Sashe 23
Uwar Sadiku Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Saida ya gama duk abinda yakeyi a cikin gidan sannan ya shiga dakinta yi mata sallama. Ita kadai ce a dakin tana zaune a kan gado domin baby tana bayan Rahma kuma suna falon kasa.
Ya zauna a dai-dai kafarta yace
‘Sannu maijego. Ya kike? Ya Baby? Babu dai wata matsala ko?’
Ta jijjiga kai
‘Ko daya babu.’
‘To ni zan wuce, Sadiku zai rufe muku kofa sai ya kawo miki mukullan.’
Ta dubi flask din da yake kan durowar gefen gado tana gyara zama tace
‘Bari na zuba maka shayi gashi yanzu na gama sha nima.’
Ya jijjiga kai
‘Ai yau bazan sha shayin nan ba don a koshe nake, ki ajiye flask dinki kiyi ta tsiyaya kina sha a hankali.’
Tayi ‘yar dariya
‘Kai haba, ai kuwa shayin irin wanda kake so ne.’
‘Ki daina tempting dina, yau a koshe nake kin san daga wajen liman nake a nan muka zauna aka bankare mana kaji da gurasa muka ci. Abincin daren ma da kyar zai sami shiga yau.’
Duk wayonta haka ta hakura ya fita ba tare da ya ko kalli flask din shayin nan ba, yayi mata sallama ya wuce wajen Aisha.
Yana fita ta fara nadama, ta san ba zai iya gane ta saka wani abu a shayin ba to amma me yasa ya ki sha? Gashi sai da ya bari ta barwa Aisha kwananta sannan ya wani ki shan shayin. Saida tayi kwalla saboda takaici; tayiwa kanta alkawarin zasu hadu gobe.
…………..
Da mukullinsa ya bude gidan kamar yanda ya saba ya shiga, tana falo tana karatun littafi da shayi kofi daya a gabanta tana sha. Bayan tayi masa sannu da zuwa sun gaisa ya dubeta yace
‘Ina abincinna yunwa fa nake ji.’
Ta kalleshi tana dariya
‘A’a, jegon har ya fara tabaka ne? Yau fa kwanan Mommy ne ko ka manta ne?’
‘Babu wani jego ai haka akeyi, tunda tana jego ai ke zaki karbi kwanan zuwa tayi arba’in don kema idan kika haihu haka zata yi. Don haka ki shirya ina nan har arba’in.’
Tayi dariya
‘Gaskiya dai ka koma, ni ban karbi wannan kwanan ba. Kawai saboda ta haihu sai kuma ka barsu ita kadai da Baby, ina laifi idan ka kwana a can din. Nifa idan na haihu babu wani arba’in duk da babu abinda za ayi amma ba zan yafe kwanan ba, ka kwana a nan din dai like just be there ba wai ka tafi ka barni da baby ba wai kai ka gama aikinka, tab!’
Kallonta yake da mamaki
‘To yanzu ya za kiyi dani.’
‘Abinci zan baka kaci ka koshi ka koma can in an kwana biyu ka dawo.’
Duk yanda ya so ya tsara Aisha ta karbi kwanan nan ki tayi, haka ta dafa masa taliya ya ci ya koshi ya sha shayi sannan tayi masa sallama ta rufe kofarta ya koma wajen Zahra.
…….
Ko da taji shigowarsa luf tayi kamar mai bacci domin tazata wani abun ya dawo dauka.
Sai da ya shiga dakinsa ya shirya sannan ya kirawota a waya domin da baiga Rahma ba yayi tunanin ko a dakinta zasu kwana. Ta zata ya riga ya fita don haka ta dauka tana mamaki.
‘Ina nan fa, a nan zan kwana.’
‘A’a, me ya faru kuma ka fasa?’
Yayi ‘yar dariya yace
‘Kanwar taki bata karbi kwanan ba.’
Nan yayi mata bayani kamar yanda Aishan tayi masa, suka ajiye waya tunda dama kiranta kawai yayi don ta san a gidan zai kwana.
Har bacci ya kwasheta tana tunanin wauta irin ta Aisha, ya za ayi abata miji kwana arba’in tace a barshi? Ko yanzu ma da akayi haka ta san idan dai Aishan ta haihu ko da tsiya-tsiya sai an bata kwana arba’in din nan tunda ita haka taga ana yi.
……….
Kwanansu daya da fitowa daga asibiti Aisha taje barka da kayan barkarta da ta tanada cikin leda; kayan baby ne masu kyau da tsada. Sai da ta tabbatar yana gidan ta shiga domin tuni ta sha jinin jikinta da matar nan.
Bayan la’asar ne suna zaune ita da shi a falonsa da Baby a hannunsa Rukayya ta shiga falon da sallama ta sanar da Mommy zuwan Anti Aishan. Har ta mike zata tashi ya cewa Rukayyan ta hawo da Antin nan mana. Kafin tace wani abu Rukayyan ta fice, bata dade ba suka dawo tana dauke da ledar yayinda Aisha take biye da ita.
Babu laifi suka gaisa da Zahran da yake a gabansa me, aka mika mata Baby ta dauka ta sa albarka. Suka dan taba hira gaba daya har Abban Sadik din, ta turawa Zahra ledar tace
‘Ga wannan babu yawa, Allah ya rayata ya kara lafiya.’
Tare suka amsa da Zahran da Abban Sadik.
Tayi musu sallama ta sauko ta koma gida, zuciyarta fari fes saboda yanda tayi barkarta a gabansa tunda ta san Zahran bata yi mata komai a gabansa.
……..
Saida aka kwana biyar sannan ya sanar da su sunan yarinya, ya saka mata Sumayya. Da kyar Aisha ta daure ta sanar da ‘yan uwanta sunan inda ta nemi Yaya Zuwaira da Yaya Zainab su zo amma kada su taho da yara don bata son fitna.
An ci burin wannan sunan kuma an shirya taro inda aka gayyato mutane da yawa, dangin Abban Sadik din ma haka suka zo da yawansu saboda Yaya Saratu aka bawa goronsu na gayyatar ta tabbatar ta hado kansu sannan suka taho.
Aisha ta riga ta tambaya ko akwai aikin da zata tayasu amma Zahra tace mata babu domin komai bayarwa za ayi a yiwo daga waje, don haka ranar sunan ba tayi shirin tafiya gidan da wuri ba. A tunaninta ma ‘yanuwan Abban zasuyi ta shigowa gidan nata amma har shadaya babu wanda ya shigo. Batayi mamaki ba domin dama ta san babu wanda yake kaunarta a danginsa, tun lokacin da suka je da Zahra gaba daya suka ki sakewa da ita. Duk da sun je ita da Abban sun bawa Hajiyan hakuri amma har kawo yanzu basu saki jiki da ita ba.
Sai wajen sha biyu saura sannan Zuwaira da Zainab suka iso, ba tare da bata lokaci ba suka shirya tare da Aishan suka wuce gidan sunan.
Tun daga bakin gate Rukayya ta hangosu, da gudu ta karasa ta kama hannun Aishan tana yi mata sannu da zuwa, ta gaida su Yaya Zuwaira sannan ta wuce gaba suka bita a baya.
Tun daga falon duk ‘yan uwan da Rukayya ta san basu taba haduwa da Aishan ba sai tace musu
‘Ga amaryar Abbanmu.’
Haka har suka wuce falon sama inda Mommy take, su Yaya Saratu ma duk suna wajen anata hira.
Suka karasa kusa da Mommy Aisha ta zauna kusa da ita su Yaya Zainab din ma suka zauna.
Gaisheta sukeyi suna mata barka amma da kyar take amsawa tana wani dauke kai.
Suka juya wajen Yaya Saratu wadda itama da kyar take amsa gaisuwar.
Yaya Murja ce kawai ta sauraresu da girmamawa, ragowar mutanen da suke wajen suka cigaba da hirarrakinsu babu wanda yake bi ta kansu. Don haka suma suka gyara zama suka fara kus-kus dinsu su kadai.
Basu dade da zama ba wata dattijuwar mata ta shigo, tun daga kafar bene take zabga kirari tana guda
‘Uwar gida Uwar Saddiku, kinyi taki kinyi ta raggo. Uwargidan Yusuf maki gani ido ya makance. Yanda duk kika dama haka za a sha Uwargida ta Uban Sadiku ko mahassada sun ki. Haihuwa kyautar Allah, ba rawar kai bace ba iyawa bace, ke Allah ya zaba uwar SADIKU matar Yusufa….’
Yaya Saratu ce ta fara mikewa ta lika mata naira dubu tana fadin
‘Kin min daidai, babu karya a cikin zancenki uwar Sadiki taci dubu sai ceto.’
Abun nata ya fara yawa kuma duk wanda ya san Aisha kishiyarta ce ya san da ita akeyi. Yaya Murja ce ta mike ta dauki kudi a jakarta ta ja matar sukayi kasa ta sallameta.
Bata dade da fita ba su Aisha suka mike Yaya Zuwaira ta karasa kusa da Zahra ta ajiye mata kudi naira dubu goma tace a siyawa Baby sabulu. Sukayi musu sallama suka fito.
A gidan Aishan suka karasa wuninsu suna jajanta mata zama da wannan matar don ko su kansu sun kula da yanda ita da ‘yan uwan Yusuf din basa ko kaunar Aisha.
Tun tuni Aisha ta san dangin Yusuf basa sonta amma sai yau ta kara tabbatarwa, don zata iya cewa a ‘yan uwansa matar Yaya Bello ce kawai ta saurareta sai kuma Innani wadda ita din ‘yar uwar Hajiya ce.
Haka aka gama taro aka watse, abincin sunan nan kuwa Aisha ko kalarsa bata gani ba domin lokacin da suka fito daga gidan ba a fara rabo ba kuma da aka fara babu wanda ma ya tuna da ita duk da an kaiwa makota abincin gida-gida.
…...
Wajen sati biyu da gama taron suna sai Yusra ta tsiri shiga gidan Aisha, haka kawai da rana ko da daddare musamman idan Abbansu yana gidan sai Yusra ta shigo. Wata rana ita kadai take shiga wata rana kuma ita da kannenta. Hatta Rukayya saida tayi mamaki saboda Yusra bata taba shiga gidanba amma sai gashi yanzu kusan duk ranar da Abbansu yake gidan sai ta shiga.
Amma da zarar Abban ya zauna an kawo abinci aka ce ta zo ta ci sai taki, tace ita ta koshi. Sai dai kawai su zauna a falo suna kallon TV.
Yau shinkafa da miya Aisha ta dafa ta hada salad ga kuma zobo. Tare suka zauna da Abban suka fara cin abincin, sai dai da kyar ta hadiye lomar farko saboda dandanon miyar bai yi ba. Ta ajiye cokalin tana jira taji mai zai ce.
Shi din ma da kyar ya hadiye wanda ya saka a bakinsa ya dubeta yace
‘Yau me ya sami miyar ne?’
Tace
‘Wallahi nima na ji, na zata ma bakina ne.’
Kamshin miyar ya canza gaba daya, gashi yana wani santsi da dandanon mara dadi. Dole ta dauke wannan miyar ta kawo musu mai da yaji suka ci abincin nan domin bata ma da wasu kayan miyan gashi abincin dare ne.
Haka suka kwana tana mamakin abinda ya bata mata miya, har gari ya waye bata gane ba don haka ta cigaba da harkokinta.
Ya zauna a dai-dai kafarta yace
‘Sannu maijego. Ya kike? Ya Baby? Babu dai wata matsala ko?’
Ta jijjiga kai
‘Ko daya babu.’
‘To ni zan wuce, Sadiku zai rufe muku kofa sai ya kawo miki mukullan.’
Ta dubi flask din da yake kan durowar gefen gado tana gyara zama tace
‘Bari na zuba maka shayi gashi yanzu na gama sha nima.’
Ya jijjiga kai
‘Ai yau bazan sha shayin nan ba don a koshe nake, ki ajiye flask dinki kiyi ta tsiyaya kina sha a hankali.’
Tayi ‘yar dariya
‘Kai haba, ai kuwa shayin irin wanda kake so ne.’
‘Ki daina tempting dina, yau a koshe nake kin san daga wajen liman nake a nan muka zauna aka bankare mana kaji da gurasa muka ci. Abincin daren ma da kyar zai sami shiga yau.’
Duk wayonta haka ta hakura ya fita ba tare da ya ko kalli flask din shayin nan ba, yayi mata sallama ya wuce wajen Aisha.
Yana fita ta fara nadama, ta san ba zai iya gane ta saka wani abu a shayin ba to amma me yasa ya ki sha? Gashi sai da ya bari ta barwa Aisha kwananta sannan ya wani ki shan shayin. Saida tayi kwalla saboda takaici; tayiwa kanta alkawarin zasu hadu gobe.
…………..
Da mukullinsa ya bude gidan kamar yanda ya saba ya shiga, tana falo tana karatun littafi da shayi kofi daya a gabanta tana sha. Bayan tayi masa sannu da zuwa sun gaisa ya dubeta yace
‘Ina abincinna yunwa fa nake ji.’
Ta kalleshi tana dariya
‘A’a, jegon har ya fara tabaka ne? Yau fa kwanan Mommy ne ko ka manta ne?’
‘Babu wani jego ai haka akeyi, tunda tana jego ai ke zaki karbi kwanan zuwa tayi arba’in don kema idan kika haihu haka zata yi. Don haka ki shirya ina nan har arba’in.’
Tayi dariya
‘Gaskiya dai ka koma, ni ban karbi wannan kwanan ba. Kawai saboda ta haihu sai kuma ka barsu ita kadai da Baby, ina laifi idan ka kwana a can din. Nifa idan na haihu babu wani arba’in duk da babu abinda za ayi amma ba zan yafe kwanan ba, ka kwana a nan din dai like just be there ba wai ka tafi ka barni da baby ba wai kai ka gama aikinka, tab!’
Kallonta yake da mamaki
‘To yanzu ya za kiyi dani.’
‘Abinci zan baka kaci ka koshi ka koma can in an kwana biyu ka dawo.’
Duk yanda ya so ya tsara Aisha ta karbi kwanan nan ki tayi, haka ta dafa masa taliya ya ci ya koshi ya sha shayi sannan tayi masa sallama ta rufe kofarta ya koma wajen Zahra.
…….
Ko da taji shigowarsa luf tayi kamar mai bacci domin tazata wani abun ya dawo dauka.
Sai da ya shiga dakinsa ya shirya sannan ya kirawota a waya domin da baiga Rahma ba yayi tunanin ko a dakinta zasu kwana. Ta zata ya riga ya fita don haka ta dauka tana mamaki.
‘Ina nan fa, a nan zan kwana.’
‘A’a, me ya faru kuma ka fasa?’
Yayi ‘yar dariya yace
‘Kanwar taki bata karbi kwanan ba.’
Nan yayi mata bayani kamar yanda Aishan tayi masa, suka ajiye waya tunda dama kiranta kawai yayi don ta san a gidan zai kwana.
Har bacci ya kwasheta tana tunanin wauta irin ta Aisha, ya za ayi abata miji kwana arba’in tace a barshi? Ko yanzu ma da akayi haka ta san idan dai Aishan ta haihu ko da tsiya-tsiya sai an bata kwana arba’in din nan tunda ita haka taga ana yi.
……….
Kwanansu daya da fitowa daga asibiti Aisha taje barka da kayan barkarta da ta tanada cikin leda; kayan baby ne masu kyau da tsada. Sai da ta tabbatar yana gidan ta shiga domin tuni ta sha jinin jikinta da matar nan.
Bayan la’asar ne suna zaune ita da shi a falonsa da Baby a hannunsa Rukayya ta shiga falon da sallama ta sanar da Mommy zuwan Anti Aishan. Har ta mike zata tashi ya cewa Rukayyan ta hawo da Antin nan mana. Kafin tace wani abu Rukayyan ta fice, bata dade ba suka dawo tana dauke da ledar yayinda Aisha take biye da ita.
Babu laifi suka gaisa da Zahran da yake a gabansa me, aka mika mata Baby ta dauka ta sa albarka. Suka dan taba hira gaba daya har Abban Sadik din, ta turawa Zahra ledar tace
‘Ga wannan babu yawa, Allah ya rayata ya kara lafiya.’
Tare suka amsa da Zahran da Abban Sadik.
Tayi musu sallama ta sauko ta koma gida, zuciyarta fari fes saboda yanda tayi barkarta a gabansa tunda ta san Zahran bata yi mata komai a gabansa.
……..
Saida aka kwana biyar sannan ya sanar da su sunan yarinya, ya saka mata Sumayya. Da kyar Aisha ta daure ta sanar da ‘yan uwanta sunan inda ta nemi Yaya Zuwaira da Yaya Zainab su zo amma kada su taho da yara don bata son fitna.
An ci burin wannan sunan kuma an shirya taro inda aka gayyato mutane da yawa, dangin Abban Sadik din ma haka suka zo da yawansu saboda Yaya Saratu aka bawa goronsu na gayyatar ta tabbatar ta hado kansu sannan suka taho.
Aisha ta riga ta tambaya ko akwai aikin da zata tayasu amma Zahra tace mata babu domin komai bayarwa za ayi a yiwo daga waje, don haka ranar sunan ba tayi shirin tafiya gidan da wuri ba. A tunaninta ma ‘yanuwan Abban zasuyi ta shigowa gidan nata amma har shadaya babu wanda ya shigo. Batayi mamaki ba domin dama ta san babu wanda yake kaunarta a danginsa, tun lokacin da suka je da Zahra gaba daya suka ki sakewa da ita. Duk da sun je ita da Abban sun bawa Hajiyan hakuri amma har kawo yanzu basu saki jiki da ita ba.
Sai wajen sha biyu saura sannan Zuwaira da Zainab suka iso, ba tare da bata lokaci ba suka shirya tare da Aishan suka wuce gidan sunan.
Tun daga bakin gate Rukayya ta hangosu, da gudu ta karasa ta kama hannun Aishan tana yi mata sannu da zuwa, ta gaida su Yaya Zuwaira sannan ta wuce gaba suka bita a baya.
Tun daga falon duk ‘yan uwan da Rukayya ta san basu taba haduwa da Aishan ba sai tace musu
‘Ga amaryar Abbanmu.’
Haka har suka wuce falon sama inda Mommy take, su Yaya Saratu ma duk suna wajen anata hira.
Suka karasa kusa da Mommy Aisha ta zauna kusa da ita su Yaya Zainab din ma suka zauna.
Gaisheta sukeyi suna mata barka amma da kyar take amsawa tana wani dauke kai.
Suka juya wajen Yaya Saratu wadda itama da kyar take amsa gaisuwar.
Yaya Murja ce kawai ta sauraresu da girmamawa, ragowar mutanen da suke wajen suka cigaba da hirarrakinsu babu wanda yake bi ta kansu. Don haka suma suka gyara zama suka fara kus-kus dinsu su kadai.
Basu dade da zama ba wata dattijuwar mata ta shigo, tun daga kafar bene take zabga kirari tana guda
‘Uwar gida Uwar Saddiku, kinyi taki kinyi ta raggo. Uwargidan Yusuf maki gani ido ya makance. Yanda duk kika dama haka za a sha Uwargida ta Uban Sadiku ko mahassada sun ki. Haihuwa kyautar Allah, ba rawar kai bace ba iyawa bace, ke Allah ya zaba uwar SADIKU matar Yusufa….’
Yaya Saratu ce ta fara mikewa ta lika mata naira dubu tana fadin
‘Kin min daidai, babu karya a cikin zancenki uwar Sadiki taci dubu sai ceto.’
Abun nata ya fara yawa kuma duk wanda ya san Aisha kishiyarta ce ya san da ita akeyi. Yaya Murja ce ta mike ta dauki kudi a jakarta ta ja matar sukayi kasa ta sallameta.
Bata dade da fita ba su Aisha suka mike Yaya Zuwaira ta karasa kusa da Zahra ta ajiye mata kudi naira dubu goma tace a siyawa Baby sabulu. Sukayi musu sallama suka fito.
A gidan Aishan suka karasa wuninsu suna jajanta mata zama da wannan matar don ko su kansu sun kula da yanda ita da ‘yan uwan Yusuf din basa ko kaunar Aisha.
Tun tuni Aisha ta san dangin Yusuf basa sonta amma sai yau ta kara tabbatarwa, don zata iya cewa a ‘yan uwansa matar Yaya Bello ce kawai ta saurareta sai kuma Innani wadda ita din ‘yar uwar Hajiya ce.
Haka aka gama taro aka watse, abincin sunan nan kuwa Aisha ko kalarsa bata gani ba domin lokacin da suka fito daga gidan ba a fara rabo ba kuma da aka fara babu wanda ma ya tuna da ita duk da an kaiwa makota abincin gida-gida.
…...
Wajen sati biyu da gama taron suna sai Yusra ta tsiri shiga gidan Aisha, haka kawai da rana ko da daddare musamman idan Abbansu yana gidan sai Yusra ta shigo. Wata rana ita kadai take shiga wata rana kuma ita da kannenta. Hatta Rukayya saida tayi mamaki saboda Yusra bata taba shiga gidanba amma sai gashi yanzu kusan duk ranar da Abbansu yake gidan sai ta shiga.
Amma da zarar Abban ya zauna an kawo abinci aka ce ta zo ta ci sai taki, tace ita ta koshi. Sai dai kawai su zauna a falo suna kallon TV.
Yau shinkafa da miya Aisha ta dafa ta hada salad ga kuma zobo. Tare suka zauna da Abban suka fara cin abincin, sai dai da kyar ta hadiye lomar farko saboda dandanon miyar bai yi ba. Ta ajiye cokalin tana jira taji mai zai ce.
Shi din ma da kyar ya hadiye wanda ya saka a bakinsa ya dubeta yace
‘Yau me ya sami miyar ne?’
Tace
‘Wallahi nima na ji, na zata ma bakina ne.’
Kamshin miyar ya canza gaba daya, gashi yana wani santsi da dandanon mara dadi. Dole ta dauke wannan miyar ta kawo musu mai da yaji suka ci abincin nan domin bata ma da wasu kayan miyan gashi abincin dare ne.
Haka suka kwana tana mamakin abinda ya bata mata miya, har gari ya waye bata gane ba don haka ta cigaba da harkokinta.