Sashe 4
Uwar Sadiku Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
‘Ina Shatun ne, kirawota. Gara muyi zancen nan a gabanta mu ji yanda za ayi.’
Ta dubi su Abdallah tace
‘Ku je ku cewa Mamanku tazo inji Baffa, sai ku zauna a can kuyi game a tab ko.’
Suka tashi da gudu suka tafi dakin Aishan. Basu dade da shiga dakin ba ta fito, ta zauna a kan kafet daga gefen Hajiya tace
‘Baffa gani.’
Yayi gyaran murya yace
‘Yauwa Shatu, da magana na zo. Akwai wani mutum; ni kaina ban san wa ya nuna masa ni ba amma dai ya ce sunansa Yusuf Muhammad Bala, kuma darakta ne shi a ma’aikatar ilimi ta jiha. Yana so na bashi izini ya zo neman aurenki. To kwanaki na san Yayanki yace min akwai abokinsa, sai dai ban san ina zancen ya kwana ba don haka nace ya bari na zo muyi magana da ke da mahaifiyarku tukunna.’
Ya dubi Hajiya yace
‘Ko ba haka ba?’
Ta gyara zama
‘Gaskiya ne Baffa, wancan din ne dai har yanzu yake zuwa kuma a yanda yake nunawa yayannasu shi a shirye yake itace bata bashi dama ba.’
Ya dubi Aisha
‘Shatu hakane? Ko bai yi miki bane abokin Yayan?’
Kafin ta bada amsa Hajiya ta tari numfashinsu
‘Babu wani yi mata da bai yi ba fa, ta dai sakawa ranta ba zata yi aure ba tunda Allah ya kashe uban ‘yayanta.’
Baffa ya dubeta yace
‘Subhanallah! Haba Shatu, rayuwar ai sai hakuri kinji, duk yanda Allah yayi da bawa kuma dai-dai ne. Da kuruciyarki baki kai ki zauna babu aure ba tunda dai akwai maneman, kiyi hakuri in sha Allah zaki dace kin ji Shatu. Kada ma na sake ji kince ba zakiyi aure ba kin ji ko?’
Ta daga kai alamar ‘to’
Ya dubi Hajiya yace
‘Ai al’amuran sai hakuri Hajiya, kin san rabuwa da masoyi sai an yi jinyar zuciya amma in sha Allah za a dace.’
Sukayi shiru na dan lokaci, Baffa ya dubi Hajiya yace
‘To yanzu wannan din a dakatar dashi kenan koko shima a bashi dama yazo tunda wancan din ma babu wata tsayayyiyar magana?’
‘To ai gata nan sai ta bada amsa.’
Ta fada tana nuna Aishan, don haka Baffa ya mayar da hankalinsa kanta yace
‘Shatu ke nake sauraro, wannan din yazo ko kuwa kun daidaita da abokin Yayan?’
Ta sake sunkuyar da kai tana fakon idon Hajiya wadda ta dauke kai
‘Baffa gara dai wannan din yazo.’
Hajiya ta bita da kallo mai cike da tambayoyi yayinda shi kuma Baffa yace
‘To babu laifi in sha Allah. Ki kwantar da hankalinki ki duba a hankali; kin riga kinyi aure kin san menene rayuwar aure don haka ba zamu yi miki auren dole ba. Idan ya zo wannan din idan baku daidaita ba shima kada kiji komai sai a cigaba da addu’a.’
Ta daga kai cikin gamsuwa da bayanin Baffa.
Yayi musu sallama ya fice.
Aisha ta mike zata bar wajen Hajiya ta dakatar da ita
‘Zo nan.’
Ta dawo ta zauna a inda ta tashi ta sunkuyar da kai, Hajiya ta harareta tace
‘Shi Musbahun me yayi miki da kuka kasa daidaitawa?’
Ta yi shiru na dan lokaci sannan ta bada amsa
‘Hajiya babu abinda yayi min, kawai dai bana sonshi ne.’
Hajiya ta bude baki tana mamaki, kafin tace wani abu Aishan ta cigaba
‘Kuma kinga daga maganganusa yana nuna min shi zai fi so na daina aiki sannan kuma gida daya zamu zauna da matarsa, gaskiya ba zan ji dadin hakan ba shi yasa naga gara mu hakura kada a bata goma daya bata gyaru ba.’
‘Ai shikenan, Allah ya sa hakane ya fi alkhairi. Bari Yayan naki yazo sai a dakatar da shi ya daina zuwa yana batawa kansa lokaci.’
Ta tashi ta koma dakinta.
Hajiya ta bi bayanta da kallo tana mamaki yanda za ace namiji kamar Musbahu wai ba a sonshi saboda dai fitna irin ta Aisha.
Tana shiga dakin ta koro su Abdallah wajen Hajiya ta fada kan gado ta kwanta ranta a bace; bata son aure amma ta rasa dalilin da yasa aure yake sonta. Ta fuskanci lallai idan batayi da gaske ba za su fara samun matsala da Hajiya don babu wanda ya kai Hajiya son ganin tayi aure, yanzu kuma ga Baffa. Wannan mutumin ma da Baffan yace zai zo bata jin zasu daidaita, za dai ta saurareshi ne kawai saboda kada ace taki kula mutane; amma gaskiya yanzu aure baya gabanta.
____
Ranar asabar da yamma sai ga kira daga Alhaji Yusuf M. B. Haka ta shirya ta fita ba don ta so ba suka zauna a gareji.
Hirar tasu babu yabo babu fallasa; ya gabatar mata da kansa, kamar yanda Baffa ya gaya mata shima ya tabbatar mata cewa shi ma’aikacin gwamnatin jiha ne kuma yana da mata daya da yara biyar; daya namiji, hudu mata.
Duk da bai wani burgeta sosai ba amma dai ta san akwai yiwuwar su daidaita don kamar shi din yana da saukin hali. Haka suka taba hira kafin suyi sallama ta koma gida.
……..
A hankali Aisha ta fara sakewa da Alhaji Yusuf M B, ba wani tsananin so shi take ba kuma zata fi so ace an barta da auren nan amma dai ta san a yanzu idan an tashi zata iya aurensa. Sun gama maganar aiki ya gaya mata bashi da matsala da aikinta, uwargidansa ma iya secondary school tayi shi yasa bata aiki amma duk da haka tana business daga gida inda take sayar da atamfofi da duk wata sutura ta mata.
A tsarinsa yana so ya hadesu gida daya da uwargidan sai dai ita Aishan ta gaya masa tafi so ya zama nata gidan ita kadai ko da cikin compound daya ne. Ya sanar da ita gidansa bashi da filin da zai gina mata wani a ciki amma dai ya tabbatar mata ba zai hadesu ba tunda bata so.Don haka ta saki jiki da shi sosai sunata soyayyarsu tunda shi din gwanin soyayyar ne.
Duk da ta amince da Yusuf amma bata daina kewar Mustafa ba, wasu lokutan ma sai taji kamar idan tayi aure taci amanar Mustafan. Idan taji haka sai dai tayi kukanta ta share hawayenta don ko ta gayawa ‘yanuwanta ma basa fahimtarta, so kawai suke tayi aure. Har gara ma Yaya Zuwaira da yake itace sakuwarta suna dan fahimtar juna, amma Yaya Zainab cewa take “Da kece kika mutu da yanzu yayi aure yana morewa da amaryarsa amma ke kina nan kina hana kanki bacci, addu’ar ma da kike masa ai ta isa ba sai kin cigaba da kuntatawa kanki ba.” Don haka bata ma son yin zancen da ita.
UWAR SADDIKU
Written by
Sakina Yazid
(Innar su Amal)
4
Tun kimanin shekaru shida da suka wuce ya so ya kara aure, don a lokacin har an je gaisuwa gidansu budurwar da yake nema; sadaki kawai za a kai a saka rana sai kuma aka wayi gari haka kawai maganar auren ta fita ransa. Yarinyar da yake nema bata yi masa komai ba amma haka kawai yaji ya daina sonta. Da farko ta so ta takura masa, amma sai Allah ya hadata da wani saurayi a daidai lokacin wanda ya fiye mata Yusuf din.
Matarsa daya Hajiya Zahra’u da yaransu biyar; Sadik, Yusra, Rukayya, Khadija wadda suke kira Dija sai Zulaiha mai shekaru uku wadda suke kira Ummi saboda sunan mahaifiyar Zahra’un taci.
Hajiya Zahra’u mace ce mai matukar kirki ga kyauta, duk wani abu da zai farantawa mijinta shi takeyi. Shima kuma ta samu yana da kulawa gashi yana mata yanda take so; musamman ma yanzu da Allah ya kara buda masa ya fara tara abun duniya. ‘Yan uwan Yusuf ma suna matukar kaunarta saboda yanda take musu kyauta kuma tana kulasu tana kula da mahaifiyarsu Hajiya.
Tun Yusuf yana malamin makaranta ta aureshi, suna tare ya karo karatu ya sami sauyin aiki ya koma ma’aikatar ilimi ta jiha; gashi yanzu har ya zama director. Wannan ne ya saka Hajiya Zahra’u take ji cewa ita kadai ce ta dace ta zama matarsa, don ita ta sha wahalarsa. Shi yasa ma wancan lokacin daya ya dauko maganar aure ta san yanda tayi ta kifar da zancen.
Bata yin tsafi don tana da ilimin addini gwargwado saboda haka ta san abinda zai rabata da imaninta, amma tana da malamanta irin na soro wadanda sukeyi mata aiki da ayar Allah, wani lokacin ma har su bata ruwan rubutu ko tofi wanda zata yi amfani da shi ko shi Yusuf din tayi masa amfani da shi.
Tunda taji anje gaisuwa wancan lokacin da ya fara maganar auren ta tashi ta tafi har garin Gaya, wajen wani malami da aka hadata da shi Malam Hatimu mai ‘yan makaranta. Tayi masa bayani so take kawai a sakashi ya manta da maganar auren nan ya daina son yarinyar. A nan take kuwa ya zana hatimi ya nade mata laya ya bata yace ta saka masa a karkashin katifarsa, idan dai ya kwana a kai ba zai sake maganar auren wannan yarinyar ba. Haka kuwa akayi, wannan aure dole aka barshi.
Bayan fasa wancan auren ne abokinsa ya bashi shawara idan ya tashi sake aure kada ya fada da wuri sai magana ta kankama, kuna shima sai ya dage da addu’a. Don haka ma tunda ya fara neman auren Aisha babu wanda ya gayawa, don har abokan nasa ma babu wanda sani.
Yayansa kawai ya gayawa wanda shine zai wuce masa gaba wajen neman auren kuma ya gaya masa bai sanarwa kowa ba don haka shima kada ya bari zancen yake wajen mata.
____
A daki ta sami Hajiya tana zaune a kan dadduma inda ta idar da sallar la’asar, ta shiga dakin da sallama ta karasa ta zauna a gaban Hajiyan bayan da ta amsa sallamarta. Hajiya ta gyara zama tace
‘To wacce sura zan biya miki da kika sakani a gaba haka kamar mai daukar karatu.’
Tayi ‘yar dariya tace
‘Kai Hajiya.’
‘To ya akayi?’
Ta dan saita fuskarta tana kokarin danne damuwar da take zuciyarta
‘Hajiya dama Yusuf ne yace zasu zo sa rana sati mai zuwa, kuma tare zasu kawo da sadaki da kayan aure duka.’
Take murmushin Hajiya ya karu
Ta dubi su Abdallah tace
‘Ku je ku cewa Mamanku tazo inji Baffa, sai ku zauna a can kuyi game a tab ko.’
Suka tashi da gudu suka tafi dakin Aishan. Basu dade da shiga dakin ba ta fito, ta zauna a kan kafet daga gefen Hajiya tace
‘Baffa gani.’
Yayi gyaran murya yace
‘Yauwa Shatu, da magana na zo. Akwai wani mutum; ni kaina ban san wa ya nuna masa ni ba amma dai ya ce sunansa Yusuf Muhammad Bala, kuma darakta ne shi a ma’aikatar ilimi ta jiha. Yana so na bashi izini ya zo neman aurenki. To kwanaki na san Yayanki yace min akwai abokinsa, sai dai ban san ina zancen ya kwana ba don haka nace ya bari na zo muyi magana da ke da mahaifiyarku tukunna.’
Ya dubi Hajiya yace
‘Ko ba haka ba?’
Ta gyara zama
‘Gaskiya ne Baffa, wancan din ne dai har yanzu yake zuwa kuma a yanda yake nunawa yayannasu shi a shirye yake itace bata bashi dama ba.’
Ya dubi Aisha
‘Shatu hakane? Ko bai yi miki bane abokin Yayan?’
Kafin ta bada amsa Hajiya ta tari numfashinsu
‘Babu wani yi mata da bai yi ba fa, ta dai sakawa ranta ba zata yi aure ba tunda Allah ya kashe uban ‘yayanta.’
Baffa ya dubeta yace
‘Subhanallah! Haba Shatu, rayuwar ai sai hakuri kinji, duk yanda Allah yayi da bawa kuma dai-dai ne. Da kuruciyarki baki kai ki zauna babu aure ba tunda dai akwai maneman, kiyi hakuri in sha Allah zaki dace kin ji Shatu. Kada ma na sake ji kince ba zakiyi aure ba kin ji ko?’
Ta daga kai alamar ‘to’
Ya dubi Hajiya yace
‘Ai al’amuran sai hakuri Hajiya, kin san rabuwa da masoyi sai an yi jinyar zuciya amma in sha Allah za a dace.’
Sukayi shiru na dan lokaci, Baffa ya dubi Hajiya yace
‘To yanzu wannan din a dakatar dashi kenan koko shima a bashi dama yazo tunda wancan din ma babu wata tsayayyiyar magana?’
‘To ai gata nan sai ta bada amsa.’
Ta fada tana nuna Aishan, don haka Baffa ya mayar da hankalinsa kanta yace
‘Shatu ke nake sauraro, wannan din yazo ko kuwa kun daidaita da abokin Yayan?’
Ta sake sunkuyar da kai tana fakon idon Hajiya wadda ta dauke kai
‘Baffa gara dai wannan din yazo.’
Hajiya ta bita da kallo mai cike da tambayoyi yayinda shi kuma Baffa yace
‘To babu laifi in sha Allah. Ki kwantar da hankalinki ki duba a hankali; kin riga kinyi aure kin san menene rayuwar aure don haka ba zamu yi miki auren dole ba. Idan ya zo wannan din idan baku daidaita ba shima kada kiji komai sai a cigaba da addu’a.’
Ta daga kai cikin gamsuwa da bayanin Baffa.
Yayi musu sallama ya fice.
Aisha ta mike zata bar wajen Hajiya ta dakatar da ita
‘Zo nan.’
Ta dawo ta zauna a inda ta tashi ta sunkuyar da kai, Hajiya ta harareta tace
‘Shi Musbahun me yayi miki da kuka kasa daidaitawa?’
Ta yi shiru na dan lokaci sannan ta bada amsa
‘Hajiya babu abinda yayi min, kawai dai bana sonshi ne.’
Hajiya ta bude baki tana mamaki, kafin tace wani abu Aishan ta cigaba
‘Kuma kinga daga maganganusa yana nuna min shi zai fi so na daina aiki sannan kuma gida daya zamu zauna da matarsa, gaskiya ba zan ji dadin hakan ba shi yasa naga gara mu hakura kada a bata goma daya bata gyaru ba.’
‘Ai shikenan, Allah ya sa hakane ya fi alkhairi. Bari Yayan naki yazo sai a dakatar da shi ya daina zuwa yana batawa kansa lokaci.’
Ta tashi ta koma dakinta.
Hajiya ta bi bayanta da kallo tana mamaki yanda za ace namiji kamar Musbahu wai ba a sonshi saboda dai fitna irin ta Aisha.
Tana shiga dakin ta koro su Abdallah wajen Hajiya ta fada kan gado ta kwanta ranta a bace; bata son aure amma ta rasa dalilin da yasa aure yake sonta. Ta fuskanci lallai idan batayi da gaske ba za su fara samun matsala da Hajiya don babu wanda ya kai Hajiya son ganin tayi aure, yanzu kuma ga Baffa. Wannan mutumin ma da Baffan yace zai zo bata jin zasu daidaita, za dai ta saurareshi ne kawai saboda kada ace taki kula mutane; amma gaskiya yanzu aure baya gabanta.
____
Ranar asabar da yamma sai ga kira daga Alhaji Yusuf M. B. Haka ta shirya ta fita ba don ta so ba suka zauna a gareji.
Hirar tasu babu yabo babu fallasa; ya gabatar mata da kansa, kamar yanda Baffa ya gaya mata shima ya tabbatar mata cewa shi ma’aikacin gwamnatin jiha ne kuma yana da mata daya da yara biyar; daya namiji, hudu mata.
Duk da bai wani burgeta sosai ba amma dai ta san akwai yiwuwar su daidaita don kamar shi din yana da saukin hali. Haka suka taba hira kafin suyi sallama ta koma gida.
……..
A hankali Aisha ta fara sakewa da Alhaji Yusuf M B, ba wani tsananin so shi take ba kuma zata fi so ace an barta da auren nan amma dai ta san a yanzu idan an tashi zata iya aurensa. Sun gama maganar aiki ya gaya mata bashi da matsala da aikinta, uwargidansa ma iya secondary school tayi shi yasa bata aiki amma duk da haka tana business daga gida inda take sayar da atamfofi da duk wata sutura ta mata.
A tsarinsa yana so ya hadesu gida daya da uwargidan sai dai ita Aishan ta gaya masa tafi so ya zama nata gidan ita kadai ko da cikin compound daya ne. Ya sanar da ita gidansa bashi da filin da zai gina mata wani a ciki amma dai ya tabbatar mata ba zai hadesu ba tunda bata so.Don haka ta saki jiki da shi sosai sunata soyayyarsu tunda shi din gwanin soyayyar ne.
Duk da ta amince da Yusuf amma bata daina kewar Mustafa ba, wasu lokutan ma sai taji kamar idan tayi aure taci amanar Mustafan. Idan taji haka sai dai tayi kukanta ta share hawayenta don ko ta gayawa ‘yanuwanta ma basa fahimtarta, so kawai suke tayi aure. Har gara ma Yaya Zuwaira da yake itace sakuwarta suna dan fahimtar juna, amma Yaya Zainab cewa take “Da kece kika mutu da yanzu yayi aure yana morewa da amaryarsa amma ke kina nan kina hana kanki bacci, addu’ar ma da kike masa ai ta isa ba sai kin cigaba da kuntatawa kanki ba.” Don haka bata ma son yin zancen da ita.
UWAR SADDIKU
Written by
Sakina Yazid
(Innar su Amal)
4
Tun kimanin shekaru shida da suka wuce ya so ya kara aure, don a lokacin har an je gaisuwa gidansu budurwar da yake nema; sadaki kawai za a kai a saka rana sai kuma aka wayi gari haka kawai maganar auren ta fita ransa. Yarinyar da yake nema bata yi masa komai ba amma haka kawai yaji ya daina sonta. Da farko ta so ta takura masa, amma sai Allah ya hadata da wani saurayi a daidai lokacin wanda ya fiye mata Yusuf din.
Matarsa daya Hajiya Zahra’u da yaransu biyar; Sadik, Yusra, Rukayya, Khadija wadda suke kira Dija sai Zulaiha mai shekaru uku wadda suke kira Ummi saboda sunan mahaifiyar Zahra’un taci.
Hajiya Zahra’u mace ce mai matukar kirki ga kyauta, duk wani abu da zai farantawa mijinta shi takeyi. Shima kuma ta samu yana da kulawa gashi yana mata yanda take so; musamman ma yanzu da Allah ya kara buda masa ya fara tara abun duniya. ‘Yan uwan Yusuf ma suna matukar kaunarta saboda yanda take musu kyauta kuma tana kulasu tana kula da mahaifiyarsu Hajiya.
Tun Yusuf yana malamin makaranta ta aureshi, suna tare ya karo karatu ya sami sauyin aiki ya koma ma’aikatar ilimi ta jiha; gashi yanzu har ya zama director. Wannan ne ya saka Hajiya Zahra’u take ji cewa ita kadai ce ta dace ta zama matarsa, don ita ta sha wahalarsa. Shi yasa ma wancan lokacin daya ya dauko maganar aure ta san yanda tayi ta kifar da zancen.
Bata yin tsafi don tana da ilimin addini gwargwado saboda haka ta san abinda zai rabata da imaninta, amma tana da malamanta irin na soro wadanda sukeyi mata aiki da ayar Allah, wani lokacin ma har su bata ruwan rubutu ko tofi wanda zata yi amfani da shi ko shi Yusuf din tayi masa amfani da shi.
Tunda taji anje gaisuwa wancan lokacin da ya fara maganar auren ta tashi ta tafi har garin Gaya, wajen wani malami da aka hadata da shi Malam Hatimu mai ‘yan makaranta. Tayi masa bayani so take kawai a sakashi ya manta da maganar auren nan ya daina son yarinyar. A nan take kuwa ya zana hatimi ya nade mata laya ya bata yace ta saka masa a karkashin katifarsa, idan dai ya kwana a kai ba zai sake maganar auren wannan yarinyar ba. Haka kuwa akayi, wannan aure dole aka barshi.
Bayan fasa wancan auren ne abokinsa ya bashi shawara idan ya tashi sake aure kada ya fada da wuri sai magana ta kankama, kuna shima sai ya dage da addu’a. Don haka ma tunda ya fara neman auren Aisha babu wanda ya gayawa, don har abokan nasa ma babu wanda sani.
Yayansa kawai ya gayawa wanda shine zai wuce masa gaba wajen neman auren kuma ya gaya masa bai sanarwa kowa ba don haka shima kada ya bari zancen yake wajen mata.
____
A daki ta sami Hajiya tana zaune a kan dadduma inda ta idar da sallar la’asar, ta shiga dakin da sallama ta karasa ta zauna a gaban Hajiyan bayan da ta amsa sallamarta. Hajiya ta gyara zama tace
‘To wacce sura zan biya miki da kika sakani a gaba haka kamar mai daukar karatu.’
Tayi ‘yar dariya tace
‘Kai Hajiya.’
‘To ya akayi?’
Ta dan saita fuskarta tana kokarin danne damuwar da take zuciyarta
‘Hajiya dama Yusuf ne yace zasu zo sa rana sati mai zuwa, kuma tare zasu kawo da sadaki da kayan aure duka.’
Take murmushin Hajiya ya karu