Sashe 74
Uwar Sadiku Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Abban ne a kan gaba har suka hau benen da dakin da aka kwantar da Zahran yake, suna biye da shi sai da aka zo bakin kofa saboda ya san Rahma tana ciki ya ja baya yace duka su shige. Ummi ce ta bude kofar suka shige gaba daya.
Rahma da Yaya Murja suna zaune a kan tabarma daga gefe yayinda ita kuma take gefe guda yayinda ita kuma Zahran take kwance a kan gadon tana danna waya.
A hankali ta tashi ta gyara zamanta yayinda suka karasa suka tsattsaya a gefen gadon, ta dan muskuta Yusra ta dauki Sumayya ta dora mata a gefen gadon. Aisha ta karasa shiga dakin da sallama Abban yana biye da ita. Ta wuce ta zauna can daga kusa da Yaya Murja yayinda shi kuma Abban ya ja kujerar da take ajiye daga daya gefen ya zauna.
Ya gaida Yaya Murja da Rahma yayi musu ya mai jiki sannan ya mike ya karasa wajen Zahran ya tsaya a bayan yaran.
Itama Aishan suka gaisa da Rahma da Yaya Murja tayi musu yaai jiki, ta mikawa Yaya Murja kwandunan da suka zo dasu tayi musu bayani. Suka dan cigaba da hira Yaya Murja tana tamabayarta mutanen gidansu.
Bayan ya gama tambayar Zahra jikin nata ya juya yayi wa Yaya Murja sallama ya dubi Aisha yace
’15 minutes, ina jiranku a mota.’
Ya mika mata hannu kamar mai karbar wani abu, ta zura hannu a jakarta ta dauko mukullin motar ta saka masa a hannunsa ya juya ya fice bayan yayi wa su Yaya Murja sallama.
Bayan ya fita Aisha ta mike ta matsa kusa da gadon suka gaisa da Zahran sannan ta yi mata jaje tare da ya jiki. Da kyar take amsa mata tana ta faman harararta don haka itama ba tare da bata lokaci ba ta koma ta zauna.
Suna hira jefi-jefi da su Rahma tana kula da agogon wayarta, minti goma sha biyar suna cika ta yiwa Yaya Murja sallama ta dubi yaran tace
‘Rukayya ku zo muje 15 minutes din yayi kada mu bar Abba yana jira’
Ta fice.
Jimawa kadan yaran suka fice bayan Yaya Murja ta tasa keyarsu.
Su Zahra basu dade da fita ba Amina ta shigo, bayan sun gaisa Yaya Murja tayi musu sallama ta tashi yayinda Rahma ta bita don tayi mata rakiya.
Amina ta dubeta tace
‘Na ga mutuniyarki sai wani sheki takeyi tana ta yiwa miji iyayi, na ga ma itace take tuka motar saboda kauna.’
Ta ja tsaki
‘Hmm! Haka Yusra take gaya min ana ta soyayya a hanya. Ki barni kawai Amina! Yarinyar nan ta raina ni wallahi. Na tabbatar da hannunta a wannan haihuwar da nayi babu rai shine ta zo ta nuna min ta kwaci mijinta. Wallahi Amina sai nayi maganin yarinyar nan.’
‘Hmmm! Kinga dai yanzu ki kwantar da hankalinki ki sami lafiya, sai ki san yanda zakiyi ki tattaro kan kudi don kinga akwai wani malami da za a hadani da shi kwanan nan kuma an ce aikinsa babu wasa. Kin san ina ta fama da Abban Asiya ina so na dauki hutun aiki na bishi Abuja yana ta faman gocewa, zargin da nakeyi wata ya ajiye a can shi yasa ko da tsiya-tsiya sai na je.’
Suka cigaba da hirarrakinsu suna shawarar yanda za a yi a sami kudi aje wajen Malami, daga baya Rahma ta dawo don haka suka canza hirar.
___
Kwana daya Zahra ta kara a asibiti aka sallameta, suna dawowa gida Rahma tayi musu sallama ta koma gidansu.
Duk wani ban baki da ban hakuri likitocin sun yiwa Zahra shi domin likita ya tabbatar mata idan ta cigaba da zama da damuwa zata haifarwa kanta da hawan jini na din-din-din, sai dai ita bata ga yanda za ayi ta kwantar da hankalinta ba. Duk wata kulawa Abba yana bata sai dai har yanzu tana ji a jikinta cewa ya san abubuwan da ta shirya kallonta kawai yakeyi.
A hankali tana kara samun lafiya tana cigaba da tunanin hanyar da zata bi ta sami kudi. Bata son ta siyar da babbar saitin gwal dinta amma dai ta fara tunanin sayar da na yaran. Bata son ta tambayi Abba kudi domin bata ga fuska ba duk da komai yana yi mata kamar yanda ya saba sai dai kawai ita din ta kasa sakewa.
Haka dai rayuwarsu ta cigaba.
---------
Kwanci tashi har an kai wajen wata uku da haihuwar da Zahra tayi babu rai, basu samu sun je wajen boka ba saboda har yanzu mahaifiyar Amina a kwance take; domin kusan za a iya cewa ta zama sai dai a kwantar a tayar. Don haka babu halin Amina tayi nisa musamman da yake tana matukar kaunar mahaifiyar tata. Haka ta hakura tana kallo mijin nata yana can Abuja ga shi Asiya tana kawo mata rahotannin cewa yana tare da matan banza a can din amma babu yanda zata yi don ya ma hanata zuwa Abujan gaba daya.
Hankalin Abba ya dawo jikinsa don haka ya nemi kudi ya sake fara business din sa; sai dai wannan karon duk wani abu da zai yi na harkar business din sai idan yana gidan Aisha ne yake yi domin ko wayar abokan kasuwancin nasa baya amsawa idan yana gidan Zahra.
Haka kowa ya cigaba da rayuwarsa.
__
Tun tuni aka samarwa Saddiku da Yusra admission a jami’ar Maryam Abacha American University wato MAAUN; Yusra tana karantar Business Administration yayinda Saddiku yake karantar Accounting. Da yake kwanci tashi babu wahala gashi a halin yanzu har suna zana jarrabawar zango na farko wato zasu gama level 1 su shiga level 2.
Tunda suka fara jarrabawa Saddiku yake gayawa Mommy ta karbar masa kudi a wajen Abba naira dubu hamsin zasu hada suyi end of session party. Sai kaucewa zancen takeyi saboda ta san yanzu bata da dama a wajen Abban yayin da shi kuma Saddikun yake sake dagewa da yi mata naci. Haka dole ya sakata tayi masa alkawarin ko da Abban bai bashi ba ita zata bashi ko da bai kai dubu hamsin din ba.
Kudaden da take hadawa domin suje wajen boka su kadai ne a account dinta domin ta hada kusan dubu dari biyu; garwar motarta da akayi accident wadda take ajiye a tsakar gida ita take jira ta sami mai siya ta hada kudin sai suje.
Wanna magiyar da Saddiku yake mata a kan kudin party ma ya kara mata kaimi wajen ganin ta dawo da hankalin Abban kansu, bata son ganin yaranta a cikin damuwa musamman Saddikun.
---------
A dakinta ya sameta tana zaune a kan dadduma ta idar da sallar isha’i, bayan ta amsa sallamarsa ya wuce ya zauna a gabanta kamar mai daukar karatu. Ta dan kare masa kallo; zuciyarta tana so ta yarda lallai Saddiku yana shaye shaye; to amma bata ga lebensa da hannayensa suna yin baki ba irin na 'yan wiwi. Abinda bata gane ba shine shi din ba hayaki yake sha ba kwayoyi yake sha masu tsada da kuma dauke hankali nan take. Ya kwantar da kai yace
‘Mommy baki turo min 50k din ba, gobe fa zamuyi final paper kuma ranar Saturday zamuyi party din.’
Tunda ya zauna dama ta san abinda zai tambaya kenan, ta jijjiga kai tana murmushi
‘Ku yanzu ba za ma ku iya tsayawa ku ga result ba kafin kuyi party din idan fa ba ku ci jarrabawar ba.’
‘Haba Mommy, ai duk mun ci. Kin san a ajin wasu foreigners ne don haka ana gama exam kowa zai tafi gida shi yasa zamuyi party din. Kusan kowa ma ya biya mu uku ake jira. Don Allah Mommy ki karba min kudin nan kinga ina cikin organizers fa.’
Suka yi shiru na dan lokaci, jimawa kadan tace
‘Abbanku yace bashi da kudi kuma ka san idan nace masa party zakuyi ma ba zai bari kaje ba, amma idan kana son 30k ni zan turo maka zuwa gobe idan kuma tayi kadan to sai dai kai kaje ka tambayi Abban.’
Da sauri yace
‘A’a Mommy please ki turo 30k din kawai.’
Suka dan taba hira yayi mata sallama ya fice.
Yana fatan idan ta bashi dubu talatin din daga baya sai ya san yanda zai yi ya takureta ta kara masa ashirin din.
Party suka shirya su uku shi da abokansa, ‘yan ajinsu na Jami’a ma basu san da wannan party din ba. Ya riga yayi alkawarin dubu dari biyu zai bayar gudummuwar party din. Ya riga ya yagi mafi yawan kudin a wajen Abban ta hanyar karyar abubuwan da aka ce su saya a makarantar, a halin yanzu dubu hamsin din kawai yake bukata ya gama hada kudin su je suyi party dinsu.
………..
Babu yanda ta iya haka ta turawa Saddiku dubu talatin daga kudin da take ta faman tarawa, sai dai duk nacinsa ta ki ta kara masa wasu kudin; ta dai gaya masa ya samo makanike ya sayi gawar motarta da yayi accident idan an biyata sai ta kara masa.
Haka ya samo har mutum biyu, sai dai babu wanda ya taya motar a kan dubu dari ma. Domin duk cewa sukeyi ba zata moru ba don har injinta ma ya tashi daga aiki. Haka ta hakura ta sayarwa da na karshen a kan naira dubu sittin da biyar. Wanda a hakan ma yace sai dai su bashi sati biyu zai kawo kudin sai ya dauki motar.
Sai bayan ya tafi Saddiku ya bishi ba da sanin Mommy ba ya karbe naira dubu goma sha biyar a kan ya kai cikon ya dauko motar.
…………..
Tun bayan la’asar ya shirya yayiwa Mommy sallama. Ya dauki motarta ya tafi party; motar da tana kallo yanzu ta zama ta Saddiku tunda da tana kokarin ta sa Abba ya saya masa tashi motar amma yanzu ta san bata da wannan damar.
Kamar yanda Abba ya saba bayan magriba ya dawo gidan. A gidan Aisha zai kwana don haka gidan Zahra ya sauka; bayan ya huta suka dan taba hira ita da shi da yaran. Sai da ya dawo daga sallar isha’i sannan yayi mata sallama ya tafi. Kafin ya fita kuma ya sanar da ita idan goman dare tayi Saddiku bai dawo ba tayi masa waya.
Rahma da Yaya Murja suna zaune a kan tabarma daga gefe yayinda ita kuma take gefe guda yayinda ita kuma Zahran take kwance a kan gadon tana danna waya.
A hankali ta tashi ta gyara zamanta yayinda suka karasa suka tsattsaya a gefen gadon, ta dan muskuta Yusra ta dauki Sumayya ta dora mata a gefen gadon. Aisha ta karasa shiga dakin da sallama Abban yana biye da ita. Ta wuce ta zauna can daga kusa da Yaya Murja yayinda shi kuma Abban ya ja kujerar da take ajiye daga daya gefen ya zauna.
Ya gaida Yaya Murja da Rahma yayi musu ya mai jiki sannan ya mike ya karasa wajen Zahran ya tsaya a bayan yaran.
Itama Aishan suka gaisa da Rahma da Yaya Murja tayi musu yaai jiki, ta mikawa Yaya Murja kwandunan da suka zo dasu tayi musu bayani. Suka dan cigaba da hira Yaya Murja tana tamabayarta mutanen gidansu.
Bayan ya gama tambayar Zahra jikin nata ya juya yayi wa Yaya Murja sallama ya dubi Aisha yace
’15 minutes, ina jiranku a mota.’
Ya mika mata hannu kamar mai karbar wani abu, ta zura hannu a jakarta ta dauko mukullin motar ta saka masa a hannunsa ya juya ya fice bayan yayi wa su Yaya Murja sallama.
Bayan ya fita Aisha ta mike ta matsa kusa da gadon suka gaisa da Zahran sannan ta yi mata jaje tare da ya jiki. Da kyar take amsa mata tana ta faman harararta don haka itama ba tare da bata lokaci ba ta koma ta zauna.
Suna hira jefi-jefi da su Rahma tana kula da agogon wayarta, minti goma sha biyar suna cika ta yiwa Yaya Murja sallama ta dubi yaran tace
‘Rukayya ku zo muje 15 minutes din yayi kada mu bar Abba yana jira’
Ta fice.
Jimawa kadan yaran suka fice bayan Yaya Murja ta tasa keyarsu.
Su Zahra basu dade da fita ba Amina ta shigo, bayan sun gaisa Yaya Murja tayi musu sallama ta tashi yayinda Rahma ta bita don tayi mata rakiya.
Amina ta dubeta tace
‘Na ga mutuniyarki sai wani sheki takeyi tana ta yiwa miji iyayi, na ga ma itace take tuka motar saboda kauna.’
Ta ja tsaki
‘Hmm! Haka Yusra take gaya min ana ta soyayya a hanya. Ki barni kawai Amina! Yarinyar nan ta raina ni wallahi. Na tabbatar da hannunta a wannan haihuwar da nayi babu rai shine ta zo ta nuna min ta kwaci mijinta. Wallahi Amina sai nayi maganin yarinyar nan.’
‘Hmmm! Kinga dai yanzu ki kwantar da hankalinki ki sami lafiya, sai ki san yanda zakiyi ki tattaro kan kudi don kinga akwai wani malami da za a hadani da shi kwanan nan kuma an ce aikinsa babu wasa. Kin san ina ta fama da Abban Asiya ina so na dauki hutun aiki na bishi Abuja yana ta faman gocewa, zargin da nakeyi wata ya ajiye a can shi yasa ko da tsiya-tsiya sai na je.’
Suka cigaba da hirarrakinsu suna shawarar yanda za a yi a sami kudi aje wajen Malami, daga baya Rahma ta dawo don haka suka canza hirar.
___
Kwana daya Zahra ta kara a asibiti aka sallameta, suna dawowa gida Rahma tayi musu sallama ta koma gidansu.
Duk wani ban baki da ban hakuri likitocin sun yiwa Zahra shi domin likita ya tabbatar mata idan ta cigaba da zama da damuwa zata haifarwa kanta da hawan jini na din-din-din, sai dai ita bata ga yanda za ayi ta kwantar da hankalinta ba. Duk wata kulawa Abba yana bata sai dai har yanzu tana ji a jikinta cewa ya san abubuwan da ta shirya kallonta kawai yakeyi.
A hankali tana kara samun lafiya tana cigaba da tunanin hanyar da zata bi ta sami kudi. Bata son ta siyar da babbar saitin gwal dinta amma dai ta fara tunanin sayar da na yaran. Bata son ta tambayi Abba kudi domin bata ga fuska ba duk da komai yana yi mata kamar yanda ya saba sai dai kawai ita din ta kasa sakewa.
Haka dai rayuwarsu ta cigaba.
---------
Kwanci tashi har an kai wajen wata uku da haihuwar da Zahra tayi babu rai, basu samu sun je wajen boka ba saboda har yanzu mahaifiyar Amina a kwance take; domin kusan za a iya cewa ta zama sai dai a kwantar a tayar. Don haka babu halin Amina tayi nisa musamman da yake tana matukar kaunar mahaifiyar tata. Haka ta hakura tana kallo mijin nata yana can Abuja ga shi Asiya tana kawo mata rahotannin cewa yana tare da matan banza a can din amma babu yanda zata yi don ya ma hanata zuwa Abujan gaba daya.
Hankalin Abba ya dawo jikinsa don haka ya nemi kudi ya sake fara business din sa; sai dai wannan karon duk wani abu da zai yi na harkar business din sai idan yana gidan Aisha ne yake yi domin ko wayar abokan kasuwancin nasa baya amsawa idan yana gidan Zahra.
Haka kowa ya cigaba da rayuwarsa.
__
Tun tuni aka samarwa Saddiku da Yusra admission a jami’ar Maryam Abacha American University wato MAAUN; Yusra tana karantar Business Administration yayinda Saddiku yake karantar Accounting. Da yake kwanci tashi babu wahala gashi a halin yanzu har suna zana jarrabawar zango na farko wato zasu gama level 1 su shiga level 2.
Tunda suka fara jarrabawa Saddiku yake gayawa Mommy ta karbar masa kudi a wajen Abba naira dubu hamsin zasu hada suyi end of session party. Sai kaucewa zancen takeyi saboda ta san yanzu bata da dama a wajen Abban yayin da shi kuma Saddikun yake sake dagewa da yi mata naci. Haka dole ya sakata tayi masa alkawarin ko da Abban bai bashi ba ita zata bashi ko da bai kai dubu hamsin din ba.
Kudaden da take hadawa domin suje wajen boka su kadai ne a account dinta domin ta hada kusan dubu dari biyu; garwar motarta da akayi accident wadda take ajiye a tsakar gida ita take jira ta sami mai siya ta hada kudin sai suje.
Wanna magiyar da Saddiku yake mata a kan kudin party ma ya kara mata kaimi wajen ganin ta dawo da hankalin Abban kansu, bata son ganin yaranta a cikin damuwa musamman Saddikun.
---------
A dakinta ya sameta tana zaune a kan dadduma ta idar da sallar isha’i, bayan ta amsa sallamarsa ya wuce ya zauna a gabanta kamar mai daukar karatu. Ta dan kare masa kallo; zuciyarta tana so ta yarda lallai Saddiku yana shaye shaye; to amma bata ga lebensa da hannayensa suna yin baki ba irin na 'yan wiwi. Abinda bata gane ba shine shi din ba hayaki yake sha ba kwayoyi yake sha masu tsada da kuma dauke hankali nan take. Ya kwantar da kai yace
‘Mommy baki turo min 50k din ba, gobe fa zamuyi final paper kuma ranar Saturday zamuyi party din.’
Tunda ya zauna dama ta san abinda zai tambaya kenan, ta jijjiga kai tana murmushi
‘Ku yanzu ba za ma ku iya tsayawa ku ga result ba kafin kuyi party din idan fa ba ku ci jarrabawar ba.’
‘Haba Mommy, ai duk mun ci. Kin san a ajin wasu foreigners ne don haka ana gama exam kowa zai tafi gida shi yasa zamuyi party din. Kusan kowa ma ya biya mu uku ake jira. Don Allah Mommy ki karba min kudin nan kinga ina cikin organizers fa.’
Suka yi shiru na dan lokaci, jimawa kadan tace
‘Abbanku yace bashi da kudi kuma ka san idan nace masa party zakuyi ma ba zai bari kaje ba, amma idan kana son 30k ni zan turo maka zuwa gobe idan kuma tayi kadan to sai dai kai kaje ka tambayi Abban.’
Da sauri yace
‘A’a Mommy please ki turo 30k din kawai.’
Suka dan taba hira yayi mata sallama ya fice.
Yana fatan idan ta bashi dubu talatin din daga baya sai ya san yanda zai yi ya takureta ta kara masa ashirin din.
Party suka shirya su uku shi da abokansa, ‘yan ajinsu na Jami’a ma basu san da wannan party din ba. Ya riga yayi alkawarin dubu dari biyu zai bayar gudummuwar party din. Ya riga ya yagi mafi yawan kudin a wajen Abban ta hanyar karyar abubuwan da aka ce su saya a makarantar, a halin yanzu dubu hamsin din kawai yake bukata ya gama hada kudin su je suyi party dinsu.
………..
Babu yanda ta iya haka ta turawa Saddiku dubu talatin daga kudin da take ta faman tarawa, sai dai duk nacinsa ta ki ta kara masa wasu kudin; ta dai gaya masa ya samo makanike ya sayi gawar motarta da yayi accident idan an biyata sai ta kara masa.
Haka ya samo har mutum biyu, sai dai babu wanda ya taya motar a kan dubu dari ma. Domin duk cewa sukeyi ba zata moru ba don har injinta ma ya tashi daga aiki. Haka ta hakura ta sayarwa da na karshen a kan naira dubu sittin da biyar. Wanda a hakan ma yace sai dai su bashi sati biyu zai kawo kudin sai ya dauki motar.
Sai bayan ya tafi Saddiku ya bishi ba da sanin Mommy ba ya karbe naira dubu goma sha biyar a kan ya kai cikon ya dauko motar.
…………..
Tun bayan la’asar ya shirya yayiwa Mommy sallama. Ya dauki motarta ya tafi party; motar da tana kallo yanzu ta zama ta Saddiku tunda da tana kokarin ta sa Abba ya saya masa tashi motar amma yanzu ta san bata da wannan damar.
Kamar yanda Abba ya saba bayan magriba ya dawo gidan. A gidan Aisha zai kwana don haka gidan Zahra ya sauka; bayan ya huta suka dan taba hira ita da shi da yaran. Sai da ya dawo daga sallar isha’i sannan yayi mata sallama ya tafi. Kafin ya fita kuma ya sanar da ita idan goman dare tayi Saddiku bai dawo ba tayi masa waya.