Sashe 67
Uwar Sadiku Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
‘Yaya don Allah ku bar maganar nan, ku bar yarinyar nan ta koma gidanta tunda ita ta ji ta gani. Idan tana can ma sai tafi dagewa da addu’a amma yanzu idan an rike ta a nan ba zata nutsu ba tunda ta fi son can din. Idan babu hali ma ni sai na koma can na dinga tayata zaman zuwa lokacin da komai zai warware.’
‘Uwani ki kyaleta, ai ba sallamarta mukayi ba kawai don mun mata aure.’
‘Ni dai Yaya gaskiya ki barta ta koma, shima Abubakar din zai zo ya same ni.’
Bata saurari Hajiyan ba ta tashi ta bi bayan Aishan.
Kai tsaye dakinta ta wuce don ta san a nan ne zata sameta. Ta zauna a gefen gadon ta dafa bayan Aishan tace
‘Yi hakuri Shatu, Abubakar din zai zo ya same ni. Wannan abun ba komai bane face jarrabawa kuma da izinin Allah zai wuce, mu da muka je har kasa mai tsarki muka roki Allah a kan wannan lamarin ai ya kamata a ce mu barki ki zauna a dakinki zuwa lokacin da komai zai warware.’
Ta share kwallarta da zanin gadon ta mayar da kanta ta kwantar a kan cinyar Anti Uwani sannan tace
‘Gara na zauna a can ni dai, kuma ina ji a jikina wannan matsalar ta kusa zuwa karshe in Sha Allah. Kuma Anti Uwani ita matarsa so take na bar gidan kin ga yanzu idan ta bude ido taga bana nan ai ta ci nasara ko?’
‘Kada ki damu ki cigaba da shiri in Sha Allahu don ranar Juma’ar zaki koma, idan ma sun ki saurarata har gidan baffanki zan je na kirawoshi ya mayar dake don na san ba zai goyi bayan wannan aika-aikar ba.’
Haka ta dauki lokaci tana lallashinta.
………..
Washegari da yamma suna zaune sai ga Baffa, Suhail ne babban yaronsa ya kawo shi saboda shi tun tuni ya hakura da tuki saboda baya gani sosai daga nesa, don haka idan zai fita sai ya jira yara.
Bayan sun gaisa da Hajiya da Anti Uwani yace
‘Kwana biyu, kin san idona ya ki ina ta so nazo na ganku to yara duk kowa ya bazama nema babu lokaci.’
Tace
‘Babu komai Baffa, ai dama komai lokacine. Allah ya kara lafiya ya ja kwana.’
‘Amin ya Allah.’
Suna nan zaune suna hirarrakinsu Aisha da su Abdallah suka shigo, sun dawo daga gidan Anti Zainab.
Bayan ta gaida Baffa yace
‘Yanzu kika zo Shatu da magaribar nan, ba kya gudun kiyi dare a hanya? Ya maigidan naki? Ina fatan dai komai ya warware.’
Ta sunkuyar da kai tace
‘Lafiya kalau.’
Anti Uwani tace
‘Ai tunda muka dawo daga Umra dama bata tafi ba.’
‘Garin yaya? Ina fatan dai ba matsalar nan ce ba.’
Hajiya tace
‘Itace dai har yanzu babu wani cigaba, don shi yasa ma nace ta zauna a nan idan ya dawo hayyacinsa ya zo su tafi.’
Da mamaki Baffa yace
‘Ikon Allah! Ko da yake malamin da na sa yake addu’a ya gaya min abun zai iya daukar lokaci amma komai daren dadewa zai yi karshe.’
Ya kalli Aishan yace
‘Shatu da kinyi hakuri kinyi zamanki a can tunda ance min an baki mai tayaki kwana, jarrabawa ce ta ubangiji kuma idan kina can din ai sai abun ya fi saurin warwarewa.’
Ta sunkuyar da kai, Anti Uwani tace
‘To ai Yayan ce ta hanata komawa ita da Abubakar, amma ita ai tana son ta koma gidanta kuma nima na goyi da bayan hakan an dai fi karfinmu ne kawai.’
Baffa ya kalli Hajiya yace
‘Gaskiya a barta ta koma Hajiya, ai hakuri akeyi. Kuma wannan abun in Sha Allah zai warware in Sha Allah.’
Ya kalli Aisha yace
‘Ki koma Shatu kiyi zamanki, sai dai idan shine yace ki tafi to tabbas muma ba zamu barki ki zauna ba. Amma yanzu hakuri zakiyi ki zauna gaba daya mu cigaba da addu’a.’
Anti Uwani tace
‘Dama gobe tace zata koma, tunda an yi haka in Sha Allahu goben sai muje na rakasu ita da Amiran.’
Baffa ya dubi Hajiya yace
‘Ayi hakuri Hajiya in Sha Allah komai zai wuce.’
‘Um,shikenan Baffa. Dama gani nayi tana can tana zama kamar me zaman kanta shi yasa nace ta dawo gida, amma in Sha Allah goben zata koma.’
‘Yauwa.’
Aishan ta tashi ta wuce daki inda su Abdallah suke can suna wasansu.
Hajiya da Anti Uwani kuma da Baffa suka karasa hirarrakinsu, sai dab da magriba Baffa yayi musu sallama ya tafi.
Yana fita Hajiya ta dubi Anti Uwani tace
‘Kun sami yanda kuke so ai sai kije ku fara shiri ke da ‘yar taki ko?’
Ta mike tana dariya tace
‘Eh, bari muje mu hada kayanmu ai zaman aure ba wasa bane kuma kowa da jarrabawarsa.’
Ta wuce daki tana dariya.
Cikin daren nan Anti Uwani ta taya Aisha suka hada kayanta. Washe gari Juma’a wajen karfe goma suka kama hanya tare da Anti Uwanin suka tsaya suka dauki Amira sannan suka wuce.
Sai da suka gama gyara gidan tsaf sannan Anti Uwani ta hau mota ta koma gidan Hajiya, ta bar Aisha da Amira.
Gaba daya Aisha ta manta basu siyo burodin karin kumallo ba gashi kuma basu da indomie a gidan. Don haka da safe wajen karfe takwas da rabi Aisha ta bawa Amira kudi ta siyo musu burodi da kwai su karya.
Tana fitowa daga gate din gidan su kuma su Yusra sun fito daga gidansu zasu tafi tahfiz don ranar aka koma hutu. Yusra ta balla mata harara, ita kuwa tayi dariya ta dagowa Rukayya hannu wadda ta mayar mata da murmushi ta daga mata hannu itama. Ta wuce ta barsu a nan Yusra tana ta faman hararar Rukayya.
--------
Tun bayan da ta haifi Sumayya bata sake yin wani tsarin iyali ba, ba wai ta damu da haihuwar bane amma tabbas a halin yanzu idan ta zo ba zata Hana ba. Duk da har yanzu Aisha bata haihu ba amma dai tana so ta haifi da namiji sannan Kuma tana so ta cika gidan da ‘yaya.
Tun cikin azumi take jin jikinta babu dadi, lokacin da ya kamata tayi al’ada har ya wuce bata sha azumi ko daya ba don haka zuwa yanzu tana da yakinin ciki ne da ita. Lafiya kalau take daukar ciki ta haihu don haka ta yanke shawarar ba zata je asibiti ba har sai cikin yayi wata hudu, zuwa lokacin idan aka yi scanning za a iya gaya mata mace ne ko namiji.
Tun kafin yaran su tafi tahfiz Jummai ta zo, don haka suma tafiya ta sallami Jummai da ayyukan da zata yi mata ta haye sama ta kwanta a dakinta. Bata Dade da kwanciya ba Shima Abban yayi mata sallama ya wuce gidan Hajiya.
Yana fita bacci ya kwasheta.
Bata farka daga wannan baccin ba sai wajen Sha biyu da kwata lokacin da yara suka dawo daga tahfiz wanda shigar Sumayya da Ummi dakin shine ya farkar da ita. Bayan sun gama yi mata sannu da gida tace su sauko wajen Jummai su ci abinci sannan su kunna TV suyi kallo. Suna fita daga dakin ragowar yaran ma suka shigo sukayi mata sannu da gida sannan suka fice
Yusra ce ta karshen shigowa ta sami waje a gefen gadon ta zauna, ta dubi Mommy din wadda har yanzu take kwance tace
‘Mommy kika ce matar Abba ta tafi?’
Cikin halin ko in kula tace
‘Eh, tun cikin azumi ma kuwa.’
‘To gaskiya Mommy ko dai bata tafi ba ko kuma ta dawo don gaskiya yau na wannan mara kunyar ‘yar tata ta fito daga gidan, don har hannu ma ta dagowa Rukayya.’
Ta tashi zaune ta kalli Yusra yayinda mamaki ya bayyana a fuskarta
‘Ikon Allah, to dama tana nan ko kuwa dawowa tayi?’
‘Ina ga dai Mommy azumi taje tayi a gida shine ta dawo.’
Ta jijjiga kai
‘Um! To shikenan idan kin sake ganin motsi a gidan kiyi min magana.’
Ta amsa sannan ta tashi ta fice daga dakin.
Duk da Yusra ta san cewa uwarta tana bin malamai amma bata san itace tayi abinda Abba ya daina kula Aisha ba, ba wai ta dauka bin malaman kuskure bane. Hasali ma a wajenta shine dai-dai tunda Mommy tace tsari ne ake nema musu. Lokacin da taga Abba ya daina kula Aisha tayi zaton asirin da Mommy tace musu ta yiwa Abban ne ya karye shi yasa ya manta da ita, don haka yanzu da ta ganta tsoro take ji kada ta sake yiwa Abbansu wani asirin duk da ta san Mommy a tsaye take a kansu.
Yusra tana fita daga dakin ta gyara zama ta kafa tagumi; Aishan nan wai me take nufi ne? Kusan shekara guda miji baya zuwa inda kike amma kin ki fita daga rayuwarsa? Wannan din wanne irin naci ne? Gashi zuwa yanzu matan unguwar da take harka da su sun fara tambayarta labarin Aisha a kan sunji a unguwa cewa auren Aishan ya mutu; duk da dai ta gaya musu itama bata san me ake ciki ba domin da ta tambaya ma Abban yace kada ta sake yi masa maganar.
Tabbas dole ta koma Doguwa; tunda dama akwai maganar Yaya Bello da take so a rabashi da Abban. Dama azumi ne ya hanata zuwa da aka sallace kuma bata da aiki sai bacci saboda cikin da take dauke da shi; ko da yake lokaci zata saka taje gidan Amina su tsara yanda za ayi don watakila ma Aminan zata iya zuwa mata Doguwan.
Haka ta karasa wunin ranar tana tunanin mafita.
--------
Ita kuwa Aisha tunda ta dawo gidanta sai ta sake mayar da hankali wajen addu’a, ranakun aiki taje aiki ta dawo ranakun Asabar da Lahadi kuma sai taje islamiyya. Rashin kulata da Abban yakeyi yana damunta sai dai da yake dinkin mayafai da takeyi yana rage mata zama haka nan sai abun yayi mata sauki;kuma ta samu ana sayen mayafan sosai don haka kusan kullam cikin aiki take Amira tana tayata.
---------
‘Uwani ki kyaleta, ai ba sallamarta mukayi ba kawai don mun mata aure.’
‘Ni dai Yaya gaskiya ki barta ta koma, shima Abubakar din zai zo ya same ni.’
Bata saurari Hajiyan ba ta tashi ta bi bayan Aishan.
Kai tsaye dakinta ta wuce don ta san a nan ne zata sameta. Ta zauna a gefen gadon ta dafa bayan Aishan tace
‘Yi hakuri Shatu, Abubakar din zai zo ya same ni. Wannan abun ba komai bane face jarrabawa kuma da izinin Allah zai wuce, mu da muka je har kasa mai tsarki muka roki Allah a kan wannan lamarin ai ya kamata a ce mu barki ki zauna a dakinki zuwa lokacin da komai zai warware.’
Ta share kwallarta da zanin gadon ta mayar da kanta ta kwantar a kan cinyar Anti Uwani sannan tace
‘Gara na zauna a can ni dai, kuma ina ji a jikina wannan matsalar ta kusa zuwa karshe in Sha Allah. Kuma Anti Uwani ita matarsa so take na bar gidan kin ga yanzu idan ta bude ido taga bana nan ai ta ci nasara ko?’
‘Kada ki damu ki cigaba da shiri in Sha Allahu don ranar Juma’ar zaki koma, idan ma sun ki saurarata har gidan baffanki zan je na kirawoshi ya mayar dake don na san ba zai goyi bayan wannan aika-aikar ba.’
Haka ta dauki lokaci tana lallashinta.
………..
Washegari da yamma suna zaune sai ga Baffa, Suhail ne babban yaronsa ya kawo shi saboda shi tun tuni ya hakura da tuki saboda baya gani sosai daga nesa, don haka idan zai fita sai ya jira yara.
Bayan sun gaisa da Hajiya da Anti Uwani yace
‘Kwana biyu, kin san idona ya ki ina ta so nazo na ganku to yara duk kowa ya bazama nema babu lokaci.’
Tace
‘Babu komai Baffa, ai dama komai lokacine. Allah ya kara lafiya ya ja kwana.’
‘Amin ya Allah.’
Suna nan zaune suna hirarrakinsu Aisha da su Abdallah suka shigo, sun dawo daga gidan Anti Zainab.
Bayan ta gaida Baffa yace
‘Yanzu kika zo Shatu da magaribar nan, ba kya gudun kiyi dare a hanya? Ya maigidan naki? Ina fatan dai komai ya warware.’
Ta sunkuyar da kai tace
‘Lafiya kalau.’
Anti Uwani tace
‘Ai tunda muka dawo daga Umra dama bata tafi ba.’
‘Garin yaya? Ina fatan dai ba matsalar nan ce ba.’
Hajiya tace
‘Itace dai har yanzu babu wani cigaba, don shi yasa ma nace ta zauna a nan idan ya dawo hayyacinsa ya zo su tafi.’
Da mamaki Baffa yace
‘Ikon Allah! Ko da yake malamin da na sa yake addu’a ya gaya min abun zai iya daukar lokaci amma komai daren dadewa zai yi karshe.’
Ya kalli Aishan yace
‘Shatu da kinyi hakuri kinyi zamanki a can tunda ance min an baki mai tayaki kwana, jarrabawa ce ta ubangiji kuma idan kina can din ai sai abun ya fi saurin warwarewa.’
Ta sunkuyar da kai, Anti Uwani tace
‘To ai Yayan ce ta hanata komawa ita da Abubakar, amma ita ai tana son ta koma gidanta kuma nima na goyi da bayan hakan an dai fi karfinmu ne kawai.’
Baffa ya kalli Hajiya yace
‘Gaskiya a barta ta koma Hajiya, ai hakuri akeyi. Kuma wannan abun in Sha Allah zai warware in Sha Allah.’
Ya kalli Aisha yace
‘Ki koma Shatu kiyi zamanki, sai dai idan shine yace ki tafi to tabbas muma ba zamu barki ki zauna ba. Amma yanzu hakuri zakiyi ki zauna gaba daya mu cigaba da addu’a.’
Anti Uwani tace
‘Dama gobe tace zata koma, tunda an yi haka in Sha Allahu goben sai muje na rakasu ita da Amiran.’
Baffa ya dubi Hajiya yace
‘Ayi hakuri Hajiya in Sha Allah komai zai wuce.’
‘Um,shikenan Baffa. Dama gani nayi tana can tana zama kamar me zaman kanta shi yasa nace ta dawo gida, amma in Sha Allah goben zata koma.’
‘Yauwa.’
Aishan ta tashi ta wuce daki inda su Abdallah suke can suna wasansu.
Hajiya da Anti Uwani kuma da Baffa suka karasa hirarrakinsu, sai dab da magriba Baffa yayi musu sallama ya tafi.
Yana fita Hajiya ta dubi Anti Uwani tace
‘Kun sami yanda kuke so ai sai kije ku fara shiri ke da ‘yar taki ko?’
Ta mike tana dariya tace
‘Eh, bari muje mu hada kayanmu ai zaman aure ba wasa bane kuma kowa da jarrabawarsa.’
Ta wuce daki tana dariya.
Cikin daren nan Anti Uwani ta taya Aisha suka hada kayanta. Washe gari Juma’a wajen karfe goma suka kama hanya tare da Anti Uwanin suka tsaya suka dauki Amira sannan suka wuce.
Sai da suka gama gyara gidan tsaf sannan Anti Uwani ta hau mota ta koma gidan Hajiya, ta bar Aisha da Amira.
Gaba daya Aisha ta manta basu siyo burodin karin kumallo ba gashi kuma basu da indomie a gidan. Don haka da safe wajen karfe takwas da rabi Aisha ta bawa Amira kudi ta siyo musu burodi da kwai su karya.
Tana fitowa daga gate din gidan su kuma su Yusra sun fito daga gidansu zasu tafi tahfiz don ranar aka koma hutu. Yusra ta balla mata harara, ita kuwa tayi dariya ta dagowa Rukayya hannu wadda ta mayar mata da murmushi ta daga mata hannu itama. Ta wuce ta barsu a nan Yusra tana ta faman hararar Rukayya.
--------
Tun bayan da ta haifi Sumayya bata sake yin wani tsarin iyali ba, ba wai ta damu da haihuwar bane amma tabbas a halin yanzu idan ta zo ba zata Hana ba. Duk da har yanzu Aisha bata haihu ba amma dai tana so ta haifi da namiji sannan Kuma tana so ta cika gidan da ‘yaya.
Tun cikin azumi take jin jikinta babu dadi, lokacin da ya kamata tayi al’ada har ya wuce bata sha azumi ko daya ba don haka zuwa yanzu tana da yakinin ciki ne da ita. Lafiya kalau take daukar ciki ta haihu don haka ta yanke shawarar ba zata je asibiti ba har sai cikin yayi wata hudu, zuwa lokacin idan aka yi scanning za a iya gaya mata mace ne ko namiji.
Tun kafin yaran su tafi tahfiz Jummai ta zo, don haka suma tafiya ta sallami Jummai da ayyukan da zata yi mata ta haye sama ta kwanta a dakinta. Bata Dade da kwanciya ba Shima Abban yayi mata sallama ya wuce gidan Hajiya.
Yana fita bacci ya kwasheta.
Bata farka daga wannan baccin ba sai wajen Sha biyu da kwata lokacin da yara suka dawo daga tahfiz wanda shigar Sumayya da Ummi dakin shine ya farkar da ita. Bayan sun gama yi mata sannu da gida tace su sauko wajen Jummai su ci abinci sannan su kunna TV suyi kallo. Suna fita daga dakin ragowar yaran ma suka shigo sukayi mata sannu da gida sannan suka fice
Yusra ce ta karshen shigowa ta sami waje a gefen gadon ta zauna, ta dubi Mommy din wadda har yanzu take kwance tace
‘Mommy kika ce matar Abba ta tafi?’
Cikin halin ko in kula tace
‘Eh, tun cikin azumi ma kuwa.’
‘To gaskiya Mommy ko dai bata tafi ba ko kuma ta dawo don gaskiya yau na wannan mara kunyar ‘yar tata ta fito daga gidan, don har hannu ma ta dagowa Rukayya.’
Ta tashi zaune ta kalli Yusra yayinda mamaki ya bayyana a fuskarta
‘Ikon Allah, to dama tana nan ko kuwa dawowa tayi?’
‘Ina ga dai Mommy azumi taje tayi a gida shine ta dawo.’
Ta jijjiga kai
‘Um! To shikenan idan kin sake ganin motsi a gidan kiyi min magana.’
Ta amsa sannan ta tashi ta fice daga dakin.
Duk da Yusra ta san cewa uwarta tana bin malamai amma bata san itace tayi abinda Abba ya daina kula Aisha ba, ba wai ta dauka bin malaman kuskure bane. Hasali ma a wajenta shine dai-dai tunda Mommy tace tsari ne ake nema musu. Lokacin da taga Abba ya daina kula Aisha tayi zaton asirin da Mommy tace musu ta yiwa Abban ne ya karye shi yasa ya manta da ita, don haka yanzu da ta ganta tsoro take ji kada ta sake yiwa Abbansu wani asirin duk da ta san Mommy a tsaye take a kansu.
Yusra tana fita daga dakin ta gyara zama ta kafa tagumi; Aishan nan wai me take nufi ne? Kusan shekara guda miji baya zuwa inda kike amma kin ki fita daga rayuwarsa? Wannan din wanne irin naci ne? Gashi zuwa yanzu matan unguwar da take harka da su sun fara tambayarta labarin Aisha a kan sunji a unguwa cewa auren Aishan ya mutu; duk da dai ta gaya musu itama bata san me ake ciki ba domin da ta tambaya ma Abban yace kada ta sake yi masa maganar.
Tabbas dole ta koma Doguwa; tunda dama akwai maganar Yaya Bello da take so a rabashi da Abban. Dama azumi ne ya hanata zuwa da aka sallace kuma bata da aiki sai bacci saboda cikin da take dauke da shi; ko da yake lokaci zata saka taje gidan Amina su tsara yanda za ayi don watakila ma Aminan zata iya zuwa mata Doguwan.
Haka ta karasa wunin ranar tana tunanin mafita.
--------
Ita kuwa Aisha tunda ta dawo gidanta sai ta sake mayar da hankali wajen addu’a, ranakun aiki taje aiki ta dawo ranakun Asabar da Lahadi kuma sai taje islamiyya. Rashin kulata da Abban yakeyi yana damunta sai dai da yake dinkin mayafai da takeyi yana rage mata zama haka nan sai abun yayi mata sauki;kuma ta samu ana sayen mayafan sosai don haka kusan kullam cikin aiki take Amira tana tayata.
---------