Sashe 72
Uwar Sadiku Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Da kyar ta tashi ta hade sallar Magriba da isha’i tana yin sallar tana tunani wato ma wucewa yayi gidan Aishan ba tare da yayi mata ssallama ba.
Nan ta zauna a kan daddumar tana ta tunani kala-kala na yanda zata bullowa wannan al’amari, domin ba zata yarda ba.
Bata ji lokacin da ya shigo gidan ba saboda tunaninta baya wajen, jinsa kawai tayi ya turo kofar dakinta ya shigo.
Bayan ya amsa sallamarta yace
‘Yanzu kika idar da sallar ne?’
‘Eh, saura shafa’i da witri.’
‘To ni zan wuce, don Allah a rufe gidan da wuri kuma idan Saddiku ya kai goman dare bai dawo ba kiyi min waya.’
‘To in sha Allah.’
Ya juya ya fice bayan ya amsa a dawo lafiya da tayi masa.
Tayi kwafa ta share kwallar da ta taru a kwarmin idonta.
---------
Ba karamar jarumta yayi ba da ya daure bai je wajen Aisha ba har akayi sallar isha’i.
Tun daga bakin gate kamshin turaren wutarta yayi masa maraba, shi kanshi ya san yayi kewar wannan turaren. Ya karasa ya sa mukullinsa ya shiga kofar falon. Babu kowa a falon, ya dan tsaya ya karewa falon kallo; sai yanzu ya tabbatar ya dade rabon da ya shigo gidan nan. Ya ji motsi a dakin baki wanda ya san Amira ce, bai hango fitila a dakinsa ba sai a dakinta don haka ya tura kofar dakin a hankali ya shiga da sallama.
Tana zaune a kan gado ta mike kafa tana ta faman danne danne a waya, bai sani ba ko ta amsa sallamarsa ko bata amsa ba don shi dai bai ji muryarta ba.
Ya karasa ya zauna a gefen gadon yayinda ta dan janye kafarta, yana ta faman binta da kallo kamar yau ya fara ganinta. Ta bude baki kamar bata so tace
‘Sannu da zuwa.’
Sai da yayi ajiyar zuciya sannan ya amsa
‘Yauwa Aisha.’
Ya cigaba da binta da kallo ba tare da yace komai ba.
Jimawa kadan ta gaji da kallon da yake mata, ta zuro kafafunta kasa daga kan gadon ta mike tsaye tana fadin
‘Ga abincinka can a kan dining table muje na zuba maka kaci dare yana yi.’
Nan da nan shima ya mike ya sha gabanta, kafin tayi wani yunkuri ya janyota jikinsa gaba daya ya rungumeta. Bata da kuzarin kwacewa domin itama tayi kewarsa don haka ta rungumeshi. A hankali ya fara bin wuyanta yana sumbata yana kara kankameta, sai da tayi da gaske ta tattara nutsuwarta ta dan tureshi tana fadin
‘Muje kaci abinci fa dare yana yi.’
Ya kalleta suka hada ido ya dan kara matsawa kusa da ita ya sumbaci lebenta, taja baya. Yace
‘Aisha ba kiyi kewata ba kenan?’
Tayi murmushi ta sunkuyar da kai
‘Hmm!’
Ta wuce gaba ya bita a baya suka nufi falon.
Bayan ya zauna a dining table din ta zuba masa abinci; kuskus ne da miyar alaiyahu da hanta. Ta ajiye farantin a gabansa ta dora masa cokali a kai sanna ta ja kujera ta zauna.
Ya dubeta yace
‘Ke ba zaki ci ba?’
Ta kawar da kai sannan ta bashi amsa
‘Na ci nawa.’
‘Yau babu jira kenan aka yi min solo.’
Tayi murmushin yake
‘Ban tabbatar zaka zo ba har sai da na ganka yanzu, shi yasa dana idar da sallar isha’i baka shigo ba na ci abincin.’
Duk yanda ya kai ga jun tausayin kansa sai da yaji tausayinta fiye da yanda yake tausayin kansa, da kyar ya danne kwallar da ta taso masa saboda baya so ya kara raunana mata zuciya. Ya mika hannunsa ya kama hannunta wanda yake ajiye a kan tebur din, ya sumbaci hannun ya rike yana cigaba da shafawa. Yace
‘Ban san da bakin da zan baki hakuri ba Aisha, ban san kuma irin hakurin da zan baki ba. An cutar dake kuma an cutar damu gaba daya.’
Ya sake sumbatar hannun.
Tace
‘Ka ci abincin kada ya huce.’
Ya saka hannunsa na dama yana cin abincin yayinda hannunsa na hagu yake rike da hannunta na dama, yana cin abincin yana kallon fuskarta.
Bayan ya gama cin abincin sai da ya tayata ta kwashe kwanukan sanna ya jata suka zauna a kan doguwar kujera falo.
Duk da TV a kashe take amma ita Aisha da ta zauna gaba take kallo shi kuma da ya tashi sai ya zauna yana fuskantar Aishan. Ya kamo hannunta ya sumbata, ya juyo da fuskarta wadda ba shi take kallo ba ya sumbaci lebenta. Ta bude baki zata yi magana ya rigata
‘Aisha. Don Allah yau kada kiyi min fushi please.’
Ta yi murmushi ta share kwallar da ta taru a kwarmin idonta. Ya kara matsawa kusa da ita yana kokarin janyota jikinsa gaba daya. Ta dage sannan tace
‘Amira tana nan kada fa ta fito.’
Ya cije lebensa ya dan ja baya, ya dubeta yace
‘Tashi mu koma daki to.’
Ya mike ya jata itama ta mike tsaye.
Yana rike da ita ya zagaya ya kashe fitilun falon domin gani yakeyi idan ya saketa zata iya tafiya dakinta tace fushi take yi dashi. Sai da ya kashe fitilun tas sannan ya jata suka shige daki.
Duk yanda ta so ta dage a wannan dare Abban Sadik bai bata dama ba, haka suka kwana suna biyan bashin juna cikin walwala.
………..
Yanda Aisha da Yusuf suka kwana suna walwala haka Zahra ta kwana cikin kunci da lissafin yanda zata yi da Aisha; domin ba zata taba bar mata Abban Sadik ba.
Gaba daya tunaninta ya kare, duk iya satar bacci haka ya kyaleta sai bayan asuba sannan ta sami baccin.
__
Cikin walwala suka wayi gari Lahadi, sai wajen karfe goma sannan suka gama breakfast a lokacin ya fice don ya dubo Zahra da yaran. Yanda ya barta jiya haka ya sameta yau, ya riga ya san abinda yake damunta kishi ne na rashin tunani ta dorawa kanta don haka ba tare da bata lokaci ba suka gaisa ya fito ya bar mata gidan tunda yara duk suna tahfiz.
Tana so ta yarda bai fahimci wanda ya raba shi da Aisha ba amma kuma tana mamakin yanda jiya zuwa yau yake nuna mata wani hali na ko in kula. Amma dai ta san dole ta saurara yanzu zuwa lokacin da zata sami kanta.
…………..
Bayan azahar Abba ya dauki Aisha suka tafi gidan Hajiya, ya riga ya san yayi musu laifi don haka suka je ya sami Hajiya da Anti Uwani ya basu hakuri. Daga nan suka wuce gidan Yaya Abubakar shima ya sameshi yayi ta bashi hakuri. Sai bayan la’asar sannan suka dawo gidan zuwa lokacin har Amira ta dora abincin dare.
Bayan sallar isha’I tana kicin tana jiyoshi yana waya da Jibrin.
Bayan ta shigo falon yake tambayarta rasit na biyan kudin hayar gidan, ta dauko daga daki ta bashi. Kafin su kwanta bacci taji alert ya tura mata kudin hayar da ta biya harda Karin dubu dari. Ta tambayeshi to karin na menene, yace
‘Duk tsawo lokacin nan ke kike ciyar da kanki kina yin komai wanda ba haka ya kamata ba ai kinga dole na biya bashi ko. Na san abinda kika ci ma ya fi dubu dari in Sha Allahu idan aka kwana biyu zan ciko sauran don na san matata akwai cinye buhun shinkafa.’
Tayi dariya.
Babu yanda bata yi da shi a kan ba sai ya sake turowa ba amma ko sauraronta bai yi ba, suka cigaba da hirarasu.
Da sati ya zagayo kuma haka ya sake daukan Aisha suka zaga danginsa.
Yanda Hajiya ta saba karbarta cikin halin ko in kula haka ta yi mata, shi kanshi Abban sai da yaji babu dadi. Ya kara jin haushi Zahra saboda wannan matsalar da ta kirkiro a lokacin da Hajiyan ta fara haduwa da Aisha itace dalilin wannan kiyayyar; sannan kuma yanzu ga ciwo ga rikicin tsufa.
Sai da suka tsaya a gidan Yaya Bello sannan suka wuce gida.
Haka rayuwarsu ta cigaba cikin walwala da adduoi.
Ita kuwa Zahra tun tana saka rai Abba zai tutsiyeta har ta sakankance bai gane itace tayi musu asiri ba. Ta cigaba da kokarin tara kudi tunda tana son aje mata wajen boka.
Shi kuma Abban ya kyaleta ne saboda cikin da yake jikinta da kuma tunanin da yakeyi a kan makomar yaransa idan yace zai yi rigima da Zahra; yaran da daman yana ganin kamar akwai gibi a tarbiyyarsu. Yana sane da yanda idan dai tana fushi da shi toh gaba daya yaran suma sai su daina kulashi sai Rukayya da Sumayya ne kawai suke kulashi ba zai ga walwalarsu ba har sai uwarsu ta daina fushi da shi. To idan ya saketa yanzu yana jin yaki za a koma yi tsakaninshi da ‘yayanshi wanda shi din ba haka yake so ba. Don haka ya kayaleta take cigaba da rayuwarta kamar bata yi masa laifi ba, musamman da yake Malam Audurahmanu ya sanar da shi idan dai ya rike addu’ar da ya bashi to lallai babu sihirin da zai sake tasiri a kansa.
__
Lokaci ya ja don haka kowa ya koma harkarsa kamar yanda aka saba.
Ranar Talata da yamma Zahra ta shirya ta tafi wajen scanning domin yanzu cikinta ya kai kusan wata bakwai tunda yana motsi sosai har tana ganin motsinsa. So take a kara tabbatar mata da cewa lallai namiji ne domin bata so abinda ya faru a haihuwar Sumayya ya sake faruwa. Kamar yanda ta zata haka aka tabbatar mata da cewa lallai namiji ne domin babu ma yanda za ayi ya zama mace.
Cikin walwala ta dawo gida, washegari kuma ta shirya ta tafi asibitin Nassarawa awo. Aka duba ta sosai awajen awon, likita ya tabbatar mata da lafiyarta da kuma lafiyar jaririnta. Don haka ta dawo gida cikin walwala bayan an rubuta mata appointment ta dawo bayan sati hudu domin sake yin awo.
---------
Ranar Alhamis ce wadda ta kama saura kwana biyar Zahra ta koma awo.
Yau din tunda gari ya waye take jin jikinta babu dadi, gashi cikin yayi mata nauyi sosai da kyar take jan kafa sannan ga mararta tana ciwo kadan-kadan. Nan da nan ta gama abinda takeyi ta koma ta kwanta don bata ma jin kwari.
Nan ta zauna a kan daddumar tana ta tunani kala-kala na yanda zata bullowa wannan al’amari, domin ba zata yarda ba.
Bata ji lokacin da ya shigo gidan ba saboda tunaninta baya wajen, jinsa kawai tayi ya turo kofar dakinta ya shigo.
Bayan ya amsa sallamarta yace
‘Yanzu kika idar da sallar ne?’
‘Eh, saura shafa’i da witri.’
‘To ni zan wuce, don Allah a rufe gidan da wuri kuma idan Saddiku ya kai goman dare bai dawo ba kiyi min waya.’
‘To in sha Allah.’
Ya juya ya fice bayan ya amsa a dawo lafiya da tayi masa.
Tayi kwafa ta share kwallar da ta taru a kwarmin idonta.
---------
Ba karamar jarumta yayi ba da ya daure bai je wajen Aisha ba har akayi sallar isha’i.
Tun daga bakin gate kamshin turaren wutarta yayi masa maraba, shi kanshi ya san yayi kewar wannan turaren. Ya karasa ya sa mukullinsa ya shiga kofar falon. Babu kowa a falon, ya dan tsaya ya karewa falon kallo; sai yanzu ya tabbatar ya dade rabon da ya shigo gidan nan. Ya ji motsi a dakin baki wanda ya san Amira ce, bai hango fitila a dakinsa ba sai a dakinta don haka ya tura kofar dakin a hankali ya shiga da sallama.
Tana zaune a kan gado ta mike kafa tana ta faman danne danne a waya, bai sani ba ko ta amsa sallamarsa ko bata amsa ba don shi dai bai ji muryarta ba.
Ya karasa ya zauna a gefen gadon yayinda ta dan janye kafarta, yana ta faman binta da kallo kamar yau ya fara ganinta. Ta bude baki kamar bata so tace
‘Sannu da zuwa.’
Sai da yayi ajiyar zuciya sannan ya amsa
‘Yauwa Aisha.’
Ya cigaba da binta da kallo ba tare da yace komai ba.
Jimawa kadan ta gaji da kallon da yake mata, ta zuro kafafunta kasa daga kan gadon ta mike tsaye tana fadin
‘Ga abincinka can a kan dining table muje na zuba maka kaci dare yana yi.’
Nan da nan shima ya mike ya sha gabanta, kafin tayi wani yunkuri ya janyota jikinsa gaba daya ya rungumeta. Bata da kuzarin kwacewa domin itama tayi kewarsa don haka ta rungumeshi. A hankali ya fara bin wuyanta yana sumbata yana kara kankameta, sai da tayi da gaske ta tattara nutsuwarta ta dan tureshi tana fadin
‘Muje kaci abinci fa dare yana yi.’
Ya kalleta suka hada ido ya dan kara matsawa kusa da ita ya sumbaci lebenta, taja baya. Yace
‘Aisha ba kiyi kewata ba kenan?’
Tayi murmushi ta sunkuyar da kai
‘Hmm!’
Ta wuce gaba ya bita a baya suka nufi falon.
Bayan ya zauna a dining table din ta zuba masa abinci; kuskus ne da miyar alaiyahu da hanta. Ta ajiye farantin a gabansa ta dora masa cokali a kai sanna ta ja kujera ta zauna.
Ya dubeta yace
‘Ke ba zaki ci ba?’
Ta kawar da kai sannan ta bashi amsa
‘Na ci nawa.’
‘Yau babu jira kenan aka yi min solo.’
Tayi murmushin yake
‘Ban tabbatar zaka zo ba har sai da na ganka yanzu, shi yasa dana idar da sallar isha’i baka shigo ba na ci abincin.’
Duk yanda ya kai ga jun tausayin kansa sai da yaji tausayinta fiye da yanda yake tausayin kansa, da kyar ya danne kwallar da ta taso masa saboda baya so ya kara raunana mata zuciya. Ya mika hannunsa ya kama hannunta wanda yake ajiye a kan tebur din, ya sumbaci hannun ya rike yana cigaba da shafawa. Yace
‘Ban san da bakin da zan baki hakuri ba Aisha, ban san kuma irin hakurin da zan baki ba. An cutar dake kuma an cutar damu gaba daya.’
Ya sake sumbatar hannun.
Tace
‘Ka ci abincin kada ya huce.’
Ya saka hannunsa na dama yana cin abincin yayinda hannunsa na hagu yake rike da hannunta na dama, yana cin abincin yana kallon fuskarta.
Bayan ya gama cin abincin sai da ya tayata ta kwashe kwanukan sanna ya jata suka zauna a kan doguwar kujera falo.
Duk da TV a kashe take amma ita Aisha da ta zauna gaba take kallo shi kuma da ya tashi sai ya zauna yana fuskantar Aishan. Ya kamo hannunta ya sumbata, ya juyo da fuskarta wadda ba shi take kallo ba ya sumbaci lebenta. Ta bude baki zata yi magana ya rigata
‘Aisha. Don Allah yau kada kiyi min fushi please.’
Ta yi murmushi ta share kwallar da ta taru a kwarmin idonta. Ya kara matsawa kusa da ita yana kokarin janyota jikinsa gaba daya. Ta dage sannan tace
‘Amira tana nan kada fa ta fito.’
Ya cije lebensa ya dan ja baya, ya dubeta yace
‘Tashi mu koma daki to.’
Ya mike ya jata itama ta mike tsaye.
Yana rike da ita ya zagaya ya kashe fitilun falon domin gani yakeyi idan ya saketa zata iya tafiya dakinta tace fushi take yi dashi. Sai da ya kashe fitilun tas sannan ya jata suka shige daki.
Duk yanda ta so ta dage a wannan dare Abban Sadik bai bata dama ba, haka suka kwana suna biyan bashin juna cikin walwala.
………..
Yanda Aisha da Yusuf suka kwana suna walwala haka Zahra ta kwana cikin kunci da lissafin yanda zata yi da Aisha; domin ba zata taba bar mata Abban Sadik ba.
Gaba daya tunaninta ya kare, duk iya satar bacci haka ya kyaleta sai bayan asuba sannan ta sami baccin.
__
Cikin walwala suka wayi gari Lahadi, sai wajen karfe goma sannan suka gama breakfast a lokacin ya fice don ya dubo Zahra da yaran. Yanda ya barta jiya haka ya sameta yau, ya riga ya san abinda yake damunta kishi ne na rashin tunani ta dorawa kanta don haka ba tare da bata lokaci ba suka gaisa ya fito ya bar mata gidan tunda yara duk suna tahfiz.
Tana so ta yarda bai fahimci wanda ya raba shi da Aisha ba amma kuma tana mamakin yanda jiya zuwa yau yake nuna mata wani hali na ko in kula. Amma dai ta san dole ta saurara yanzu zuwa lokacin da zata sami kanta.
…………..
Bayan azahar Abba ya dauki Aisha suka tafi gidan Hajiya, ya riga ya san yayi musu laifi don haka suka je ya sami Hajiya da Anti Uwani ya basu hakuri. Daga nan suka wuce gidan Yaya Abubakar shima ya sameshi yayi ta bashi hakuri. Sai bayan la’asar sannan suka dawo gidan zuwa lokacin har Amira ta dora abincin dare.
Bayan sallar isha’I tana kicin tana jiyoshi yana waya da Jibrin.
Bayan ta shigo falon yake tambayarta rasit na biyan kudin hayar gidan, ta dauko daga daki ta bashi. Kafin su kwanta bacci taji alert ya tura mata kudin hayar da ta biya harda Karin dubu dari. Ta tambayeshi to karin na menene, yace
‘Duk tsawo lokacin nan ke kike ciyar da kanki kina yin komai wanda ba haka ya kamata ba ai kinga dole na biya bashi ko. Na san abinda kika ci ma ya fi dubu dari in Sha Allahu idan aka kwana biyu zan ciko sauran don na san matata akwai cinye buhun shinkafa.’
Tayi dariya.
Babu yanda bata yi da shi a kan ba sai ya sake turowa ba amma ko sauraronta bai yi ba, suka cigaba da hirarasu.
Da sati ya zagayo kuma haka ya sake daukan Aisha suka zaga danginsa.
Yanda Hajiya ta saba karbarta cikin halin ko in kula haka ta yi mata, shi kanshi Abban sai da yaji babu dadi. Ya kara jin haushi Zahra saboda wannan matsalar da ta kirkiro a lokacin da Hajiyan ta fara haduwa da Aisha itace dalilin wannan kiyayyar; sannan kuma yanzu ga ciwo ga rikicin tsufa.
Sai da suka tsaya a gidan Yaya Bello sannan suka wuce gida.
Haka rayuwarsu ta cigaba cikin walwala da adduoi.
Ita kuwa Zahra tun tana saka rai Abba zai tutsiyeta har ta sakankance bai gane itace tayi musu asiri ba. Ta cigaba da kokarin tara kudi tunda tana son aje mata wajen boka.
Shi kuma Abban ya kyaleta ne saboda cikin da yake jikinta da kuma tunanin da yakeyi a kan makomar yaransa idan yace zai yi rigima da Zahra; yaran da daman yana ganin kamar akwai gibi a tarbiyyarsu. Yana sane da yanda idan dai tana fushi da shi toh gaba daya yaran suma sai su daina kulashi sai Rukayya da Sumayya ne kawai suke kulashi ba zai ga walwalarsu ba har sai uwarsu ta daina fushi da shi. To idan ya saketa yanzu yana jin yaki za a koma yi tsakaninshi da ‘yayanshi wanda shi din ba haka yake so ba. Don haka ya kayaleta take cigaba da rayuwarta kamar bata yi masa laifi ba, musamman da yake Malam Audurahmanu ya sanar da shi idan dai ya rike addu’ar da ya bashi to lallai babu sihirin da zai sake tasiri a kansa.
__
Lokaci ya ja don haka kowa ya koma harkarsa kamar yanda aka saba.
Ranar Talata da yamma Zahra ta shirya ta tafi wajen scanning domin yanzu cikinta ya kai kusan wata bakwai tunda yana motsi sosai har tana ganin motsinsa. So take a kara tabbatar mata da cewa lallai namiji ne domin bata so abinda ya faru a haihuwar Sumayya ya sake faruwa. Kamar yanda ta zata haka aka tabbatar mata da cewa lallai namiji ne domin babu ma yanda za ayi ya zama mace.
Cikin walwala ta dawo gida, washegari kuma ta shirya ta tafi asibitin Nassarawa awo. Aka duba ta sosai awajen awon, likita ya tabbatar mata da lafiyarta da kuma lafiyar jaririnta. Don haka ta dawo gida cikin walwala bayan an rubuta mata appointment ta dawo bayan sati hudu domin sake yin awo.
---------
Ranar Alhamis ce wadda ta kama saura kwana biyar Zahra ta koma awo.
Yau din tunda gari ya waye take jin jikinta babu dadi, gashi cikin yayi mata nauyi sosai da kyar take jan kafa sannan ga mararta tana ciwo kadan-kadan. Nan da nan ta gama abinda takeyi ta koma ta kwanta don bata ma jin kwari.