacin tabbas tunaninta irin na Yaya Murja ne.
Ta danyi gyaran murya wanda ya janyo hankalin Yusra ta dubeta, ta kawar da kai tace
‘Yusra Abbanku aure zai yi.’
A dan razane tace
‘Aure Mommy!’
‘Um, ya sami wata bazawara wai mai yara biyu shine zai aureta. Next week ma za a daura auren.’
Ta kara zaro ido
‘Next week Mommy? To ya akayi ba wanda ya sani.’
‘Hmm! Munafurci mana irin na da namiji. Ko nima ban sani ba sai jiyan yake gaya min wai asabar mai zuwa za a daura masa aure saboda tsabar wulakanci.’
Ta fara kada kai
‘Hmmmn! Amma gaskiya bazawarar na ta wanki kan Abba. Tab! To yanzu kuma ina yace zai sakata tunda bai bamu notice ba ai ba lallai mu iya kwashe kayan dakin kasa zuwa next week ba.’
‘Wai ya kama hayar wannan gidan na kusa da gidan su Mashkur, a nan zata zauna.’
Mamakin Yusra ya karu, ta ce